Showing 57001 words to 60000 words out of 168608 words
qare domin kece kika fi dacewa da Adam ba wannan yarinyar ba dan wannan tsantsar muguta ne kawai take son nunawa"kai dai baba ka dan boye damuwarka baba" .
D'akin ya d'auki shiru tamkar babu wasu halitta acikinsa sai na qara ac dake aiki da kuma saukar numfashinsu haka zalika baka jin motsin komai daga sai na tsuntsaye dake shawagi kasancewar a gra suke hindu ta sauke numfashi tana mai kamo hannunta mahaifinta cikin nata "idan kaje me zaka cewa mami akaina ? " zan so nasan abinda zakace baba idan ma hali kaje tare dani ayi komai akan idanuna shekaru sha biyar kenan , tun inada shekaru sha shida nake dakon soyayyarsa bazan iya jurar rasashi ba, bazan zuba idanu wata ta mallakesa ba "zan fad'a mata komai akan soyayyarki ni ko ta biyu ce kizo bazan damu ba burina ki kasance matsayin mata acikin gidansa , ki zama tmkr sauraniya, ki yi yadda kike so nima nayi yadda nake só da kamfanunuwansa ."" nan take ta had'e fuska tamkar dariya ba muryarta a kausashe ta cigaba da mgn "muddin a ta biyu zanzo nasan bazai ta'ba aurena ba , ya adam fa yana da tsari acikin rayuwarsa shi din ba mutun bane kamar sauran mutane bashi da raayin tara mata "wa yace miki bashi da raayin haka ? zai yi raayi dan uwarsa Allah dai ya kai mu gobe tare zamu wajen uwarsa kafata kafarki ."
Baba qarami ya mike tsaye ya goya hannunwansa abaya yana girgiza kai yana duban hindu kafin daga bisani ya matso kusa daita sosai ya soma mgn can kasa kasa kusan mintuna goma yana mata mgn murmushin jin dadi né ya bayyana akan fuskarta " idan bata yarda ni na zama matarsa ba I will killed mrym idan ni ban samesa ba to babu wacce zata mallakesa anan gidan duniya yadda take mgnr zaka fahimci da gaske take kuma har cikin ranta abinda take nufi kenan ganin byn maryam ."
Washegari da misalin karfe goma na safiya a kofar shiga bangaren hjy zulaiheart tayi masu kai tsaye a babban falon gidan suka iske mami zaune yayinda d'aya daga cikin masu aikinta ke zaune tana mammatsa mata yatsun kafafunta sallamarsu baba qarami tasa mami dauke idanunta daga Kan tv ta maida kansu tana sakin fuska sai dai kallo d'aya tayi masa ta fahimci akwai damuwa atattare dashi ,aranta tayi addua allah yasa ba wata matsalar bace ta taso , ta amsa sallamarsu tana cewa "sannuku da zuwa !" baba qarami ya samu waje ya zauna akan kujerar dake fuskantarta yayinda hindatu ta zauna a kasa kan kafet a gaban mami ta sunkuyar da kanta kasa tmkr mai neman gafara tare da gaishe da mami cike da ladabi ta amsa tana mami ta maida hankalinta ga baba qarami tana nazarin fuskarsa sannan ta kalli yarinyar dake zaune a gabanta tace "salaha tashi kije Ki bamu guri cikin sauri yarinyar ta mike tare da fadin "tô !"
Mami ta sake maida hankalinta sosai garesu sannan ta fara magana a natse "baba qarami fatan dai lafiya dan naga yanayinka ba kamar yadda na saba ganinka ba yace "lafiyar dai da sauki "ta gyara zamanta cikin tsananin damuwa "daman dai na lura da hakan dan ba haka yanayinka yake ba kai din mutun ne mai faram faram duk sanda za'a ga fuskarka cikin murmushi take tô ina jinka fad'a abinda ke tafe da kai ."
Naunayen ajiyar zuciya ya sauke yana sake gyara zama yace "zulai jiya baba babba yazo min da wata magana akan hukuncinki akan Adam" ta gyada kai tana sauke numfashi "haka ne nasan zaka fi kowa jin dadi "tabbas naji dadi sai dai wani hanzari ba gudu ba nima na dade ina son had'asu aure da hindatu "mami tayi shiru tana dubansa da hindu dake zaune tana nazarinta tana son gano wani abu atattare da hindu domin dai ita din macece mai tsananin baseera tare da saurin karantar mutun sai data numfasa sannan tace "ita hindatu tana son shi ne ?
"tabbas tana tsananin sonshi na tsawon shekaru tunda tashi da soyayyarsa ta tashi ni ne mutun na farko data fara sheidawa da fari na nuna mata illar rayuwar data jefa kanta na afkawa soyayya da qarancin shekarunta alokacin na tmbyeta meye dalilinta na son shi ? me ya dauki hankalinta akanshi ? tace ba dan yana dukiya da kyau ba ,yau da zai wayi gari bashi da komai bashi da hannu bashi da kafa koda akan titi zasu rayu zatai rayuwa dashi kawai son shi ta keyi dan Allah alokacin shekarunta shashida né kawai wanda ni nake ganin bata san ma me take ba bama tasan meye soyayyar ba yasa take fadin haka ahankali baba qarami ya fayyacewa mami komai akan soyayyar da hindu ke ma ATA babu abinda ya rage numfashi mami tayi ta saukewa tana girgiza kai cikin tausayawa tana kallon hindu data sake dukar da kanta kasa sosai ."
"Masha allah naji dadin wannan abu sosai soyayya mai hade da zumunci allah ya bamu ikon sada zumunci dan allah ba dan kwadayin ko neman wata biyan bukata ba ". ta sake numfasawa ta cigaba da magana "nima daman tun farko burina kenan adamcy yayi aure biyu" ahankali baba qarami ya kalli inda hindu take wacce mgnr mami yasa ta dan dago kanta mami ta cigaba da magana "zan yi iya kokarina hindu na kawo karshen damuwarki duk da adamcy baya da raayin ajiye mata biyu amman zanyi convincing dinsa domin kawo farinciki arayuwarki da yarda allah ."
da sauri hindu ta kalli mahaifinta shima din ita yake kallo domin dai yasan diyarsa da tsananin kishi zata fi bukatar ganin ita kadai ta mallakesa Kmr yadda ta sheida masa kallon da takewa mahaifinta só take yace a fasa auren da mrym gbdy ya aureta shi kuwa baba qarami a hakan ma maganar tayi masa dadi "fatana mu hadu muyi addua akan lamari sannan mu nemi zabin allah allah kuma yasa gogan naka ya yarda ya amince ya hadasu su biyu din , ku bani lokaci kadan zan yi magana dashi duk abinda mukayi dashi zan nemeka da wannan maganar suka kawo karshen zance sukayi mata sallama ."
Suna shiga dakin baba qarami hindu ta fara zubar da hawaye acikin slow voice tace " baba ina ji ajikina ya adam bazai aureni ba dan dai idan amincewarsa zaa tsaya nema wallahi bazai ta'ba amincewa ba bugu da qari ni banason sharing dinsa da kowa nafi son ni kadai dan sam ban dace da zama da wata aba kishiya ba zan só mu rayu dagani sai shi ta karashe mgnr tana shesheka murmushi baba qarami yayi tare da fadin "hindu kalleni nan " ta tsura masa idanunta Kmr yadda ya bukata "ki kwantar da hankali babu wani abu acikin ya haduku biyu din amincewarsa shine abinda muka fi bukata a yanzu dan zaki iya kawar daita byn auren ki zauna ke kadai keda kike da baiwa iri iri nasan zaki bawa babanki mamaki haka dai baba qarami ya tasa hindu a gaba yana kwantar mata da hankali babu laifi hindu ta saki jikinta tare da karfafa zuciyarta sai dai ta rantse muddin bata samesa babu wata mace da zata mallakesa tana raye ."
****
Sanye ATA yake cikin farin yadin vol mai shegen haske da tsada a hankali yake taku yana gyara zaman hullarsa baki haka zali takalmin dake sanye da kafafunsa black cover shoes ne tsintsiyar hannunsa daure da agogon rolex yana dumfaro falon kamshi turarensa ya mamaye koina Kmr shagon turare yana gama qarasowa yace wa hisham "muje ko ".kai me yasa bakasan ka bawa mutun rai ka bashi hakuri ba duk lokacin dana bata ina zaman jiranka da muje ko zai qare " ina laifin kace hisham Afuwa kayi hakuri muje abokina km danuwana."
Dogon tsaki yaja kawai batare dayace uffan ba .
"matsalata da kai kenan ka gama bata lokaci amman zaka wani jawa mutane tsaki still bai ce komai ba
ya nufi hanyar dakin mami tana zaune ya shigo ta dago a natse tana duban kofar ganin shine cikin shigar da tafi qauna ta saki fuska cikin tsananin farinciki tace "Masha allah adamcy nah kayi kyau sosai allah yayi maka albarka ,sai dai wannan uban wanka da kashi haka kmr yau daurin aurenka, ai ko yau né daurin aurenka sai iyakarka hk kai ni kamar ma har da hoda ka shafa ko? Tsuke bakinsa yayi dan tsokanar sweetheart dinsa na yau yazo da wani salo ana zaman lfy me zai yi da wani hoda shi ba mace ba ."
"sweetheart ni zan fita amman zan dan jima ban dawo ba dan yau zaa bude kamfanin tace mai petir da sinadarin gas "Alhamdulillah masha ,allah allah yasa albarka arayuwarka data kasuwancinka allah ya tsare min kai ,yadda zaka fita lafiya allah ya dawo da kai lafiya sharrin mutun da aljani Allah rabaka dashi yace "Ameen !atakaice ya juya a natse yana taku tmkr wani jinin saurata "sai na dawo sweetheart ." a dawo lafiya adamcy nah ta fad'a tana cigaba da kallon bayansa "yau tsawon kwana uku kenan tana son sheida masa bukatar baba qarami amman ta kasa, ita kanta tana jin tsoron tunkararsa , tayi dukkanin tunaninta ta rasa ta ina zata fara shigo masa da maganar , auren mrym ma da yaya ya amince yanzu kuma ta sake kawo masa mgnr wata tasan tattara wa kawai zai yi ya gudu ya barta dasu ."
har ya kai bakin kofa yana shirin d'aura hannunsa akan handling din kofar ya tsaya cak ya waigo
bayansa adaidai lokacin da mami ta sauke numfashi da girasa ya tambayeta ,ta girgiza masa kai kawai tamkr wata marainiya "ko akwai damuwa ne ?ta sake numfasa wa kana tace " babu komai adamcy nah ina dai kallonka ne kayi min kyau sosai shigar ta amshi jikinka "me yasa bazanyi amfani da wannan damar na fad'a masa bukatar kanin mahaifinsa ba ? tayi mgnr acikin ranta da sauri zuciyarta ta gargadeta "karki soma yace ya fasa auren gbdy gashi goben nan zaa je neman masa auren mrym numfashi ya fesar "saboda Ke nayi shigar dan nasan zaki ji dadi gaahi yau juma'at "ai kuwa naji dadi kwarai da gaske na kuma gode sosai allah ya baka zuria masu albarka yadda kake ji dani kake min biyayya Allah baka masu yi maka bai amsa ba ya sa kai ya fice daga dakin zama ta cigaba da yi tana tunanin mafuta zata jajurce da tsayuwar dare domin neman zabin allah dan shine kawai mafuta agareta."
Aunty abinda na gama jin bayanin ibrahim taji kafafunta suna barazanar kasa daukarta lokaci daya zuciyarta na barazanar tarwatsewa Ibraheem ya matso yana girgiza Aunty abinda wacce ta dawo tmkr mutun mutumi "abida abida!! lafiyarki what's wrong abida?abida tayi shiru kawai tana sauke numfashi batare data amsa ba " baba babba zasuje nemawa ATA auren maryam gobe goben nan idan dai ba karya kunnuwanta suka jiye mata ba haka taji ya fito daga bakinsa " ibrahim me naji kace ? tana bukatar ya sake maimaitawa babu bata lokaci ya sake maimaita mata " wai tukunna wace maryam zai aura ?"maryam dai wacce Ke zaune a gidan mami diyar kaninta ita zai aura "da gaske ka tabbatar mrym zai aura ? ya gyda mata kai kawai yana maida hankalin Kan wayarsa dake qara "
"ina sam sam wannan aure bazai taba yuwa ba ta runtse idanunta da karfi ATA jarumin nmj né uwa uba kyau da natsuwa da Kamala ga tarin dukiya dasanin yakamata ai babu macen data dace dashi sai sultana gani yana mata wani irin kallo tayi saurin dawowa haiyacinta sunanta ya sake kira tare da jawo hannunta ya zaunar daita akan kujerar daya tashi cike da rauni tare da yin kasa da murya yace "abida meke damunki ?babu abinda ke damuna nidai dan Allah kar aje neman auren nan wai ma waye ya hada wannan auren ?shi ATA din da kasan ne ya zabi auren mrym din ?"ta karasa maganar cikin tsananin tashin hankali da bacin rai akan fuskarta ."
"me yasa ?saboda me kar aje neman auren ?"
Meye damuwarki da aurensu ? kanta ta rike da duka hannuwanta ta fuskancesa cikin sanyin murya tace "sbd sultana né bazan só ATA ya auri wata ya bar sultana ba "ita sultana tana son shi ne ?eh ammm daman umma ce ke ...."sai km tayi shiru ta kasa qarasa mgnr. "auren nan fa kamar anyi shi an gama domin babu wani abu ko mahalukin daya isa ya hana wannan auren mami da kanta ta hadata wannan auren ,ATA nason yarinyar ko baya sonta wannan shine bansani ba amman zuwa neman aure wannan dole ne gara ma ki binne duk abinda ke ranki karki shigo da wata magana da zata janyo matsala cikin jin haushi tace "idan kuma rabon sultana né fa ?har ya bude baki zai bata amsar tmbyrta wayarsa ta sake daukar qara ya dauka yana duba screen din wayar sunan ATA yaga yana yawo cikin sauri ya mike ya dauka ya soma mgn yana juyawa zuwa kofar fita tana ganin fitarsa ta mike tsaye ta soma zagaye falon tana maimaita abinda ya fada mata ashe kuwa zaayi wulakanci acikin gidan nan ko ta wani hali koda tsiya koda tsiya tsiya sai tayi duk abinda zatayi sultana ta shiga gidansa koda ata biyu ce ."
*****
"Maryama kyakkyawar budurwa ce mai kyan gaske doguwa ce sambal dan tsawonta bai sa ta rankwafa ba sai dai ita din ba fara bace haka zalika baza'a kirata da baka kirin ba chocolate colour ce tsayinta ya fito sosai domin irin matan nan ne masu shape din cocakola tana da siririn hanci da manya idanuwa masu matukar d'aukar hankali dan duk wanda tsautsayi yasa ya kalli cikin kwayar idanunta sai ya kusan suma saboda wasu sirrika da Allah ya hallita acikinsu masu kallon cikinsu ne kawai zasu iya karar da yanayin da suke tsintar kansu ."
idan tayi murmushi kuwa zaka ga siraran wushiriyarta sama da kasa sun bayyana wanda sune suke qara haskaka kyawunta ,ga gaban goshinta kwance suke da suma luf luf !! duk da kanta a daure yake a koda yaushe da d'ankwali amman kallo daya zaka mata ka gano irin matan nan ne masu yalwan gashi sannan tana da kafa mai kyau haka ma yatsun kafafunta zara zara ne lullube da farata masu matukar haske haka zalika muryarta idan tana magana dan dole ka tsaya ka saurareta kuma dole ka kalleta ."
Maryama ta samu tarbiya mai kyau daga gurin mahaifiyarta tayi karatunta na primary har zuwa matakin jami'an acikin jahar lagos kuma duk akarkashin kulawar gwanaty , haka bangaren karatun alqurni baa barta abaya ba domin tun tana primary ta sauke alqurni km hakan bai sa ta daina zuwa islamiyya ba idan kaga bataje ba sai dai wani aiki ne ya sha kanta ."
kyawun maryama mai tsayawa ne arai sai dai duk da wannan kyawu nata bata da wani tsayayyen saurayi duk wanda yazo neman aurenta dayazo sau d'aya zuwa sau biyu zai daina zuwa batare da wani dalili ba koma karshe taga ya koma gurin kaulat diyar kanwar babanta Aunty hassana gata da kyau sosai na bugawa a jarida amman mutane na mata kallon mai bakin jini abun yana d'an damunta sai dai bata nunawa dan ba samari bane a gabanta karatunta ya fiyye mata komai mahimanci koda yaushe ka kalli fuskar maryama zaka ganta a daure sakamakon rashin farinciki shiyasa mutane suke mata kallon mai tsananin girman kai ."
Sannu ahankali maryama take tafiya tamkar tana jin tausayin qasa ko macijiya dan babu wani karfi a tattare daita cikin shiga ta Kamala riga da sket dinki zamani da kuma dogon hijab mai hannu har qasa fuskarta manne yake da bakin nikaf kalar hijab din jikinta wanda ya zame mata jiki a duk sanda zaka ganta a waje ko a makaranta da wannan nikaf din zaka ganta sam bata yarda ta fita koina batare dashi ba a cikin gidansu ne kawai zaka iya ganinta sadaka yayinda kafad'arta Ke makale da jaka baka mai dogon igiya ,a zahiri kana kallonta kasan a matukar gajiye take dan yanayin tafiyarta ma ya qara yin slow sa'banin na sauran lokuta sakamakon ranar data kwaso gefe da gefenta qawayenta ne subai'a da sumaiya ne suka sakata a tsakiyarsu ."
Tafiya suke a natse suna hirar yadda jarabawar su ta qarshe ta kasance adaidai jeaction din ummahani street suka rabu da kawarta sumaiya tayi hanyar hagu da zai kaita unguwar daji suka cigaba da takawa da subai'a itama dai tafiya kadan sukai tayi dama wato markaz ya saura ita kadai ta cigaba takawa zuwa unguwarsu market street batayi wani doguwar tafiya ba ta qaraso unguwarsu bata tsaya akoina ba sai kofar qaramin get din gidansu wanda kallo daya zaka masa kasan na masu rufin asiri ne dan bazaa kira gidan da gidan mai kudi ba haka zalika bazaa kiran gidan da gidan talaka fútik ba daidai misali gidansu ginin da ne kuma ginin kasa ne filasta ne ya rufawa ginin gidansu asiri da kuma jamar dake rayuwa acikin gidan ."
a natse ta shigo haraban gidan nasu idanunta ya sauka akan kaulat wacce ta sha kwaliya cikin atamfar chiganvy gold black touch of milk ,kallo daya tayi masu ita da wanda ta gani tsaye ta dauke idanuwanta zuwa wani bangaren tana cigaba da tafiya dan wanda suke tsaye da kaulat din ba bako bane a wajenta tasha ganinsu tare ."duk da bilal baya ganin faukarta amman duk sanda ya ganta yana rasa natsuwarsa a kullum burinsa yaga fuskarta yaga yaya take ,kasa cigaba da motsi yayi daga inda yake tsaye yabi tafiyar maryama da wani irin kallo komai nata a natse most especially tafiyarta abun burgewa shi kam ina ma zata yarda ko sau d'aya ta bude nikaf din yaga fuskarta yasan zatai kyau duk da bai ta'ba ganin fuskarta ba."
Kaulat na ganin irin kallon da yake mata taja dogon tsaki yayinda maryama bata sake duban inda suke tsaye ba ta cigaba da tafiya zuciyarta na matukar jin tausayi kaulat dan babu abinda tasa gaba sai aikin tara masu samari marasa inganci a gida