Showing 54001 words to 57000 words out of 168608 words
yake tsaye sanye da farar jallabiyya mai gajeren hannu ajikinsa gashi kan nan nashi sai sheki yake zubawa tamkar balarabe kallon second biyar mrym tayi masa tayi saurin d'auke kanta sakamakon mugun kallo da yake jifanta dashi .matsowa kusa da aunty shahida yayi sosai fuskarsa a hade babu alamun murmushi "babu abinda za'a ta iyayi wanda zai dakusa wannan soyayyar dake dawainiyya da zuciyata da gangar jikina Ina son princess so mai girma sannan gara ki fad'a mata babu iskanci da sakarci a gidana dan bazan dauka ba ."
Take kwakwaluwar mrym ya shiga ceculating abinda mgnrsa take nufi kenan akwai wacce yake so aka takura masa aurenta ?take jikinta ya kama kyarma ya ware hannuwansa duka cikin jin dadi "okay a she fa bata san da wannan zance ba fa ?"gsky ya kama ta san cewar akwai wata acikin zuciyar Adamcy Kuma ko ba dade ko bajima muddin na ganta zata kasance cikin rayuwata bukatata na ganta domin nafi bukatarta fiyye da komai ."
gbdy mrym dake zaune taji babu dadi acikin ranta "tabbas wannan shine dalilin dayasa bai maraba da aurenta wani bakinci ya ziyarci qirjinta ta mike tsam zuciyarta cunkushe ta nufi kofar fita tana fita aunty shahida ta soma magana cikin fushi "wai me yasa kake yin hk ne sam bai dace ba? "me Kuma nayi byn gskyr dake cikin Raina na fada gara tasani ? ''idan kana yiwa mrym hakan bazamu ji dadi ba , rainmu zai dinga baci fiye da bacin ran daka gani yanzu acikin kwayar idanuna ,dan bazamu yarda ka fifita wata banza can akanta ba banzar ma da ba gskiya bace .
"duk son da nake maka zan iya ajjiyeshi gefe na hukuntaka hukunci mai tsanani akan mryam ,kada ka sake makamancin wannan maganar a gabanta wannan ya zamo Karo na karshe ya jiyo sautin mahaifiyarsa wacce ta shigo byn fitar mrym nunfashi ya fesar yana cewa ''relax sweetheart insha Allahu an gama ya fice ya barsu "Allah ka shirya Adamcy na rasa meke damunsa " meke damunsa kuwa ban da iskanci aunty shahida ta katse hjy zulaiheart , nifa wani lokacin sai naji kmr Abar had'in nan kar yazo ya bata zumunci ."babu wani zumunci da zai bata wannan auren Allah ya rigada ya hadashi tunda gashi har ya amince ayi ,da yarda Allah rayuwar gaba zatai dadi "Allah yasa inji cewar aunty shahida.
Da fari baba qarami hjy zulaiheart taso ta kira ta sanarwa hukuncin data yanke kasancewar shi yana bangaren baya inda mallakinsa yake sai dai tayi tunanin ta fara sanarwa baba Babba kasancewarsa babba a tsakaninsu a yanzu saji daga bakinsa
tayi murmushin Jin dadi dan tasan baba qarami zai ji dadi sosai idan labarin auren adamcy dan kusan kullum sai yayi mata maganar ."
*****
a natse ta fara neman layin qanwarta hjy nuriyya wacce ta kasance abokiyar wasanta iyayensu uwa d'aya Uba d'aya Kuma akwai shakuwa sosai a tsakaninsu tana zaune a kasar london tun aurenta har zuwa wannan lokacin acan ta haifi yaranta duka iyakarta da naija ziyara ko wani sha'ani mai mahimmam. suka gaisa cike da farinciki Inda hjy zulaiheart take sanar mata batun hada Adamcy aure da maryam " Kai alhamdulillah masha Allah gsky abu yayi kyau sosai Allah ya sanya alkhairi ya nuna mana lokaci ,wannan karon zanyi k'okari na shigo kasar kafin lokacin domin ayi biki dani ".
Hjy zulaiheart tace "gsky kam anyi bukukuwa duk baki samu damar shigowa naija ba "haka ne kam amman inshallahu zan shigo wannan bikin nayi ne no any excuse ta k'arasa maganar tana murmushi suna cikin hirar hjy zulaiheart tace "nuriyya wai kuwa kina jin labarin bilkisu ?dip hjy nuriyya tai tmkr an d'auke wuta nepa tana jin wani irin daci acikin ranta sai data yi kusan minti biyar sannan tace "bana Jin labarinta Kuma bana son na ji labarin Inda take , kuma Ina son ku shareta ku cireta acikin zuciyarku har abada Kmr yadda mukayi yarinyar data nuna mana bamu Isa daita ba ,sannan bata sonmu ta zabi rayuwa ko babu mu me yasa zamu damu daita ?
"ni dai duk wanda zai nemata acikinku yaje amman ni nuriyya bana ciki kuma babu hannuna babu kafa ta ciki "naunayen ajiyar zuciya hjy zulaiheart ta sauke tana cewa " dan Allah nuriyya kiyi hakuri ko babu komai rayuwarta qaddara ce Allah ne ya d'aura mata wannan rayuwar babu yadda zata gujewa qaddararta ,wallahi duk sanda ta fado min sai na zubar da hawayen tausayinta , da nasan Inda zanganta wallahi zan nemota .
"Kune fa kuka damu daita ko nace ke dan duk cikinmu babu me zanceta wallahi sai ke ,bata ga wuya bane shiyasa bata dawo ba, wallahi nafi son rayuwa ta juya mata baya ta dawo tana kuka tana rokonmu kullum mummunar adduar da nake mata kenan sannan Ina adduar duk tsanani karta dawo mana da zuria Kmr yadda hhyrmu take addua ."
"wannan addua ta rashin haihuwa a tsakaninsu batayi ba ku daina mata mummunar addua gskiya "ai babu abinda ya kamaceta da wuce mummanar addua " yanzu dai kiyi hakuri muyita mata addua da fatan alkhairi a duk Inda take lokaci nata tafiya a lisafinsa shekaru ashirin kenan rabonmu daita , kiyi hakuri dan mu barwa Allah komai sannan muyi mata adduar Allah yasa ta waiwayo mu cikin koshin lafiya naunayen ajiyar zuciya hjy nuriyya tayi sannan tace "shikenan big sister ai abinda kikace shi zamuyi cike da qauna yar'uwarta hjy zulaiheart sukayi sallama da yaruwanta suna gama wayar uncle Umar ta kira ta sheida masa tana son ganinsa ."
Ranar asabar da misalin karfe hud'u na yammaci baba bAbba yazo bisa Kiran da hjy zulaiheart tayi masa , byn sun gaisa hjy zulaiheart ta karanto masa hukumcinta akan ATA cike da farinciki uncle Umar yace "masha Allah wannan hukuncin yayi Kuma mun gamsu dari bisa dari dan burin mu bai wuce muga adam ya ajiye iyali ba ,bugu da Qari zaa sake karfafa zumunci a tsakanin inshallahu zan sheidawa sauran yan'uwana sai mu saka ranar da zamu ga alhj saidu dan zamu so a daura auren nan kusa". "wannan maganar tayi Kuma naji dadinta sosai dan haka a fara sheidawa baba qarami dan nasan murnarsa sai tafi ta kowa domin duk yafi mu d'auki son ganin Adamcy yayi aure ta k'arasa maganar tana murmushin jin dadi "ai kuwa daga nan ma bangarensa zan shiga na fara sheida masa Allah ya sanya alkhairi ya nuna mana lokaci "Ameen ya Allah,Allah kadai yasan murnar da zaiyi idan yaji ya sha lemu da kayan snaks din da'aka jera masa suka zarce da tautaunawa kafin daga bisani sukayi sallama ."
Baba qarami na zaune akan kujera me zaman mutun uku sai ga baba Babba wanda ya kasance yaya garesa Kuma Kani ga mahaifin ATA yana ganinsa ya saki fuska tare da farincikin ganinsa ya d'an mike tsaye cike da girmamawa ya bashi hannu suka gaisa sannan ya nuna masa mazauni atare suka zauna "sannu da zuwa yaya ! "ya gida da iyalin fatan suna lfy?"alhamdulillah kowa Lafiya yake ya naka iyalin ?"Suna lfy ya bashi amsa yana murmshi ya mike ya dauko masa abun sha "bazan sha komai ba daga bangaren hjy zulaiheart nake na sha " .
suka yi shiru na second biyu sannan baba babba ya fara magana a tsanake " kamar yadda na fad'a mk daga bangaren hjy zulaiheart nake tayi decide ta had'a Adam aure da diyar kaninta abdulrauf " what ?"when ?ya fada a matukar rude yana Jin wani irin abu ya caki kahon zuciyarsa , yayi saurin runtse idanuwanshi "zulaiheart na bukatar wannan labarin ya zamo Kaine ka fara jinsa bisa kokarinka na son ganin adam ya ajiye iyali dan haka nan da sati me zuwa zamu gana da yayan mahaifin yarinya alhj saidu ."
shiru baba qarami yayi har sanda yayansa ya dasa aya ya mike tsaye"to ni zan wuce duk abinda ake ciki zan kiraka a waya a fusace baba qarami ya mike Shima yana cewa "yaya wannan wace irin maganar banza ce kazo min dashi sannan kana k'okarin sa kai ka wuce ka barni ? yayi mgnr a fusace yana sa hannu ya daki center table din dake tsakiyar falonsa wanda ke d'auki da ruwan lemu kala dabam dabam ,nan take wasu glas cup suka tarwatse yana huci yake kallonsu "yanzu ni dana cin burin ya zabi daya daga cikin ya'yana ya aura shine dan munafurci zata hadashi da diyar kaninta saboda son Kai irin nata ?
"ya'yana yafi dacewa Adam ya aura ba wannan yarinyar ba ya sake dukan table wanda hakan yasa gbdy ahlin da ke numfashi a part din suka bayyana" burina bai wuce ya'yana ko jikokina su had'a iri da dashi ba yayi mgnr yana kallon cikin kwayar Idanu dan uwansa ."me yasa zaka fadi haka idris? "eh na fad'a yayi mgnr yana cakunar wuyan dan'uwansa da iyakacin karfinsa yana maxurai abinda bai taba faruwa ba a tsakankanisu ,hindatu wacce suke kira da hindu ta samu guri ta zauna tana kallonsu zuciyarta na rawa dan ta dade a tafkin qaunar ATA mahaifinta ne ya hana a fito da soyayyar a cewarsa yana jiran lokaci yau ga lokaci ya zo masu a wani iri .
sauran kuwa hankalinsu ne yayi kololuwar tashi ganin yadda mahaifinsu ke rike da wuyan dan'uwansa uwa d'aya Uba d'aya .Wallahi yaya Kai kare ne da bai san ciwon kanshi ba ! "shin ya'yana basu dace dashi bane ka bani answer ?uncle Umar yayi shiru kawai yana kallon hannun uncle idris dake rike da wuyansa batare daya ce uffan ba.
"me yasa kazo min da wannan banzar labarin mara dadin ji ?ya k'arasa maganar yana sakar masa wuya yana dubansa yana huci "saboda mu bamu Isa ta hada jini damu ba shiyasa ta za'ba masa acikin dangi ta ?"to me zai faru idan na hana auren ?"zan hana wannan auren ta karfin tsiya yayi mgnr yana d'aga hannunsa sama sannan ya dungule ya naushi bangon falon sai da gurin ya tsage ya tsaya yana huci da kallon wani bangare ."
Baba babba ya tsaya abayansa hankalinsa a matukar tashe " maganarka gaskiya yayanmu suka fi dacewa da aurensa sai dai kayi hakuri dan'uwana bana tunanin da wata manufa zulaiheart ta had'a wannan auren ,idan baka manta ba shekara nawa ana fama da yaron nan akan ya fitar da mata yayi aure bana tunanin zata ki had'a zuria da daya daga cikinmu sannan da kasan kana da wannan burin me yasa baka fito dashi ba ?
Baba qarami bai ce uffan ba illa numfashi da yake sauke da sauri sauri gumi na karyo masa "dan haka kayi hakuri karka bari wannan matsalar ta zamo Silar da za'a samu matsala ka bar wannan burin bayan anyi wannan auren sai ayi maganar a had'ashi da daya daga cikin yaran".
"Kai kare idan ka sake yin min wannan maganar banzar sai na datseka gbdy Komai naka banga ta yadda nawa burin zai zama daga baya ba muddin d'aya daga cikin yarana basu yi nasarar shiga sawun farko ba babu wacce ta Isa ...."
"kayi hakuri ka yafe min ban fad'i haka dan quntata maka ba ya fadi hk kasancewarsa me saukin Kai sannan marason tashin hankali yafi son yayi rayuwarsa cikin salama duk maganar da baba babba yake sam baba qarami bai juyo ba ",shi wannan Karen zai wuce sai kaji daga garesa sai dai ya kamata ka sakin ranka dan wata rana ....saurin d'aga masa hannu baba qarami yayi still bai juyo ba sai dai qirjinsa sai faman bugawa yake Uncle Umar ya juya cike da matsanacin firgici da yanayin dan'uwan nasa ."
sai lokacin baba qarami ya juyo yabi bayansa da wani irin mugun Kallo Idanunsa a waje har sanda takunsa ya kai uku bai juyo ba haka shima baba qarami bai daina kallonsa ba .a sanyaye fahad dansa yabi bayan baba babba zuciyarsa na rawa dan shi kansa ya koka da abinda mahaifinsa yayi ya raka uncle Umar sai dai bai Kai shi har bakin get ba a tsakiyar hanya ya barshi yana bashi hakuri "karka damu fahad na gode allah yayi maku albarka ya amsa da Ameen ya dawo part dinsu da sauri .
falon ya d'auki shiru na tsawon lokaci yana tsaye yana tunanin bayanin daya samu daga bakin dan'uwansa a yanzu wanda yake jinsa tamkar dalma acikin zuciyarsa , "uhmmmm yanzu dai ta nuna mana cewa itace uwar Adam Kuma ita kadai ke da iko akan shi ?sai mugani idan shi din d'an mace ne Baba qarami yay maganar yana jan tsaki a fili tare da watsa katuwar harara da mugun kallo kamar tana gabansa fahad ya d'auki farin glass cup ya tsiyaya masa tattacen ruwan inibi ya mika masa "kasha baba kaji sanyi a ranka yasa hannu ya Kar'ba ya rike shi gam a hannunsa sai dai bai sha ba haka zalika bai ajiye ba."
"zan iya kasheki akan wannan haukan da kika yi zulaiheart domin Ina da tanadi da buri akan adam ya karasa maganar yana filinging da cup din hannunsa a fusace Wanda yasa take yaransa maza da mata tare da matarsa suka sake shiga rud'ani cike da matsanacin firgici suna kallonsa gabansu na faduwa ban da Hindu data samu guri ta kame akan kujerar da mahaifinta ya tashi zuciyarta tafi ta kowa zafi da tuttukin bakinciki tare da shiga tashin hankali" Fahad ...." !
ya kira sunan dansa Wanda aka kira da hkn ya d'ago ya kallesa a matukar tsorace batare da yace komai ba "abinda na fada Ina nufi har cikin zuciyata gara ta bar duniya ko ita yarinyar ta bar duniya akan rasa burina yayi maganar yana nuna sa da d'an yatsansa "wannan shine Karo na sau babu adadi da take kawo mana tashin hankali tun dan'uwanmu na raye dan haka Ina son kasheta na huta da ganinta a doron duniya muddin ba daya daga cikin ya'yana adam zai aura ba ."
daya bayan daya suka shiga kallon junansu cike da mamakin jin furunci mahaifinsu hatta hindu wannan karon atsorace take kallon mahaifinta ta gigita kwarai da gaske "a kullum kokarina naga na kawar daita a duniya darajan halakar da nake son qullawa adam yasa na barta ya karasa maganar a kausashe .yayi taku daya biyu ya tsaya gaban hindu yana kallonta "kece ya kamata ace kin auri adam ba wannan yarinyar ba kije kiyi rayuwa tamkar sauraniya a gidansa ki taka kowa yadda kike so sannan ki juya duk Wanda kika ga dama wannan hannun nawa babu abinda yasani a halin yanzu kamar ya wahalar da zulaiheart ya gigita ta hanyar azabtuwa mai muni ,ya matso kusa da hindu Sosai suna fuskantar juna "wannan karon fuskarsa da murmushin mugunta akanta "ke hindu ko zakiyi iya karfin halin kashe min zulaiheart?
Wani sanyayyayen murmushi ne ya bayyana akan fuskarta wanda mahaifinta ne kawai ya fahimci manufarsa ganin yadda ahlinta suke kallonta a tsorace yasa tayi saurin waskewa tace "baba me yasa kake mgn fiyye da kaida ?gsky sam sam hakan bai dace ba tayi maganar tana kawar da idanunta gefe al'amun bata ji dadi ba gumin da ya tsatsafowa sauran yanuwanta suka shiga gogewa suna sauke numfashi da ajiyar zuciya atare Jin abinda tace daman km ita kad'ai ke iya fadawa mahaifisu mgn kai tsaye batare da shayi komai ba , a hankali ya juya yana taku cikin tsananin damuwa da tashin hankali suka juya gbdy suna kallon bayansa har ya shige bedroom dinsa yana shirya yadda zai kawar da hjy zulaiheart ko mrym daga doron duniya .."
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a tura 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 13
"Baba qarami na kwance har kusan tsakiyar dare ya kasa runtsawa dan sam bacci yaki zuwan masa sai faman juyi yake akan makeken katifarsa ,yayinda matarsa hjy aljannatu ke d'akinta kwance tana sharar bacci amman shi kuwa baba qarami sai tufka yake yana warwara ya d'an zabura ya mike zaune daga kwanciyar da yay, ya had'e hannunwansa duka waje d'aya "babu tantama hjy zulai tana da manufar had'a wannan auren yasan tayi haka ne dan kar wani acikinsu yaci arzikin d'anta , kunga idan ta had'asu aure da diyar d'anuwanta dole dai arzikinsa yana tare daita , dan da zarar mrym ta haihu dashi komai na adam zai dawo nata gbdy zuwa yanzu dai bai san abinda ya kamata yayi ba ko hanyar da zai bullo masu a maida auren Kan diyarsa ."
Sosai kwakwaluwarsa tayi zurfi cikin tunani neman mafuta har bai san sanda hindu ta shigo d'akin ba , ta matso kusa dashi ta tsaya tana jijjiga baba qarami wanda yayi nisa cikin duniyar tunani "baba baba !! " ta kira sunansa har sau biyu ajere sannan yayi firgigib ya dawo haiyacinsa " wai meye haka baba?" me yasa zaka damu kanka akan wannan 'yar qanqanuwar matsalar ?" baba qarami bai iya amsa wa ba sai zuba mata rinannun idanunshi da yayi yana dubanta har lokacin yana maimaita abinda ta fad'a " ai a wajensa wannan ya wuce gagarumin matsala ba qanqanuwa ba ko ita kanta tasan da zaman haka ta dai fad'a ne dan kwantar masa da hankali shi kuwa hankalinsa bazai ta'ba kwanciya ba matukar ba ganinta yayi a matsayin matar adamu ba ."
"Dan girman Allah baba ka kwantar da hankalinka mubi komai a hankali idan muka bari suka fahimci wani abu attare damu bazamu iya nasara akansu ba " cikin wani irin murya mai gyaraye da tashin hankali had'e da rud'ani yake furta "bazan iya ba hindatu , bazan iya kwantar da hankalina ba muddin ba ganinki a gidan adamu nayi a matsayin matarsa ba ,maganar aurensa da mrym ta dokeni fiyye da tunaninki ,Allah Allah nake gari ya waye naje ga zulai ayita ta