Showing 138001 words to 141000 words out of 168608 words

Chapter 47 - Mar'adam's Book 1 Hausa Novel Complete

komai dan ban san abinda nayi masa ba daya canza da shukura" to ai ba soyayya bace a tsakaninsu da shukura ita kanta salma rashin fahimta ne ku dawo Kmr yadda kuke dan dazu da kanshi yazo neman ki"


"Nemana kuma me kuma zai min ai ni na rigada na yafesa har abada ,aa maryama ban sanki da fushi ba Kiyi hakuri idan ya dawo ki samu ku sasanta kanku kinji bai kamata ba dama shi irin wannan sabanin ai dole yana zuwa a mijin da zaka aura ,ido kawai ta zuba masa kafin daga baya ta sunkuyar da kanta kasa ahankali ta furta to "baba ina kuma alqawarin da kayiwa abban kausar ?yayi shiru yana dan nazari "maryama da na zama qaramin mutun ta bangaren mahaifin mlm yahuza ai gara na zama ta bangaren alqasim maude domin shi zai min uzuri kuma idan na hada yusif da yaruwarki sakina ko shukura nasan komai zai wuce ."

Tayi shiru kawai hawayen takaici suka nemi zubo mata daga idanuwanta gbdy ta rasa abun yi kawai ta mike ta koma banger su ta fad'a dakinta ta kwanta ta kudundine kanta ta fara rusa kuka mara sauti dan tasan wannan ma ya zama ba rabonta ba tunda ma baba da kanshi ya furta mata haka yanzu ita hk rayuwarta zata qare cikin kunci da wahala "me ta tsare masu da basa qaunar cin gabanta? duk wani abu da suka san zai zama cigaba arayuwarta basa so ."


Mmn sudais

💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗


*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.


Page 25

Allah sarki maryama kwana tayi kuka har sai da garin allah ya waye sakamakon haka fuskarta ta kunbura ita kanta ta rasa dalilin me yasa take kuka rashin yusif da zatayi ne ko kuwa dawowar mlm yahuza ne ?a zahirin gsky duk bbu ko daya aciki dalilin zubar hawayenta ,zubar hawayenta bai wuce na rashin qaunar da baba gali yake nuna mata kiri kiri ba, lamarinsa yana mugun daure mata kai ."


Tarasa gane kanshi ,mai hakan yake nufi da aikatawa? anya ma kuwa baba gali yana cikin haiyacinsa dan kwananan abubuwan da yake sun qara shan bambam dana da ? al'amarin ya damu maryama har yasa kwalkwaluwar kanta Ke neman tarwatsewa ,da gaske dai baba gali da sauran dangin mahaifinta basa qaunarsu sai ma a yanzu ta qara gane cewa ba dalilin haduwar iyayenta bane silar qiiyayyarsu garesu daman can basa qaunar mahaifinsu ."

Babu kuzari ajikinta haka ta tashi da safe aunty da habib suka damu sosai da ganin sauyi atattare daita idanuwansu na kanta lokaci zuwa lokaci suna lura da damuwar da take baibaye daita sai dai basu ce mata komai ba sanin ko sun tmyeta zata fad'a masu babu komai, amman ita maryama tana lura da yanayinsu nason yi mata magana ."

aikinta data saba na safe tayi bayan ta kammala ta shiga wanka wanda zuwa lokacin Auty ta gama girki ta fito cikin doguwar rigar tana zama aunty ta kawo mata nata abincin tasa abincin agaba tana tsakura yayinda zuciyarta ke mata tuni da abubuwan da suka faru jiya atsakaninta da yusif ta jisa dabam akan mlm yahuza ,ko kadan zuciyarta ta kasa daina tunaninsa ba wai dan tana sonshi ba dan gsky daga haduwarsu jiya bata ji cewar tana son shi ba ta dai amincewa aurensa ne saboda ta samu saukin rayuwa ,soyayya kuma tasa aranta bayan sunyi aure zata so shi daman ita kuma ba dabiarta bace saurin zurmawa soyayya ."

Tana tsakurar abinci sannu ahankali har taci rabi ta dauki plet din da taci abincin ta kai inda suke yin wanke wanke ta dawo ta nufi hanyar dakinta tana qoqarin shiga aunty ta kira sunanta cikin muryarta mai tsananin tausayawa agareta ta juyo a natse tare da amsawa sannan ta dawo inda take zaune ta durkusa agabanta ,aunty ta dubeta sosai ta sauke numfashi tace "yanzu princess har akwai damuwar da zata dameki ki kasa fad'a min ?

Nan da nan ta rikice domin dai bata son fad'a mata komai sannan bata son tasan ma tana cikin damuwa dan ita a ganinta gara ta boye damuwarta muryarta a matukar sanyaye tace "aunty ai bana boye miki komai kuma Kinsan idan akwai abinda Ke damuna kece mutun ta farko da zan fadawa tunda bani da wacce ta fiki ko babu komai adduarki nada matukar mahimanci agareni "yanzu zaki iya rantsewa da Allah babu abinda ke damunki ."?

Maryama tayi shiru dan bazata iya rantsewa ba kuma bazata iya sanar daita ba dan zata fita shiga damuwa ita kuma bata qaunar ganin damuwarta wallahi akan taga aunty cikin damuwa gara ita ta qare rayuwarta aciki ,duk maganar da aunty ta keyi ba tace uffan ba illa ta sunkuyar da kai kawai tana sauraronta zuciyarta na karkarwa , duk yadda aunty taso taji wani abu daga bakinta amman taki ita dai ta karbi qaddarata na rashin yusif."


Haka ta kasance acikin gidan zuciyarta babu sukuni kwana uku da faruwar abun sai ga mlm yahuza yazo gurinta har da bata hakuri yana mai jinjina abinda yayi mata ,yace shi kanshi yayi mamakin abinda yayi ,wai shine yake kin kulata kuma shine yayi soyayya da shukura ? yana magana Kmr zai yi kuka wanda ita ahalin da take ciki bata jin tausayinsa kuma bata jin zata karbe shi ta barwa duk wata mai so kai auren ma ta hakura dashi har abada ."

duk hirar da yake mata baya mata dadi wani irin tsanar shi taji yana shigarta sannan duk nacinsa haka ta wuce ta barsa ta koma cikin tana tunanin yadda alamarin zai kasance shin idan yusif yaji hukuncin baba gali ya zai yi ?."zai amince ne ko kuwa dai shima zaa kawar masa da tunaninsa ne kamar yadda akayiwa mlm yahuza? " bani da gata bani da kowa sai allah da kuma mahaifiyata ta sheidawa kanta haka ."

"mai zai hana ki fadawa mahaifiyarki gskyr lamari sannna ki tashi tsaye da addau zuciyar ta ,ta fad'a mata haka? zan dai tashi da addaua amman bazan iya fadawa aunty komai ba dan zata fini shiga damuwa gara idan maganar ta fito taji daga sama ta kwanta shiru tana kallon saman dakin hawayen na gangarowa ta gefen idanunta ."


Kuka take har da shesheka wanda bata ma san sautin muryar kukan na fita ba, cikin haka aunty ta turo kofar dakin ta shigo ganinta haka yasa taji wani gagarumin tashin hankali da sauri ta qaraso kusa daita ta zauna tana kiran ainihin sunanta "maryama !
a matukar firgice ta dawo natsuwarta ta mike ta zauna tana goge hawayenta da hannuwanta duka ,aunty ta tsura mata ido kawai tana kallonta dan gbdy rasa abinda ke mata dadi arayuwarta take idan taga maryama cikin damuwa ."

A dan fusace tace "kukan me kike yi ?wani irin bugawa qirjin maryam ya shiga yi nan take ta shiga kokuwa da numfashinta dake barazanar daukewa sakamakon kukan da take sannan ahankali ta shiga girgiza wa aunty kai alamun babu komai "babu komai kike kuka haka maryama ?"yanzu bazaki fad'a min damuwarki ba ?"Ke kenan kullum cikin damuwa cikin zubar da hawaye nasan acikin kwanakin nan akwai abinda ya faru wanda kike boye min meye shi sannan waye yazo wajenki ."?

hawayen da take kokarin maidawa suka samu nasarar gangarowa bisa kuncinta cikin sauri ta shiga gogewa wasu na sake gangarowa cikin muryar kuka ta soma magana "da fari dai mlm yahuza ne yazo "mlm yahuza kuma ?me yazo yi?tayi mata tmbyr a jere tana dubanta qirjinta na bugawa da karfin gaske "wai ya dawo ! shiru aunty tayi tana nazarinta sannan tace "shine dalilin shigarki damuwa ?maryama ta girgiza mata kai tana cewa "bashi bane!

"to menene ni ?" abinda Ke damunki nake bukatar sani "ban san me yasa baba gali baya qaunata ba ta qarasa mgnr tana zubar da wani hawaye "Kawai dan baya qaunarki shine zaki zauna kina kuka kina damun kanki ?ai ba dole sai ya soki ba, rayuwar nan fa da kike ganinta ba kowa bane zai soka, sai ku fito ciki daya da mutun yace bai sonka bare shida dan uwa yake a wajen mahaifinki ."

aunty ta kamo hannunta daya cikin nata sannan ta kai dayan hannunta tana goge mata hawaye "ki cire wannan damuwar ki manta da batun bai sonki wata rana sai labari kuma maganar dawowar mlm yahuza karta daga miki hankalinki tunda nan kusa zakuyi aure da yusif naunayen ajiyar zuciya ta sauke tana sake matso ruwan hawaye idanunta "Allah sarki aunty ai shima ya zama ba rabona ba ta fad'a a kasan ranta zama aunty tayi tana rarrashinta har bacci ya dauketa sannan ta mike ta bar dakin ."

*****
A yammacin ranar litini wanda yayi daidai da kwanan nuzla uku a police station labarin halin da take ciki ya samu jama'ar dake rayuwa acikin abdullahi estate kowa ya shiga damuwa matuka amman banda hindu dan ita murna tayi sosai dan ta fahimci itama tana cikin masu son abinda take so , hisham kam yafi kowa shiga damuwa yayinda hjy salema banda kalmar inna lillahi wa inna ilaihi rajiun babu abinda take furtawa da zubar da hawaye ."

"Ya'yan hjy salema suna zaune gbdynsu a cikin parlour'nta cikin jimami har hisham wanda ya fita haiyacinsa ATA ya shigo bakinsa dauke da sallama ,baa kai ga amsa masa sallamar da yayi ba hisham ya tashi a matukar fusace ya soma magana cikin zafin rai "me ya kawo ka ?" me kake takama dashi ?ya tmbyesa .ATA ya zauna yana duban screen wayarsa" laifin me nuzla tayi maka? me ta tsare maka ?komai zata maka ai bata cancanci kayi mata haka ba ? zaka iya yiwa nana hauwa'u haka ko zaka iya yiwa zabiba haka ?" ATA bai kulasa ba dan yasan baya haiyacinsa so ya rigada ya zautar dashi."


"Mutumin banza dan rainin hankali kawai da bai san mutuncin na gaba dashi ba ,kace baka son yarinya amman gashi akanta kasa an kama yarinyar mutane ATA bai dago idanushi ba ya cigaba da kallon screen din wayarsa yana cewa "ka shiga hankalinka hisham zaka iya fad'ar komai na barka dan nasan a haukace kake ,amamn idan ka sake hadani da yarinyar nan zan ajiye haukan soyayyar dake damunka a gefe nayi maka wulakanci."

"Kai ne dai mahaukaci amman ni lafiyata lau "hisham zamu samu matsala !mun dade bamu samu ba ,nace kana sonta !! baka sonta me yasa zaka sa akama nuzla ?nan zuciyar ATA ya motsa ya somawa hisham wani kallo mai tattare da tashin hankali ganin kar abun ya zama fad'a a tsakaninsu baba babba ya takawa hisham burki ."


ahankali ATA ya soma warware komai da sakon da nuzla ta aika masa dashi "nayi wannan bayanin ne saboda hjy da kuma baba Babba sai ku yanuwanta dan kusan dalilin da yasa ta shiga hannun hukuma "ban bada umarnin ayi mata komai ko a ta'ba lafiyar jikinta ba ,abinda yafi zama mai mahimanci shine bincike kuma ana kanyi abinda nake son gbdynmu mu fahimta yana da kyau mun san daga inda matsalar take wacece ta kashe mubina ?

"wallahi ni ba akan yunkurin kashe wannan yarinyar yasa na damka nuzla hannun hukuma ba dan ko nana hauwa'u aka kama da laifin kisa ko yunkurin kisa da kaina zan damkata ga hukuma haka zalika nuzla qanwata ce Kmr yadda nana hauwa'u take a wajena ,tayi kuka tayi rantsuwa akan bata aikata ba amman wacce ta aikata tana tare damu kuma nasan muddin ba nuzla bace hakika muna tare da mai yin kissan dan haka da zarar an kammala bincike da kaina zan dawo daita gida mu san abun yi amman ya zama dole mu san wacece ta kashe mubina acikinmu ."


parlour'n ya dauki shiru duk suka zuba masa ido kawai suna kallonsa da sauraronsa bayan kamar minti goma ATA ya numfasa sannan ya kalli inda hajiya salema take zaune tana faman kuka "kuyi hakuri hjy km ki kwantar da hankalinki matsawar babu hannun nuzla acikin zakiyi farinciki yana gama fadar haka yayiwa baba babba sallama ya nufi kofar fita yana zabgawa hisham harara ."

tsaye hindu take tare da jingina jikinta da bangon dakinta ta hade hannuwanta duka waje daya ,sosai tayi nisa cikin duniyar tunanin yadda zata kawar da maryam a doron duniya tun kafin akai ga daura masu aure da adam ,dan ta gwamaci ta kasheta idan yaso itama akasheta kowa ya rasa adam din gbdy ."

ji tayi an dafa kafadarta ta juyo a hankali idanunta ya sauka akan baba qarami ta sauke naunayen ajiyar zuciya tana runtse idanunta yayinda gabanta Ke dokawa da wani irin karfi "karki illa kanki akan wannan dan iskan yaron da bai san mutuncin mutane ba "kafi kowa sani baba ina mutuwar son shi wannan maratuncin da dukkanin rayuwata kuma kafi kowa sanin bazan iya rayuwa babu shi ba, amman kana ji kuma kana gani kana da ikon da zaka sa umarni kawai zaa bashi ya aure ni amman kaki kayi komai akai wallahi baba ji nake kamar na mutu ta kamo hannun baba qarami ta kai daidai saitin qirjinta yaji yadda qirjinta ke bugawa da sauri sauri ."

gbdy ya sake shiga rudani duk tunaninsa ya tsaya ya rasa ta ina zai fara ga matsalarsu ta kamfani da kullum cikin rigima ake ga qaddarar data dade da fadawa diyar daya fi so da qauna "idan bazakayi komai akai ba ni zanyi koma nace na fara zan kuma cigaba daga inda na tsaya dan bazanyi asararsa ba sai dai duk mu taru muyi asararsa ,wallahi idan ban kashe mrym acikin estate din ba zan shirya inda zan kasheta "tsaki yaja yana cewa "ban san me yasa kike son Kiyi kisa akan wannan dan iskan yaron ba baba qarami ya fad'a yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa ."

matsawa tayi kusa dashi ta qarasa bakin gadonta tana jan zanin gadon tana sake shimfidawa "hakika zanyi abinda yafi kissa akanshi idan akwai ,kuma zan mutu amman kafin na mutu duk sai na rabashi da masu sonshi idan kuma nayi nasara asirina bai tono ba zan mallakesa idan kuma ban mallakesa ba shima zan kashesa a karshe na kashe kaina da kaina shikenan na mutu cikin salama ta qarasa mgnr tare da kwanciya tana mai kamkame jikinta waje daya wani son ATA ne Ke sake ratsa koina a sansar jiknta yayinda tsumammiyar soyayyarsa data dauki tsawon shekaru tana yi masa ya dinga taso mata kuka ta fashe dashi dan tana son rage wa kanta radadin dake makale a tsokar dake qirjinta a fusace baba qarami ya fice ya bugo kofar dakin da karfi har sai da qararrawar zuciyarta ta amsa ."

Ammi da nana hauwa'u diyana humaira suna zaune a saman kujera,yayinda maryam ke zaune a qasan carfet humaira na yi mata kitso hirar abinda ya faru da nuzla suke kadan kadan suna mamakinta diyana tana cewa "wallah gara da yaya adam yasa aka ka mata ni yanzu nake tunanin ma itace ta kashe mubina "babu mamaki dan mutun abun tsoro ne inji cewar humaira ."

"A'a karki ce haka diyana Allah ne kadai yasan wanda ya kashe mubina tunda ita ba anan aka kasheta ba kuyi wa yaruwarku kyakkyawan zato , mami Kiyi tunani da kyau da irin wukar da akayi yunkurin kashe maraym da ita aka kashe mubina , me yasa zakiyi zarginta ?sannna akan wani dalili har zata aikata hakan akan mubinarmu bayan gabadayanmu muna son mubina nana hauwa ta tmyta ? Wannna fa ba zargi bane tunda yaya adam yasa aka kamata kunsan akwai wata a kasa babu rami me ya kawo rami ."?

"Ni kuma nafi tunanina akan yaya adam ne inji cewar humaira "akan yaya adam kamar ya ? duk suka kalleta fuskarsu da alamun tambaya "ai ta dade tana son shi kusan ranar da mubina ta furta agabanmu cewar tana mutuwar son yaya adam hankalinta ya tashi .
duk suka natsu suna sauraron humaira ta cigaba ai bayan mun rabu ni ta fad'a min amman alaokacin cewa tayi tunda mubina ta rigata furtawa ita ta hakura sai kwatsam sai ga mutuwarta ni tun lokacin naso na fasa maganar amman nayi shiru gudun abinda zai je yazo ."nana hauwa tayi shiru kafin daga baya ta numfasa bata tunanin nuzla zatai haka dan ko byn mutuwar mubina ta dade tana jin mutuwar ,ita kam maryam ta yarda da hakan dan lokacin da akayi yunkurin kasheta kowa yazo amma ita bata zo tayi mata jaje ba ."

"Lallai mami danki yayi kasuwa dan ita karon kanta a ynzu ta fara jin son shi aranta amman kuma meye a attare dashi da kowa Ke son shi haka ? tana jinsu suka cigaba da hira batare data tsoma bakinta ba ."suna cikin hirarsu ATA ya sanya hannunshi ya turo qofar falon tare da sallama akan labbansa duk da bai bude muryarshi sosai ba,maryam dake kallon kofar shigowa ta dago fararen idanunta suka sauka cikin nashi sanda yake takowa cikin falon mami na masa duban mamakin dawowarsa adaidai lokacin sosai ya dauki hankalin maryam dan yayi wani fresh ya qara kyau kaman wani sabon matashi amma fa fuskar nan tashi tana nan kamar koda yaushe babu annuri a hade da miskilancin wanda na yanzu ya qaru "

Kallo daya yayi mata tai saurin janye idanuta akan shi shima ya maida kallonsa kan mami fuskarshi babu yabo babu fallasa"Lafiya dai ko adamcy Nah naga ka dawo by this time ?"Lafiya qalau sweetheart ..." Ya fadi alokacin da yake qoqarin zama a saman daya daga cikin kujerun falon idanunshi na kallon sama suka hada baki suka gaisa ya amsa da "Lfy !
kawai "Adamcy yanzu me ake ciki akan halimatu ne ? ni kaina yanzu bazance komai ba sai abinda hukuma suka ce " ya fad'a yana furzar da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login