Showing 75001 words to 78000 words out of 168608 words

Chapter 26 - Mar'adam's Book 1 Hausa Novel Complete

jikinta akan kujera tana jin bakinciki abubuwan da suke faruwa daita allah ya bata kyau ya bata ilimi tana da nagarta amman bata san dalilin da maza suke gutunta bayan sun kawo kansu wajenta ba , tana zaune tana tunanin taji sautin muryar aunty salma"maryama !maryama!!ke dan uwarki wannan wani irin rashin mutunci né kalmarta ta katse mata tunaninta ta dawo haiyacinta tana magana cikin bacin rai "au zama ma kikayi dan iskanci ni nawa mijin bai kwanta ya huta ba yana can neman abinda zaku ci shine ke zaki zauna saboda sakarci banza da tunanin banza daga yarinya tazo tana sakarci da munafurci sai ki nemi waje ki zauna kina tunanin iska dana banza da wofi allah dai yasa komai zai faru abanza né tunda bashi da wani amfani ana da kyau amman ya zama na banza ."
"tô ai dole ya zama na banza  tunda mugun hali yayi yawa "

tarasa me ta tsarewa aunty salma  acikin gidan nan zuwa yanzu bata tunanin iya kiyayya ce kawai ta fara tunani har da hassada take mata akan halittar da allah ya bata idan ba haka ba tana mata komai iya bakin gwargwado tayi mata shara tayi mata wanki idan ta kama wanke wanke duk tana yi dan dai a zauna lafiya da kuma kar ayi masu gorin ciyar dasu daake acikin gidan shiyasa sau tari bata son fita tsakar gidansu tafi son tayi zamanta a daki dan da zarar ta fita ko ita ko aunty hassana sai an samu wanda yasata aiki ko ya zageta ko mata gori ."
muryarta a sanyaye tace "yanzu ni aunty salma me nayi miki ?akwai abinda kike bukata da banyi miki ba ?ta rike baki au tambayata ma kike yi  saboda yanzu kin kawo karfi an balaga an balallage an zama iyayen mata ? "


"allah yasa ba ita kadai ta balaga ta zama iyayen mata ba wadan da suka balaga suka zama iyayen mata suna da yawa " suka tsinkayi muryar habib abayansu  yana harararta ta juya tana kallonsa
"zo ki fitar mana daga daki kafin na miki dukan mutuwa "uwarka da ubanka basu isa ba bare kai qaramin dan iska  bazan fita ba idan kana iyawa zo ka fitar dani tattaccen d'an  iska ."

Jin haka yasa cikin fusata ya nufota gadan gadan maryama ta mike da sauri  ta shiga tsakani tana cewa "Uhm uhm after dad babu ruwanka daita "tô wallahi kice mata ta fita ta bar mana dakinmu "au har wani takama kake da dakin aro? "dakin aro ne a aka bawa uwarka  byn kai a kusa da dakin kashi aka haifeka idan bakasani ba kasani ga dakin daaka yi cikinka ga masai Shege ma shegen girman tsiya anyi mugun gado a wajen uwa ".

Ya daga hannu zai kai mata mari maryama ta rike hannunsa a rikice cikin muryar kuka tace "haba habib ka barta mana ta fadi duk abinda take son fad'a ai bakinta ne tunda mu din ba shegu bane meye abinda zai dameka arziki kuma  na allah né "kinga makira banason iskanci da munafurci ki barshi yayi min abinda ya ga dama amman gamawarsa ke da wuya zanci uwarsa da shi kansa dan wallahi duk iskanci da yayi akan uwarsa zan rama dan ita ce daidai ni ba shi qaramin dan tasha  ba ,yana yawo suki suki duk yunwa ta gama cinyesa tayi maganar cikin daga murya ".

"Dan allah   kiyi  hakuri  karki saka aunty cikin fadan nan habib yayi Kuskure amman kiyi hakuri bazai sake ba habib ka bata hakuri ".
"What!"
"Allah ya tsareni na bawa wannan matar hakuri kar allah yasa tayi hakuri ko ki fitar mana da wannan mahaukaciyar matar koni yanzu najata na fitar daita sha shar mata mara sallah mai dotti kawai hannu aunty salma ta daga zata wanke masa mari taji ya rike mata hannu sannan ya tsura mata idanunshi cikin sarkewar murya yace "kin gama ta'ba lafiyar kowa acikin gidan nan yanzu ke har yanzu a tunaninki kin kai matsayin da zaki cigaba da marena na kyaleki ? tô  idan kina wannan tunanin ki daina yanzu dan zaki ya girma ya wuce wannan tozarcin dan bake ba hatta wanda ya ajiyeki acikin gidan nan  kanin mahaifina kenan ba bai isa ba bare ke banza jaka dabba mai hali irin na dabbobi mara hankali ."

a fusace ta fixge hannunta tare da cewa "da uwarka kakeyi itace jaka dabba  ai ,dan marasa mutunci irin tsiya irin jaraba tana fada yana maida mata ita kuwa maryama sai faman kuka take tana bawa aunty salma hakuri data gaji ma sai tayi shiru kawai tana kuka tana kallon fuskar habib dake tsine mata yana hadawa da yaranta da kaf dangin mahaifinsu da yasan basa qaunarsu  a maganganunsa ta fahimci babu wanda ya tsana kamarsu aunty salma ta fice cikin fushi ta bar dakin cike da tsananin damuwa ."

Maryama ta zauna jagwaba akan kujera tana mai runtse idanunta habib ya lumshe idanunshi "shiyasa kullum suke takura miki wannan sanyin naki yayi yawa ki zama mutun ki nuna masu zamani ki nuna ma kema yar zamani ce sai ku dawo daidai dasu ba kullum ki zauna kina asarar hawayenki a banza ba .""haba after dad mutunci aunty zamu duba yanzu kasan halin matar nan sai taje tayi mana wata kullaliyar a wajen baba gali ".

"taje dan kutumar ubanta shima dan kutumar ubansa yazo daidai nake  da kowa allah ya taimakesa yazo  idan ban raba masa kanshi gida hudu ba kice Shege ne , anan zan jira zuwansa ya fad'a yana huci tmkr zaki ta mike ta kamo hannunsa ta zaunar dashi ta zauna kusa dashi tana shafa masa baya dan ta fahimci ya dauki zafi dayawa "kayi hakuri komai me wucewa ne wata rana sai labari abinda ya baka dariya wata shi zai saka kuka ka bar aunty salma da duk wanda zai fad'a son rashi acikin gidan nan akanmu."


ita fa aunty salma bata da laifi gani tayi yanuwan mahaifinmu suna yi mana yau da sun  ga kima da darajanmu wallahi bata isa ba amman nasan wata rana idan ance tayi bazatayi ba kayi hakuri kaji danuwana rarrashinsa tayita har ya sauko tace "kaje kayi sallah nima zanje nayi kafin aunty su dawo ni na godewa allah ma da bata nan bare taga abun bakinciki  kuma allah yasa kar aunty salma ta fad'a wa baba gali "ta fad'a masa mana Ke kike tsoronsa yazo ni yau a gida ma zanyi sallah ina jiran duk abinda zasu dashi bari ma naje na nemo atakobina wacce zan fellewa mutun kai dashi ."

"Dan girma Allah kayi hakuri meye hadinka da takobi kai ba dan daba ba "na zama yau "allah ya tsareni allah kiyaye bazaka zama haka ba Kiyi adduar karsu zo da hauka ya fad'a tare da shigewa dakin aunty kofar  tabi da kallo kafin daga baya ta mike taje tayi alwala ta fita ta tada sallah tana cikin sallah tajiyo sallamar   aunty tana kiran sunanta  tana jin habib ya fita yana cewa "sallah take aunty sannu da zuwa "
"Yauwa habib a she kana gida ?nima ban jima da shigowa ba ina kika je ne ?kai habib zaka fara tambayoyinka kenan babu  damar kaga na fita murmushi  yay yana sake cewa "aunty ina kike je ?munje duba jikin  hafsat ne ta haihu amman cs aka mata ".bai sake cewa komai ba saboda ya fahimci  kowace hafsa take nufi diyar aunty fatima yayar mahaifinsu aunty ta mike ta shige dakinta domin yin sallah ."

Byn mintuna goma maryama ta fito daga dakinta  zuwan dakin aunty  duk jikinta a sanyaye lokacin aunty tana kan dadduma ta idar da sallah tana dai zaune  "aunty sannu da zuwa "yauwa my princess ya zaman gida ?ta gyada mata kai alamun Lfy!"ya na ganki wani iri ko akwai abinda me damunki ne ?tayi shiru kawai tana jin faduwar gaba "kin dan daura mana wani abu kuwa ?ta bude bakinta ahankali tana shirin bawa aunty amsa suka jiyo hayaniya shiru tayi tare da kasa kunne muryar baba gali ne ta mike da sauri jikinta har rawa yake ta nufi kofar fita itama aunty ta biyo bayanta a tsakiyar falon suka gansa tsaye tare da aunty salma da aunty  hassana sai hargagi suke tamkar wasu karnuka yayinda habib ya shiga kitchen ya dauko zabgegiyar takobinsa mai tsine ya koma bakin dakalin kofar fita  ya zauna  yana wasa  takobinsa ,aunty hasana ta nufo inda yake shi kuwa habib kanshi na kasa yana cigaba da wasa takobinsa  jira kawai yake suyi masa wata maganar banza ."

Aunty ta kalli maryama ta kalli habib tana bukatar qarin bayani cikin fusata aunty salma tace babu irin qare maku zagin da wannan tantirin yaron bai yi ba ta uwa ta uba har da ce mana dabbobi jakuna aunty hasana tace "da ubansa yake Shege dan Shegiya "da sauri ya mike yana zagayesu da takobi  kiiiii kake jin tsinin bakin takobi asimintin falon basu ba hatta aunty da maryama sun tsorata "kai ko ka fara shaye shaye ne ko meye ?"da sauri ya juyo kan baba gali da yayi mgn fuskarsa a tsuke alamun bai son ya kawo masa raini "dan ubanka da kake zare masa idanu ka dauka zamu ji tsoronka ne ?"

"a'a nasan bakwa jin tsorona kamar yadda nima yanzu babu wannan tsoron duk wanda ya nemi zaman lafiya ayi wanda yace sabanin haka yake bukata bismillah ni bazan bata bakina ba sassara mutun kawai zanyi na aika sa lahira ."ya fad'a yana tsoka takobi daidai kafar baba gali ."

Da wani saurin gabadayansu suka ja baya suna kallonsa da mamaki kamar yadda aunty Ke kallonsa "tunda ku kun zama ahlin sheidan bakwa jin wani yare sai na dabbobi bismillah  nima zan nuna muku akwai digon wannan dabbar ajikina  ,tunaninku me zakuyi da kuka wani kwaso jiki gbdynku kuka zo ?
"To wallahi  yau koni ko ku duk wanda ya zagi uwata da yaruwata sai na yanke masa harshe byn na raba kanshi gida hudu ."

zaro idanuwa sukayi suna sake ja  baya dan ya daga takobin hannunsa daga aunty hassana har aunty salma suka koma bayan baba gali suka boye cikin  karfin halin yace " bamu bane dabbobi da uwarka kake aiko jin haka Ke da wuya habib yayi kansa gadan gadan  zai sara mata takobi  aunty ta rike masa hannu tana zabga masa mari cikin muryar kuka tace "meke damunka habib ta fad'a tana kwace takobin tayi jifa dashi  "zaka kasheni ne  ?

"Ai da zai kashe dabba irinki da mun samu kwanciyar hankali "inji cewar aunty salma .
aunty kina jinsu ko bani takobina na sassara
shegu yan kutumar uba .."inna lillahi wa inna ilaihi rajiun allahumma ajirni fi musibatihi   Waklifli khairan minha tana gama fadar haka ta durkushe kasa tana cewa "yanzu habib irin tarbiyar dana baka kenan ?maryama ta durkusa kusa daita tana mai rike hannunta tana ma habib wani irin kallo mai cike da tashin hankali ".

"Me  yasa bazaka koyi danne fushinka ba ?me yasa zaka min haka habib ? me nayi maka dana cancanci haka habib ? "Kuji makira ina allonki allonki yana jahannama ,makira  mata kin gama koya masa yadda zai ci mutunci mutune shine  yanzu kizo kina kukan munafurci yau zamanku ya qare acikin gidan nan ku hada ina ku ina ku ku bar mana gidan nan mun gaji da ganinku daga Ke har wadan nan mataiyatan yayan naki bama bukatarku."inji cewar baba gali ."

nan da nan habib yayi kan baba gali duk da yaso ya rabu dashi ganin mahaifiyarsa tana kuka dan a duniya babu abinda ya tsana sama yaga ana cin mutunci mahaifiyarsa da yar uwarsa baya son ana zagar masa su bare a zagi qaddararta da binta da muyagun kalamai ko zubar hawayenta  ,wuyan baba gali yake shirin damka ya


jiyo sautin muryar aunty cikin kuka tana cewa "wallahi habib idan ka ta'ba shi sai na tsine maka albarka "cak ya tsaya yana kallon baba gali ido cikin ido jikinsa na wani irin rawa tamkar mazari ."


Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
     MAR'ADAMS
     💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗


*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access  idan an tura sai a turawa wannan  09136918331  alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.


             Page 16

Ahankali   maryama   ta  mike  daga  cinyar  umma   hawaye  ne  sha'be sha'be  akan   kuncinta
ta tsurawa umma  manyan    idanunta  wad'an da   suka   canza   kala  tana kallonta   batare  da   tace  uffan  ba  ,duk  yadda  taso  ta daure  ta  tsaida  hawayenta  kasawa   tayi  hawaye  take   zubarwa  sosai  cikin  tashin  hankali  mai  tsanani ita  kad'ai  tasan  halin  bakinciki  data  tsinci   kanta   ciki   adalilin   jin  labarin   iyayenta ."labarinsu  yayi  matukar  d'aga  mata  hankali "a  she  wahaalarsu  da  tsanar  da'aka yi  musu   acikin  family's  ta  samo  asali  ne  daga  soyayyar  iyayensu ?  haka nan  taji   tausayin  kansu  na   sake  shigarta   . "

     Koina   ajikinta   yayi  sanyi  yayinda   falon  ya  d'auki  shiru  ,yadda  maryama  tayi  shiru tana zubar da  ruwan hawaye  tana sake tariyo  halin  da  iyayenta  suka tsinci  kansu  adalilin  soyayya haka ma  umma  bata  sake  cewa  komai  ba  " ahankali  wani  irin  so  da  qaunar   mahaifiyarta da qaninta  habib   ya  qara  shigarta"  allah  sarki  aunty  "hakika  kinga   rayuwa,  hakika   ahlinki  sun  d'auki  zafi  dayawa  akanki  ."

"hukuncinsu  yayi tsanani  dayawa  domin  allah Ke had'a  soyayya  alokacin  daya so ba  dabarar  mutun  ba  ,ba  son ran mutun  bane  ,domin  kuwa  idan da  dabarar  mutun  ne  ko  son ran mutu da  mutanen  duniya  dayawa  basu  tsinci  kansu  cikn
ta ba ."

a qalla  sun  d'auki  minti  goma a haka  suna  kallon  juna   sannan  maryama ta  lumshe  idanunta da sukai   jajur  alamun  tarin  quna da bakinciki ahankali  umma  ta  numfasa  "maryama !  ta  kira sunanta  a  natse , ahankali  ta motsa  lip's  dinta  alamun ta amsa dan  zafin  da  zuciyarta  keyi  ya danne  fitowar  muryarta "ki  godewa  allah  ba  kuka ya  kamata kiyi   ba  maryama."


    "ki  godewa  allah  daya  qaddara  aure  a tsakanin  iyayenki  da  har  aka sameku  ta  hanyar  sunanh "  "Alhmd!ta  furta  a can kasan   makoshinta   tana  dafe  kanta  dake  sara da mugun karfi "ya  kai  ki godewa  allah  ki  sake  gode  masa  ko  bai  kai ba ? kanta  ta  gyada  mata  alamun "eh!.

"To  ki  manta  da  duk  abinda na  fad'a  miki  muje  Kiyi  sallah  kici  abinci  ki kwanta ki huta "  da  karfi  maryama  ta  fizgo  magana  "bazan  iya manta komai  ba ,a halin  yanzu  ma   ganin  komai   nake kamar   a yanzu  ya  faru  har  nayi  danasani  umma nayi  danasani   jin  wannan  mummunar   labarin  rayuwa  irin  rayuwar   da  iyayena  sukayi  rayuwar kaskanci  ne a wajena."

    "why  umma? "me  yasa  komai yake  faruwa  damu haka ?ahankali  ummah  ta  shafa  kanta
zuwa gadon bayanta  tare da cewa "kiyi  hakuri  maryama kowa da  kalar  irin  tasa  qaddara a yanzu  jajurcewa  zaki qara  akan  wanda  kikayi  har kika samu  cikar  burinki  na  zamowa  cikakkiyar  mai  ilimin  lissafi  ,kiyi  qoqari  ki tsaya  bisa  kafafunki  domin  tallafawa  rayuwar   mahaifiyarki   daya  qaninka   domin  ina  hango  tarin nasara  da  kwanciyar  hankali  atattare  dake , bilkisu  na  bukatar  farinciki  ,maryama  nasan  da sannu  zaki  zamewa  bilkisu  sanyin  idaniya  amman  fa  sai kin manta  komai  maryama  kin rungumi  qaddarar  rayuwarku ."


"Na  yarda  da  qaddara  ummah  domin  yana  daga  cikin cikar  imani  mutun , na yarda da qaddara  amman  umma  aunty  tayi  kuskure  arayuwarta  bance  laifi   bane  dan  taso mahaifina  amatsayin  da  yake amamn  iyaye  fa  umma ? "manzon   sallahu  alaihi  wa salam  yace "ridal  lahi  fi ridal walidaini , wa sakad'ul  lahi fi sakad'il  walidai ."yarda  allah  yana  tare  da  yarda  iyaye, haka zalika fushin  allah yana  tare  da  fushin  iyaye  allah  ya  fifita  iyaye  akan  komai most  especially  uwa ummah ,babu  uwar da  taza ji  dadin irin rayuwar da  aunty  tayi ."

umma  tayi  shiru  kawai  tana sauraronta "misali  na kwatantawa  aunty  irin  abinda  tayiwa iyayenta ya  zataji ? na  kawo  mata  in responsible  man  nace  naji  nagani  sai  shi  duk  tarbiyar da tayi  tsawon  shekaru  tana  bani nasa  kafa na  rugujeta ya zataji ?" magana  ta   gaskiya   iyeyenta  da yan' uwanta   sun d'auki  zafi  dayawa  amman  aunty  ta fisu  laifi  kuma  lallai  ya  kamata  taje  ga  iyayenta  ta  roki  gafararsu sannan  ta  koma  cikin  danginta zuciyarta ta  samu  salama ."

   "wallahi  yadda  nake  jin  habib araina  bazan  iya  barinsa  saboda  wani  ba  bare  iyayena  da suka kawoni duniya ba ,abun  da ciwo  ummah  ba  kamar  yadda  kuka  d'auka  bane  kema  uwa ce ummah , aunty  ta  kona  zuciyar mahaifiyarta   dayawa,  yanzu na gano duk  aunty  ce  silar  shigarmu   cikin   matsala , iyayenta  na  can  suna  fushi daita  har  yau  ta  yaya   kike tunanin zataji  dadi ?"ta  yaya  kike  tunani  zan  iya  bata  farinciki  byn  ga  inda  zata samu  fiyye  da  nawa  ."?

maryama  ta  kalli  umma  cikin  sarewa  ta cigaba  da  magana " umma  abun na  da matukar  ciwo  irin  ciwon  dake  cin  zuciya da  bargo  ,ciwo  ne da  bashi da  magani  da   mafuta  har  sai  ka  had'u  da  mahad'inka , shiyasa a kullum  idan  na  kalli  aunty  sai naji  tamkar  tana  boye  mana  wani  abu  mai  mahimanci  ga  rayuwarta , ashe  gsky  né  hakika bakinta  bazai  iya  furta  mana komai  akan  rayuwarta  ba  matsawar  ita  din  uwa  ta  gari 
ce , dan   allah  umma  Kiyi   min  rai ki  raba  zuciyarta  da  wannnan rayuwar  idan  kuma  baki  yi  ba ni  zanyi  ,zan  rabata da  nauyin  dake   daskare  a  qirjinta ."


Tana  gama  fadar  haka ta  mike  a hankali  tana  share hawayen idanunta  da  suka  gagara tsayawa  tana  jin  wani  zafi a qirjinta , bazata  cigaba da d'aukar  wannna  nauyin  ba , koda  aunty bata  amince  ta  koma  ga yan'uwanta  ba ,lallai  ita   zata nemosu  a duk  inda  suke  acikin garin  nan  ."muryarta  a sanyaye  tace "umma ni   zan  wuce  sai   da  safe  " kai  kawai  ummah   ta   gyada  mata  sannan   maryama   ta  fara  tafiya  umma   tayi   shiru   tabi   bayanta da  kallo  tana  kallon  yadda  take d'aga  zara  zaran yatsun kafafunta da  kyar  tamkar  wacce  bata  da laka ."


  " A

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login