Showing 105001 words to 108000 words out of 168608 words
kawarta subai'a suka je adamawa domin suyi cam for three weeks bayan sunyi sati uku a adamawa alokacin mlm yahuza yayiwa wani mutun magana akayi masu change of location ita da kawarta daga adamawa aka dawo dasu lagos inda zasu fara bautar qasa a Z &A comapany dake kan titin guness bayan ciku cikun da mlm yahuza yayi masu domin shine ya shiga ya fita ya kar'bo masu letter suka kai wa nysc aka kar'besu a kamfanin bayan sun dawo lagos suka fara savieces dinsu wannan taimako da mlm yahuza yayiwa maryama ya wanke zuciyar habib yaji ya shiga ransa har ma ya fara kiransa da otherhaif kuma yake girmamasa yana mai jin ba qaramin dace yaruwarsa tayi ba domin kuwa samun maza irinsa suna da matukar wahalar samu ."
"gashi shi dai ba wani zurfi yayi a boko ba dan karatunsa iya diploma ne amman yana da hanya kuma yasan mutane sosai dan shugaban RRS mai ci alokacin abokinsa ne tare sukayi karatun tun daga primary har zuwa secondary inda anan suka rabu amman har gobe suna mutunci da abota , fara bautar qasa yayiwa maryama dadi dan daman zaman gidan ya isheta dan tun da suka qare karatu babu inda take zuwa bayan islamiyya gashi ita daman fita bai dameta ba saboda ita ba maabociya son yawo bace amman wahalar da take sha da yawon sata aiki da mutanen gidansu keyi yasa tayi maraba da da wannan fitar tata kullum fatan allah ya taimaketa tana qare bautar qasa ta samu aiki ."
Ranar wata asabar tana zaune shiru a side dinsu tana tunane tunane akan sakina tana matukar qaunar sakina aranta ta kasa jurewa abubuwan da take mata batare da tasan laifinta ba ,zuciyarta ta bata shawarar taje ta tmbyeta ko wani laifi tayi mata wanda yasa ta canza mata ,nan take ta amince da shawarar zuciyarta , dan hk ta mike tsam ta fito ta nufi side dinsu ta yi sallama a tsakar gida babu wanda ya amsa mata dan haka ta wuce daki inda tafi tunanin sakina take mintuna sha uku da zamanta amman sakina bata ko kalleta ba ."
Ahankali maryama ta tunkarareta da abinda ya shiga a tsakaninsu "haba "yar uwata mai na yi miki ki ke fushi dani tsawon Lokaci ko magana ba kya min mai nayi miki da hukuncina ya cancanci haka.?""Cewa na yi kin min wani abu?sakina ta tambayeta tana mai kallo cikin idanuwanta maryama ta sauke nata idanun ganin irin kallon da Sakina ke mata. Ta ce"tô Sakina tsawon lokaci naga bakya min magana, in da nayi miki laifi ne sai ki sanar dani na nemi yafiyarki bana jin dadin yadda kike nuna ko in kula gareni tsaki kawai sakina taja ta fice tana magana cikin ranta wanda sam maryama bata ji dadin abinda tai mata ba "na shiga uku maryama ta fada a ranta me zai sa sakina ta yi min haka kawata kanwata kuma yaruwarta masoyiyarta?ya Allah ka sanyaya zuciyar sakina akaina idanunta cike da hawaye ta baro side dinsu ."
Ranar wata laraba aunty salma da yaranta biyu suna zaune a tsakar gida aunty salma ta dubi sakina "wai Ke kwana biyu nan mai yake damunki ne sai ki dinga kadaita kanki kina wani shiru idan wani abu aka miki bazaki fad'a ba sakina tace" ko na gaya miki ba iya magance min zakiyi ba duk da ku ka jawo halin da muke ciki nida yaruwata shukura ,maryama dake kokarin shigowa cikin side din nasu ta dan. tsaya ta kasa kunne aranta tace "allah sarki ashe yaruwata laifi akayi mata tayiwa gidan kudin goro kowa bata shiri dashi."
aunty salma tace " koma me akayi muku zurfin cikinku ne ya janyo muku Ke kanki kinsani duk damuwarku kema kinsan zanyi qoqarin magance muku ita matukar ina numfashi acikin duniyar nan sanar dani menene aka muku da har yake saka ki cikin kunci "kusan rabin yan makarantar islamiyyarmu sun san yadda shukura ke son mlm yahuza amman kiri kiri kuna kallo wannan banzar ta juya abun ya koma kanta gashi har ana batun saka rana aure ."
Da alamun aunty salma taji dadin furucin sakina akan maryama domin duk irin kunci da halin koin kula da suke ciki da sakina bata gani ba bare ta shiga cikin maganar tayi musu sulhu "aunty salma tace" to meye keda yaruwarki ? maryama ta fahimci kalmar cikin zolaya tayi maganar ,ai kuwa nan da nan sakina da shukura suka bata rai cikin nuna tsantsar tsana "wannan banzar ce yaruwarmu daace kun koresu a gidan Kmr yadda kika ce ai da bata yiwa shukura kwacen saurayi ba yanzu gashi nan muna ji mun gani wanda shukura take so dole zata hakura "a'a waya gaya maku ai babu wani maganar wani hakuri ,kuyi hakuri tunda kun fad'a min ku bani kwana uku zaku ga abinda zai faru."
hankalin maryama ya tashi kwarai da gaske har yasa daga nan bata sake sanin abinda suka cigaba da tautaunawa ba saboda wani daci da zuciyarta ta dauka ."jiki a matukar ta sanyaye ta dawo side dinsu "ita bata san shukura tana son mlm yahuza ba da sam bazata amince da soyayyarsa ba sai ma ta hadasu amman yanzu ya zatayi ?ko da yake ta fahimci wani sabon salon cin zarafi ne ake son bullo mata mata dashi dan arabasu dan haka zata bari adduarta tayi karfin da bazasu samu nasara akanta ba tun daga ranar bata sake runtsa idanuwanta ba wajen kiyamul laili domin kiyamullaili tana qarawa nauyin mizanin bawa, tana qarawa mutun hasken fuska da samun kwarjini da d'ga darajan mutun acikin mutane kariya ga dukkan sharri tare da biyawa bawa bukata."
Duk bayan kwana biyu mlm yahuza yana zuwa wajenta Kmr yadda ta tsara masu dan bata son yawon zance ,tun bayan kwana biyu sunyi da mlm yahuza zai zo sai dai har karfe takwas na dare daya saba zuwa bai zo ba amman ta rasa dalili hakan ta kasa hakuri ta shirya tsaf ta fito zuwa bangaren Ummah ta iske shukura tana zance sai dan kasancewar dare bata lura da wa take zance ba sai dai kawai kamshin turarensa yayi mata kama dana mlm yahuza amman ko kadan bata kawo shi bane ta shiga bangaren umma tana zaune suka gaisa
Daga nan suka shiga hirar duniya har sanda shadaya ta buga ta mike tayi mata sallam ta koma side dinsu cikin tsinkewar zuciya dan bgabanta banda luguden bugawa babu abinda yake ."
Shigowarta kenan daga wani kamfani kai zanenta domin tallatawa ,da baba gali ta soma ci karo "yar gwal idan kin huta ina son magana dake dam taji gabanta ya fadi tun da take arayuwarta bata jin ranar da baba gali yace yana son magana makamanciyar haka ba km wai yar gwal yana son magana daita tabbas akwai mahimmiyar magana , bata kawo komai aranta ba sai tunanin watakilla ko mgnr mlm yahuza ce tayi karfi tunda ya sha fad'a mata yana son manya su shiga ciki ta nufi bangarensu ta kammala komai nata a natse ganin shima ya fita masaalaci tayi sallah har ishai sannan ta dawo parlour ta zauna zuciyarta na tunanin akan maganar da baba gali zai yi daita duk da bata san abinda zai sanar daita ba amman sai maganar ta tsaya mata arai cike sa fargaba ."
Karfe tara daidai umma ta aiko a kirata ita da aunty nan fa gaban maryama ya cigaba da fad'uwar da yake , tare suka fito da aunty alokacin shukura ta shigo daga zance tuni aunty ta wuce dan har ta kusan isa bakin side din umma, haka nan ta kalli shukura dake zaune kusa da aunty salma dake cin abinci atsakar gida ta sake gaishe da aunty salma ta wucesu ta shiga bangaren umma ta gaisheta cike da girmamawa umma taji dadi sosai ta tmbyi lafiyar habib ."
shiru ne ya biyo baya har na kusan mintuna asirin sai ga aunty salma da aunty hassana sannan byn an gaisa umma ta numfasa tace "Maryama wata tmby nake son nayi miki game da yaron nan dan gidan lawan yaro ?"dam taji bugawar da qirjinta yake ya qaru , tayi shiru domin bata damar tmbyrta ta cigaba da magana "tsakanin keda shukura wa yace yana só né ?"
Maryama tayi shiru lokacin da maganar ta doki dodon kunneta wannan wace irin magana ce akwai abinda umma batasani ba a tsakaninta dashi ?amman dai koma menene batasan abinda yasa take mata wannan tmbyr ba, ta bude baki zata bata amsa abinda Ke tsakaninsu sai kunya ta hanata tayi kasa kawai idanuwanta "Maryama tmbyrki nake baki ce komai ta sake yin shiru a karo na biyu tana son jin ba kece wacce kuka fara son juna ba har yake zuwa zance wajenki ba ? ta sake yin shiru tana son bata amsa sai dai bazata iya sanar daita ba tunda gashi ita da kanta tasani kuma tana da masaniyar wajenta yake zuwa, ita me yasa umma zatayi mata wannan tmbyr akan abinda ta rigada tasani tunda sau tari ita ke cewa taje idan yazo bata son fita ."
"Abinda yasa na kiraki nake tmbyrki shine dazu da yamma byn fitarki kai zane yan gidansu sunzo domin auren diya a gidan nan kuma sun bayyana wacce suka zo nema ni da azatona kece yahuza yake zuwa wajenki ashe yaruwarki shukura yake so ."
ba idanuwanta ba hatta numfashinta da kwakwa luwarta sai da suka daina aiki wani tsayawa tayi na wani lokaci kafin ta sauke naunayen ajiyar zuciya ta juya idanuwanta kana tashiga tunani da kwakwa luwarta batace komai ba saboda tashin hankali daya risketa ta sunkuyar da kanta qasa kawai tana jin damuwa mai tsanani "
"Magana nake maryama kinyi shiru daman bake yake nema ba yauruwarki yake nema ?ta qara yin mata tmbyr bata san abinda zatace ba ganin zata batawa kanta lokaci da jama'ar dake wajen yasa ta dago kanta tace "tunda shi da kanshi ya sanar da wacce yake nema ai babu laifi umma , umma tayi shiru kawai tana dubata ina son gane abun ne domin ni a tunanina Ke din ce yake zuwa wajen ki kawai ta dago tace "ba wajena yake zuwa ba wajenta yake zuwa tana gama fadar haka ta mike da sauri dan zamanta a waje zai yasa ta zubar da hawaye ta bayan bangarensu inda aunty Ke aiki ta labe tana kuka mara sauti dan kar wanda ya ganta ta tsaya anan ta rarrashin kanta ne dan karta dagawa danuwanta hankali."
Sai datayi mai isarta sannan ta fito ta shiga falo kai tsaye ta wuce habib dake zaune yana kallon ball dakinta ta shiga ta kwanta lamo akan katifa ahankali kalaman mlm yahuza daya dinga furta mata suka dinga dawo mata cikin kwakwaluwarta da taimakonsa gareta hakika bazata ta'ba mantawa dashi arayuwarta ba ta dinga girgiza kai shikenan shima ta rasashi ,hawaye suka dinga zuba daga idanunta bata san tana shesheka ba sai dataji muryar habib yana cewa "kamar shesheka nake ji heartbeat tayi saurin gyara kwanciyarta tayi shiru tare da lullube kanta tana tunani abinda ya kamata ta fad'a masa idan ya qaraso gareta domin dai abinda yake gudar mata kenan gashi ya faru daita ta runtse idanunta sosai alamun ta fara bacci ganin hk habib ya juya ya koma falo ."
Bangaren umma kuwa gyara zama aunty tayi ta kallesu "hakika bakuyi adalci ba saboda ni nasan wannan yaron wajen maryama yake zuwa me zai sa shukura zata qaunaci wanda yake son maryama har ku iyayenta kusan hanyar da kuka bi kuka raba maryama dashi ?mgnr tayiwa ummah dadi ko babu komai yau zata gwada kunjinta akan damuwarta
Aunty salma ta gyara zamanta itama tasoma magana Kmr tana jira "kada a kawo maganar rainin hankali acikin maganar nan kina tunanin shukura zatace tana son shi ne ?".
"to kisani diyata bazata ta'ba cewa tana son wani ba shine da kanshi yace yana sonta kuskure yayi yace yana son maryama dan kawai ya samu hanyar da zai ce yana son shukura bude kunnuwanki da kyau yahuza ya dade da soyayyar shukura acikin ranshi nauyinta kawai yake ji dan hk ya fara gwada soyayyar daga kan maryama ganin bata da wani matsayi da aji ya dawo hanyar madaidaiciya ba kuma diyata tace tana son shi ba idan kuma har abun ya dameki sai kisa diyarki ta sameshi kice ya daina son shukura ya dawo kanta."
"Uhm kawai aunty ta furta a fili sannan a fili tace allah kai ne allah kai ka kawo ma maryama yahuza amatsayin wanda yake sonta byn ta rasa sauran kuma na tabbatar yahuza yana son maryama da gsky Allah kai kasan abinda akayi aka shiga tsakaninsu ya Allah kayi mata sakayya nasan zaka kawo mata wani wanda ya fishi komai "Wai me maganarki take nufi ?kina nufin an kwacewa maryama saurayi ne ko me ?"wannan ai gskyr da kowa ya rigada yasani ce maryama yake so kuma dan ita yake zuwa gidan nan ,na rasa wannan maseefar babu damar aga maryama da cigaba duk yadda zaa yi sai anyi an rabata dashi ".
"Dakata dakata!! su waye dasu waye idan zakiyi mgnrki Kiyi mgnrki a inda bazai zame miki damuwa ba , ina maryama take ?me ye tafi sauran mata da idan ta samu cigaba ake rabata dashi ?ita din gwal ce ko me ? inji cewar aunty hassana "tunda yaro yace ga wacce yake so ai magana ya qare sai ayi shirin aure "a'a hasaana wannan ba magana bace allah baya son zalinci kuma baya son wani bawan yayi ,hakika idan akayi auren nan an zalici maryama "umma ki rabu dasu hassada ke damunsu akan maryama ,amman maryama din da kuke gani tafi gwal wallahi kuma kaf zuriarku babu macen data kaita allah na tuba idan nayi alfahari ka yafe min ba alfahari nayi ba gsky na fad'a ."da sannu hassadar zata cinyeku ni natashi allah ya bamu alkhairi allah yayi mata zabin abinda yafi zama alkhairi arayuwarta da izinin allah maryama sai ta kawo maku wanda bazaki iya kwacewa ba tana gama fadar haka ta mike ta bar falon ."nan fa hayaniya ta kaure aunty hassana na zaginta aunty salma na qarawa ummah kuma tana basu rashin gsky ."
Aunty ta shigo parlour'n tana kuka nan da nan hankalin habib ya tashi ta wuce shi ta nufi dakin maryama tana kwance har lokacin tana zubar da hawaye tana tuno daddan kalaman mlm yahuza gareta atare suka fad'a dakin ta qarasa ta zauna bakin gadon ta kamo hannun maryama ta damke cikin nata jikinta har ya dauki zafi ta fashe da wani sabon kuka wanda yasa kukan maryama ya fito fili ta yunkura ta mike zaune cikin mawuyacin hali tana cewa "why aunty ?me yasa kike asarar hawayenki akan dan wannan abun ? "duk fa abinda kaga allah bai baka ba to ba rabonka bane Kiyi hakuri ki daina kuka please cikin rawar muryar habib yace "aunty meke faruwa ,abinda kake gudu dai ne ya sake faruwa sun rabata da yaron nan yahuza yaron kirki "what !?"
"Wallahi habib sun rabata dashi wai shukura zai aura ba maryama ba amman babu komai akwai allah wani irin ihu yayi yana kurma uwar ashariya ya juya maryama tayi saurin durowa ta rike masa hannu ya juyo ya kalleta "ki sakar min hannu heartbeat ba shukura ba hatta shi kansa mlm yahuza sai naci ubansa yau koni koshi girgiza masa kayi tayi "bashi da laifi nasan akwai abinda akayi masa domin da kunne naji komai nan ta zayyana masu hirar aunty salma da yayanta akan mlm yahuza, dan haka kasani mlm yahuza baya cikin haiyacinsa ,mlm yahuza mutumin kirki ne idan nace banji zafin rabuwa dashi ba nayi karya jikinsa a matukar sanyaye ya zame a zauna qasa ya dafe goshinsa da hannunsa daya yana jin ciwon abinda ya faru" yanzu abinda shukura tayi mana kenan ya fad'a cikin jin haushin ,to ya zamuyi mu mun dogara da allah aunty ta sake riko hannun maryamu "Allah yayi maku albarka a rayuwarku ,allah ya baki miji na gari, idan da rabo Allah ya juyo da hnkln yahuza ya dawo gareki ya kula dake ."
"Maryam tana kuka aunty tana yi tana goge mata hawaye "Kiyi hakuri maryama "kema aunty Kiyi hakuri bana son ki daga hnkln ki akan matsalar nan ,in sha Allah nan kusa Allah zai bani wani "In sha Allah bazai dade ba Allah karka barmu da iyawarmu ka iya mana dukkanin abinda bazamu iya ba har kusan karfe dayan dare suna tare kuma duk mgnr mlm yahuza suke aunty bata so tayi nesa da maryama , tafi son bacci ya zo mata tana tare daita
don Allah ki daina damuwa kinji ' yata ki kwanta Kiyi bacci Allah yayi miki albarka yayi wa rayuwarki data ' ya'yan da zaki haifa albarka, In sha Allah bazaki dangwama a hk ba Allah zai saukaka mk na yafe miki duka laifukan da kikayi min wnd na sani da wnd bn sani ba daga hk tayi shiru tana goge hawayen idanun maryama , amma tamkar sake kara mata su ake .
Ba sosai damuwa yake tasiri acikin zuciyar maryama ba bare irin wannan damuwar da idan da sabo ta saba amman tabbas wannan damuwar ta doketa sosai dan duk kwanaki bata iya bacci adduar nenan zabin allah kawai takewa kanta zuciyarta chunkushe da bakinciki mara misaltuwa har akayi kiran sallah asuba bata runtsa ba hakan yasa ta mike da kyar ."
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 21
Duk da ba wani son mlm yahuza take ba amman tunanin rabuwa dashi Kullum yana bibiyar zuciyarta dan duk