Showing 105001 words to 108000 words out of 168608 words

Chapter 36 - Mar'adam's Book 1 Hausa Novel Complete

kawarta  subai'a  suka  je adamawa  domin   suyi   cam for three  weeks  bayan  sunyi  sati uku  a adamawa  alokacin  mlm yahuza   yayiwa    wani  mutun magana  akayi   masu  change  of  location  ita  da kawarta   daga  adamawa   aka  dawo  dasu lagos inda  zasu  fara  bautar  qasa a   Z &A    comapany   dake  kan  titin  guness  bayan  ciku cikun  da  mlm  yahuza  yayi  masu domin  shine  ya  shiga  ya  fita  ya  kar'bo  masu   letter   suka  kai wa  nysc  aka kar'besu  a kamfanin  bayan sun dawo  lagos  suka  fara savieces  dinsu  wannan taimako da mlm yahuza yayiwa maryama  ya  wanke   zuciyar  habib  yaji ya shiga ransa har ma ya fara kiransa da  otherhaif kuma yake  girmamasa yana mai jin ba qaramin dace yaruwarsa tayi ba domin kuwa samun maza irinsa suna  da matukar wahalar samu ."

"gashi shi dai ba wani zurfi yayi  a boko ba dan karatunsa  iya  diploma  ne  amman  yana  da  hanya kuma yasan  mutane  sosai dan shugaban RRS  mai ci alokacin abokinsa ne tare sukayi karatun tun daga primary har zuwa secondary inda anan suka rabu amman har gobe suna mutunci  da abota , fara  bautar qasa yayiwa maryama dadi dan daman  zaman gidan ya isheta dan tun da suka qare karatu babu inda take zuwa bayan  islamiyya  gashi ita daman fita bai dameta ba saboda ita ba maabociya son yawo bace amman wahalar da take sha da yawon sata aiki da mutanen gidansu keyi yasa tayi maraba da da wannan fitar tata kullum fatan allah ya taimaketa tana qare bautar qasa ta samu aiki ."


Ranar  wata  asabar  tana  zaune  shiru a side dinsu  tana tunane  tunane  akan  sakina  tana matukar  qaunar sakina  aranta ta kasa jurewa   abubuwan da take mata batare da tasan laifinta  ba ,zuciyarta ta bata  shawarar taje ta tmbyeta  ko  wani laifi tayi  mata wanda yasa ta canza mata ,nan  take  ta amince da  shawarar  zuciyarta , dan hk ta mike tsam ta fito ta nufi side dinsu ta yi sallama a tsakar gida babu wanda ya amsa  mata  dan  haka  ta wuce daki  inda tafi  tunanin sakina take  mintuna sha uku da zamanta  amman  sakina  bata ko kalleta ba ."

Ahankali  maryama ta  tunkarareta  da abinda ya shiga  a tsakaninsu "haba "yar uwata  mai na yi miki ki ke fushi  dani  tsawon Lokaci  ko  magana ba kya min  mai  nayi miki  da hukuncina ya cancanci haka.?""Cewa na yi kin min wani abu?sakina  ta tambayeta tana  mai  kallo  cikin   idanuwanta  maryama ta sauke nata  idanun  ganin irin  kallon da Sakina ke mata. Ta ce"tô  Sakina tsawon  lokaci   naga  bakya min  magana, in da nayi miki laifi  ne sai ki sanar dani na nemi yafiyarki bana jin dadin yadda kike nuna ko in kula gareni  tsaki kawai sakina  taja ta fice tana magana cikin ranta wanda sam maryama  bata ji  dadin abinda tai  mata ba  "na shiga uku maryama   ta fada a ranta me  zai sa sakina ta yi min  haka  kawata kanwata kuma yaruwarta masoyiyarta?ya Allah  ka  sanyaya  zuciyar  sakina  akaina  idanunta   cike da hawaye ta baro  side dinsu ."



Ranar  wata  laraba  aunty  salma da yaranta biyu suna zaune a tsakar  gida  aunty  salma ta dubi sakina "wai  Ke  kwana  biyu  nan mai yake damunki ne  sai  ki dinga kadaita  kanki  kina wani shiru idan wani  abu   aka miki  bazaki fad'a ba  sakina tace" ko na gaya miki ba iya magance  min zakiyi ba duk da ku  ka jawo halin da muke ciki nida  yaruwata shukura ,maryama dake kokarin shigowa cikin side din nasu  ta  dan. tsaya  ta kasa kunne aranta tace "allah  sarki ashe  yaruwata  laifi akayi mata tayiwa gidan kudin  goro  kowa bata shiri  dashi."

aunty  salma tace " koma  me akayi  muku   zurfin cikinku ne ya janyo muku Ke kanki kinsani duk damuwarku  kema  kinsan zanyi qoqarin magance  muku   ita matukar  ina numfashi  acikin duniyar nan  sanar  dani  menene  aka muku  da har  yake saka ki  cikin kunci "kusan rabin yan makarantar islamiyyarmu  sun  san  yadda shukura ke son mlm yahuza  amman  kiri kiri  kuna kallo wannan banzar ta  juya abun ya koma  kanta gashi har ana batun saka  rana  aure ."


Da alamun  aunty  salma  taji dadin furucin sakina akan maryama  domin  duk irin kunci  da halin koin kula da suke ciki da sakina bata gani ba bare ta shiga cikin maganar  tayi musu sulhu "aunty salma tace" to meye  keda yaruwarki  ? maryama ta fahimci kalmar  cikin  zolaya tayi  maganar ,ai kuwa nan da nan sakina  da shukura suka bata rai cikin nuna tsantsar  tsana "wannan banzar ce yaruwarmu daace kun  koresu a gidan Kmr  yadda kika ce ai da bata yiwa  shukura  kwacen  saurayi  ba  yanzu  gashi nan muna  ji mun gani  wanda shukura take so  dole zata hakura "a'a waya  gaya maku ai  babu wani  maganar wani  hakuri  ,kuyi  hakuri tunda kun fad'a min ku bani  kwana uku zaku ga abinda zai faru."

hankalin maryama  ya tashi  kwarai da gaske har yasa  daga  nan bata  sake  sanin abinda suka cigaba da tautaunawa ba  saboda wani daci da  zuciyarta ta dauka ."jiki a matukar ta sanyaye ta dawo side dinsu "ita bata san shukura tana son mlm yahuza ba da sam  bazata  amince da soyayyarsa ba sai ma ta hadasu  amman yanzu ya zatayi ?ko da  yake ta fahimci wani sabon salon cin zarafi ne ake son bullo mata  mata  dashi  dan arabasu dan  haka zata bari adduarta tayi karfin  da bazasu samu nasara akanta ba  tun daga ranar bata sake runtsa idanuwanta ba wajen kiyamul laili  domin  kiyamullaili  tana  qarawa nauyin mizanin  bawa, tana qarawa mutun hasken  fuska  da  samun kwarjini da d'ga darajan mutun acikin mutane kariya ga dukkan sharri  tare da biyawa bawa bukata."

Duk  bayan  kwana  biyu  mlm  yahuza  yana  zuwa wajenta  Kmr yadda ta tsara  masu dan bata  son  yawon  zance ,tun bayan kwana biyu  sunyi da mlm yahuza zai  zo sai dai har  karfe  takwas na dare daya saba  zuwa   bai zo  ba amman ta rasa dalili hakan ta kasa  hakuri  ta  shirya  tsaf ta fito zuwa bangaren Ummah  ta iske  shukura  tana  zance  sai  dan kasancewar  dare  bata lura da wa take zance ba sai dai  kawai  kamshin  turarensa  yayi  mata kama dana  mlm yahuza amman  ko  kadan  bata kawo shi bane ta shiga bangaren umma tana zaune suka gaisa
Daga  nan  suka shiga hirar duniya har sanda shadaya ta buga ta mike tayi mata sallam ta  koma side dinsu  cikin  tsinkewar zuciya dan bgabanta banda luguden bugawa babu abinda yake ."

Shigowarta  kenan  daga  wani  kamfani  kai  zanenta domin  tallatawa  ,da  baba gali ta soma ci karo "yar gwal  idan kin huta ina son magana dake dam taji gabanta  ya  fadi  tun da take arayuwarta bata jin ranar da baba gali yace yana son magana makamanciyar   haka  ba  km  wai  yar gwal  yana son  magana  daita  tabbas  akwai  mahimmiyar magana , bata kawo komai aranta ba sai tunanin watakilla ko mgnr mlm yahuza ce tayi karfi tunda ya sha fad'a mata yana son manya su shiga ciki ta nufi bangarensu ta kammala komai nata  a natse ganin shima ya fita masaalaci tayi sallah har ishai sannan ta dawo parlour ta zauna zuciyarta na tunanin akan maganar da baba gali zai yi daita duk da bata san abinda zai sanar daita ba amman sai maganar ta tsaya mata arai cike sa  fargaba ."

Karfe tara daidai  umma ta aiko  a kirata  ita da aunty   nan fa   gaban  maryama   ya cigaba  da fad'uwar da yake , tare suka  fito  da aunty  alokacin shukura ta shigo daga zance tuni aunty ta wuce dan har ta kusan  isa  bakin side din  umma, haka nan ta kalli shukura dake  zaune  kusa da aunty salma dake cin abinci  atsakar gida ta sake gaishe da aunty salma ta wucesu ta shiga bangaren umma ta gaisheta cike da girmamawa  umma taji dadi sosai ta tmbyi lafiyar habib ."

shiru ne ya biyo  baya har na kusan mintuna asirin sai ga aunty salma da aunty  hassana sannan byn an gaisa umma  ta numfasa tace "Maryama wata tmby nake son nayi miki game da yaron nan dan gidan lawan yaro ?"dam  taji bugawar da qirjinta yake ya qaru , tayi shiru domin bata damar tmbyrta ta cigaba da magana "tsakanin keda shukura wa yace yana só né ?"

Maryama  tayi shiru lokacin da maganar ta doki dodon kunneta wannan  wace irin magana ce akwai abinda  umma batasani ba a tsakaninta dashi ?amman  dai koma menene  batasan abinda yasa take mata  wannan tmbyr ba, ta bude baki zata bata amsa abinda Ke tsakaninsu sai kunya ta hanata tayi kasa kawai  idanuwanta "Maryama tmbyrki nake baki ce komai ta  sake yin  shiru a karo na biyu tana son jin ba kece wacce kuka fara son juna ba har yake zuwa zance wajenki ba ? ta sake yin shiru tana son bata amsa sai dai bazata iya sanar daita ba tunda gashi ita da kanta tasani   kuma tana da masaniyar wajenta yake zuwa, ita me yasa umma zatayi mata wannan tmbyr akan abinda ta rigada tasani tunda sau tari ita ke cewa taje  idan yazo bata son fita ."


"Abinda yasa na kiraki nake tmbyrki shine dazu da yamma byn fitarki kai  zane  yan gidansu sunzo domin auren diya a gidan nan kuma sun bayyana wacce suka zo nema ni da azatona kece yahuza yake zuwa wajenki ashe yaruwarki shukura  yake so ."
ba idanuwanta  ba hatta numfashinta da kwakwa luwarta sai da suka daina aiki wani tsayawa tayi na wani lokaci kafin ta sauke naunayen ajiyar zuciya  ta juya idanuwanta kana  tashiga   tunani da kwakwa luwarta batace komai ba saboda tashin hankali daya risketa ta sunkuyar da kanta qasa kawai  tana jin damuwa mai tsanani "

"Magana nake maryama kinyi  shiru daman bake yake nema ba yauruwarki yake nema ?ta qara yin mata tmbyr bata san abinda zatace ba ganin zata batawa kanta lokaci da jama'ar dake wajen yasa ta dago kanta tace "tunda shi da kanshi ya sanar da wacce yake nema ai babu laifi umma , umma tayi shiru kawai tana dubata ina son gane abun ne domin ni a tunanina Ke din ce  yake zuwa wajen ki kawai ta dago tace "ba wajena yake zuwa ba wajenta yake zuwa tana gama fadar haka ta mike da sauri dan zamanta a waje zai yasa ta zubar da hawaye ta bayan bangarensu inda aunty Ke aiki ta labe tana kuka mara sauti dan kar wanda ya ganta ta tsaya anan ta rarrashin kanta ne dan karta dagawa  danuwanta hankali."

Sai datayi mai isarta sannan  ta fito ta shiga falo kai tsaye  ta wuce habib  dake  zaune yana  kallon ball dakinta ta shiga ta kwanta lamo akan katifa ahankali kalaman mlm yahuza daya dinga furta mata suka dinga dawo mata cikin kwakwaluwarta  da taimakonsa  gareta  hakika  bazata   ta'ba  mantawa dashi  arayuwarta ba ta  dinga  girgiza kai shikenan shima ta rasashi  ,hawaye  suka dinga zuba daga idanunta bata san tana shesheka ba sai dataji muryar  habib  yana cewa "kamar shesheka nake ji heartbeat  tayi  saurin  gyara kwanciyarta tayi shiru tare da lullube kanta tana tunani abinda ya kamata ta fad'a masa  idan ya qaraso gareta domin dai abinda yake gudar mata kenan gashi ya faru daita  ta runtse idanunta sosai alamun ta fara bacci ganin hk habib ya juya ya koma falo ."


Bangaren umma kuwa gyara zama aunty  tayi ta kallesu "hakika  bakuyi adalci ba  saboda ni nasan wannan yaron wajen maryama yake zuwa me zai sa shukura zata qaunaci wanda yake son maryama har ku iyayenta kusan hanyar da kuka bi kuka raba maryama dashi ?mgnr  tayiwa ummah dadi ko babu komai yau zata gwada kunjinta akan damuwarta
Aunty salma ta gyara zamanta itama tasoma magana Kmr tana jira "kada a kawo maganar rainin hankali acikin maganar nan kina tunanin shukura zatace tana son shi ne ?".

"to kisani diyata bazata ta'ba cewa tana son wani ba shine da kanshi yace yana sonta kuskure yayi yace yana son maryama dan kawai ya samu hanyar da zai ce yana son shukura bude kunnuwanki da kyau yahuza ya dade da soyayyar shukura acikin ranshi nauyinta kawai yake ji dan hk ya fara gwada soyayyar daga kan maryama ganin bata da wani matsayi da aji ya dawo hanyar madaidaiciya ba kuma diyata tace tana son shi ba idan kuma har abun ya dameki sai kisa diyarki ta sameshi kice ya daina son shukura ya dawo kanta."

"Uhm kawai aunty ta furta a fili  sannan a fili   tace allah kai ne allah kai ka kawo ma maryama yahuza amatsayin wanda yake sonta  byn ta rasa sauran kuma na tabbatar yahuza yana son maryama da gsky Allah kai kasan abinda akayi  aka shiga tsakaninsu ya Allah kayi mata sakayya  nasan zaka kawo mata wani wanda ya fishi   komai   "Wai me maganarki take nufi ?kina nufin an kwacewa maryama saurayi ne ko me ?"wannan ai gskyr da kowa ya rigada yasani ce maryama  yake so kuma dan ita yake zuwa gidan nan ,na rasa wannan maseefar babu damar aga maryama da cigaba duk yadda zaa yi sai anyi an rabata dashi ".

"Dakata dakata!!  su waye dasu waye idan zakiyi mgnrki Kiyi mgnrki a inda bazai zame miki damuwa ba , ina maryama take ?me ye tafi sauran mata  da idan ta samu cigaba ake rabata dashi ?ita din gwal ce ko me ? inji cewar aunty hassana "tunda yaro yace ga wacce yake so ai magana ya qare sai ayi shirin aure "a'a hasaana wannan ba magana bace  allah baya son zalinci kuma baya son wani bawan yayi ,hakika idan akayi auren nan an zalici maryama "umma ki rabu dasu hassada ke damunsu akan maryama ,amman maryama din da kuke gani tafi gwal wallahi kuma kaf zuriarku babu macen data kaita allah na tuba idan nayi alfahari  ka yafe min ba alfahari nayi ba gsky na fad'a ."da sannu  hassadar  zata cinyeku  ni natashi  allah ya bamu alkhairi  allah yayi mata zabin abinda yafi zama alkhairi arayuwarta da izinin allah maryama sai ta kawo maku wanda bazaki iya kwacewa ba tana gama fadar haka ta mike ta bar falon ."nan fa hayaniya ta kaure aunty hassana na zaginta aunty salma na qarawa ummah kuma tana basu rashin gsky ."


Aunty ta  shigo  parlour'n  tana  kuka  nan da nan hankalin habib ya tashi ta wuce shi ta nufi dakin maryama tana kwance  har lokacin tana zubar da hawaye  tana tuno daddan kalaman mlm yahuza gareta atare suka fad'a  dakin  ta qarasa ta zauna bakin gadon ta kamo hannun  maryama ta damke cikin nata jikinta  har ya  dauki  zafi  ta fashe da wani sabon kuka wanda yasa kukan maryama ya fito fili ta yunkura ta mike zaune  cikin  mawuyacin  hali tana cewa "why aunty ?me yasa kike asarar hawayenki akan dan wannan abun ? "duk fa abinda kaga  allah bai baka ba to ba rabonka bane Kiyi hakuri ki daina kuka  please cikin rawar muryar habib yace "aunty meke faruwa ,abinda kake gudu dai ne ya sake faruwa sun rabata da yaron nan yahuza yaron kirki "what !?"

"Wallahi habib sun rabata dashi wai shukura zai aura ba maryama ba amman babu komai  akwai allah  wani  irin ihu yayi yana kurma uwar ashariya  ya juya  maryama tayi saurin durowa ta rike masa hannu  ya juyo ya kalleta "ki sakar min hannu heartbeat  ba shukura ba hatta shi kansa mlm yahuza sai naci ubansa yau koni koshi girgiza masa kayi tayi "bashi da laifi nasan akwai abinda akayi masa domin da kunne naji  komai nan ta zayyana masu hirar aunty salma da yayanta akan  mlm yahuza, dan haka kasani mlm yahuza baya cikin haiyacinsa ,mlm yahuza mutumin kirki ne idan nace banji zafin rabuwa dashi ba nayi karya jikinsa a matukar sanyaye ya zame a zauna qasa ya dafe goshinsa da  hannunsa  daya  yana jin ciwon abinda ya faru" yanzu abinda shukura tayi mana kenan ya fad'a cikin jin haushin ,to ya zamuyi mu mun dogara da allah  aunty ta sake riko hannun maryamu "Allah yayi maku albarka a rayuwarku  ,allah ya baki miji na gari,  idan da rabo Allah ya juyo da hnkln yahuza  ya dawo gareki  ya kula dake ."


"Maryam tana kuka aunty tana yi tana goge mata hawaye "Kiyi  hakuri  maryama "kema aunty Kiyi hakuri  bana son ki  daga hnkln ki akan matsalar  nan ,in sha Allah nan  kusa  Allah zai bani wani "In sha Allah bazai  dade ba  Allah karka barmu da iyawarmu ka iya mana dukkanin abinda bazamu iya ba  har kusan karfe dayan dare suna tare kuma duk mgnr mlm yahuza suke aunty bata so tayi nesa da maryama  , tafi son bacci ya zo mata  tana  tare daita
don Allah ki daina damuwa kinji ' yata ki kwanta Kiyi bacci Allah yayi miki albarka yayi wa rayuwarki data ' ya'yan da zaki haifa  albarka,  In sha Allah bazaki dangwama a hk ba Allah zai saukaka mk  na yafe miki duka laifukan da kikayi min wnd na sani da wnd bn sani ba daga  hk  tayi shiru tana goge hawayen idanun maryama , amma tamkar sake kara mata su ake .

Ba  sosai  damuwa  yake  tasiri  acikin zuciyar maryama ba  bare irin wannan damuwar da idan da sabo ta  saba amman tabbas wannan damuwar ta doketa  sosai  dan duk kwanaki   bata iya bacci adduar nenan zabin allah  kawai takewa kanta zuciyarta chunkushe da bakinciki mara misaltuwa har akayi kiran sallah asuba bata runtsa ba hakan yasa ta mike da kyar ."


Mmn sudais

💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗


*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan  littafin  na kudi ne mai bukatar karantashi   byn na kammalashi zai  biya 1000 ta wannan  account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura  domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina  (Hausa bakwai ) a YouTube.


Page 21





Duk da ba wani son mlm yahuza take ba amman tunanin rabuwa dashi Kullum yana bibiyar zuciyarta dan duk

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login