Showing 57001 words to 60000 words out of 168608 words

Chapter 20 - Mar'adam's Book 1 Hausa Novel Complete

qare  domin   kece kika fi dacewa da  Adam  ba wannan yarinyar ba dan  wannan  tsantsar muguta ne  kawai  take  son  nunawa"kai dai  baba ka  dan  boye damuwarka baba" .


    D'akin  ya  d'auki  shiru  tamkar  babu  wasu halitta  acikinsa   sai  na  qara  ac  dake  aiki  da kuma saukar  numfashinsu  haka  zalika baka  jin  motsin  komai  daga  sai  na  tsuntsaye   dake  shawagi  kasancewar  a  gra suke  hindu ta sauke numfashi tana mai kamo  hannunta  mahaifinta  cikin  nata "idan  kaje  me  zaka  cewa  mami  akaina ? " zan so nasan   abinda  zakace  baba  idan  ma  hali  kaje tare dani  ayi  komai  akan  idanuna  shekaru  sha biyar kenan ,  tun   inada  shekaru  sha  shida  nake  dakon soyayyarsa  bazan  iya  jurar  rasashi  ba, bazan zuba idanu  wata ta mallakesa ba "zan fad'a mata komai akan  soyayyarki  ni   ko  ta  biyu ce kizo  bazan damu   ba  burina  ki  kasance matsayin   mata  acikin  gidansa , ki zama tmkr sauraniya, ki yi yadda kike so  nima  nayi  yadda  nake só da  kamfanunuwansa  ."" nan  take ta  had'e  fuska  tamkar  dariya ba  muryarta  a  kausashe  ta  cigaba da mgn "muddin  a ta  biyu  zanzo  nasan   bazai ta'ba aurena ba , ya  adam  fa yana da tsari  acikin  rayuwarsa  shi  din ba mutun bane  kamar sauran mutane bashi da raayin tara mata "wa yace  miki  bashi  da  raayin haka ? zai yi raayi   dan uwarsa  Allah dai ya kai mu gobe tare zamu wajen  uwarsa  kafata  kafarki ."

Baba  qarami ya   mike  tsaye ya goya  hannunwansa abaya  yana  girgiza  kai yana duban hindu kafin daga  bisani  ya matso kusa daita sosai  ya  soma mgn   can  kasa kasa  kusan mintuna goma yana mata  mgn murmushin  jin dadi  né ya  bayyana akan fuskarta " idan bata  yarda ni na zama  matarsa  ba  I will  killed mrym  idan ni ban samesa  ba  to babu wacce  zata mallakesa anan  gidan  duniya yadda take  mgnr zaka fahimci da gaske  take  kuma  har cikin ranta abinda  take nufi  kenan ganin byn maryam ."

Washegari  da   misalin  karfe  goma na   safiya  a kofar  shiga  bangaren  hjy  zulaiheart  tayi masu  kai tsaye a babban  falon  gidan suka  iske  mami zaune  yayinda  d'aya  daga  cikin  masu aikinta ke zaune   tana  mammatsa  mata  yatsun  kafafunta sallamarsu baba  qarami tasa mami  dauke idanunta  daga  Kan tv ta maida kansu  tana  sakin fuska  sai  dai kallo d'aya tayi  masa  ta  fahimci  akwai damuwa  atattare  dashi  ,aranta tayi addua  allah yasa ba wata matsalar  bace  ta taso , ta amsa sallamarsu  tana cewa "sannuku  da zuwa !" baba  qarami  ya samu waje ya  zauna akan kujerar  dake  fuskantarta yayinda  hindatu  ta zauna a kasa kan kafet  a gaban mami ta  sunkuyar da kanta  kasa  tmkr mai neman  gafara  tare da gaishe da mami cike da ladabi  ta amsa  tana  mami  ta maida hankalinta ga baba qarami   tana   nazarin fuskarsa sannan ta kalli yarinyar  dake zaune a gabanta tace "salaha tashi kije   Ki  bamu  guri  cikin  sauri  yarinyar  ta mike tare da fadin  "tô !"

       Mami  ta sake maida hankalinta sosai  garesu sannan ta fara magana a natse "baba qarami fatan dai lafiya  dan naga yanayinka  ba kamar yadda na saba ganinka ba  yace "lafiyar dai da sauki "ta gyara zamanta cikin tsananin damuwa "daman dai na lura da hakan dan ba haka yanayinka yake ba kai din mutun ne mai faram faram duk sanda za'a ga fuskarka cikin murmushi take tô ina jinka fad'a abinda ke  tafe da kai ."

Naunayen ajiyar  zuciya ya sauke yana sake gyara zama  yace "zulai  jiya baba babba yazo min da wata magana akan hukuncinki akan Adam"  ta gyada kai tana  sauke  numfashi "haka ne nasan zaka fi kowa jin dadi "tabbas  naji  dadi  sai  dai   wani  hanzari ba gudu  ba nima na dade ina son had'asu  aure da hindatu   "mami tayi shiru tana dubansa da hindu dake   zaune  tana  nazarinta tana son gano wani abu atattare  da hindu domin dai ita din macece mai tsananin  baseera tare da saurin karantar mutun sai data  numfasa sannan tace "ita hindatu tana son shi ne ?

"tabbas  tana tsananin sonshi na tsawon shekaru tunda tashi da soyayyarsa ta tashi ni ne mutun na farko data fara sheidawa da fari na nuna mata illar rayuwar data jefa kanta na afkawa soyayya da qarancin shekarunta  alokacin na tmbyeta meye dalilinta  na son shi  ? me  ya  dauki hankalinta akanshi  ? tace ba dan yana dukiya  da kyau ba ,yau da  zai  wayi  gari  bashi da  komai  bashi da hannu bashi da kafa  koda akan titi zasu rayu zatai  rayuwa dashi kawai son shi ta keyi dan  Allah alokacin shekarunta shashida né  kawai  wanda ni nake ganin bata san  ma me take ba bama tasan meye soyayyar ba yasa take fadin haka ahankali baba qarami ya fayyacewa  mami komai akan soyayyar da hindu ke ma ATA  babu abinda ya rage numfashi mami tayi ta saukewa tana girgiza kai cikin tausayawa tana kallon hindu data sake dukar da kanta kasa sosai ."


"Masha allah naji dadin wannan abu sosai soyayya mai hade da zumunci allah ya bamu ikon sada zumunci dan allah ba dan kwadayin ko neman wata biyan bukata ba ". ta sake numfasawa ta cigaba da magana  "nima daman tun farko burina kenan adamcy  yayi aure biyu"  ahankali baba qarami ya kalli inda hindu take wacce mgnr mami yasa ta dan dago kanta mami ta cigaba da magana "zan yi iya  kokarina hindu na kawo karshen damuwarki duk da adamcy baya da raayin ajiye mata biyu amman zanyi convincing   dinsa  domin  kawo farinciki arayuwarki da  yarda  allah ."

    da  sauri  hindu ta kalli mahaifinta shima din ita yake  kallo domin dai yasan diyarsa da tsananin kishi zata fi bukatar ganin ita kadai ta mallakesa Kmr yadda ta sheida masa kallon da takewa mahaifinta só take yace a fasa auren da mrym gbdy ya aureta  shi kuwa baba qarami a hakan ma maganar tayi  masa dadi "fatana  mu hadu muyi addua akan lamari sannan mu nemi zabin allah allah kuma yasa  gogan naka ya yarda ya amince ya  hadasu su biyu din , ku bani lokaci kadan zan yi magana dashi duk abinda mukayi dashi zan nemeka da  wannan maganar suka kawo karshen zance sukayi  mata sallama ."

   Suna shiga  dakin baba qarami   hindu ta fara zubar da hawaye acikin slow voice tace " baba ina ji ajikina ya adam bazai aureni ba dan dai idan amincewarsa zaa tsaya nema wallahi bazai ta'ba amincewa ba bugu da qari ni banason sharing dinsa da kowa nafi son ni kadai dan sam ban dace da zama da  wata aba kishiya ba zan só mu rayu dagani sai shi  ta karashe mgnr tana shesheka murmushi baba qarami yayi tare da fadin "hindu kalleni nan " ta tsura masa  idanunta Kmr yadda ya bukata "ki kwantar da hankali babu wani abu acikin ya haduku biyu din amincewarsa shine abinda muka fi bukata a yanzu dan zaki iya kawar daita byn auren ki zauna ke kadai keda kike da baiwa iri iri nasan zaki bawa babanki mamaki haka dai baba qarami ya tasa hindu a gaba yana kwantar mata da hankali babu laifi hindu ta saki jikinta  tare da  karfafa zuciyarta sai dai ta rantse muddin bata samesa babu wata mace da zata mallakesa tana raye ."


****
Sanye  ATA  yake  cikin  farin yadin vol  mai shegen haske da tsada  a hankali yake  taku yana gyara  zaman  hullarsa  baki  haka zali takalmin dake sanye da kafafunsa black cover shoes ne tsintsiyar hannunsa daure  da  agogon rolex   yana dumfaro falon kamshi turarensa ya mamaye koina Kmr  shagon turare yana gama qarasowa yace wa hisham "muje ko ".kai me yasa bakasan ka bawa mutun rai ka bashi hakuri ba duk lokacin dana bata ina zaman jiranka da muje ko  zai qare  " ina laifin kace hisham Afuwa kayi hakuri muje abokina km danuwana."
Dogon tsaki yaja kawai batare dayace uffan ba .

"matsalata da kai kenan ka gama bata lokaci amman zaka wani jawa mutane tsaki still bai ce komai ba 
ya nufi hanyar dakin mami tana zaune ya shigo ta  dago a natse tana duban kofar ganin shine cikin shigar da tafi qauna ta saki fuska cikin tsananin farinciki  tace "Masha allah adamcy nah kayi kyau sosai allah yayi maka albarka  ,sai dai wannan uban wanka  da kashi haka kmr yau  daurin aurenka,  ai ko yau né daurin aurenka sai  iyakarka hk kai  ni kamar ma har da hoda ka shafa ko? Tsuke bakinsa yayi  dan tsokanar sweetheart dinsa na yau yazo da wani salo ana zaman lfy me zai yi da wani hoda shi ba mace ba  ."

"sweetheart ni zan fita amman zan dan jima ban dawo ba dan yau zaa bude kamfanin tace mai petir da sinadarin gas "Alhamdulillah masha ,allah allah yasa albarka  arayuwarka data kasuwancinka allah ya  tsare  min  kai  ,yadda zaka fita lafiya allah ya dawo da kai lafiya  sharrin mutun da aljani Allah rabaka  dashi  yace "Ameen !atakaice  ya juya a natse yana taku  tmkr wani jinin saurata "sai na dawo sweetheart  ." a dawo lafiya adamcy nah ta fad'a tana cigaba da kallon bayansa "yau  tsawon  kwana uku kenan tana   son sheida masa bukatar baba qarami amman ta kasa, ita  kanta tana jin tsoron tunkararsa , tayi  dukkanin tunaninta ta rasa ta ina zata fara  shigo  masa da maganar , auren mrym ma  da yaya ya amince yanzu  kuma ta sake kawo masa mgnr wata tasan tattara wa  kawai zai yi ya gudu ya barta dasu  ."

har ya kai bakin kofa yana shirin d'aura hannunsa akan handling din kofar ya  tsaya cak  ya waigo
bayansa adaidai lokacin  da mami ta sauke numfashi  da  girasa ya tambayeta  ,ta girgiza masa kai kawai tamkr   wata   marainiya "ko akwai damuwa ne ?ta sake numfasa wa kana tace " babu  komai  adamcy nah  ina dai kallonka ne kayi min kyau sosai shigar ta amshi jikinka "me  yasa  bazanyi amfani da wannan damar  na fad'a masa  bukatar kanin mahaifinsa ba ? tayi mgnr acikin ranta  da sauri zuciyarta ta gargadeta "karki soma yace ya fasa auren  gbdy gashi goben  nan zaa je neman masa auren mrym  numfashi ya fesar "saboda Ke nayi shigar dan nasan zaki ji dadi gaahi yau  juma'at  "ai kuwa naji dadi kwarai da gaske na kuma  gode sosai allah ya baka zuria masu  albarka yadda kake ji dani kake min biyayya Allah baka masu yi maka bai amsa ba ya sa kai ya fice daga dakin  zama ta cigaba da yi tana tunanin  mafuta zata jajurce da tsayuwar dare domin neman zabin allah  dan shine kawai mafuta agareta."


Aunty  abinda  na gama  jin bayanin  ibrahim  taji kafafunta suna  barazanar kasa daukarta lokaci  daya  zuciyarta na barazanar  tarwatsewa Ibraheem ya matso yana girgiza Aunty abinda wacce ta dawo tmkr mutun mutumi "abida abida!! lafiyarki what's wrong abida?abida tayi shiru kawai tana sauke numfashi batare data amsa ba " baba babba zasuje nemawa ATA auren maryam  gobe goben nan idan dai ba karya kunnuwanta suka jiye  mata ba haka taji ya fito daga bakinsa  " ibrahim me naji kace ? tana bukatar ya sake maimaitawa babu bata lokaci ya sake maimaita mata " wai tukunna wace maryam zai aura ?"maryam dai wacce Ke zaune a gidan mami diyar  kaninta  ita zai aura  "da gaske ka tabbatar mrym zai aura ? ya gyda mata kai kawai  yana maida hankalin Kan wayarsa dake qara "

"ina sam sam wannan aure bazai taba yuwa ba ta runtse idanunta da karfi  ATA jarumin nmj né uwa uba kyau da natsuwa da Kamala ga tarin dukiya dasanin yakamata ai babu macen data dace dashi sai sultana gani yana mata wani irin kallo tayi saurin dawowa haiyacinta  sunanta ya sake kira tare da jawo hannunta ya zaunar daita akan kujerar daya tashi cike da rauni tare da yin kasa da murya yace "abida meke damunki ?babu abinda ke damuna nidai dan Allah kar aje neman auren nan wai ma waye ya hada wannan auren ?shi ATA din da kasan  ne ya zabi auren mrym din ?"ta karasa maganar cikin tsananin tashin hankali da bacin rai akan fuskarta ."

    "me yasa ?saboda me kar aje neman auren  ?"
Meye  damuwarki da aurensu ? kanta ta rike da duka hannuwanta ta fuskancesa cikin sanyin murya tace "sbd sultana né bazan só ATA ya auri wata ya bar sultana ba "ita sultana tana son shi ne ?eh ammm daman umma ce ke ...."sai km tayi shiru ta kasa qarasa mgnr. "auren nan fa kamar anyi shi an gama domin babu wani abu ko mahalukin daya isa ya hana wannan auren mami da kanta ta hadata wannan auren ,ATA nason yarinyar ko baya sonta wannan shine bansani ba amman zuwa neman aure wannan dole ne gara ma ki binne duk abinda ke ranki karki shigo da wata magana da zata janyo matsala cikin jin haushi tace "idan kuma rabon sultana né fa ?har ya bude baki zai bata amsar tmbyrta  wayarsa ta sake daukar  qara ya dauka yana duba screen din wayar sunan ATA yaga yana yawo cikin sauri ya mike ya dauka ya soma mgn yana juyawa zuwa kofar fita tana ganin fitarsa ta  mike tsaye ta soma zagaye falon tana maimaita abinda  ya  fada mata ashe kuwa zaayi wulakanci acikin gidan nan ko ta wani hali koda tsiya koda tsiya tsiya sai tayi duk abinda zatayi sultana ta shiga gidansa koda ata biyu ce ."

*****
  "Maryama kyakkyawar budurwa ce mai   kyan  gaske  doguwa ce sambal dan tsawonta bai sa  ta  rankwafa ba sai dai ita din ba fara  bace haka zalika baza'a  kirata  da baka kirin ba  chocolate colour ce  tsayinta ya fito  sosai  domin irin matan nan ne masu  shape din cocakola  tana da siririn  hanci  da manya  idanuwa masu  matukar d'aukar hankali  dan duk wanda tsautsayi yasa ya kalli  cikin kwayar idanunta sai ya kusan  suma saboda wasu sirrika da Allah ya hallita acikinsu masu kallon cikinsu  ne kawai zasu iya karar da yanayin da suke tsintar kansu ."

idan tayi murmushi kuwa zaka ga siraran wushiriyarta sama da kasa sun bayyana wanda  sune suke  qara  haskaka  kyawunta  ,ga gaban  goshinta kwance suke  da suma  luf luf !! duk  da kanta a daure  yake a koda yaushe da d'ankwali  amman kallo  daya  zaka  mata  ka  gano irin matan  nan  ne  masu  yalwan  gashi  sannan tana  da  kafa  mai kyau haka ma   yatsun  kafafunta zara zara ne  lullube  da farata masu matukar haske haka zalika muryarta idan tana  magana dan dole ka tsaya ka saurareta  kuma dole ka kalleta ."

Maryama ta  samu tarbiya mai kyau  daga  gurin  mahaifiyarta tayi  karatunta na   primary  har zuwa  matakin  jami'an  acikin jahar lagos  kuma   duk  akarkashin kulawar  gwanaty  , haka bangaren karatun  alqurni  baa  barta abaya ba  domin tun tana primary ta sauke alqurni  km hakan bai sa ta daina zuwa islamiyya ba idan kaga bataje ba sai dai wani aiki ne ya sha kanta ."

    kyawun maryama mai  tsayawa ne arai sai dai duk da wannan kyawu  nata bata da wani  tsayayyen saurayi  duk wanda yazo  neman aurenta dayazo sau d'aya zuwa sau biyu zai daina zuwa  batare da wani dalili ba  koma  karshe  taga  ya koma gurin kaulat diyar  kanwar   babanta  Aunty  hassana  gata   da kyau sosai na bugawa a jarida amman  mutane  na  mata  kallon  mai bakin  jini  abun yana d'an  damunta  sai dai bata nunawa dan ba samari bane a gabanta karatunta  ya fiyye mata  komai mahimanci  koda yaushe ka kalli fuskar maryama  zaka ganta a daure sakamakon rashin farinciki shiyasa  mutane  suke mata kallon mai  tsananin girman  kai   ."

Sannu  ahankali  maryama take tafiya tamkar tana  jin tausayin qasa  ko  macijiya dan babu wani karfi  a tattare daita cikin shiga ta Kamala  riga da sket dinki zamani da  kuma  dogon  hijab  mai  hannu  har  qasa  fuskarta  manne yake da bakin  nikaf  kalar hijab din jikinta wanda ya zame mata jiki a duk sanda zaka ganta a waje ko a makaranta   da wannan nikaf din zaka  ganta  sam bata yarda ta fita koina   batare dashi  ba  a cikin gidansu ne kawai zaka iya ganinta sadaka  yayinda  kafad'arta Ke makale da  jaka baka mai dogon igiya ,a zahiri kana kallonta kasan a matukar gajiye take dan yanayin tafiyarta ma ya qara yin slow sa'banin na sauran lokuta  sakamakon ranar data kwaso  gefe da gefenta  qawayenta ne  subai'a  da sumaiya ne suka sakata a tsakiyarsu ."

   Tafiya  suke  a natse  suna hirar  yadda  jarabawar su ta qarshe  ta kasance adaidai jeaction din ummahani street   suka rabu da kawarta  sumaiya tayi hanyar hagu da zai kaita unguwar daji suka cigaba da takawa da subai'a itama dai tafiya kadan sukai tayi dama wato markaz ya saura ita kadai ta cigaba takawa zuwa  unguwarsu market street batayi  wani  doguwar tafiya ba ta  qaraso  unguwarsu bata tsaya akoina ba sai   kofar  qaramin  get din gidansu  wanda  kallo daya zaka masa  kasan na masu rufin asiri  ne  dan bazaa kira gidan da gidan mai kudi ba haka zalika bazaa kiran gidan  da gidan  talaka fútik ba daidai misali  gidansu   ginin  da ne kuma ginin kasa ne  filasta  ne ya rufawa ginin gidansu asiri da kuma jamar dake rayuwa  acikin  gidan ."

a natse ta  shigo  haraban gidan nasu idanunta ya sauka akan kaulat  wacce  ta sha kwaliya cikin atamfar  chiganvy gold black touch of milk  ,kallo daya tayi masu  ita da wanda ta gani tsaye ta dauke   idanuwanta  zuwa wani bangaren  tana cigaba da tafiya dan wanda suke tsaye  da kaulat din ba bako  bane a wajenta tasha ganinsu tare  ."duk da   bilal  baya ganin faukarta amman  duk  sanda ya ganta yana rasa natsuwarsa a kullum burinsa yaga fuskarta yaga yaya take ,kasa cigaba da motsi yayi  daga inda yake tsaye  yabi tafiyar maryama da wani irin  kallo  komai nata a natse  most especially tafiyarta abun burgewa shi kam ina ma zata yarda ko sau d'aya ta bude nikaf din  yaga fuskarta yasan zatai kyau duk da  bai  ta'ba ganin  fuskarta ba."

Kaulat  na ganin irin kallon da yake mata  taja  dogon  tsaki yayinda maryama bata sake  duban inda suke tsaye ba ta cigaba da tafiya zuciyarta na matukar jin tausayi kaulat dan babu abinda tasa gaba sai  aikin tara masu samari  marasa inganci  a gida 

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login