Showing 99001 words to 102000 words out of 168608 words

Chapter 34 - Mar'adam's Book 1 Hausa Novel Complete

habib Ke mata fatan alkhairi idan wani abun farinciki ya sameta tace "na gode  sosai yaya ."


Habib yace "a she dai yaya  ka  gane  shiyasa sai  na zaba mata na durje mata  miji  dan ita din ba kalar kowani nmj bace "kaga yaya karka kulashi  mu je ciki  mu  qara gaisawa "wucewa sadam yayi side d'in Ummah  maryama da  habib  na biye da shi sunata hiran duniya..."

Zama sukayi a parlour'n  sadam ya fara kiran  "Ummah  Kina ciki ne? Eh! Ganin nan  zuwa dan albarka har ka dawo ne? sadam yace" eh ! gashi na  kawo  miki maryamarki "ban gane ka kawo min maryama ba maryama da muke yini tare dan gulma zakace ka kawo min ita Bari dai nazo ganin nan fitowa ."

Bata  wani bata  lokaci ba ta fito cikin  doguwar riga  qaton  tray ta aje  a gaban sadam  na fruits bismillah  sannu da zuwa yau har da habib  to duk sannuku "Ina yini "Habib  yace " lafiya lau  habib Ummah ta kalli sadam ta kalli maryama  sai taga sun maseefar dacewa ina ma su kasance maaurata suna hirarsu gwanin ban shaaawa  habib ya fahimci  maryama kunyar sadam take ji sosai dan taki fad'ar abinda ya kawo su gashi shi yunwa yake ji ."

Maryama  tace after dad  ya kamata mu wuce dare nayi  "a'a  har  zaku  tafi kenan maryama  to ai  bakuci  komai  ba "karki damu Ummah  "ban  gane  karta  damu  ba kinga nifa banason kunyar nan  take wai ma wa Kike jin kunya anan  umma  ko  yaya  sadam ,?maryama tayi shiru tana mai sunkuyar da kanta qasa tana wasa da yatsun hannunta "kinga  Ummah  nan ya fad'a  mata abinda ya kawosu "kai maryama  amman shine zaki jashi ku wuce to  kuci me idan kun wuce?  allah ya kyauta wannan kunyar taki  kaga habib bari nazo ta fad'a tana mikewa tsaye ta nufi kitchen ".

Bata wani bata lokaci ba ta dawo hannunta d'auke da wani madaidaicin kula cike da abinci sannan da wata leda cike da su cincin  wanda tayiwa sadam ta miqa ma maryama tace gashi  kai km habib ka  rike kula " mungode Ummah !Suka fito maryama nayi masa mitar abinda  yayi  dariya kawai  yayi yana cewa "ina ganin gara  kawai  ayi yar gida mu huta da samari masu  mana patrol  "kai dai kasani  ni nasani ko gaskiya suna tafiya suna jan juna har suka qaraso falonsu  habib ya zauna yana kiran "washhhh allah maryama ta cire hijab dinta ta ajiye  akan kujera  tace "habib bari na kira aunty  kanshi kawai ya gyada mata ."

Ahankali ta shiga d'akin sai dai abinda yayi matukar daga mata hankali shine ganin mahaifiyarta kwance rigingine akan katifa hannunta rike da wani hoto tana kallon hoton hawaye na zuba daga idanunta  tana tuna irin rayuwar dadin da tayi ada kafin shigowar ussein rayuwarta ,bata haskowa kanta irin rayuwar da take ba sai data hadu da ussein soyayyarta ta gurba tunaninta ."

yayinda maryama ke kallon mahaifiyarta da ita kadai ta rage mata a duniya yanzu a natse ta qara taku biyu domin son ganin hoton waye a hannunta take kallo tana kuka  wasu mutane tagani guda biyu cikin shiga na alfarma suna cikin koshin lafiya da farinciki ko baa fada mata ba tasan hoton iyayenta take kallo cike da nadama lumshe idanunta tayi "iyaye ba abun wasa bane , aunty iyaye suna da kimar da darajan da  bazaa iya mantasu ba ."

ahankali taji sautin muryarta tana fita  cikin kuka "nayi  kewarka baba , nayi kewarki mamana yanzu ku har yanzu  bakuyi kewata ba ?yanzu ku baku yafe min ba ko nemeni ba? wallahi ina sonku nayi kewarku ,nayi  kewar  kowa da kowa  ta fad'a tana mai daura hoto a saman  qirjinta tana shafawa tana kuka.."

Ahankali maryama ta juya tana zubar da hawaye masu zafi ta koma falo ta zauna kusa da habib tana sheshekan kuka nan take ya birkice ya soma tambayarta "heartbeat me kuma ya fara ?kukan me kike yi ? Ina aunty ?yayi mata tmbyr ajere cikin tsananin tashin hankali tasa gefen rigarta ta goge hawayen "yau aunty ta tuna da iyayenta tana daki tana kallon hotonsu tana kuka ni nasan zuciyarta na cike da qaunarsu shiyasa kaga ina son ta koma garesu ."

"habib  soyayyar  iyaye  da  yanuwa  baa  wasa  dasu wallahi a tsakaninsu soyayya ce mai karfi ka misalta hakan akanmu musan da qaddara  amman an cuci aunty an yi sanadiyyar rabata da kowa nata ,ta bar iyayenta akan soyayya gashi ta rasa soyayya taki bin umarnin iyayenta gashi duniyar taki mata dadi maryama tana kuka habib na rarrashinta har kukan nata ya ragu adaidai lokacin da sukaji tahowar aunty tayi saurin share hawayenta tana cewa ".

karka nuna mata komai da sanyi jiki ta qaraso "kun samo abinda zaku dan ci ?eh mun samu har da cinci tô maza kuci ku kwanta tayi maganr cike da rauni aunty kizo muci tare "aa ku dai kuci ku koshi aa wallahi tare zamu ci habib ya mike ya kamo hannunta ya zaunar daita ya bude kula abinci yana cewa kai abincin nan zai yi dadi maryama ta dauko spoon ta dibi abinci zata kai bakin aunty habib yayi sauri ya kwace spoon "bani ni zan bata da kaina suka sa da dariya ya soma bata abinci abaki yana fada mata kalamai masu sanyi ."

"idan nayi kudi bazan yi nesa dake ba zan kasance tare dake ,dan allah aunty ki daina damuwa akan komai kinji ki dinga tunawa cewa kina damu mu din zamu zame miki farinciki a rayuwarki Wallahi sai mun sa kinyi alfahari damu ki cigaba da addau ga heartbeat nan kwanan nan zata fara bautar qasa yanzu ma ina mata  processing yadda zaa dawo daita lagos né daga adamawa wannan farinciki  ya rage tarin qunar da zuciyar aunty take ciki  tace "allah yayi maku albarka yayiwa rayuwarku albarka in sha allahu bazaku dangwama haka ba allah zai saukaka maku rayuwa ,Allah nake roko ya daukaka min ku na yafe  maku duk abinda kuka min da wanda nasani da wanda ban sani ba suna cin abinci suna debewa juna kewa ."

******

da misalin karfe 9:00 na washegarin ranar lahadi mr ata ya fito  parlour'n  mami  ,duk  jikinsa yayi sanyi har wata  katuwar  rama  yayi  daman ya lafiyar kura ?ba wani jikin kirki bane dashi  kusantowar aurensa da maryam yasashi jin    kmr  ana  fixgar  ransa  ,shiru ne  ya  ziyarci  parlour'n yana tunane  tunane yana jin kamar idan ya tafi france  kar  ya  dawo  domin a lissafinsa sauran kwanaki goma cif a daura masa aure da yarinyar daya tsana fiyye da komai arayuwarsa   byn  kmr  mintina goma mami  ta qaraso  da kanta ta  had'o masa abun kari , chips  da soyayyen kwai  da  ruwan tea mai kauri , ta janyo qaramin table  gabansa ta  ajiye kana ta zauna kusa dashi ta tsura masa ido tana kallonsa batare datace komai ba ."

ya dauki cup din tea ya kai bakinsa ya kurbi kadan yana mai runtse  idanunshi  shiru har wasu mintuna suka shude yana zaune itama tana zaune tana kallonsa da kyar ya bude baki "sweetheart! "kaci abinci first before anything adamcy , sannan kar naji  kayi  magana  kaci abinci  kawai yaushe rabon ka sanyawa cikinka  abinci  bare a samu magani yayi aiki ajikinka ? ji yadda ka dawo acikin kwanaki uku kacal  ka taimakeni kaci wani abu  kanshi  kawai ya iya d'aga mata batare da ya kalli inda abinci yake ba, saboda sam  baya jin cikinsa  zai iya amsar komai  shima da zata taimakesa da tasa an fasa auren nan da yarinyar an hadashi da wata zai hakura da princess dinsa ya amshi koma wacece  duk da zuciyarsa princess kawai take so da son gani numfashi ya dinga  saukewa ."sweetheart  dina me yasa  kika  manna min wannan auren  haka?
" sweetheart  zaki  kasheni da kanki wallahi at least ki sake gara min dama koda  na  tsawon wata guda ne  ."


"to me  zan  maka adamcy nah daya wuce haka ?
"me  kake  son  nayi  idan  banyi maka  haka ba ?
gani nayi  kana  neman hargitsa min kwakwaluwa da qarar da rayuwarka a banza "me kake tunani mutane zasu ce idan   bakayi aure adaidai wannan lokacin ba ? wallahi zaka shiga zargin mutane ,mutun har mutun kamamme kamar ka ka zauna babu aure ko kana neman mata ne adamcy bansani ba da kake gudun aure ."

wani  irin kallo yayi mata mai nuna mata bayayi "to idan bakayi me kake jira ?maryam  yaruwarka ce fa "yanzu kai kafi son ka dauko min suruka daga waje alhalin ga wacce tasan darajata take sona nake sonta diyar danuwana yanzu idan an fasa auren nan  me kake son na cewa mutane da yan'uwana ,dan Allah dan annabi in banda   da rigima irin naka ba me ye laifin maryam ..?

"wani far yayi da idanu zuciyarsa na dokawa  da numfashinsa da yayi kokarin d'aukewa yayi saurin dawowa dashi gangar jikinsa sannan yace "sweetheart  ni bance tana da laifi ba amman  ki duba lamarin da  kyau  tunda nace bana sonta ai  sai a  hakura kawai  kowa ya kawo zabinsa . "kai rufe min baki ban son shirme banza, ka daina ganin ka had'a komai kana da kudi  kayi tunani zaka iya  juya ni  ."Wannan  aure sai  anyi shi muddin ina raye ."


ya marairace muryarsa  sosai  tmkr  mai shirin zubar da hawaye sannan yace "wai sweetheart me yasa kike ganin kmr  wannan yarinyar ce kawai zata iya kulawa dake  ? Allah  sweetheart ki daina mata kallon haka  saboda irinsu sune masu bawa dangi kunya  wallahi duk lokacin da naji kince min itace zata san darajarki  bakinciki nake ji kmr na kashe kaina saboda ni duk macen dana kawo miki dolenta ta soki tayi miki biyayya bama Ke ba sweetheart hatta yayyuna biyu din nan dolenta ta bisu  lalacewar mace daga miji ne  ni kuma bazan ta'ba bada wannan damar ba .. "


"Sauran kwanaki  goma a daura maka aure da maryam  a lissafina gobe  ko jibi jirginka zai cale zuwa qasar  france  fatana allah ya kaika lafiya ya dawo da kai lafiya shahida ta  gama shirya komai na aure  fatan alkhairi da dawo da niyyar  angeancewa lafiya and if you do anything  stupidty I will del with you kai ma kasani ina sonka fiyye da tunaninka amman hakan baya hana idan kayi ba daidai ba naki hukuntaka tana qoqarin mikewa hisham ya shigo ya gaishe da mami cike da girmamawa sannan ya zauna kusa da ata  daya   runtse tsumammun idanunsa tun byn da mami ta soma magana "yaakayi mutumina ya karfin jikin hope you are getting better?"numfashi kawai ya sauke wanda Ke nuna masa alamun ya amsa hisham ya cigaba da magana "har yanzu sultan da fahad basu dawo da komai ba fa  Kmr ma sun dauki abun matsayin shiririta tsabgogin gabansu kawai suke."


"ina sane da komai kai kasan bana canza maganata ina jiran na dawo daga france ne suna zaune suna hira mb ya shigo haka ma yaya Ibrahim ya shigo duba jikin mr ata tare da aunty abida har da yesmin wacce ta dane jikin mr ata haka ma yammatan gidan
d'aya byn daya  suka dinga shigowa suna gaisheshi da kyar yake bude bakinsa   yana amsa musu cikin rashin sakin fuska , cikin wasu  mintuna  aka cika gaban mr ata  da kayan motsa baki , amman babu abinda yaci  illa coffee daya dinga  tsiyaya a  cup yana  kurba ahankali ahankali   shima yana  sha ne kawai saboda  sabon da yayi dashi ."


Parlour'n ya dan rage mutane  ya saura daga hisham sai ata   nuzla da diyana  har ma da mrym da nana hauwa'u suka  shigo parlour'n bakinsu  d'auke  da sallama hisham na ganin nuzla ya saki fuskar  ganin masoyi yarsa  gbdy suka hada baki wajen yi ma mr ata ya jiki  banda nuzla  Kmr koda yaushe da kyar ya amsa  masu hisham  yana kallon fuskar nuzla yayinda  nuzla taja ta tsaya daga gefe can ta jingina bayanta da bango ta rungume hannuwanta duka bisa kirjinta tare da tsura ma mr ata  fararen idanunta tana kallonsa cike da matsanancin soyayyarsa  yadda ko kallon mrym da zai aura bai yi ba  abun yayi mata dadi sosai yadda bai son mrym abun na mata dadi har yana bata kwarin gwiwa dan tun daga ranar daaka saka ranar aurenau take jin haushinta sannan take cikin damuwa mai tsanani  ."

ahankali ta bud'e bakinta tace "yaya  sannu ya jiki banza yayi mata Kmr bai ji ba nan kuwa yaji sarai hisham yayi qasa da murya  yace "ata ana maka sannu da jiki "naji !ya fad'a atakaice  dan ya fahimci wani abu a attare daita ba tun  yau ba  yana hankalce da irin kallon da take masa a duk sanda zasu hadu tun a office din aunty shahida yaso yaci ubanta allah ya taimaketa "take gabanta ya shiga fad'uwa sbd fargaba dan ganin ko kallon inda take tsaye bai ba illa kur'ban ruwan coffee  daya cigaba dayi kuma taji amsar daya bawa hisham kuma tasan sauran ma
sunji abinda ya fad'a  ."

ahankali ta juya ta nufi kofar fita cikin bacin rai sannan sauran yanuwanta suka biyo bayanta "amman ai ya kamata ka amsawa gimbiyata ya sake yin mgn can qasa"gsky hisham baka da hankali km kana bani kunya yanzu kai da gaske sonta kake "?sosai ma kuwa ina sonta sai dai ita bata sona ..""what ?" Wallahi haka ta fad'a ai naso bikin a hadashi da naka amman ya zanyi tunda tace bata só na hakura amman nasan sonta ne zai kasheni "amman shine ka kyaleta baka ci ubanta ba?
aa babu wannan ai kai ma kasan yadda soyayya take ka duba yadda baka son mrym kake son yarinyar mafarkinka "ka daina kawo wannan misalin ni bana son wannan yarinyar ita ma kuma bata sona kaga akwai matsala wajen namu hadin ko ka fahimceni ."?

"Misali ina sonta to ya zama dole dan ubanta ta soni sannan misali da'ace tana sona nima bazan dinga jin tsanarta haka ba duk da nasan nawa rashin son ne babban matsala dan ita prentending ne kawai nasan babu macen da zata kalleni tace wai bata sona dama ne kawai bata samu ba ,ya fad'a yana jan tsaki ka kira min auta  "me zata maka  ?Kai dai kira min ita kawai   yau  yarinyar nan zataci ubanta da me  tafika da zata ce  bata sonka ?shiru hisham yayi yana kallonsa a she haka ata yake sonshi jiki a sanyaye ya dauki wayarsa ya kira nana hauwa'u cikin kankanin lokaci ta bayyana a falon "yaya gani "je kizo min da nuzla yanzu yanzu kafarta kafarki "okay yaya ta juya da sauri ."su kuma suka cigaba da tautaunawa ."

Bayan mintuna goma sai gasu sun shigo nana hauwa'u ta  kama  gabanta  ta bar nuzla tsaye cike da fargaba  ta dan saci kallon hisham dake zaune taga ya sakar mata murmushi  ta kalli mr ata taga ya hade rai sai kafarsa daya yake girgizawa har  kusan mintuna  shabiyar tana tsaye sannan tace "yaya gani wai ..."da sauri ya dakata daita ta hanyar daga mata "waye wannan ?ya nuna mata hisham dake zaune "yaya hisham ".

"Very good meye a tsakaninku ?nothing ta bashi amsa atakaice ba hisham ba hatta mr ata sai daya dago tsumammun idanunshi ya tsura mata yana kallonta "kika ce nothing kenan baki san yana sonki ba ?nasani but na fad'a masa gaskiya ni bana son shi dan ..."enough ! bana  bukatar  jin  maganarki ko wani abu  kije ki fara shirin aurensa nan da kwanaki  goma  ." cikin firgici da tashin hankali ta shiga d'aga kafafunta zuwa inda yake zaune  "me yasa  yaya ?" dan Allah kayi hakuri karka min haka  wallahi ni bana son shi a matukar tsawace yace "nace karki sake fad'ar wata  magana anan , karki   sake kula kowa  acikin masu sonki shima wanda kike so ki kashe  soyayyarsa  acikin zuciyarki ki so wanda yake sonki  .."



Mmn sudais

💗💗💗💗💗💗
     MAR'ADAMS
     💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗


*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan  09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.


           Page 20

jikinta  na  wani  irin  rawa  ta k'araso ta  durkushe a gabansa har  bata  san  sanda  ta d'aura hannuwanta  duka bisa cinyoyinsa  tana  kallon  cikin   kwayar  idanunsa da  suka  rikid'e  suka  canza   kala   a wulakance  ya   zame   jikinsa  yana  mai  kawar  da   fuskarsa   gefen  hisham  dake  zaune   tmkr   mutun  mutumi  yana   kallonsu   cike  da  matsanancin  tashin   hankali   ,shi   kuwa  mr  ata  alamun  baya  son  kallon  fuskarta  ne   yasa   shi    maida  idanunshi  kan  hisham  ".



"dan  allah   dan  Allah !!  yaya  adam  kayi   hakuri    ta  kai  hanuta  tana  qoqarin   juyo  da  fuskarsa  gareta  domin  su  fuskanci  juna , zuciyarta  na  wani  irin    bugawa  da  karfin  gaske  take  kallonsa haka  ma  hisham  zuciyarsa ce take ta bugawa fiyye da   kaida   ya  soma jin  wani sauyi na   daban  a gabadaya  ilahirin   jikinsa   wanda  ke  gauraye da tsantsar   tashin  hankali,  shi  kuwa  mr  ata  mamakinta   yasa   gbdy   ya qasa   magana   duk da maganar   yake  son  yi .


Kwayar   idanunta  suka   cicciko  da  ruwan   hawaye muryarta a sarke  tace "dan   Allah  yaya   kayi   hakuri   karka  bari  wannan  auren  ya  kasance  domin   zuciyata   bazata  iya d'aukar wannan  nauyin  ba,   wata razananniyar  tsawa  ya buga  mata  wanda  ya  kamata  ace ta  tsorata   ta dawo da  hankalinta   jikinta   amman   ina  sai  ma  sake  narkewa  tayi  a wajen  zuciyarta  babu  tsoron  komai  acikinta , muryarsa  a kausashe   yace " tashi   ki   bar  nan  ki   kuma  fara  shirinki   kamar  yadda   na  fad'a  miki   oya  leave ."


"dan  Allah  ka  saurareni  yaya  "ya  girgiza  mata  kai   yana   cewa "   I don't  want  to listing anything  from   you  just  leave  now "dan   allah  yaya  adam  kayi   hakuri  ka  saurareni    akwai  maganar  da  idan  na  fad'a  maka   nasan   zaka   fahimceni "ata dan  Allah  ka  barta  ta  fad'i  abinda  ke zuciyarta    Hisham  yayi  maganar   yana  qarewa  jikin nuzla  dake  rawa  tmkr   mazari  da   kallo  , yadda  take 

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login