Showing 114001 words to 117000 words out of 168608 words
ya bashi amsa da haka ,allah sarki allah ya jikinsa shima yasa suna aljanna Ameen ai kasan ita maryama bata fiyye son shiga cikin mutane ba mussaman idan bakin fuska ne allah ya zuba mata kunya gashi ita har ta qare karatunta na digree yanzu haka ta fara bautar qasa ta kuma yi saukar alquranin mai girma tana da hadda uzu arbain da wani abu akanta ."
"kai masha allah a she dai kuna da zakakura acikin dangi ?"sukayi dariya kawai suna yiwa ussein addau "gsky ussein yayi saa arayuwarsa duk wannan rashin jin maganar daya ta'ba amman allah ya albarkacesa da samun yarinya mai kokari haka "? wallahi abun na allah ne yaransa ma duk masu natsuwa sai ma ka gansu, yabon ummah sam bai yi kowannensu dadi ba amman babu yadda zasu yi tunda umma ce
kuma sun san adalilin ta suka zo gidan"ai ina qaunar ussein domin shi din mutun ne mai barkwanci da son mutane ai naso na dawo qasar nan na iske shi a raye maryama tana cikin dakin ummah duk tana jin maganar Alhaji alqasim da ummah tana jin matukar qaunar mahaifinta alokacin da bataji tahirinsu da mahaifiyarta ba amman daga baya dataji komai sai ta daina kewar babanta duk da ba wani saninsa tayi ba dan duk lokacin data tunashi sai damuwarta ta ninku acikin zuciyarta ganinta shine ya raba aunty da yanuwata ,bugu da qari yadda kowa yasan mahaifinta baya jin magana."
kuka taji ya kwace mata "Ke shukura je ki kira min maryama taí Jim dan tasan tana dakin ummah amman dan bakinciki karta gaisa da bakin yasa ta fice Jim kadan ta dawo tace "aunty tace bata nan ,bata nan kuma ?ummah ta furta a fili tana qoqarin neman layin aunty can bayan Kmr second goma maryama tajiyo muryar ummah na kiran sunanta "maryama maryama !! hakan yasa tai saurin mikewa ta share idanunta da gefen hijab dinta ta fito ko hada idanu ta kasa da bakin saboda tsura mata idanun da matarshi da shi kanshi Alhaji alqasim sukayi ."
"Haka diyar ussein ta girma lallai dan mutun sai allah ussein din guda nawa yake har da 'ya haka ?ita dai maryama gaisuwa ce kawai nata domin bata da abun cewa hjy mustafshira ta shafa kanta sannunki kinji ya aiki da fatan yana tafiyar miki yadda ya kamata kyakkyawa dake tubarkalla masha allah shine kika fitowa kizo mu gaisa ko ?
Ta dan yi murmushi ta dago kanta tana kallonta amamn still ta kasa cewa komai "me ya sameki kamar kuka naga kinyi bata san hawaye na makale da idanunta ba da sauri tasa gefen hijab dinta tana sharewa hjy mustafshira ta qaraso ta dagata daga tsugunno datayi ta dan rungumeta ajikinta "babu mamakin maganr da mukayi ta mahaifinta ce tasa ta kuka ita kanta ummah ta shiga damuwar ganin hawayenta ,ki daina kuka kinji allah zai kai rahama kabarinsa Kiyi hakuri ki cigaba da yi masa addaua shi kanshi yana can yana alfahari da samu diya kamarki mai riko da addini kai kawai ta daga mata tana qara goge kwallar data taru a idanunta aunty salma da aunty hassana da yaransu kuwa babu abinda suke aikin yi sai harare harare iri iri da bakinciki ."
"Ai mahaifiyar ce ta shigo dazu muka gaisa ko ? alhj alqasim ya tambaya yana duban baba gali "Eh itace baba gali yayi saurin fad'ar haka ai tunda ussein ya mutu taki koma wajen danginta bare tayi wani auren ta cigaba da zama anan ai kasan yadda akayi aure danginta saboda rashin son useein din suka sall.."
"Eh nasan komai abban sadam duk ya fad'a min alokacin amman dai nayi tunanin komai ya wuce zuwa yanzu Alhj alqasim ya katse maganar ya zura hannu cikin aljihunsa ya zaro kudi bandir daya na yan dubu dubu ya damka ma maryama taki amsa tare da cewa ya barshi sai ummah ce ta karba ."
Gabadaya sai daya bisu da kudi yana cewa" in sha allahu zan sake dawowa nan kusa tare da yarana gbdy asan juna kafin mu tattara mu bar qasar yayi gaba yaya sadam ya bishi da baba gali hajiya mustafshira bata saki hannun maryama har bakin mota ita dai bata ce komai ba binta kawai take da alamun tausayinta ne ya game jikinta sai faman hakuri take bata sukai sallama tayi mata godiya sosai suka shiga mota suka tafi ."
Ita da yaya sadam da baba gali suka koma gida kai tsaye dakinsu ta nufa da yamma ummah ta shigo ta mika wa aunty kyautar kudin data samu aunty tace "a'a bazan karba ba ummah saboda me balkisu ? Ki rike kawai domin kece mai yin hidima acikin gidan nan bare ma akanmu wannan ai ba wani abu bane amana ce rike a hannuna, ni dai kawai ki rike ."
"to ki cire wani abu aciki aunty tasa hannu ta zari dubu daya ummah ta girgiza kai tana cewa allah baki isa ba kin kuwa san ko nawa ne dubu dari ne fa shine zaki cire dubu daya ta raba kudin biyu ta mika mata rabi allah sunyi yawa ummah bazan karba ba nifa ba butulu bace nasan ya kamata ta cire naira dubu biyar tana cewa wallahi iya su sun isa allah yasa albarka rantsuwar datayi yasa ummah bata qara cewa komai ba ta mike ta koma wajenta ."
Da yammacin ranar maryama ta shirya zata wuce makaranta islamiyya "aunty ni na wuce makaranta sai kin dawo princess idan kinga malam yahuza ki gaishe min dashi maryama tayi shiru tana kallonta
"Eh haka na fad'a har yanzu zuciyata tana qaunarsa dan haka kice masa ina gaishesa "to ! kawai maryam ta fad'a tasa kai ta wuce zuciyarta cunkushe da damuwar abinda baba gali yayi shi kansa alhj alqasim din yasan maganar bata dace ba shiyasa ya katsesa ".
ta kusan kai bakin get din Ardus salam ta hango mlm yahuza yana tahowa ta hanya mai fitar da mutun afanla ta cigaba da tafiya a natse adaidai lokaci daya suka iso bakin get ta gaishesa ya amsa fuskarshi babu annuri sosai bata damu ba domin sakon aunty kawai take son isarwa "aunty tace tana gaisheka "na gode kawai yace yayi gaba ya barta tsaye abun yaso ya bata haushi amman tunawa datai baya cikin haiyacinsa yasa bata ji komai ba sai dai ta kasa cigaba da daga kafafuwanta tayi shiru kawai bata san a tsaye take ba ashe ta kasa tafiya ne sai da wata kawarta lauratu tazo wucewa .
"Ke kuwa tsayuwar me kike anan kamar mai jiran wani nan ta diririce "Ke na hango ai kin kusan qarasowa shi yasa na tsaya ta dai jita ne kawai amman alamunta basu nuna hakan ba suka shiga makaranta tare koda mlm yahuza ya shigo ajinsu domin kara masu karatu ko inda take baya kallo sabanin da in har yana cikin ajin murmushinsa kadai ya isheta bayan an tashi ta dan tsaya hira da kawayenta koda suka rabu ta nufi hanyar inda suke tsayawa dashi anan ta ganshi shi da shukura ko kunya babu tasan kuma duk sharrin shukura ne dan ta gansu sosai ne hakan bai dameta ba tunda idan kayi da kyau zaka ga da kyau idan ma akasin haka kayi zaka girbi abinda ka shuka ta wucesu cikin fushin zuciya har ta isa gida abun na cinta arai wai yanzu duk abinda mlm yahuza yake fad'a mata akan soyayyarsa ya tashi abanza ya koma kan shukura hakika basu yi mata adalci ba amman ta barwa allah komai ."
*******
Zaune mr ata yake acikin masaukinsa yana jiran abokinsa bashir sosai yayi kyau sai dai ace masha allah dan yanayin gyara tattare da kulawar da jikinsa yake samu ya hana shekarunsa bayyyana dan idan ba kaji shekarunsa ba bazaka ta'ba cewa ya kai 40 wani abu ba , zaka dauka shekarunsa basu wuce talatin a duniya ba fatar jikinsa kawai ka kalla kasan kudi suna aiki ba karya haka ma kayan jikinsa tun daga kan wondo rigarsa takalminsa har zuwa agogon dake makale a hannunsa dukansu tsadaddun gaske né ,shine ma ya zana da kansa kaf duniya su uku kawai ke da irinsa shi mb sai bashir abokinsa rolex ne mai shegn kyau ."
ya hade rai sosai kana kallonsa kasan yana cikin damuwa mai tsanani maganganun sweetheart dinsa yake tunowa a wayar da sukai daita a wannin data gabata. inda take sake jadda masa alqawarin da yayi mata kafin ya bar qasar , koda yayi qoqarin sake lallabata cewa tayi "kada kace min komai bana son jin wani kalaman yaudararka gareni ,kasani a wata biyu din da kace zakayi yau sauran sati daya ka dawo ."amman idan bazaka dawo ba ,ka cigaba da zama adamcy kayi son ranka kayi abinda kaga dama kayi abinda kaga yafi maka arayuwa ,amman kuma idan ka san zaka dawo ka dawo kamar yadda mukayi alkwari da kai ,karka dawo da wani abu a zuciyarka ka bar duk wani mugun nufinka a inda kake ,karka dawo gareni da mugun nufi ka barni na cigaba da rayuwa babu kai domin dawowarka da wani sabon salon yaudara ko mugun nufi zai sa nayi maka abinda har ka mutu bazaka daina mamakina ba abun bazai mana kyua ba adamcy ta fad'a tana kashe wayarta."
zuciyarsa ta sake cika da tashin hankali "ina zai ma
iya karya alqawarin da yayi sweetheart dinsa ?
ya shiru kawai yana ciza gefen lips dinsa ,ina bazai iya ba bazai iya karyar mata da zuciya ba ita din jigon rayuwarsa ce zai iya yin komai domin yaga ya faranta mata kamar yadda yasan zata iya sadaukar masa da faricinta haka shima a yanzu ma da yaji muryarta tausayinta ya cika zuciyarsa "
ahankali ya daga tsumammun idanunshi ya sauke su akan agogon dake daure a hannunsa 11:44 am tsaki yaja "what a heck sannan ya gyara zamansa "kada kace min komai bana son jin wani kalaman yaudarar ka gareni ,kasani a wata biyu din da kace zakayi yau sauran sati daya ka dawo ."amman idan bazaka dawo ba ,ka cigaba da zama adamcy kayi son ranka kayi abinda kaga dama kayi abinda kaga yafi maka arayuwa ,amman kuma idan ka san zaka dawo ka dawo kamar yadda mukayi alkwari da kai ,karka dawo da wani abu a zuciyarka ka bar duk wani mugun nufinka a inda kake ,karka dawo gareni da mugun nufi ka barni na cigaba da rayuwa babu kai domin dawowarka da wani sabon salon yaudara ko mugun nufi zai sa nayi maka abinda har ka mutu bazaka daina mamakina ba abun bazai mana kyua ba adamcy ."
"shine kawai abinda yake ta yawo acikin kwa kwaluwarsa "why sweetheart ?me yasa kika kasa fahimtata instead ki barni tunda na nuna bana son auren nan ya allah ka kawo dalilin da zai sa a fasa auren nan na huta tsaki yayi inda fuskar princess keta masa yawo a cikin idanunsa da sauri ya runtse idanunshi dan a halin yanzu baya son ko tunawa daita ahankali akayi knocking din kofar parlour'n yana daga kwance yayi nisa cikin tunani shiru bashiri yana jiran a bashi izinin shiga amman shiru daya daga cikin masu tsaronsa ya dan leko dakin yana ringine amman bai bawa mai yin knocking din izinin shiga ba ."
Dan haka ya dawo ya bawa bashir izinin ya shiga dan ya rigada yasan ko waye bashir din a wajensa kuma tun safe ya sheida masu zuwansa,bash ya shigo parlour'n bakinsa dauke da sallama shiru mr ata bai amsa ba ."bashir ya zauna yana fuskantarshi sai dai kusan mintuna goma mr ata bai bude kwayar idanunshi akan bashir ba haka zalika bai ma san da shigowarsa ba ya yunkura ya tashi ya isa inda mr ata yake ya dafa shi a matukar zuciye ya bude idanunshi da niyyar saukewa wanda ya dafa shi maseefa ganin amininsa yasa ya sauke naunayen ajiyar zuciya "kai mutumina meke damunka ne haka duk kayi wani irin ina lura da kai tunda ka sauka a qasar nan kake yawon tunani ?bashir ya fad'a tare da zama a gefensa kallonsa yayi zuciyarsa na zafi "yaushe ka shigo kuma me yasa ka shigo baka nemi izinina ba ?"
Ajiyar zuciya bashir ya sauke sannan yace "kai dai anyi dan iska ina tmbyarka kana tmbyta yanzu dai fara bani amsar tmbyata tukun sai na baka taka numfashi ya sauke mai zafi ,kai dai bari kawai ina cikin rudani auren dole zaa min , bashir ya zaro idanuwa "Ata din dana sani zaawa auren dole ? no no it can be possible ya qarasa mgnr yana dan murmushi,kai ma dai ka fadi haka wai kamata zaayiwa auren dole kamar muna in does day nan ya kwashe komai ya fad'a ma bashir har da alqawarin da yayi wa mami , wallahi bana son yarinyar nan kiyayyarta bazata misaltu a zuciyata ba gbdy zuciyata bata bugawa idan na ganta, kaga mutuwa kusa kenan dariya sosai bashir yayi tuni mr ata ya kule kallonsa yayi rai a bace ,kaji min dan iska ina fad'a maka damuwa kana mun dariya to wallahi maza tashi ka bar nan yanzu ."
"Sorry my friend hukunci mami ne ya bani dry kai da yanzu bata zatar da wannan hukunci akanka ba haka zaka qare rayuwarka kana yaudarar kanka shin zaka tuna kafin mu rabu da kai last na fad'a maka wannan yarinyar mafarkinka ba mutun bace sannan ka guji ranar da mahaifiyarka zata gaji tayi maka irin wannan auren kace bazatayi ba ?kaso wannan yarinyar marym karkazo hannu kazo kana sonta ta samu dama akanka."
" dan Allah bash ka bar wannan maganar ka bar kawo min maganar zan sota ya zaayi na sota ma ?"mr ata ya fad'a cikin tsananin damuwa zan cigaba da rayuwata haka zan bar zuciyata babu kowa cikinta yadda zan cire soyayyar princess a zuciyata bazan bawa kowace mace damar shiga ba sai dai na qare rayuwata haka ,haka dai suka cigaba da tautaunawa bashir na bashi kwarin gwiwar yayiwa mahaifiyarsu biyayya ."
Ana sauran kwana hud'u mr ata ya dawo ya kira mami ya sheida mata ai kuwa taji dadi har ta kasa boye murnar ta , ta tattara kan masu aikinta domin su gyara gida da kuma sauya wasu abubuwa dake gidan sakamakon dawowar dan lelenta jirgin karfe hudu daidai na yammaci ranar lahadi zai sauke su tare da babban yaronsa da masu tsaronsa da sukayi tafiyar tare dan haka mami ta hana kowa sakat acikin gidan daga masu aiki har maryama babu wanda ya zauna suna tsaye bisa kafafunsu duk da tun jiya sun yi redy wasu abubuwa da suka san yafi bukata maryam tana wanke hannunta tana qoqarin fitowa daga kitchen sai ga mami abakin kofar kitchen din suka hadu mami ta kalleta da murmushi kwance a fuskarta ."
"tun daga parlour nah na biyu nake ji kamshin girki fatan kice kikayi komai da kanki ?Allah mami ki tambayi tabawa duk ni nayi su kawai wanke wanke sukeyi gsky idan duk wannan kamshi daga hannunki ne naji dadi Kwarai da gaske dan tun banga abincin ba miyona ya tsinke muje kawai na fara da jin dandanon girkin kafin adamcy ya qaraso ,ai mami idan kikaci sai kunnenki yayi rawa ,haka né hajiya duk ita tayi gsky babu abinda muka tayata sai wanke kwanuka ,hakika tayi qaqari sosai ."
"ai kam yau zan bada maki mai yawa dan tun daga parlour'na nake jiyo kamshi muje suka koma cikin kitchen din tare mami na bude manya kuloli kula farko alkubus da miyar naman rago kula ta biyu shimkafa bastimatic ce da teaw wanda yaji naman kaza sai kula ta uku wanda sakwara ce da miyar egusi wanda yaji ganye ugu da nama da busashen kifi "masha allah mami ta furta a fili "lallai adamcy nah zai ci dadi ,yau kam nasan har da santi zai yi murmushi mrym tayi tana cewa" allah yasa mami allah yasa ya yaba da girkin tayi maganar cikin sanyin murya ,karkiji komai diyata zai yaba ta fada tare da daukar qaramin spoon ta dibi miyar farko ta kai bakinta ".
"Woww miyar nan tayi dadi sosai daya bayan daya ta dinga d'an dana miyar tana lumshe idanunta tana santi da yabawa maryam din ,da gaske mami tayi dadi?sosai tayi kawai abu daya ne zan gyara miki shima idan mutun ya kasance mai son cin maggie dayawa a abinci ne bazai ta'ba miki gyara ba "meye shi mami ?ta tmbyeta cikin tsanani damuwa jikinta har rawa yake ,ki natsu ki kwantar da hankalinki ba wani abu bane maggie zaki rage zubawa miya dayawa ,tun daga tafashe kinsa maggie kuma kinga zakiyi amfani da ruwan miya wajen hada miya dan haka baki bukatar zuba maggie dayawa acikin miyarki yanzu kenan maggie yayi yawa ta fada cikin tashin hankali?bawani yawa bane kawai na gyara miki ne dan gaba idan hannunki yana zarcewa a maggie matsala ne."
" wannan ne kawai maggie yayi yawa ko duka miyar né ?Ki kwantar da hankalinki kusan duka ne amman karki damu aa mami dole na damu dan wallahi idan yasan ni nayi na shiga uku gara kawai na sake wani ."What ? "mami ta furta tana dubanta babu abinda zaki sake anan haka zai ci har yayi santi
ta sauke numfashi tana cewa "amman mami karki ce ni nayi kice kece kikayi dan allah idan yasan ni nayi wallahi karshenta bazai ci ba ,mami ta kalli agogon dake hannunta kinga karki damu muje ki shirya dan jirgin adamcy ya kusan sauka nima bari nayi sauri na shirya kafin a dauko shi yazo yana yiwa mutane naci dan tun jiya yace bazai ci komai ba sai ya dawo ."
Mami ta bawa masu aikinta dake tsaye umarnin su fito da kulolin zuwa dinning suna shirya dinning suna hira suka jiyo sallamar hindu gabdaya suka amsa mata kallo daya mami tayi mata ta dauke kanta tana sanye cikin wani