Showing 108001 words to 111000 words out of 168608 words

Chapter 37 - Mar'adam's Book 1 Hausa Novel Complete

yadda take qoqarin ta yakicesa daga tunaninta abun ya cutura ba dan komai ba sai dan tsananin kirkinsa da tausayinsa gareta komai na duniya ya fitar mata a rai hatta zaman gidansu ya fita ranta saboda Harare hararen da take sha daga kowace fuskar ta mutan gidan wanda hakan yasa ta kasa samun sukunu ta rasa da me zataji da kwace mata saurayi da suka yi ko kuwa da nemanta da fitina da suke yi ?."


Tana kwance shiru akan   katifa  kamar mai barci alhalin ba baccin take ba. aunty ta leko d'akin tana kiran sunanta "princes baki ta shi bane ? tasan dole ta kasan tashi saboda abinda ya faru dole zai hana zuciyarta sukuni ."ahankali maryama ta yunkura ta mike daga kwanciyar da tayi ta ari murmushi da sukuni ta dasa a ranta tana cewa "aunty na tashi , tayi haka  ne dan kada aunty ta gano har yanzu abinda ya faru yana ranta har yasa ta qara mata zancen addu'ar ma data kwana yi cikin dare ya d'an sanyayyar mata da zuciya, kuma har ranta taji ta samun sauki dan har yanzu data mike tana maimaita adduar Allahuma ajirni fi musibatihi wa aklifini khairan minha yafi sau babu adadi dan bata san iyaka adadin data yi ba , aunty ta riko hannunta cikin nata suka fito zuwa parlour ta zaunar  da maryama ta lumshe idanunta cikin sanyayyar muryarta tace "aunty ina after  dad ?"



"Tun safe ya fita zuwa  filin  kwallo amman nasan yana kan  hanya dawowa yanzu  numfashi ta sauke  da  karfi   sakamakon  tunawa datai yau asabar ce  daman kuma   ranar asabar da lahadi sune ranakun daya ware domin zuwa filin kwallo , ta mike  tsaye a natse ta  nufi hanyar kitchen domin had'a kan kayan wanke wanke ta jiyo sautin muryar aunty   tana  cewa "ina zaki ?" .

          "zan shiga kitchen na had'a kayan wanke wanke na wanke ne ." tayi maganar cike da raunin zuciya Kmr  zatayi  kuka , shiru aunty tayi tana kallonta cike da tausayawa kallo d'aya zaka mata ka fahimci bata cikin natsuwarta da kwanciyar hankali tayi wata muguwar rama " ga abinci akan table ki d'auko kizo ki karya kafin ki fara aiki ."

ta sauke numfashi sannan ta rausayar da kwayar idanunta bata jin cin komai amman kuma bazata iya cewa aunty bazata ci ba  dan tasan bazata ji dadi ba dan damuwarta damuwar aunty ce , idan ta runtsa aunty ta runtsa ,idan ta kwana Jin  motsinta to haka itama bazata runtsa ba ,ta dinga kai kawo kenan a tsakanin d'akinta da nata ."


Jikinta a matukar sanyaye ta qarasa inda kular abincin yake ta bud'e ,shiru tayi tana kallon   abincin , sai  data  d'auki  second  goma  tana kallon   abincin sannan ta kalli aunty   fuskarta d'auke  da  tambaya "ummah ce ta aiko mana dashi , sanyayyen   ajiyar zuciya maryama  ta sauke   sannan ta d'auko Kula tazo ta zauna kusa  da aunty ta fara ci a  natse , ba wani abincin kirki taci ba ta rufe kular tana qoqarin mikewa tsaye  aunty tace "har kin yi me kenan princess ? " ki koma ki qara cin abinci duk fa kwanakin nan ina  lura  dake  ba wani abinci kirki kike ci ba ,ki taimakeni ki manta da abinda ya faru ga gobe can tana d'aga muna hannu kullum cikin miki addua nake , nayi imani allah bazai barki haka ba zai kawo miki wani mafi alkhairi."


"Wallahi aunty na koshi ne sannan idan ban hakura ba ya zanyi aunty ? nasan haka Allah yaga dama dani kuma na kar'bi qaddarata ni kawai mlm yahuza nake tausayawa domin duk ranar da zai dawo haiyacinsa sai yayi kukan bakinciki abinda ya faru , tana gama fadar' haka ta shige kitchen ta ajiye kular abincin da taci ta rage ta fara da had'a kan kayan wanke  wanke ta wanke  sannan ta share d'akunansu ta fito da sharar har tsakar gidansu domin kasancewar weekend ce kuma daman ta saba hakan a duk ranar weekend ."

Lokacin data fito duk mutanen gidan suna zaune suna hira ganinta suka hau fad'a
fad'ensu da suka saba akanta  musamman aunty salma da aunty hassana da  yaranta   kaulat da  Islam dan ita sakina  shiru tayi tana sauraronsu haka ma shukura sai dai duk lokacin da suka had'a ido da shukura sai ta zabga mata harara ,sai dai allah da ikonshi sam bata ji komai game da abinda tai mata ba illah iyaka tausayin mlm yahuza dana mahaifiyarta dake ranta ,adadin soyayyar aunty gareshi mai  yawa  ce,   domin shine saurayi  na farko  da aunty taji ta gamsu dashi ,shine mutumin da rabuwarsu ta ta'ba zuciyarta ,shine wanda har ta tsaya tayi mgn akan ba'a mata adalci ba duk sanda yazo kuwa sakon gaisuwarta zuwa gareshi kad'ai ta kai ashirin, banda yabo da qara mata kwarin  gwaiwa da take mata akanshi."


Bayan ta gama aikinta taje tayi wanka ta shirya kanta cikin Jallabiya maron touch of white ta d'aure gashin   kanta da  rebbon  kasancewar  tana da   yalwan   gashi mai  tsoho  sannan  tasa mayafin jallabiyar ta  daure  kanta  ,tana zaune kusa da aunty yayinda hanuta Ke rike da reza ta d'aura kafarta d'aya akan cinyarta tana yanke kunbunan kafafunta suna hira da aunty inda take fad'awa mahaifiyarta tana son zata  1829 super market siyan abubuwan bukatanta  ,aunty ta amince tace "sai da yamma kenan zaki ?"a'a idan after dad  ya dawo yanzu  zamu je tare dashi "princess me yasa bakya iya zuwa koina sai tare da habib ne ?" wallahi aunty bana jin dadi tafiya ni kadai ne sai naji Kmr zaa saceni bare irin wurare nan da jama'a suke cika Kinsan ni fa yawon mutane na matukar   tsoratani."


"ai na  sani princess amman dai ya dace ki saba da yin wasu abubuwa Ke kad'ai saboda kinsan wata rana zakiyi aure gashi kinsa habib aranki dayawa karki manta habib nmj ne shi din d'anuwan wasu ne tunda nan gaba aure zaiyi "
" babu wacce ta isa ta shiga tsakanina da 'yaruwata , babu wannan matar a nan gidan duniya wannan shine sallama da habib yayi sannan   ya shigo parlour'n sosai ya furta sallama ."


atare maryama da aunty suka amsa masa maryama ta d'ago kwayar idanunta daga abinda take ta zuba masa tana sakar masa murmushin farinciki yana tsaye sanye da wondo da riga na yan kwallo na kamfanin arsenal kayan sun amshi jikinsa sosai  ,suna matukar  kama da habib sosai abu d'aya ne ya bambamtasu shine launin fata shi fari ne sol yayinda ita kuma ta kasance chocolate colour ."

Aunty tayi murmushi tana dubansa tana sake maimaita maganarta "to ai gsky ne kai d'anuwan wasu ne  mana ,dan girma Allah aunty ki daina furta cewa ni din d'anuwan wasu ne , wasu suwa kenan ? "yan'uwan matar da zaka aura mana ta bashi amsa da haka tana kunshe  dariyarta "dan girman allah ki daina fad'ar wannan mgnr nifa babu matar data isa ta juyani ,haka zata ganmu ta barmu mu cigaba da rayuwarmu kamar yadda muka faro babu wacce ta isa ta raba mu ko shiga tsakaninmu bakiji sunan da nake kiranta dashi ba bugun zuciyata ? bani da kowa sai ke daita , uwa d'aya uba d'aya , jini d'aya ina jinta araina fiyye da komai dake cikin duniyar nan "dan allah kama mana baki zaka cika mutane da dadin baki har ka girma kayi auren muga yanayinka ,amman a yanzu babu abinda zaka fad'a na yarda da kai nawa nawa suka cika baki irin naka a karshe ..."

"A'a aunty akwai shakuwa mai karfi atsakanina da habib ai duk wacce tace zata shiga tsakanin mu allah ma bazai barta ba bare bana tunaninta hakan ,shi kansa ma bazai d'auko mana matar da zata rabamu ba , matar da ma ni da kaina zan zaba masa inji cewar maryama ta  fad'a  tana murmushi "yauwa heartbeat fad'awa male taji da kyau, nima koda wasa bazan kawo irin wannan matar ba ,sai ma wacce heartbeat ta za'ba min Kmr yadda zan za'ba mata miji anan gaba yana fad'ar haka yasa kai   zai shiga bayi maryama tace "karka dade zaka rakani 1829 "okay ki shirya kafin na fito ya qarasa shigewa ciki ta mike tsam tana cewa aunty "bari naje na sake shirya na fito ."


    ta shirya cikin wata doguwar rigar   atamfa   yellow  touch  of   black atamfar   ba  wata  sabuwa bace  dan  ta  dan  kode  sai  dai  fés  take  agoge  sai takalmi flat  kasancewar maryama mayar saka flat ce cikin kankanin lokacin habib ya fito yana kiranta yana d'aura agogo a tsintsiyar hannunsa na gama ke nake jira fa "ganin nan   fitowa   nima na gama hijab  kawai  zan  saka  da  nikaf ,byn   second   biyar   ta  fito  suka yiwa aunty sallama "sai mun dawo aunty ."

" to sai kun dawo Allah ya tsare min ku habib ka kular min da yarinya na baka amanarta yayi murmushi yana cewa "to ni kuma wa zai kular miki dani ? ."kai   wannan yaro   wannan yaro akwai manyamce  ku dai je Allah ya tsare karku dade suka fice suna fitowa suka hango yaya sadam a haraban gidan hannusa  daya  rungume a qirjinsa yana waya da murmushi akan fuskarshi suka gaishesa hannu kawai ya d'aga masu suka wucesa ."


Basu suka dawo gidan ba sai daf da magariba habib ya wuce massalaci maryama ta cire nikaf dinta tare da hijab ta fad'a bayi domin yin alwala bayan ta idar da sallah suna zaune sai ga dan sako daga umma

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login