Showing 69001 words to 72000 words out of 168608 words

Chapter 24 - Mar'adam's Book 1 Hausa Novel Complete

taji nan fa suka sake din kewa da ussein soyayya  ta  sake karfi   har tafi nada da zara ta fito daga gida  suke haduwa dashi  km ni na tabbatarwa kaina  bazasu ga junansu su bar junansu  hk ba  tunda sun dandani juna dole sai sunyi wani abu duk da  shiedar zina tana da wahala  "to ! bazan manta ba ranar wata asabar da safe ta fito daga gidansu da nufin zuwa islamiyya kai tsaye dakin ussein ta zarto ashe ana biye daita abaya batasani ba har ta shiga dakinsa  tana shiga suka fara abinda suka saba suna cikin wannan halin sai shigowar mutanen gidansu  sukaji  tana rungume ajikinsa  aiko ranar munga tashin hankalin da bamu ta'ba gani ba ."



Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
     MAR'ADAMS
     💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗


*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number  din 1438775094 Aishat abdullahi access idan  an tura sai a turawa wannan  09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.


      
               Page 18

"wato  afa  akan dai  yarinyar nan ce  da  nazo  akanta  yar  kanin mijina  daya  mutu ya barmana amatsayin  riko  to malam  kamar yadda kasani  banason  yarinyar nan na  tsani  na  ganta  dan  ina ji ajikina  akwai  nasarori  da  anan  gaba  zata  iya  samu  domin soyayyar  da  mutane  suke  nuna mata  kamar  ma aikinka  na  farko bai  ci  ba, yanzu  haka samari  sunfi  biyar  da  suka  nuna suna sonta  sai  dai  dadin  abun  da zarar  sun  zo  lokaci  kad'an   sai su  gudu ."


    "to  ga  aikin  nan  yaci  zaki  ce kamar  aiki  bai ci ba , ai  haka  zasu dinga  zuwa  suna  'bata  mata lokaci  suna  wucewa  batare  da tasamu  wanda  zai  aureta  ba babu  fa  wanda  zai  like  mata acikinsu  sai  matsiyaci da  zarar masu  arziki  sunzo  zasu  gudu ."

"Ai  ni  ba  abinda nake só kenan ba ,ai  bana  son  ko  matsiyaci  ma yazo  wajenta   nafi  son  ta  qare  rayuwarta  a kaskance  a bauta  da  wahala , sai  tawa  yar  saurayin da  yake  sonta  mutun d'aya  ne kuma  ba  wani mai abun  kirki bane  gashi  kace  yarinyata  zata  samu   farinjin  samari  masu  kyau  da kudi sai gashi  sa'banin  haka  nake  gani  madadin  maryama  tayi  bakin jini  acikin  mutane  da samari  duk  banga haka ba ."

"kullum  farinjinta  sake  qaruwa yake  jamaa  suna  matukar  qaunarta  basa  son  kula ya'yana koina  akaje  sai  dai  ace a  gaishe da  maryama  amman  banda ya'yana , wani  abun  bakinciki afa  har  yaran  nawa  suma kullum maryama , suna  matukar  sonta  sunki  su  gane ita din  matsalarsu ce,  ko  wani  abu  nayi  mata  sai dai  kaji  suna  min  fad'a  suna nuna  min  rashin  daidai  nan  ta tsaya  ta  sauke  numfashi da ajiyar zuciya  ,afa  yace  "to  yanzu ki takaita  matsalarki  me  kike son ayi ?

Aunty  salma  ta  gyara  zama  tace "ina  son  a fara  rabata  da ya'yana ina  son  naji  sun  tsaneta  fiyye  da  yadda  nake  jin  tsanarta  acikin  raina  wannan  shine  kawai muradina  kafin  nazo  neman wani bukatar  ."afa  yayi  murmushi yace "ai  wannan  shi  yafi  komai  sauki ki  tafi  gida  kawai  zaki  ga aiki da cikawa  cikin  sati  biyu  masu zuwa , amman  ina  son  ki  dawo kafin  kwanakin su cika  akwai abinda  zan  baki  indai  har  na baki  ki  kai   amfani  dashi  magana  ta  qare  amman  yanzu zan  fara  jaraba  'yan  abinda bazaa  rasa ba ."

aunty  salma  tayi  godiya  ta  ajiye masa  kudi  ta  fice  tana  faman zuba  godiya  tana  cigaba da zagi da  maseefar  kiyayyarta  da maryama  har  ta  fice  daga  gidan afa  ta  dawo  gida  tana saka da warwara  dan ita ko kashe maryama afa  zai  yi  tana só saboda  tsanar  datai  mata  yarinya sai kace lu'u lu'u ai muddin tana  cikin  gidan  sai  ya'yanta  sun  rigata  samun  gidan  aure kafin  tayi  ,idan  kuma  har  zata yi auren  zata sa afa  yayi  mata aikin  da zata  auri  matsiyacin  daya fi ubanta  talauci ."

*****
Bayan  kwana  biyu  da  faruwar wannan  alamarin  maryama  tana tafiya  cikin  kayan  islamiyya ta Ardus-salam   yayinda  hannunta ke rungume  alqurani , yammaci ne duk  mazan  unguwarsu  sun  dawo  daga   aiki  duk  inda  ta  wulga  sai an  kalleta da  shaawar  tafiyarta   tmkr  bata  son  taka qasa tana   cikin  tafiya  taji  tafiya  abayanta  bata  juya ba dan  hakan  baya  daga  cikin d'abiarta ,  sai  ma   qara  saurin da tayi  ta cigaba da  tafiyarta saboda tasan  kowaye  ita yake  bi  zarginta  ma  cikin  samarin  unguwarsu  ne   dan  akwai  masu  nuna  suna  sonta  acikinsu ."

"maryama  wannan  uban sauri haka  da  kike  zabgawa ko dan gudun  kar  na  biyoki ne ?ta  tsaya cak  lokacin  data  fahimci  muryar malamin  islamiyyarsu ne  na Ardus-salam  mlm  yahuza  ta juyo a natse  ta  dubeshi  cikin nikaf dinta  tare  da  girmamawa ta gaishesa  ."ya  gyara  tsayuwarsa  yana kallonta , kunyarta  ita  tafi  komai tsoratashi  ,duk  iya  takun  saurayi  in  har  ya  had'u  da  mace  mai kunya  yana  samun  karaya matuka  a zuciyarsa ."

yayi  dan  murmushi  irin nasu  na ustaz "maryama  har  kullum zuciyata  bata  da  sukuni  jiddan wala  khairan  ,na  kasa mantawa dake  ,bani  da wani  sukuni  face na  samu  amsarki  game  da bukatata  dana  kawo  miki  ."yayi  shiru  tare  da tsayawa  yana sauraron  yaji  me  zatace  nan take  tayi  kicin  kicin  tamkar wacce  aka  tsare  da wuka  zaa yankata sai da ta  dauki  second  goma  sannan  tace "uhm  !sai   kuma  tayi  shiru  ta  qasa  qarasa  abinda zata fad'a  maganar ta makale acikin zuciyarta  shi  kanshi ganin motsa  lip's  dinta  bai  sawa ranshi cewar zatace  uffan ba  bayan  abinda ta furta  ba ."
ba  yau  bane farko haka  zalika  yasan  ba  yau  bane zai  zama   karshe ya  saba tareta a hanya  ta kasa ko  ambaton  sunan shi  bama shi  kadai  ba  kusan  mutane  suna  yawon  fad'ar  haka akanta   bata  da  yawon  surutu  da  saurin  sabo  da  mutun  duk wanda  ka  ganta dashi  tana d'ar d'ar  alamun  tsoro  shima dan matsayin  da  yake  dashi  na malaminta ne  yasa  har  ta tsaya akan  hanya  babu wanda ya kai ta tsaya  dashi  akan  hanya ".

"Maryama  idan  na lura  da yanayin  fuskarki  ba soyayyata bace  baki  amsa ba  amman kuma bazan  tabbatar akan cewar kin amsa  ba  ,tunda a kwayar idanunki kawai  nake  iya  karantawa shine kunya  ce ta  hanaki  ki  fad'ar   abinda  Ke  cikin  zuciyarki maryama  ki  daure  ki sanar dani menenê  acikin  zuciyarki  akaina  ko  zuciyata  zata  samu  sukuni da natsuwa  ?".


shirun  dai  da  baya  só  shi  tayi dan  bata  da  abinda  zatace  masa  ,bazata  iya  wata  soyayya ba  da'ace  ta d'aurawa  kanta  soyayyar  samari  da  lokacin da suke  guduwa  suna  barinta da ba qaramin  tashin  hankali  zata  shiga ba  gara  ta qarasa rayuwarta  haka  tunda  soyayya  ba  dole bane  arayuwar   mutun  haka  ma  aure   sunah ne matukar  mutun  zai  iya  rike   kanshi   domin  acikin
Sahbbai  ma  akwai  wad'an da  suka mutu basuyi aure  ba  dan  haka  mutun  zai  iya zamansa  haka   kuma   aure   da  haihuwa  bashi  bane   karshen   duniya  a ganinta  ko  babu  shi  mutun zai iya  rayuwarsa ."

"hakika   maryama   duk   cikin  unguwar  nan  kai  garin  nan  ma  gbdy  har  cikin  islamiyyarmu banga  diya  macen  da  take  burgeni   kuma   zuciyata  take dawainiya   da tarin  soyayyata  kamar ki ba ki samar  da  amsar  soyayyata a cikin  zuciyarki   ko zan samu farinciki da  sukuni  koda  ta  wata  sigace  da  zan fahimta ."sosai  hankalinta  ya  kai  kololuwar tashi  tama  qasa  tsayuwa  bisa kafafunta , kafafunta suka   shiga karkarwa  ,yana  son  ya  bata dama  ta  wuce  gida  saboda  halin  daya  karanta  atattare  daita amman  kuma  bai  gaji  da  kallonta  ba  kuma shi yasani ko zai kwana  tsaye  atare  daita  bazai gaji  ba , sakina  da kanwata ne suka  zo  zasu  giftasu malam yahuza  yayi  sauri yace "sakina ku tsaya  ga  maryama  tsaye  ku wuce  gida  tare ."

Shukura  ta  kallesa  tana  jin  wani  irin  tuttukin  bakinciki   acikin   zuciyarta   abun  yayi matukar  bata  mamaki  maryama  tare da mlm yahuza malamin da  take  matukar  só  amman  tsoro da  shakkansa   ya   hanata   fito  da  soyayyarsa
"malam ! kawai  tace  tayi  gaba  tana  jan  tsaki  acikin  ranta  dan tasan muddin  tayi a fili ta kad'e  har  ganyenta  dan  mlm  yahuza  babu wasa  wajen  disfila  d'alibai  da  iya  karatu  da  d'aukar  wanka  ga  tsantsar  kyau  shiyasa  kowani  d'alibi  ke  matukar  jin   tsoronsa  a kaf  ardus-salam  babu  malamin  da'ake   shakka  da só kamarsa  da yawa yammata  na   qaunarsa ."sakina  kam   jikinta  a matukar sanyaye  ta  wuce  batare  datayi  mgn  ba  maryama  ta  bita da  idanuwanta  wani  abu ya soki zuciyarta  domin tun safiyar yau ta lura  sakina  ta  canza  mata abun ya  matukar d'aure  mata  kai amman  tayi  mata  uzuri  da cewa yanayin  rayuwa  ne ."

Mlm  yahuza  bai  sake  magana ba sai  tunanin  kunyar  shi da sakina taji  dan  ganinsa  da maryama  yasa  ta  kasa  tsayawa dan haka  yace "maryama  sai  gobe  idan  mun  had'u  a makaranta amman  fa  kisani  bazan  ta'ba  daina  tsaidake  anan  ba har sai ranar  dana  samu  na  cire  kunyar nan  kika  amince min  "Kanta  kawai  ta  gyada  masa muryata  a  matukar sanyaye tace "sai  da  safe  ta  juya  ta  cigaba da  tafiya  a natse  bai  bar wajen ba  sai  da  tayi  nisa  sosai  ta 'bacewa  ganinsa  ."

yana  juyawa  sukai   ido   biyu   da  mlm  umar mai hausa  atare   sukai  murmushi "wato  kai  har  kullum bazaka daina  wahalar da kanka akan maryama ba  ko ?"Mlm yahuza ya qarasa  inda mlm umar yake ya tsaya  yana cewa "ya  zanyi  umar  allah  ya  jarabeni  da  soyayyar  maryama  bazan  iya hakura  daita  ba "kai   kuma  allah  ya  jarabi mata dayawa  da  sonka  ba ?"wannan kuma  damuwarsu  ce ,ai  dama  haka  zaka  fad'a  duk  kuna  son  maso  wani  ,kai  ma ka tausayawa masu  sonka  sai  allah  ya duba lamarinka  ".

"Allah  ma  ya sani  babu  wacce nasan  tana  sona  bare na tausayawa  ya fad'a yana wani  sham kamshi  "Uhm uhm  mutumina  banda  fad'ar son  rai   duk  wanda  ka  fadawa  haka  zai  d'auka  bakasan  abinda kakeyi  ba ,"kaga  umar rabani da wannan  zance  mu  barta  matsawar  bata  sarauniyar  mata zaka  min  ba "karka  duba yanayin  gidansu  maryama  amman  dai  kai  kanka  kasan  tafi  karfin  aurenka , maryama  macece  daya  kamata wani  hamshakin mai kudi  yayi wuf daita ."

dan  murmushi  mlm  yahuza  yayi yace "haka  ne  amman  ai  duk  mace   bata  fi  karfin  auren  nmj ba kuma  kowani   mutun  yana da nashi  matsayin  da  zai  iya  burge mace , kuma  ina  dashi  ina da quality da  mace  zata  soni  koda kuwa   bani   da  kosisi  bugu  da  qari  ita  mace  ba  kudi  take  bukata a soyayya  da  kulawa  take so ni  nan  kuma  zan  kula da maryama   ."

"da  me  zaka  kula  daita ?karka  manta  ita  din  cikakkiyar 'yar boko ce , yarinyar  da  idan  ta  fara aiki  yanzu  sai  ta  d'auki  nauyin ciyar da  mutanen  gidanku  gbdy  dan haka  banga abinda zai sa ka dinga wahalar  da  kanka  kana 'batawa kanka  lokaci  akanta  ba , kayi hakuri ka rabu daita  domin dai babban goro sai  magogin karfe ."


Mlm yahuza  ya  dan ji  zafin maganar  malam  umar dan haka ya  rage  farar  fuskashi "wai me kake  nufi ? kana nufin dan  ita din yar boko ce  tana da  kyau na bugawa a jarida  kana tunanin zata samu aiki  nan  gaba  zai sa ta  iya fin karfin  halittar  ubangiji "? yahuza  abinda  nake  son ka fahimta duk  wad'an nan  abubuwa da  kake  gani  fifiko ne a tsakaninka  da maryama  kawai  abinda  nake so  kaji  aranka  tafi  karfinka tafi  karfin  aurenka  ."

"kaga  dan  allah  mlm ka  barni ka zuba  min  ido ba wahalar banza nake  yi  ba ina cikin zuciyarta kunyar da take yawon nunawa akaina ta wadatar dani cewar nayi mata , nan  gaba kad'an zata fahimtar  dani  ."Ka  dai  bi a sannu kar  wata  rana  kana zaune wani hamshakin  mai  kudi ya shigo har cikin  unguwar  nan  ya  aureta .".

"bari  kaji  babu  wani  mai  kudin da  zai  aureta  domin  suma  masu kudin  sunfi  son ya'yan masu kudi yanuwansu , ita  maryamar da ba  galihu ne  daita  ba ,ai  ba uban da  zai  shigo  cikin  wannan  rubabbiyar  unguwar   ya   kwashta ai  duk wannan  kyawun  nata akan  irinmu  zai  qare "yana  gama fadar haka ya  juya  dan  baya  son  ya  sake 'bata  masa  rai ."


Tafiya  kawai  maryama  take zuciyarta  cike  da  kunci  da  tunani  barkatai  ba  kuma  akan mlm  yahuza  ba   sai  sabon  sauyin  data  gani  akan  fuskar  sakina  dan  na  shukura   mai  sauki ne idan  da  sabo  ta  saba  ita  da yaran  aunty  hassana  haka  suke mata  amman  sakina  fa  basu saba  haka  ba  suna  matukar  qaunar  junansu  tun  suna  yara su din  masoya  ne  na  hakika ."


da  wannan   tunani  ta  qarasa  cikin   gidansu   kai   tsaye   ta  nufi  bangaren su  sakina   domin  tambayarta  dalilin  sauyawarta  ashe  wahala ce  ta  shigo  daita  tana sallama  aunty  salma  tace " Yauwa maryama  d'auki   tsintsiyar  ki   share  min  d'akuna  tas   shine  amsar  sallamar  da aunty salma tayi  mata  kamar  tace  bazatai ba amman  ta  kasa  ta  ajiye alquranin  dake  hannunta  ta  d'auko  tsintsiya  ta  fara  shara  batare  da wata  damuwa  ba ."

tana  shara  aunty  salma  na  zaginta  ita  da  shukura   amman  sakina  na  zaune  batace  komai  ba  sa'banin da da bata  yarda a  zageta  ko  sakata aiki  akan  idanunta  ,tana  shara wani  gurin  da  simiti  wani gurin babu  ga  kuma  sakina  na   zaune ta  d'ago  idanunta  a  natse ta  kalleta  taga  kurar sharar  na zuwa inda  take  muryata a sanyaye tace "sakinata   ina  ganin  sai  kin  d'an  tashi  kinga  kurar  tana  zuwa  inda  kike  ta  wani  watso  mata harara  "ai  gudun  ruwanki  nake  kallo  naga zaki shareni  ko  kuwa   ."?

maryama  tayi  shiru  tsaye  tana karantarta  akwai  wulakanci  acikin   maganarta  "ke  kika  kyaleta  aunty  sakina  amman  banda  jakanta  irin  nata tana   kallon  mutane  suna  zaune zatace  su  matsa , banza  shasha  kawai   mai  siffar  mayu ." inji  cewar  shukara  dake  zaune  kusa  da  aunty  salma  abun  bai  yiwa  aunty salma  dadi  sosai  ba  domin  kuwa  sakina taso ta furta ma  maryama  haka  ba shukura ba  ,sakina  kam  tun maganar  farko  datai  bata  qara ba  ta  tashi  cikin  bacin  rai  ta  shige  daki tana jin  wani  zazzafan  kiyayyar  maryama  ."


Maryama  tayi  shiru  kawai  tana bin    shukura  da  kallo "me  kuma  hakan  yake  nufi  dani ? me na yiwa  sakina  ni  kuwa  daga  jiya zuwa  yau  take  fushi  daita  hk ."tayi wa  kanta  tambayar  da  bata  da mai  bata  amsa  sai  sakina  ita  zagin  shukura  bai  dameta  ba kamar  sauyawar  sakina  ta gyada kanta  ta  cigaba  da  shara  tana tunanin  laifin  da taiwa  sakina  har ta  qarasa  ta  wanke  hannunta  da kafafunta  ta d'auki  quraninta ta shiga  d'aki  inda  sakina  take  zaune  akan  gado  tana  cika  tana batsewa  tana  ganin  maryama ta  sake  had'e rai Kmr  taga  mugun  abu  maryama bata damu ba ta zauna  kusa  daita  ta  soma  janta  da mgn taso  tmbyrta  laifin  da  tayi  mata  amman  ganin  yadda  take barsarwa  yasa  tayi  shiru  daga  karshe ta wuce  zuciyarta  cike  da  matsanancin damuwa ."

*******

Da  misalin   karfe  d'aya   na  ranar  laraba  wanda  yayi  daidai  da sauran  kwana uku  jirgin  mr ata  ya tashi   zuwa   france   amman  har  lokacin  jikinsa   sai  a hankali  daga  matsanancin  ciwon  kai  ya dawo  masa  ciwon  gabobin  jiki  dan  ko  miyo  baya iya  had'eyewa  sosai  mami  ta  sauko  daga  saman   d'akin    mr  ata  tare da  likitansa  byn  mami  ta sallame  doctor  rafeeq  ta  dubi  maryam  da  nana  hauwa'u tace   "yayanku  fa  yau   tsawon  kwana   biyu bashi  da  lafiya  ku  shiga  ku  gaishesa  keda maryama  ,jiki  sanyaye  suka  ce" to!  suka  mike atare  suka   hau sama ."

A natse   sukai  knocking  wanda  nana   hauwa'u  ce  tayi   mryam  na  bayanta  ara'be  kusan  second  goma   suka  d'auka  tsaye sannan  ya  basu   damar  shigowa  d,akin  ,da  sallama  suka  shiga  parlour  suka   gansa  kwance   akan  doguwar  kujerar kushin ya   runtse  idanuwanshi  yana   sanye  da  riga  fari  sol  da  gajeren   wondo  iya  gwiwarsa  yayinda   hannunsa  d'aya  Ke  daidai  saitin  zuciyarsa  ya  d'an  bud'e  idanuwanshi  kad'an  ganinsu  yasa  ya    maida  idanuwanshi  ya  runtse  gam."

nana  hauwa'u  tace "sannu  yayanmu  ya jikin  naka kayi  hakuri  walllahi  bamu  san  baka  da  lafiya ba sai  yanzu  da  mami ta sauko  take  fad'a  mana  " shiru  yayi   bai  amsa  mata ba  nan  da nan  maryam ta  shiga  hankalinta  dan tasan  ita  kam  sai ya  had'a   mata  da  tsaki  muddin  tayi  masa  sannu   suna  zaune  shiru  nana  hauwa'u  ta d'an ta'ba maryam  tana  mai  mata  alamar  ta  gaishesa wani abu mai  d'aci  daya  tsaya  mata a  wuya ta had'iye  ta  bud'e  baki  muryarta na  rawa "yaya  sannu "ta fad'a  atakaice  ilai  kuwa  tunaninta ya tabbata  dan kuwa  bai  amsa  ba  sai  ma  tsakin  daya  ja yana  cewa "auta  ya  bani   abun  na  sha a fridge da  saurinta  ta mike ta isa  inda  qaramin  fridge  dinsa   yake  ta  bud'e  donsimo ta  d'auko  masa ta had'a masa  da  ruwa  ta ajiye  masa  akan  table din  dake  gabansa  ."

"gashi  yaya Allah ya  baka  lafiya  ya  d'an  motsa lip's  dinsa  alamun ya amsa ya mike  zaune  da  kyar  batare  daya  kalli  inda  mrym  take  ba  itama bata sake  kallon  inda  yake  ba sai ma fuskarta  dake  kallon  wani   katon hotonsa  dake manne  da bangon falon   sanye  cikin  kananan  kaya  riga  da  wondo  milk  colour  touch  of  black  ya  zura  hannuwansa  duka  cikin  aljihun  wondonsa idanuwanshi manne da  farin  glass  fuskar  nan  tashi  a had'e  Kmr koda  yaushe  "auta  !
Ya  kira  sunan  nana  hauwa'u  ta amsa da "na'am yaya! "shiga  bedroom  ki d'auko  min wayoyina da sauri  ta shiga wayoyin na kan katifarsa ta  d'auko tana  danna  gefen  wayar  inda  nan take wayar ta kawo  haske  screen ta  duba  fusakar  wayar wata kyakkyawar  fuska ta  gani  kanta  babu  d'ankwali gashin  kanta  ya  zubo kad'an ya rufe mata gefen  idanunta ."

ta tsurawa hoton ido sosai nan ta gane zane ne ba asalin  hoto ba ahankali take tafiya tana  kallon  fuskar  wayar  duk  da  zane  ne  ,amman  yarinyar  tayi  matukar  yi  mata  kyau ta kai  masa  tana cewa "yaya  zanen dake  kan screen din wayarka yayi min kyau  sosai wacece ?"tayi  masa tmbyr  tana duban mrym  da  hankalinta baya kansu yana can kallon mr ata , tana kallon kyaun da allah yayi masa ba abinda yafi  burgeta dashi kamar sheidar sallarsa daya fito

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login