Showing 78001 words to 81000 words out of 168608 words
inda ta bar mahaifiyarta anan ta sameta tare da habib suna hira da alamun shi baya cikin damuwa kamar ita." bata tsaya ba byn tayi sallama tace "aunty sai da safe tana gama fadar haka ta wuce ta nufi d'akin baccinta bayanta suka bita da kallo , yanayinta kad'ai ya fahimtar da aunty akwai tarin damuwa atattare daita shiru kawai tayi tana tunani "har yaushe maryama zata yi farinciki arayuwarta ?".
A natse aunty ta mike tabi bayan maryama tana jin tsinkewar zuciya haka shima habib akan kujerar da take zama idan zatai zane suka isketa ta dafe kanta tana sheshekar kuka atare suka qaraso suka zauna abakin gado suna fuskantarta shigowarsu yasa ta tsaida kukanta wanda taso tayisa sosai har taji natsuwar zuciyar."
dogon numfashi aunty taja tare da cewa "na shiga uku ni bilkisu " ta furta cikin tsananin tashin hankali dan bata qaunar abinda zai d'agawa yaranta hankali shi kuwa habib hannun maryama ya kamo cikin nashi ya damke da karfi cikin tsananin tashin hankali " heartbeat meke damunki ?." muryarta a raunane tace "babu komai after dad "ya babu komai zaki shigo cikin damuwa , yanzu mun shigo mun ganiki kina kuka amman kice babu komai ki fad'a min idan akwai abinda ke damunki ."
shiru tayi tana cigaba da shesheka "ki sani bamu saba boyewa juna komai ba idan kika min haka baki min adalci ba ,ko km damuwar dazu ce ? still dai shiru tayi ,sosai suka d'aga hankalinsu ita kuma taki cewa komai sai faman ajiyar zuciya ta saukewa ." damke hannunta ya sake yi sosai yana rokonta "dan allah heartbeat karki daga mana hankali ki fad'a min kukan me kike yi ?kallonsa kawai tayi tana lumshe idanuwanta ganin yadda hankalinsa yay matukar tashi da yadda ya d'aga hankalinsa ya matukar bata tausayi daman kuma haka ne idan daya yana cikin damuwa dole ne daya shima ya tsinci kanshi cikin damuwa."
"Yanzu princess bazaki koyi dauriya akan kowacce irin damuwa bace domin ki tsira da rayuwarki da rayuwarmu gabadaya ,Ke kenan kullum cikin zubar da hawaye akan damuwa me yasa zaki dinga asarar hawayenki tare da qoqarin kashe kanki abanza ."?
"Gara dai ki fada mata gsky aunty domin ita rayuwar nan da take ganinta wani lokacin idan abubuwa suka wa mutun tsanani dole mutu ya rage wasu abubuwa domin tsira da rayuwarsa da lafiyarsa."
hawayen da take qoqarin maidawa ne suka samu nasarar gangarowa bisa kuncinta cikin sauri tashiga gogewa wasu na sake gangarowa duk yadda suka dinga kwantar da kai da murya dan suji damuwarta amman taki fad'a masu komai domin da zarar ta bude baki hawaye da sheshekan kuka Ke hanata magana dole tasa suka daga mata kafa suka fice d'aya bayan d'aya daga dakin da zumar zasu lalla'bata gobe ta fad'a masu dalilin kukan ."
tafi mintuna goma byn fitar aunty da habib zaune sannan ta yunkura ta tashi tana sauke naunayen ajiyar zuciya ta shiga bayi ta d'auro alwala ta fito ta gabatar da sallahr magariba da isha'i tare da shafa'i da wutiri byn ta idar ta koma kan katifa ta zauna tare da jingina bayanta da pillow ta rungume hannuwanta duka a qirjinta ."
ahankali ta runtse idanunta tana tariyo komai daya faru dasu tun suna yara "Kenan adalili rasa mahaifi da kaka yasa rikonsu ya dawo hannun abban sadam ."tun tana qarama yar shekara hud'u a duniya ta taso cikin so daga bangaren abban sadam da umma da mahaifiyarta amman daga bangaren aunty hassana da sauran 'yan'uwan mahaifinta kuwa saboda haushin da kiyayyar mahaifiyata yasa suka dinga nuna masu tsana da tsamgwama , sun ci wuyarsu sosai most especially Ita ganin kiyayyar dangin mahaifinsu da irin tsanar da baba gali yayi masu ya bawa aunty salma damar cin kashi akansu da mahaifiyarta ."
tun daga lokacin kuruciya har zuwa girmanta abinda yake rage mata zafin gidan shine soyayyar umma bancin ita kowa a gidan baya sonsu amman kuma wani lokaci shi kanshi baba gali ya kan tausaya masu in dai ba fad'a sukai da sakina ba ko yarshi qarama ba , idan tayi mata laifi ta d'an daketa shine zai fito da 'bacin ransa har ya fito da zallar kiyayyarsa ,kuma tun da ta lura son ya'ya ne dashi domin ba ita ba ko uwar data tsugunna ta haifesu baya raga mata akan ya'yansa ."
"yayan baba gali uku ne aliyu sakina wacce sa'artace sai mai bi mata salamatu wacce taci sunan hajiya kakarsu ana kiranta da shukura bata fi shekara sha bakwai ba a yanzu ,itama babu yabo babu fallasa suna d'an shiri daita sai dai idan taga uwarta na fushi da zagina bata hanata sai ma dai ta zugata domin itama tana nuna kishinta akainta idan taga umma tana tarairayata ko wani ."
Baba gali dinki yake ada rasuwar abban sadam yasa gidan buredi da rikonsu ya koma hannunsa alhamdulillah babu laifi ita din mai qokari ce ta kowani fanni boko da arabic ga baiwar zane da Allah ya bata ."
Alokacin baya kullum ta allah sai aunty tayi masu special lesson ita da habib kusan kokarinta ta samu ne a wajen mahaifiyarta ,duk unguwar da makarantarsu ana maganarsu akan ilimi bokon da suke dashi haka duk gidan ba masu jin turanci kamar ita da habib ko wani abu za'a tambaya ita ko habib ake tambaya mahaifiyarsu ta tsaya masu akan karatunsu shiyasa ma education dinsu yayi very fast kuma à sanadiyar qoqarinta ita da kawarta subai'a yasa gwanati ta dauki nauyin karatunsu zuwa lagos state university ".
bangaren sakina da sauran yaran gidan matsalar iyayensu ne dan basa maida hankali akan karatun yaransu gashi sam basu da isashen ilimin boko ko Arabic barin ma aunty salma karta ji labari ba arabi ba boko sai uban girman kai ,sau tari idan shukura tazo koyon wani abu a wajenta bata só sai ta nuna ai itama tasani dan me zatazo wajenta akarshe idan tayi mata zero take samu a makaranta shiyasa da yarinyar ta gane ta daina bata idan tace ta kawo kai tsaye take ce mata bataso zero zataci ."
hatta alwala ba daidai aunty salma take yi ba kuma sallah ma bata dameta ba ,tun suna yara baba gali Ke mata fad'a akan tarukun sallah din da take yi amman taki ta daina shi kansa daya gaji sai ya rabu daita ya dinga Kwa'bar yaransa da yin sallah sanin in har dan uwarsu ne sai dai kar su yi babu abinda ya dameta dan idan ma koyi zasu yi daita sai dai su koyi taruku sallah."
Su kuwa aunty bata yarda tana gama dauro alwala zata tura habib zuwa masalaci ita km ta umarceta taje tayi alwala sannan a kullum dare auty ta kan fito tsakar gidan tare dasu har sakina kasancewar tana qaunarta ta koya masu darasin lissafi , tana daukar lokaci akansu har sai taga sun gane sannan ta bukaci wanda yake da damuwa a bangaren karatunshi ko baka da matsala zatai 'yan tambayoyi ana bata amsa idan bata gamsu da amsar ba ta qara yi masu bayani , bangaren karatun alqurni kafin suyi bacci sai aunty tasa sun karanta izawaka da tabaraka kafin su kwanta da safe kuma sai sunyi murajaa alqurni sannan su shirya su wuce school ko islamiyya ."
A ranar batayi isashen bacci ba ga tsananin tunani ga kwadayin son ganin yan'uwan mahaifiyarta gargadin kanta ta shigayi akan fad'awa soyayya da ma ko waye idan kuma soyayyar ta zama dole sai dai tayi a gidan aurenta ga duk wanda ta aura har asuba tayi maryama batai wani yi baccin kirki ba shiyasa kiran sallahr farko acikin kunnenta akayi ta gyara kwanciyar ta koma ta kwanta bacci kad'an tayi ta lalubo wayarta ta duba taga biyar da rabi saura lokacin sallah yayi dan har an tada sallah a matsalacin unguwarsu ."
a hankali ta mike zuciyarta cike da damuwa bakinta dauke da adduar tashi daga bacci ta kai tafukan hannunta tana shafa fuskarta sannan a natse ta zuro kafafunta ta sauko ta shiga bayi ta dauro alwala ta fito cike da sanyin jiki ta gabatar da sallah asuba byn ta idar ta d'auko alqurni ta soma karatu cikin suratul baqara anatse ta kai idanunta ga window d'akin taga gari ya fara sha tayi azkar din safe tana nan zaune tana lazimi har shida saura sannan ta koma ta kwanta akan sallaya nan da nan bacci mai nauyi ya dauketa ba ita ta tashi ba sai goma saura ."
Ta mike da kyar bakinta dauke da salati sakamakon qirjinta dake wani irin bugawa ta
gyara gadonta ta fita ta dauko tsintsiyar shara
ta share d'akin ta fito har falo ta shiga d'akin mahaifiyarta bata ganta ba tasan may be ko tana byn gida wajen yin wanki ,dan wannan kaida ne kullum safiya sai tayi wanki kayanta wani lokacin da nasu ta share d'akin tasss ta fito da sharan zuwa falo ta shiga kitchen ta hada kayan wanke wanke ta wanke atake ta goge koina ta sharo sannan ta hada da share falo tayi mopping ta koma daki ta cire kayan jikinta ta shiga wanka bata wani jima ba tayi alwala ta fito kai tsaye ta shimfida daddumar sallah ta sallacci salatul duhu byn ta idar ta shirya kanta ta kwanta lamo cikin zullumi ta kamkame jikinta waje daya wani iri take ji a duk gbdy ilahirin jikinta soyayya irin wacce iyayenta sukayi bazata ta'ba yarda ta jefa kanta cikinta ba".
Ta godewa allah daya bata kyakkyawar zuciyar da bata da lokacin maza ,bata jin soyayyar ko wani nmj ta ratsa koina ajikinta ,duk wanda yazo da sunan sonta ya dawo ya gudu bata taba jin haushi ko kewarsa bare ta damu kanta akansa ita fa gsky tafi ganin laifin mahaifiyarta akan abinda iyayenta sukai mata kuma taji dadin mutuwar mahaifinta akan rayuwarsa domin daa kalleta ace ita din diyar dan shaye shaye da neman mata ne wallahi gara mutuwarsa akan rayuwarsa, data dangwama tana masa adduar shiruya allah gara ta qare rayuwarta wajen yi masa addua samun rahmar Allah ."
Da misalin karfe goma sha d'aya da rabi daidai na safe aunty duk ta damu tun jiya rabon tasa maryama a cikin kwayar idanunta ga dai alamun ta tashi dan har tayi ayyukanta na yau da kullum data saba dan ga parlour nan a gyare tsab sai zuba kamshi yake koina tsab daga ita har habib sun kasa samun kwanciyar hankali bare su karya ,sai ma wata faduwar gaban data ziyarci zuciyarsu ."
mikewa aunty tai ta nufi dakinta shima habib ya biyota kusan atare suka shiga dakin har suka shigo maryama batasani ba tana can duniyar tunani tare da rafka uban tagumi da sauke numfashi a hankali ahankali, da sauri suka qarasa gareta dan yadda suka ganta ya matsifar daga masu hankali fiyye da jiya dan har wani doguwar rama tayi atare suka kira sunanta suna tmbyrta "wai maryama menene damuwarki ne ?"
"heartbeat banason ganinki cikin damuwa saboda duk duniya babu wanda nake so byn Allah da aunty sai ke karki bari tunani yasa mu rasaki ya fad'a idanuwanshi na kanta "bansan me yasa kike son kashe kanki akan damuwa ba wanda ni a tunani kowace irin damuwa ce zaki iya hadiyeta". aunty ta qarasa maganar tana furzar da iska me zafi daga bakinta a hankali ta mike ta koma kan kujerar aikinta ta dauko farar takardar daya ta ajiye akan table domin samun damar cigaba da aikinta ta zaro pencil har kala uku ta fara zane sai dai zuciyarta rawa take nan da nan idanunta suka cika da ruwan hawaye tarasa dalili daga jiya zuwa yau ta sake rasa sukuni da farincikinta, bata jin shaawar komai babu abinda take so da bukata kamar ta kadaice kanta ."
Aunty ta dakatar daita daga abinda take tana dubanta zuciyarta na mata wani irin suya a game da halin da take ganin maryama din ciki wanda bata san silar faruwar haka ba maryama bata dago ta kalleta ba ta cigaba da abinda take gbdy kamaninta ya canza ,ahankali habib ya shiga rarrashinta da nasiha mai kashe jiki gbdy fuskarsa ta canza Kmr zai yi kuka , Ita kam aunty kasa furta komai tayi ta zuba masu idanunta tana jin tarin damuwa ganin hk yasa maryama ta soma magana kamar bata son yi "abinda muka bukaci Auny ta fada mana taki jiya umma ta fada min babu abinda ta boye min sai wanda batasani ba." ta karasa mgnr tana dago kanta Tare da sauke naunayen ajiyar zuciya sannan ta sakin wani sabon kuka lokaci daya shima kwayar idanunshi suka kada suka canza nan take yaji tsanar dangin aunty ya shigesa kasamcewarsa nmj kuma duk nmj dole yayi kishin mahaifinsa nan take ya yanke cewar a zuciyarsa bazai furtawa aunty komai akan yanuwanta ba koda kuwa ita kanta uwar gayya ta amince zata koma garesu amman shi babu shi babu su har abada ."
"Tô princes kinji kadan daga cikin tarihin rayuwata kuma ina fatan kin gamsu ?shiru kawai maryama tayi tana kallonta tare gyada mata kai "good my princess kinga rana ya fara ki tashi kici abinci ki kwanta ki dan huta kafin lokacin sallah yayi ta fada tare da mikewa tsaye "yanzu aunty haka rayuwa zata cigaba da tafiya ?tayi maganr cikin raunin murya aunty taja ta tsaya tana dubanta tare da nazarin maganarta "ina nufin haka zamu cigaba da rayuwa batare da kin san matsayinki a wajen iyayenki ba ?
"karki damu dan ni har yanzu bana bukatarsu arayuwata ina ganin kuma ku ciresu acikin zuciyarku "ni daman a yanzu dana gama jin komai na ciresu araina dan basu da wani amfani a wajenmu gara mu qarasa rayuwarmu haka batare dasu ba "haba habib me yasa zaka fadi haka shikenan ita aunty haka zata qare rayuwarta ? kai yanzu zaka iya rayuwa babu ita da kake goya mata baya ?"tayi maganr cikin tsananin fushi "kai daya kamata mu taru mu shawo kanta shine zaka ce haka .?"
guntun numfashi ya sauke yana cewa "lallai heartbeat kina da aiki mutanen da suka wulaqanta mana mahaifi dan kawai talaka ne shine zamu tashi muje wajensu alhalin bamu da komai muna nan dai a yadda suka san mahaifinmu babu wani cigaba da muka samu gsky ni bazanje inda suke ba kuma har abada "gsky habib ya kamata ka tsaya kayi tunani da kyau abinda ubanka yayi bai kyauta ma iyayen aunty ba, ni nan naji dadin dana girma baya raye wallahi da cigaba da ganin rayuwarsa gara mutuwarsa a wajena ."kallonta habib yayi yadda ta zuba masa idanunta cikin bacin rai tana fidda numfashi da kyar "ni babu wani tunani da zanyi akan wannan matsalar ke ma kuma ki bar magana a iya nan dan banga abinda zai sa naje gurin makiyanmu ba kuma ni banga abinda mahaifinmu yayi ba daya cancanci tozarci irin wanda akayi masa ba tun kafin ya qarasa maganar qirjin aunty yayi wani irin bugawa da karfi duk da bata bukatar iyayenta arayuwarta amman bataji dadin kalmar habib din ba ."
"wallahi wallahi habib idan ka sake furta wannna kalmar zan balain baka mamaki "kinga ni tafiyata ya nufi kofar fita yana cewa "allah dai ya baki hakuri amman babu abinda zai kai mu gurin makiyanmu ya qarasa fita ,jikin aunty yayi sanyi ta bude baki zata yi magana sai kuma ta kasa cewa komai "aunty !.
maryama ta kira suannata ,a hankali aunty ta motsa lip's dinta "naam !"karki dauki maganar habib da mahimmanci domin shi yaro ne ke uwa ce da muke kallo muke koyi daita kuma kece malamammu dake nuna mana daidai da ba daidai ba ,ki natsu aunty da kyau ke mai ilimi ce allah subuhanahu wata ala yace acikin suratul ahkhaf aya ta arabin da biyar وَوَصَّيْنَا الْإِنْسَانَ بِوَالِدَيْهِ إِحْسَانًا ۖ حَمَلَتْهُ أُمُّهُ كُرْهًا وَوَضَعَتْهُ كُرْهًا ۖ وَحَمْلُهُ وَفِصَالُهُ ثَلَاثُونَ شَهْرًا ۚ حَتَّىٰ إِذَا بَلَغَ أَشُدَّهُ وَبَلَغَ أَرْبَعِينَ سَنَةً قَالَ رَبِّ أَوْزِعْنِي أَنْ أَشْكُرَ نِعْمَتَكَ الَّتِي أَنْعَمْتَ عَلَيَّ وَعَلَىٰ وَالِدَيَّ وَأَنْ أَعْمَلَ صَالِحًا تَرْضَاهُ وَأَصْلِحْ لِي فِي ذُرِّيَّتِي ۖ إِنِّي تُبْتُ إِلَيْكَ وَإِنِّي مِنَ الْمُسْلِمِينَ
Allah yana yiwa mutane wasiha ne akan su kyautatawa iyayensu , mahaifiya ta d'auki cikin mutun ,tana mai shan wahala ,kuma ta sauke shi cikin wahala ,da daukar cikin da yaye d'a na tsawon wata talatin har lokacin da karfin mutun zai kai girma yasan ciwon kansa har zuwa karshen ayar ,cikin girmamawa ta cigaba da magana "kiyi min wannnan alfarmar aunty , wallahi dan kinje garesu a halin yanzu ba kasawa bane bugu da qari iyayenki suna da hakki akanki babu ruwan allah da abinda sukai miki ".
"maryama mu bar maganar nan ta wuce dan allah sannan ki fito ki karya kar abincinki yayi sanyi tana gama fad'ar hk ta juya ta fice daga dakin shiru tayi kawai tare da bin kofar dakin da kallo idanunta na kawo ruwan hawayen tana tausayin mahaifiyarta bata san meke damun mahaifiyarta ba akan iyayenta sam sam bata son ana mata maganarsu tamkar wanda akayiwa farra'u amman tasan abinda zatai zata janye jikinta tare da tsananta addua akan lamarin allah ya daidaita da iyayenta da yanuwanta ,yinin ranar a daki ta yini taki fitowa taci komai ."
*****
Tun karfe takwas na safe maryam da mami da masu aikinta ke faman kai kawo a kitchen suna qoqarin had'awa mr ATA breakfast sosai mami take lura da yadda maryam take gudanar da aikinta , babu laifi tafi da kokari sosai sannan ta rage son jikin da take dashi wajen girki suna girki suna hira mami ta cigaba da nuna mata wasu abubuwa suna cikin aiki sai ga sallamar hindu ta shigo maryam ta amsa tare da lekawa tace "hindu ce ki shigo muna kitchen muna aiki ne."
wani irin kallon tayi mata wanda yasa maryam taji wani iri ajikinta ,hindu ta tsaya bata shiga kitchen din ba kamar yadda maryam tace ta samu waje ta