Showing 45001 words to 48000 words out of 168608 words

Chapter 16 - Mar'adam's Book 1 Hausa Novel Complete

.

damuwarta  daman yayi   aure  tana  son  taga aurensa  taga  ya'yansa  kamar  yadda  taga na sauran  yaranta   amman  duk  da  haka  bazata sakar  masa fuska  ba dan tasan halinsa kamar yunwar cikinta canzawarsa  bai da wuya  ya  d'auki  mintuna masu tsawo  agabanta bata  daga  Kai ta  kallesa ba sai ma  ta mike zata  bar masa  d'akin , ya mike da sauri  jikinsa na kyarma  ya  tareta  dan sosai ya hango  damuwa qarara akan  fuskarta  ya sake kamo hannuwanta  duka cikin nashi  , ta  fizge  a fusace tana watsa masa harara   "sweetheart  kiyi hakuri  dan girman Allah  wallahi  zan  aureta  trust Adamcy  zai  aureta tunda  yace  zaiyi wallahi wallahi zan aureta Koda kuwa  zan rasa rayuwata....."

hannunta d'aya  tasa ta zare  hannunta daga cikin  nashi   ta tsura masa  idanunta  "wallahi  ban  san  Inda ka d'auko halinka  ba ,  sam mahaifinka   ba haka yake  ba  mutumin kirki  ne, mahaifinka baya  uhm  baya  uhm bare miskilanci ,  kullum cikin neman   yadda  zai kyautata  mana daku ya'yansa da  'yan'uwansa yake ,  a kullum mahaifinku  so  yake   ku  zama na gari a rayuwa  sannan  masu  jin  kan iyaye  da tausayi  Allah ya  duba  bayan mahaifinku  cikin kaf  ya'yan  mahaifinka   Kai ne  kawai  ka  fita dabam acikinsu  da wasu halaiya Kai ma  Kuma wannan  halin miskilancin da zafin zuciyar  ne  illarka tun kafin ya  rasu ya fad'a  yace bashi  ka d'auko ba .bari na  fad'a maka gsky  wannan halin naka sam ba  nashi  bane  Kai ka san  Inda ka samo  abunka dan shi ba haka yake yi  ba,  dan ta mahaifinka    duniya  bazai  tashi ba  ,ga rikon addinin  ga  tsananin zumunci da sanyi hali ."

ga lokaci   yazo daya kamata  ka tattara biyayyar  Uba  da  uwa ka had'a   kayi  min amman kullum cikin musguna min  kake akan zance aure  auren da kai ne kaji dadinsa ,  wallahi duk macen  data  samu  miji   irin mai  halin mahaifinka  ta gama dace  a duniya da lahira ni kaina  kullum kukan da nake  yi  kenan mahaifinka  ya bauta mana  ya sangartani   sannan ya bautawa  zumunci  Allah   ya  jikansa yasa aljanna ce makomarsa  ka canja  idan  zaka  canza tana gama  fad'ar  haka ta  fita ta barshi cike da zafin zuciya."

Jiki  a  sanyaye  ya bar d'akin  zuwa nashi  yana shiga   d'akinsa  ya shiga zariya   kwalkwaluwarsa ta  shiga tunani , sai dai  Kansa ya  toshe  ya  cunkushe guri d'aya  ya kasa tunanin  komai ya  zauna a bakin gado ya  had'e  hannunwansa duka  a  ha'barsa  yana  tunanin  can  byn wasu mintuna   ya  mike ya koma  kan  bedside ya zauna  yayi shiru yana kallon  d'akin  ,sake  mikewa  yayi  ya  d'aura Kashi  akan  katifa  yana Jin   quna a ransa.

zuciyarsa  na  dokawa  da matsanacin karfin  gaske ya  tashi ya nufi falonsa ya  bud'e  fridge  ya d'auki kwalin   stute superior cranberry   me sanyi ya d'auki  glass  cup ya d'aura  drink akan  center  table  ya  juya jiki a mace ya  koma  zuwa  d'akinsa ya  d'auko kwalin sigari  rotimax   ya  dawo    ya    koma  kan  kujera ya zauna  ya  tsiyaya ruwan lemun   ya d'aura kafafuwansa  akan table tare  da hard'esu guri d'aya  ya Kai  Karan sigari bakinsa  ya  kunna ya fara  zuka a hankali yana fitar  da  hayaki "yaushe rabonsa da sha ? sam bazai tuna yaushe rabonsa dasha ba  cike da izza itama sigarin yake zuka idan ba  an fad'a  maka ba bazaka  ta'ba  sanin  shi din mashayin    shigari  bane koda yake  baya sha  sai idan ya tsinci Kansa cikin ' bacin   rai mai tsanani  " .

yayi  shiru  yana zuka sigari  yana  tunani   mahaifinsa   yasan  da yana raye duk runtsi  da hkn  bata faru  dashi ba , shiyasa yake son mahaifinsa  Sosai wasu hawaye  masu zafi suka zubo  masa  wanda  rabonsa  daya zubar da hawaye  har  ya manta a tsawon rayuwarsa amman  yau  ya tuna qalbinsa masoyinsa  , ana  cewa mutun  yafi  son mahaifiyarsa  akan mahaifinsa  shi  dai sai dai
sonsu  yazo d'aya  a ransa , yasan soyayyarsu suyi  kanka  da juna  ,mahaifinsa ya  soshi  har  cikin  ransa  idan  yana  cikin damuwa  sai ya  fishi shiga  damuwa ,   haka idan yana cikin farinciki  ,daf  da zai  rasu  da zarar ya kyalesa sai  ya  fashe  da kuka alokacin  hjy zulaiheart  ke tmbyrsa  dalilin  kuka  sai  yace  "ba kowa nake wa kuka  ba  sai  Adam ,Ina jin  tausayin  rayuwar Adam  bashi da  dan'uwa kamar sauran mutane naso sun kasance su biyu ya samu abokin shawara  "a  she tabbas shi  din  abun  tausayi ne bai  ta'ba  sani ba sai a  tsakanin   wannan lokacin da abubuwa  suka  kwa'be masa  yan'uwansa mata sun had'e kai da mahaifiyarsa yasan da yana da dan'uwa nmj zai iya bin bayansa Koda kuwa zaa fi  karfinsa  ne hawaye ke gangaro  masa  kamar  karamin yaro  yana  cigaba da  busawa  cikinsa hayaki  ."

ranar  a zaune ya kwana cikin   tsananin   tashin  hankali  Kash da Kashi  damuwar auren dole da za'a masa da  tunanin  Nurul qalbinsa   dan   da  zarar  ya  runtse  idanuwanshi dan bacci  sai  yaga hoton princess dinsa  tana  gargadinsa  akan  auren da zai yi  tana gudu tana binsa  tana furta kar yayi aure ya  barta  .tsawon sati  guda  tunda daya amince  da  batun auren mryam  bai sake zuwa Inda  mami   take  ba yana  d'akinsa  yaki barin ya  had'u  da kowa   dan gbdy  fita  ya fita ransa gbdy  soyayyar princess ya  dawo  masa sabo fil  ganin  tunanin  bazai bar kanshi  ba yasashi  mikewa daga kwance da yake  tare  da  zura  takalmi  silifas   ya  fito ya  shiga d'akin  zanensa ya tsaya a gaban hotonta  shiru yana  kallonta kmr yayi mata  mgn  ta amsa fuskarta  d'auke da murmushin  da shine ya zanata  ."

Hannu  ya  kai  ya  ja hoton  a zuciye   ya  yaga  yana  furzar da iska mai zafi daga  bakinsa"A ina kike  tsawon shekaru  ?"a Ina  zan  ganki ?"kin hanani  ganinki,kin hanani sukuni   daga yau kin zamo tarihi  gareni  bazan sake damuwa  dake ba ,bazan sake tunaninki ba zan manta dake arayuwata ,zan cire soyayyarki a zuciyata tunda baki da imani baki da tausayi ya fad'a yana wani irin ihu tare da daga hannuwansa duka sama "haaaaaaaa!!!

  "Hauka  yake  sosai yana  wargaza  komai  dake  cikin  d'akin tare da cigaba da yaga hotunan zanenta  yana  filinging  dasu  har  da  system  dinsa da tsarkar wuyansa wanda zanen hotonta ne aciki , gbdy  ya  hargitsa d'akin  yana  watsi  da komai   har  sanda  mahaifiyarsa  ta shigo  hannunta  rike  da cup wanda  yake d'auke  da ruwan coffee,  bedroom dinsa  ta shiga bata gansa ba dan ita kanta ta kasa jurewa rashinsa na tsawon   kwanaki , ganin baya ciki ta fito har zata fita   ta jiyo sautinsa  a hargitse dan haka ta shigo d'akin ."

ta tsay a bayansa  ta cigaba da kallonsa cikin tsananin tashin hankali mara misaltuwa  bai sani ba  yayi  zurfi  cikin tsananin  damuwa  cikin haka  ya  sake d'aukar hoton  zanen princess  yay  sama dashi sai akan fuskar hjy zulaiheart ta runtse   idanunta da sauri   jikinta na  rawa kamar   ance  ya juyo  ya ganta  tsaye  tana kallonsa  cikin tsananin tashin  hankali  sanye da doguwar  rigar shadda  milk  colour mai  dogon hannu    kyam   idanunta a  kanshi  ta kasa daukewa  ."

cikin  sauri  dunkule hannunsa ya naushi iska tare da durkushewa   kasa  ya  soma tattara kayan  daya  hargitsa yana  cewa "so..sorry  sweetheart am really  sorry    cikin  in Ina, numfashi  ta sauke da ajiyar  zuciya  sannan ta zauna  a  bakin  gado batare  da  ta ajiye  cup din hannunta ba sai dai har lokacin idanunta na Kansa tana jin ciwo da zafin halin da yake ciki   ,kusan minti biyar tana zaune tana kallonsa yana faman tattara d'akin yana mata  sannu  sannan ta fara magana a tsanake  ." kayi hakuri   Adamcy  karka  damu  da  wannan"

  ya  k'arasa  kwashe  kayan  da  yayi waste dasu  zuciyarsa  na zafi  da quna  "kana jina  Adamcy   ita  rayuwa  babu  takurawa  idan baka sameta  anan ba wata  Killa  zaka sameta a aljanna  ,yakamata  ka gane   hakan , karka  shiga rud'ani  idan an  fad'a maka  gasky  illa  ka dinga  yarda   dashi , komai na duniya  babu  sauki  kmr yadda  ka d'aukeshi sai   an   jajirce  be a man Adamcy  karka lalata rayuwarka  akan yarinyar  mafarkinka ."

"kamar  yadda  na  sha fad'a  maka ba kowani mafarki  ke  zama gaskiya ba , ta mike a hankali   ta k'araso  gurinsa ta riko hannunsa  tayi  taku  biyu ta  zaunar dashi akan kujera  kwaya d'aya  dake d'akin , madadin ta bashi coffee  din hannunta sai  ta  fita  gabanta na dokawa da matsanacin karfi dan nan duniya idan akwai abinda ta tsana to bai wuce  damuwar tilon d'anta ba , sam  bata son ganinsa  cikin damuwa ko  wannan auren ma zata yi masa ne dan dole  saboda tasan  muddin batayi masa ba zai iya kare rayuwarsa haka  batare da yayi ba  ."

ko  cikakken minti  biyar  batayi ba ta  dawo  da gorar   ruwa  mai  sanyi  ta mika  masa , babu  mutsu ya kar'ba  ya  kafa a bakinsa bai  cire ba sai daya shanye  tasssss sannan ajiye  yana sauke numfashi taja hannunsa zuwa bedroom dinsa yana biye daita  yana zance  zuci .ya yarda  tabbas  mahaifiyarsa na sonshi kuma gsky take fad'a masa akan yarinyar  mafarkinsa  sai dai ya rasa dalilin da  har wannan lokacin ya kasa yarda iya mafarki  ne  kawai  soyayyarsa  zata tsaya ..."

Tana shiga d'akinsa ta  zauna akan gado  ya kwanta  ya  d'aura kanshi akan   cinyarta  yana mai Jin   damuwarsa tana raguwa ,  a hankali ta Kai hannunta  saman  sumar kanshi ta fara  shafawa   tana mai sake jin  tsananin  son  d'anta  Ina ma  zata ga wannan yarinyar a zahiri da babu abinda  zai  hana bata  mallaka masa  ita  ta kowani  hali  ba ."
ta  dade  zaune har bacci yayi  awon gaba dashi Sannan ta d'auke kanshi ta  maida kan pillow ta lullu'be  masa rabin jiki ta sauko  ta  qara  masa karfin  ac ta kashe masa wuta   ta  duka tayi  kissing  din foring head dinsa tana sake shafa  sumarsa sannan ta  nufi  kofar fita  tana  rufo  masa kofar ."

  Koda ta koma d'akinta  kasa  runtsawa tayi   tana tsaye akan ka'fafunta tana Kai wa Allah  kukanta akan lamarin  tilon d'anta  sai da  tayi  sallah asuba sannan  ta d'an  kwanta Shima  bata  wani dade ba  ta farka ta  shiga wanka ta fito  ta shirya cikin  doguwar  riga   ta sanya  awarwaro da zobin   ziniri ta feshe ilahirin jikinta da turaren humura  mai sanyi kamshi hjy zulaiheart  kenna  Allah yayita  da son kwaliyya da son kamshi  tun tana matashiyarta  har zuwa wannan lokacin da tsufa yazo mata  ta  fito zuwa  babban  parlour'nta  tare da  danna bell din bangaren   masu aiki kafin  kace me  gbdy sun  hallara   sun   zube  a gabanta  suna gaisheta cike da girmamawa. ta  dubesu  tare da amsawa cikin tsananin farinciki dan tana da sakewa da masu aikinta bata zalintarsu sannan bata son su zalinceta yadda take jin dadin zama dasu haka suma suke yabonta da yi mata fatan alkhairi a rayuwarta .

Fuskarta a sake ta bawa 'yan aikinta  umarni abinda  take bukata su dafa a ranar wanda zai zamo  na sadaka ne  kasancewarsa juma'a  "yau  za'a yi  abincin sadakan   da aka saba yi amman ina son  a qara  hannu  sannan a had'a da  wake  da shinkafa Ina son a rabawa  yara kanana  suka  amsa  da "to"  sannan kowace ta soma k'okarin  mikewa "ke tabawa ..." wacce aka kira da tabawa ta tsaya sauran  suka kama gabansu dan fara aiwatar da aiki "ki shirya breakfast  wa sauran jamar gida idan kin gama ki hanzarta sanar dani  ."

"shikenan hajiya itama ta fad'a  tare da juyawa da sauri ." Hjy zulaiheart tana zaune mrym da nana hauwa'u suka  shigo  duk suka zauna suka sanyata a tsakiya  kowacce hannunta empty   babu Komai kamar Koda yaushe  sun baro wayoyinsu    na  gado  a d'akinsu  d'aya byn daya suka  gaisheta   ta amsa cike da sakin fuska a fili  tace   "yau  dai babu danne danne waya ko Kuma an  gaji  da rike wayar ne ?
sukayi murmushi  nana hauwa'u tace " ai tun wuri nayiwa marsi kashedi muddin yaya adam zata aura ta saukakawa kanta akan shiga yanar gizo "wannan haka ne domin zai iya kawo rashin jituwa a tsakaninsu abinda bazan so  faruwarsa ba kenan  nafi bukatarta zaman lfy atsakaninsu. 

ta Kalli bangaren da  nana hauwa'u take zaune  tace " ya batun shari'a da ake da yarinyar da ake zargi ta kashe mubina ne har yanzu na kasa fahimtar gskyr magana gashi Adamcy nata k'okarin shiga cikin maganar  uncle jay ya hana ?"ai gsky gara da  uncle jay ya hana  wani shari'a za'a yi mami  Abar ko waye da Allah kawai mubina dai ta rigada ta mutu bazata dawo ba komai za'ayi ,haka Allah ya qaddaro mata nata mutuwar zata  rataya a wuyan wani inshallahu ruhinta na aljanna suka had'a baki gurin cewa" Ameen "

" mrym tashi ki shiga  ki d'auko min wayata a daki na kira naji yadda ake ciki  ta  mike  tsam ta shiga cikin  bedroom din hajiya zulaiheart ta iske wayar akan katifarta ta d'auka tana duba fuskar wayar nan take gabanta yayi wani mummunar fad'uwa  sakamakon idanunta daya sauka akan hoton ATA  tayi shiru tana kallonsa cikin suit bakake  idanunshi manne da farin  glass yayinda  fuskarsa ke  d'auke da murmushin gefen baki wanda bai gama bayyana ba hakan km qara masa kyau  yake , ta lumshe idanunta tana Jin wani iri a gbdy ilahirin jikinta ,ada sam bata jinsa aranta amman  tun sanda  yasa  akayi kiranta akan batun soyayyarsa ta soma Jin wani Abu akansa komai nashi mai kyau tamkar shi ya hallici kansa ."

jiki a sanyaye ta Kai mata wayar  ta amsa tana kokarin neman layin uncle jay byn sun gaisa take tmbyrsa halin da'ake ciki "mgn dai daya ce nace  abarwa Allah abar ruhin diyata ya samu salama  ".
"uncle jay taya zaka fadi haka  byn kasan zuciyar  sha'awanatu  bazataji dadi ba   ? "nasani   amman  yarinyar nan da ake tuhunma  ba itace tayi kisan ba , tabbas makashin mutun d'aya ne da wanda ya kashe mubina da wanda ya kashe sadear mutun d'aya ne  amman ba wannan yarinyar bace, ita dai ta taka tsawun barawo ne gbdy bincike ya nuna makashin da hannun hagu yayi kisan  ita  Kuma hadiza  hannun dama take amfani dashi  sam gbdy babu alamun sheidar hannunta  ,yanzu  haka an gama duk wani bincike  ranar monday kotu zata wanke  yarinyar Allah dai ya jikan  mubina yasa ta huta  "Ameen Hjy zulaiheart ta furta a fili tana mai tausaya masa "ko me suka yiwa wannan makashi da yake musu kisan gilla?   "Allah masani  "sun dan jima suna waya sannan sukayi sallama .

"Maryam ...!" mami  ta kira sunanta gbdy ta tattara duk wani attention dinta zuwa gareta tana kallonta "Ina saka rai zuwa  karshen satin  nan za'a yi mgnr bikinku  da  Adamcy  " gabanta ne ya sake fad'uwa kmr zai fasa qirjinta yayo  waje "ya kamata ki sake kwarewa agurin girki da sauran abubuwan da yake da bukata  dan haka daga yau kice zaki cigaba da kulawa da komai na bangaren abincinsa  kinji ko ".
ta gyada mata Kai  kawai tare da amsawa da "to !" hawaye na ciccikowa acikin kwarnin  idanunta tayi saurin dennewa  ta rasa dalilin da take tsananin Jin  tsoronsa da tsoro  aurensa."

"  ki  samu natsuwar zuciya ki tashi kije yanzu ki tmbayesa abinda yake bukatar ci a hankali ta mike jikinta na rawa kamar mazari  ta nufi part dinsa
akan hanyarta ta tsaya tana  daidaita natsuwarta sannan ta k'arasa kofar shiga falonsa tayi sallama ba'a amsa ba har ta juya taji sautin muryarsa yana cewa ",waye ne ? ta juyo da sauri "ni ...nice ta fad'a da sauri jikinta da bakinta na rawa "ke wa kenan ? ya sake tmby tayi shiru jikinta na cigaba da rawa hawaye na sake cikowa a idanunta  ta rasa dalilin  hawayen  nata  Jin shiru yasa ya taso da kyar yana mika  daga shi sai gajeren wando  army  green  iya cinyarsa da farar singlet wanda suka bayyana  surar  jikinsa a fili ake iya ganin  kwantaccen sumar dake kwance  a cinyarsa  da  qirjinsa haka kan nipples dinsa  sai farin silifas dake sanye da kafafunsa da farin agogo da alamun aiki yake ."

A tsaye ya ganta a bakin kofar gbdy bata cikin  haiyacinta a hankali ta d'ago ta  kare masa kallo saboda kusancin da suka samu muryarsa a kasalance yace  "ke lafiyarki  tsayuwar me kike yi anan  ya fad'a fuskarsa a murtuke"kayi hakuri please mami  ce tace nazo na tambayeka abinda zaka ci a girka maka "  ya tsuru mata Ido  a zahiri yake iya hango yadda qirjinta ke  bugawa wani dogon tsaki yaja a fili ya juya ya koma ciki ya barta tsaye . juyawa tayi tana daga kafafuwanta da kyar ta dawo parlour'n ta tsaya hjy zulaiheart ta dubeta "yaakayi me yace zai ci ?hannuwanta ta tsarke cikin juna sannan ta bud'e baki da kyar "wai a dafa masa komai."

mami  ta fad'ad'a fuskarta da murmushin jin dadi , ita Kuwa nana hauwa'u sarai ta fahimci wani abu a tattare da marsi tasan sarai ba abinda yace mata  kenan ba   "to shikenan maza ki shiga ki dafa  masa  abinda  yazo cikin tunaninki amman ki natsu sosai kinji. "ta gyada mata tana cewa "sister muje ki tayani "me .....?dan girman Allah ki rufa min asiri na tsira da mutuncina ke dai kije Allah ya bada sa'a kiyi kokari yayi dadi  sosai ta k'arasa maganar tana kakkabe hannunta. "haba sister ki taimaka mana kin san fa  komai tare mukeyi ,nasani amman ban da wannan wallahi bazan Saka hannu ba abinci yazo bai yi dadi ba ya had'amu yaci ubanmu"  hjy zulaiheart tayi murmushi "Kai Adamcy hukuma kowa tsoronsa yake ji amman Kuma fa yana da sauki Kai Kinga mryam  yi tafiyarki kinji  duk abinda baki gane ba kizo ki tambayeni Simi Simi ta juya ta shiga kitchen kmr ta daura hannunta  tayita kuka dan tasan muddin tayi kuskure sai yaci ubanta duk iya k'okarinta na dafa  masa rice and stew bai ci ba ya wuce juma'a ."

*****
Da  misalin  karfe  biyu  na  rana  bayan  an  sauko  daga massalaci  hajiya   zulaiheart  da  kanta  ta fito  zuwa  haraban  gidan ta fara  rabawa yaran dake shigowa haraban estate din sadaka  wake da shimfa  acikin takeaway fari tare  naira dari  biyar biyar sababbin yayinda  ATA  ke tsaye daga can nesa kadan da inda take kunnensa manne da waya yana tafiya a hankali irin na jinin saurarata

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login