Showing 96001 words to 99000 words out of 168608 words

Chapter 33 - Mar'adam's Book 1 Hausa Novel Complete

sake durkusawa a wajen  batare da tasan abinda zata fada ba,  tana  mai   bakincikin  irin   kalar   rayuwar  da  mahaifinta  yayi a  sanda yake  raye, gashi ya  bar duniyar  amma  basu  huta  ba , wannan wace  irin rayuwa  ce ? me yasa wasu yanuwa suke yin haka ? "tasani da ubansu mai  arziki  ne da  duk abinda yayi babu mai tuna masu  bare  har a zagesu   dashi  ."

tsaki   baba   gali  yaja  yana cewa  " Munafukar  banxa  sai  anyi  magana  kisa  mutane a gaba kina kuka,  da  ubannaku  bai shaye shaye  ba  zaa fada? daya  zauna da mutane lpy  zaa ki  fada ?kullum yana cikin d'auko  mana  magana  gashi ya mutu ya bar iri  an  iya  tujara iya tujara  sauran  shaye shaye .."

"Allah  bazai sa  ba  ,baba  ka daina masa mugun fata "me ya saura yaro ya zama dan daba ai sauran shaye shaye, habib zai yi  magana   maryama  tayi saurin dakatar  dashi  tana cewa "walalhi karka sake cewa komai ai ga  irin abinda ka haifar ko ?"ni dai na fada maku  maza ku san ynd zaku  yi  ku bar mana  gidanmu tunda  gdn bana ubanku bane,"


  maryama da  tarin  qunar  zuciya  da qunar  rai take zubar da hawaye  tafi  karfin minti  goma a durkushe  sai daga baya ta koma  inda  tabar aunty ta durkusa  kusa daita  hawaye na  zuba a idanunta Itama aunty  hawayene take zubarwa a  nata  idanun  tana  jin ciwon abinda  habib  yake  duk da tasan  gsky  yake  fad'a  masu  amman  bata só  yana  fadar duk  abinda yazo   bakinsu  dan  kome  zai faru bazasu  ta'ba  sonta ba  har   yau   tarasa  me  tayi   masu  mai  zafi  a duniya  da  suka  kasa  yafe  mata  sannan suka  kasa   danne  tsanarsu akanta  da  yaranta ."

Habib  ya  kalli  aunty  ya  kalli  maryama  itama  duk   kuka  suke  maryama  kam har  da  shesheka  tana  rarrashin  aunty " ku  sani  ku  daina wulakantamu na  kyale  ,  kusani  nadamarku  ta  kusan  zuwa  a nan  kusa  kuma  munafurcinku  ya  kusan  qarewa domin  bazan   sake  yarda  da  iskancinku  dan   kuwa  kun  bari  d'an  zaki  ya  girma yayi  girman  da  zai  iya  kasheku  d'aya byn  d'aya  ,gidan  nan kuma babu mai  korarmu  acikinsa  sai dai a d'aga sa  d'ungurungun  dinsa  a sakashi  a  kasuwa  a  siyar a bawa kowa  hakinsa  kowa  ya  kama gabansa"


"Ai  kuwa  baka  isa  ba  wannan  gidan  ubanmu  ne kai   har ubanka  ya  gama  iskancinsa  ya koma  ga  Allah  cima  kwance ne bai  da  gidan  da  zaka yi wannan taqamar  da   kake  yi  "kai  da ba cima  kwance  bane  sannan  bakayi    iskancin    ba  ina naka  gidan  daka  gida  yake  ? "sannan .."
"habib  dan   girman    Allah  .." saurin  d'aga wa  maryama  hannu  yayi   ta hanyar  dakatar  daita " ki  barni  dasu  heartbeat  wallahi  kowa  sai  na  bashi  size dinsa   yau  idan sunce basu da mutunci   zan  nuna  masu   ni  d'an  zamani  ne , ya  d'an  tsaya yana  kallonsu  d'aya  byn  d'aya ,nan  take   ya   hango   tsananin  tsoronsa   da shakkarsa   acikin   kwayar   idanunsu "oya   kuna  iya   wucewa   ku  bar  mu  cigaba  da  rayuwarmu  ko  sai  na   fitar  daku d'aya  byn  d'aya?".


A yadda  suke  kallonsa  sun  fahimci   zai  iya jansu ya  fitar  dasu  kmr  yadda  ya fad'a  dan  haka  aunty  hassana ta kalli aunty "sai  ki  daina kukan munafurci  tunda  burinki  ya  cika kin  haifa  mana  maseefa  amman in sha allahu  maseefar  akanki zai qare   tunda  ya  fara  zama  d'an daba    tana   gama   fadar  haka ta fice  daga   d'akin  tana zage zage 
aunty  tayi saurin  runtse  idanunta  tana  jin  zafin  kalmar  data  danganta  mata  d'a  dashi , itama  aunty  salma  tace   "shegu  a  haka  zaku  qare  jiya  iya  yau  babu   cigaba ta  nufi    hanyar  fita " da sauri  habib  yace "Ke  ina  naki  cigaban  da  kika  samu yake  ? "Ke  da  ko  sallah  bakya  yi ,  qazama  mara  sallah  mai   dotti  kawai  kije ki  gyara  tsakaninki  da  ubangijinki  zai  fiyye  miki  sauki  akan  shiga  rayuwar wasu  ."


shi  kam  baba  gali  cewa  yayi  "bilkisu  Ina  tarbiyar  taki ?yau a gaban  idanunki  d'anki  yake nuna min  iyakata "to  sai  me dan na nuna  maka  iyakarka  a gaban  idanunta ?  "kai  da  bakaji tsoron gaban  idanunmu kake  nuna rashin qaunar  mahaifiyarta ba   kiri kiri  kake  zaginta  agaban   idanunmu akwai  abinda  yafi  wannan ciwo ?  wallahi  idan bakasani ba kasani  yanzu  abinda  kukayi  mata a da  tayi hakuri  ta shanye yanzu  ta  haifi d'an da zai kwatar mata  'yanci  zan goge wannan tarihin  idan  ka  cigaba da tsayuwa zafin jinina  zai iya sa na d'auki takobin  can na file  maka kai  dashi ko na  raba  katon kan nan  naka   gida  hud'u  idan yaso  nima  akasheni  salin alin baba  gali ya fice batare da  ya sake  cewa   uffan ba."

Yana  fita habib  ya  qaraso inda  aunty da  maryama  suke  durkushe  suna kuka "cike da  girmamawa yace "ku daina kuka  in sha allahu ku daina kuka acikin gidan nan  , kun  daina  damuwa matsawar  ina  raye  zan tsaya maku , zan  kula daku da zarar na gama  karatu  zan ...."bana  son jin komai  daga  bakinka  habib na   fahimci  kana  bukatar  na bar muku  gidan  nan  shiyasa ka kirkiro  abinda za'a koreni daga cikinsa  tana gama fad'ar haka bata  tsaya  jin  abinda  zai  ce ba ta  mike  ta  shiga  d'akinta  ta d'auko  mayafinta  kawai  ta fito zata  fice  ta  bar masu gidan ."


Atare  maryamah  da  habib  suka sha  gabanta  cikin  tsananin tashin hankali  "haba  aunty  ya  zaki mana  haka  ?kiyi  hakuri  aunty hakika  habib  bai  kyauta ba amman  karki  tafi  ki  barmu ."maryama  dan'uwanki   baya  bukatata  acikin  gidan nan  yana bukatar  na  tafi  na bar  masa filin gidan  nan  ya cigaba da rayuwa  ta qarasa maganar  tana  zubar da hawaye  ta  tabi  gefen maryama zata raba  ta  wuce  ."


habib  ya  riko  mata hannu "kiyi hakuri  aunty  ki fad'a min abinda kike  bukata nayi miki  alkwarin  wallahi  zanyi  kisani  idan  kika bar gidan  nan  bashi  da  wani amfani a  wajenmu "yana da amfani mana tunda gashi  kayi  son  ranka  kasa an zageni  anci  mutuncina  anci na iyayena  ai gara na kama  gabana  tunda zamana acikinsa  babu abinda yake haifa min  sai  damuwa da bacin rai ".


Kuka ya  kufce  ma  maryama  ta  d'an  rufe  fuskarta da  tafukan  hannuwanta  saboda  tuttukin  da zuciyarta  Ke yi "kai  ma  kasan  abinda  kayi  ba daidai   bane  har  ka  iya  cire  hannu  zaka  doki baba  gali   wallahi  baka  kyauta  ba   tunda  kasan halinsu  to  meye  amfani  tsayawa  kana  fad'a yana fad'a "ki  fahimci wani  abu  heartbeat  wad'an nan mutane basa  qaunarmu  ,babu  abinda Ke cikin zukatansu sai tsanar mu " tunda mun san halinsu sai mu  kiyaye  abinda  zai  kawo  sa'bani  dasu  shima kukan   yake yi  "suna  nuna  mana  bambamci akan ya'yansu  ,suna  quntata  mana  suna  da  fuskar  gazawa  garemu  musaman   akan ya'yansu  yanzu laifin  me kikayi ma aunty salma ta shigo tana zaginki ?"maryama  bata  sake  cewa komai ba illa ta cigaba da kukanta haka ma aunty batayi magana ba illa qoqarin zare hannunta da take cikin nashi ."

"na  tuba  aunty  bazan sake ba ki fad'a min abinda kike so ,nayi miki alkwarin  bazan  sake  ba ya fad'a yana zubar da hawaye itama ta goge hawayen dake zuba  akan  kuncinta  ta cigaba da mgn "daga yau babu ruwanka da  kowa acikin gidan nan  duk abinda  zasuyi  ko  zasu fad'a akanmu ka kawo ido kasa masu , kai ba zagi  ko dukana zasuyi  babu ruwanka a rashin yace ba dai duka ba amman a zahiri yace "to aunty an gama ."wallahi  abinda kayi yau din nan ba irin tarbiyar daaka  bamu  bace "in sha  allahu  bazan  sake ba heartbeat  ki bata hakuri  bazan sake ba  kamo  hannun aunty maryama  tayi suka koma kan kujera mai  zaman  mutun uku da duk  ashon jiki ya  batattake suka zaunar  daita  tare  da sakata a tsakiyarsu  suna bata hakuri ."


Kamar  yadda  mlm  yahuza  ya sanarwa  nafisa  byn sallahr ishai zai  zo  sai ga  yaro yana sallama  da maryama  lokacin  suna zaune a falon aunty  ta dubeta amman ita ko  ajikinta sakon da yaro ya fad'a aunty tace "maryama bakiji  bane ?ta  d'an  dubeta ta share yaron ya tsaya yana jiran abinda zaace   "to sai  ki  tashi kije "ina kenan aunty?"bakaji ana sallama daita bane "gsky   babu  inda zata ban san dalilin da yasa da mutun yazo nemanta ba  sai ki bata damar fita baki  san ko waye ba mazan da duk 'yan  iska ne da zarar sun fara zuwa kamar abun arziki da zance aure ya shigo sai su gudu su barta  ni  gsky babu wanda zai sake zuwa ta fita ."


"Maryama  tashi  Kiyi  maza  kije ki dawo  saboda ki samu ki d'an huta   karki  dade  duk da nasan ba  dad'ewar zakiyi ba ,ina dalili da zakace  bazata  ba kai zaka aureta ?ya  marairaice  murya "bani  zan  aureta  ba  amman  at least  aunty  ki duba  lamarin  nan kawai  suzo  suna  'bata  mata  lokaci  da  dagula  mata  lissafi "Babu  wani  dagula  lissafi a haka  allah  zai  kawo  mata  wanda  zai  aureta  ,ina  son  kasan  wani  abu  habib   duk   cikin  masu  zuwa neman   auren  maryama  babu mijinta  acikinsu , duk  lokacin da mijin  yazo  to  babu  makawa  sai  anyi   domin  babu  mai  aurenta  matar  wani  kai  yaro  je  kace gata nan  zuwa  yaron  ya  juya  da sauri dan  daman  amsar da yake jira kenan  zata  fito  ko  kuwa  bazata fito ba  ."

maryama  ta  tashi  ta  shiga  d'aki dan  tasan  ko  waye  yazo  ta d'auki  hijab  dinta  ta  fito "amman dai  ni  aunty  a wajena  ba  daidai bane  ,ni  fa  kamar  mahaifinta ne a matsayina na  namiji  acikin  gidan  nan  amman  me yasa  sai a dinga  nuna  min  iyakata  acikin gidan  nan  , na  fiku  sanin halin mazan  wannan  zamani  babu komai  acikinsu  sai  tsabar  yaudara ".


Aunty  ta  kallesa  saboda yadda yake  maganar  tamkar  wani babban  mutun  tace "wai  har guda  nawa  kake  habib  ?" duka shabakwai  gare  fa  kawai dan allah  ya  baka  jikin  girma "ni dai gsky  ban  yarda  ta  fita  koina ba  girgiza kai aunty  tayi  tana kallon  yadda yake kamaninsa yake canzawa  a  kullum  yana  komawa na  mahaifinsa  tun ba yau ba kusan  kowa  yana  fad'in  kamanin nasu  "gaskiya  habib  kar  ka  zama  mai   hana   neman   auren ."


tsayawa   maryama  tayi   tana kallon  fuskar  habib  daya had'eta tmkr  ance  masa  idan  ta  fita guduwa  zaa  yi  daita ,ahankali ta kira  sunansa  "after dad "
"Karki  wani   kirani  da  wannan sunan  dan  dani  din  ina  da wannan  matsayin  da  za'a  dinga bin  umarnina " ta  qaraso ta zauna kusa  dashi  ta  riko  tafin  hannunsa  cikin  nata  tana kallonsa  da  idanuwanta  da  suka canza  kalla "after  dad me kake so dani ?"ta fad'a tana kallon yadda shima  ya  zuba  mata  ido  yana kallonta ."

"Abinda  nake  so  duk  wanda  yazo karki  qara  fita  koina idan abinda  ake  miki  acikin  gidan  nan  baya  damunki  ni  yana damuna  ,sau  nawa  kina yi  saurayi  agidan  nan a karshe  ko ya  gudu  ko a kwace  miki shi acikin  gidan  nan ?to  ai  duk ba mijinta acikinsu  ne ,no no aunty akwai cutarwa aciki "to   nufinka  yanzu  haka  zata  zauna  babu   mai  zuwa wajenta ?"allah  aunty dasu  dinga 'bata  mata  lokaci  gara  ta  zauna haka  idan  na  girma  na  qare karatuna  zan  mata  komai zan siya  miki  gida  da  mota  itama heartbeat  zan  siya  mata  zan kai ku  aikin  haji  ,kai  har  sojoji  zan daukar  maku  escort  duk  inda zaku  su  dinga  rakaku  aunty da maryama  basu  san  sanda murmushin  jin  dadi  ya  bayyana akan  fuskarsu  ba "shikenan  after dad  bazanje  koina  ba  domin kai  din tmkr  uba  ne  a gareni "yauwa  heartbeat  sai  yanzu  naji hankalina  ya  kwanta muyi  zamanmu ."


aunty  ta  kallesu  ta  girgiza  kai "wallahi  wannan ba rayuwa bace kin  wani  zauna  ya  tasaki  gaba  yana  miki  zakin  baki  ,wallahi ki daina  biye  masa  Ke  macece dole  kina  bukatar  Kiyi  aure shifa nan  gaba  kad'an  zai  ce  zai  yi aurensa  dan  wannan  da  son girman  tsiya  nasan .."no no aunty karki  hadamu da  heartbeat  babu wani  aure  da  zanyi  na  barta  idan  dole  sai  tayi  aure  ni  zan kawo  mata  miji  wanda  zai  dinga kwantar  mata  da  hankali  duk ranar da  yayi  gangancin ' bata mata  rai  na  zage  naci  ubansa ".


"Lah  lah  lallai  habib  abun  naka babba  ne  "allah  aunty  sai ma ya cika  qaidodina  sannnan "wannan  ai  gara kuje  kuyi  auren  kotu  ku  huta maryama  tai  murmushi  tana jin dadin  yadda  dan'uwanta  ke tsananin   qaunarta  "babu kotun da  zamu amman dole a kular min  da  heartbeat ko kuwa a tashi mutun aiki "uhm  kaga   tashina  ta  mike  tsaye  "  bari  naje na bawa  baba  gali da hassana  hakuri na dawo ."


"haba  aunty  ai  komai  ya  rigada ya wuce  wani  hakuri  kuma  zaki basu   salon  su  samu  damar ci miki  mutunci  "? A'a  sai  naje  zaman  lafiya  yafi  zaman dan sarki  ina  zan  iya  dasu  gara dai naje ."Yauwa  aunty  kije  ki basu hakuri  wannan  ai ba komai bane wata  rana  sai  labari  kai ma ya kamata  ka bita  kabasu hakuri wani  irin kallo ya watsa mata  yana cewa "allah  kiyaye ai ni .."sai  kuma  yayi  shiru  sakamakon tuna alkwarin  da  yayiwa  mahaifiyarsu ."

"ai  babu  abinda  zai  sa  naje da habib  sai ya  qara  dagula  lissafi sunan wani police a isokoko ni na wuce sai  na   dawo "to  aunty sai  kin  dawo  tasa kai ta fice daga dakin  ta barsu suka cigaba da hirarsu mai  cike  da  kulawa da soyayya shi kam mlm yahuza tsawon mintuna nan duk yana tsaye  yana jira   Fitowar maryama ya  duba  agogon  dake  daure da  taintsiyar  hannunsa  yaga lokaci  ya  tafi  daman  kuma  yaron daya  aika  ya  sheida  masa komai  dan haka a natse ya juya sai dai ya kudurce aransa  zai  dawo  gobe."


Ahankali  aunty  take  tafiya  tana tunane tunane abinda zatace idan ta isa gaban baba gali a natse tayi sallama  cikin  bangaren  nasu  basu amsa  mata sallamar ta  ba  dan haka  taji  gabanta ya shiga faduwa  kafin ta kai ga yin wata  magana taji aunty salma ta hau surfa mata maseefa  kamar kullum "me ya  kawo  bangarenmu  "ba komai bane  hakuri nazo baku akan  abinda  habib  yayi ,ya gama ci mana mutunci a gabanki shine  dan  munafurci  kika kwaso  jiki   bayarwa  , shegiyar  munafuka kin wani marairaice  fuska    bayan kin gama zuga d'anki yayi mata walima ta uwa da uba zaki wani kwaso jiki to yanzu hakurin  me kika zo bamu  ?".

Numfashi aunty ta sauke ta samu waje ta zauna kusa da baba gali da ko kallon inda take bai yi ba a tun sanda ta shigo "kuyi hakuri gabadayanku in sha allahu nayi maku alkawarin wannan shine karo na farko da karshe da hakan zai faru ...."dakata  bana son jin komai daga  bakinki  dan duk abinda zai fito daga cikinsa karya ne ni dai abinda nake buqata "ki dauki yayanki ku bar mana gidanmu tunda ussein yake raye bai tsina mana komai ba sai tujara gashi nan ya barwa dansa tsaraba har kamar ni wannan yaron zai dinga gasawa magana kuma a gabanki kina kallo  yaron da ya kamata kiyita dukansa har sai kin kusan auna shi lahira amman kika zauna dan tsabar son ya'ya kina kallonsa yana surfa mana zagi ta uwa da uba  ai wallahi bazai yuwu ba ."


Sake durkushewa tayi Kmr zatayi kuka batare da tasan abinda zata sake fad'a ba sai dai ita kanta a halin yanzu tana mai bakincikin hada  zuria dasu tsaki aunty salma  taja tana cewa "munafukar banza  munafukar wofi sai anyi magana ki wani  durkushewa mutane  "ni dai ba wani tashin hankali nazo dominsa ba nazo ne dan na baku hakuri dan nasan danku bai kyauta ba "ni wannan yaron ba d'a bane domin kuwa d'ana bazai min haka ba hakuri aunty  tayita basu da kyar baba gali yace komai ya wuce amman tajawa habib kunne aunty salma dai ce taki  hakura   ta mike tana masu sallama "sai da safenku allah kuma ya huci zuciyarku babu wanda ya kulata acikinsu har ta fice zaginta aunty salma take cikin tsananin tsana  ."

Daga bangaren baba gali na aunty hassana ta shiga itama dai  tujara  tayi  mata  ta uwa da uba kaf danginta  babu  wanda ta  bari  bare iyayenta zuciyarta  tayi  nauyi  kamar an d'aura mata dotse da kyar ta yunkura ta mike ta fito tana tafiya zuciyarta na  kokawa. a inda aunty ta fita ta bar yaranta anan ta dawo ta samesu zaune  suna  hira "har  kin  dawo  aunty  ?suka  had'a baki murmushi  tayi  tare da d'aga  mata kai  alamar" eh! my princess na dawo ".

"Yaya  kuka  qare fatan sun hakura "Eh to  sun hakura my  princess!ta fad'a zuciyarta cike da raunin kuka dan shi take bukatar yi a halin da take ciki  shi kam habib bai ce uffan  ba  illa  ya  cigaba  da  sauraronsu"my princess Kinga dare yayi  bamu  samu  girka komai  a gidan nan  ba ni yanzu ban san me zamu dan girka muci  ba "wallahi  aunty amman bari naje wajen Ummah watakilla bazamu rasa abinda zamu ci ba maryama  ta fad'a  idanun  habib  yana  kanta "ko  zaka   raka ni ne? ta  fad'a tare da miqewa..."Muje ! kawai abinda ya fad'a kenan maryama tayi murmushi "makalema kawai  "kima  ce  bita zai zai  ki  huta  gbdy muje  suka jera ."


Suna  fita suka had'u da yaya sadam  ya  fito  daga side d'in  din baba gali zai shiga side din ummah cike da farinciki habib ya qarasa suka gaisa! "A she rabon mu had'u ne yaya yasa heartbeat tace nayi mata rakiya ."ai ko baka fito ba  yanzu  nake  shirin  zuwa  tambayarka a wajen  aunty !Ya mika masa hannu ya kwana biyu  ina  fata dai komai  lafiya? "Lafiya  lau  habib  kawae aiki ne ya  boye  ni 2days ya karatu ?yace "alhamdulillah.!"


maryama ta bude baki da kyar ta gaishesa ya amsa mata cike da sakin fuska "Lafiya  su aunty maryam"ji tayi kunya ya kamata da kirata aunty da yayi ! Ya gida da karatu ?Alhmdllh! ta fad'a  cikin jin kunya"kema dazu   nake tambayarki  wajen Ummah take bani labari mai dadi lallai kin fita zakka acikin matan gidan  nan kin tsaya kinyi karatunki yadda ya kamata allah yasa muji sakamakon mai kyau you're  the  best  maryama  duk nmj daya sameki a matsayin mata baqaramin dacewa yayi  ba Allah yasa sawa karatu albarka dad'i maryama  taji sosai  dan duk cikin yanuwanta sadam ne kawai sai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login