Showing 12001 words to 15000 words out of 168608 words
baka da aure wallahi kimar ka raguwa take , nima nan da kagani kokarin shawo kan nuzla nake kaga idan allah ya taimakeni ta amince kawai sai a hada bikinmu tare." Mr ATA yaja dogon tsaki ya zabga masa harara Kmr kwayar idanunshi zasuyo waje "naga alamar kai ma baka da hankali kamar wannan "ya fada tare da juya yana kiran all you of are very stupid ."
Ahankali mr ATA yake daga kafafunsa batare da ya sake yin wata magana ba dan idan yace zai cigaba da magana sai dai d'ura masu zagi , yana tafiya yana sake jin bacin rai duk wanda ya gansa yasan yana cikin damuwa ,dan haka masu kula da lafiyarsa duk suka shiga hankalinsu kowa na taka tsantsa ,da sauri escort dinsa suka biyosa cikin kamewa da taka tsantsan kiyaye aikinsu , dan duk lokacin da ransa yake a bace yafi dakatar da mutun daga aiki ."
muhd bello ya biyosa suka jero tare zuwa Inda akayi parking din motocinsa escort suna kokarin bude musu murfin mota yayinda hisham ya juya ya nufi gidansu ."mr ATA na qoqrin shiga mota Kira ya shigo wayarsa ya tsaya cak hade da tura hannunsa cikin aljihunsa ya ciro wayar yana dubawa sunan aunty shahida ya gani yana yawo akan screen din wayar ya furzar da iska me zafi sannan ya danna koren maddanin ya manna wayar a kunnensa yayi shiru yana sauraronta "
can bangaren aunty shahida ta fara magana saboda tasan ba magana zai yi ba "kana Ina yanzu ? shiru ya cigaba da yi yana ciza lips dinsa na kasa sai data sake maimatawa sannan ya bude bakinsa da kyar "Ina shirin barin gida yanzu "to karka kuskura ka bar gida batare da kabawa mami hakuri ba "naji zan dawo anjima da daddare dan tayi fushi sosai yanzu yayi maganar yana runtse idanunshi zuciyarsa na suya "no kaje yanzu saboda nasan ranta yayi mugun 'baci shiyasa kaji nace haka Kuma bana son tayi fushi da kai adam kasan mami na matukar hakuri damu most especially kai tana hakuri da kawaici akan komai, wannan ma ka kaita makura ne "to ni yaya kuke son nayi da rayuwata ne ?
"hakuri sannan kabi umarninta ta fada atakaice "shikenan haka ni rayuwata zata qare cikin kunci Kunki ku tsaya ku fahimceni ? "Wani fahimtarka Kuma zamu tsaya yi tunda an baka lokaci Kaki kayi komai akai ?"fatanmu kayiwa mahaifiyarmu biyayya ka rike mana amanar maryam karka cutar daita sannan na tabbatar maka zakaji dadin maryam dan .."Kinga shahida karki dameni da wani amana ko zan ji dadinta kar in cutar daita "yayi saurin katseta ta hanyar fadar haka " kanku kawai kuke dubawa baka duba halin da zan shiga akan auren nan haka kawai zaku cutar dani akan wani auren baza "shahida kai tsaye ko adam ? "ta tambayesa numfashi ya sauke bai ce komai ba " kiran sunana yau babu ladabi ba komai ba ?"share wannan maganar raina ne ya baci zan zo office din na sameki idan na gama da sweetheart mu tautauna wasu abubuwa daya shafeni ,"
"karka sake Adam kazo min da wani tsari ko rashin kunya dan ba zan tsaya naji raayinka ba sannan kasani bazan dauki raini ba ,dan iskanci tun yaushe ake fama da kai ? shekara biyar kenan ana fama da kai ka fito da mata Kaki kullum ka zaunar da mutane kana masu karyar baka samu tru love ba ,haka kawai kanata batawa kanka lokaci abanza,tukun nama kana wannna iskanci na ji da kai da fadin rai yaushe zaka samu tru love ."?" kai wace shegiyar ce ma zata dauki wannan wulakanci da ji da Kan da kake fama dashi ? ai daman karshenka kenan ayi maka auren dole kaje can ka karata kowa ya huta dan .."bai tsaya Jin abinda zata sake cewa ba ya sauke naunayen ajiyar zuciyar yay disconnecting din Kiran Yana adduar samu sausauci daga gurin mahaifiyarsa ."
ya maida wayar aljihunsa ya koma cikin gidansu a Inda ya bar sweetheart dinsa anan ya isketa zaune gefenta maryam ce ke matsa mata kafafu suna hira cike da tsantsar biyyaya kyakkyawar datjijuwa me tsananin kyau da nagarta da sanin ya kamata da son zaman lafiya da lumana ta d'ago a natse idanunta sanye da farin glass wanda da gani na Kara lafiyar idanu ne ta zuba masa Ido tana mai tsananin qaunar d'anta ."kamshin dadd'adan turarensa (Reed ) mai sanyi da sanyaya zuciya tare da Kashi jiki da sace zuciyar duk wanda sautsayi yasa ya shaka yasa maryam ta fahimci ya sake dawowa falon ,a hankali ta bar abinda take ta dago idanunta dan tabbatarwa kanta shi din ne ko kuwa , ai ganinsa tsaye kikam kamar wani jami'in tsaro ba dan kasuwa ba yasa nan take qirjinta ya shiga dokawar daya Saba a duk sanda zata d'aura idanunta akanshi sannan ta dinga kokuwa da numfashinta kenan har sanda zai bar gurin ."
Ahankali idanunsu ya tsarke cikin juna wani irin kallon banza me hade da harara ya sakar mata babu shiri ta zare hannunta daga kafafun Mami ta mike tayi dakinsu ,Koda ta shiga dakin ma kasa samun natsuwar zuciya tayi ta rasa dalilin da yasa take tsatsanin Jin tsoronsa haka da Jin faduwar gaba akansa sannan ta rasa dalilin dayasa ya tsaneta haka koda bai fada mata ba tasan baya qaunarta dan tana ganin tsanarta acikin kwayar idanunshi ."
bayi ta bud'e ta shiga qirjinta na dokawa ta kulle kanta dan ganinta shine Inda yafi mata saukin zama ta rarrashi zuciyarta shiru tana tunanin ta nesanta kanta dashi zai samammata kwancinyar hankali, sai dai ina hakan ma ba mai yuwa bane domin mami bazata yarda ba wani sabon tashin hankali ya caki zuciyarta nan take faduwar da gabanta ke yi ya qaru ya wuce misali hattar cikinta sai kadawa take tayi Imani a lokacin da tana da ciki tsab zai fice ya barta ."
cike da ladabi da biyayya ya dan saki rashin kadan ya k'araso ya durkusa a gaban mahaifiyarsa kmr zai mata sujjada "Sweetheart! ya kira sunanta bata amsa ba ta cigaba da kallonsa "kiyiwa Allah kiyi hakuri ki bar maganar nan a tsakankanimu karki bayyanata bare kowa ya sani ita kanta yarinyar idan ta sani sannan taji rashin amincewata zataji babu dadi a ranta ," shiru hjy zulaiheart tayi taki cewa uffun har sanda ya dasa Aya " Allah ya huci zuciayrki hjy sweetheart dan nasan zuciyarki na tattare da fushina amman kiyi hakuri ki yafe min abinda nayi " yana gama fadar haka yaja bakinsa ya sake yin shiru yana sauke numfashi ,hjy zulaiheart ta kafeshi da idanunta sosai ta cigaba da kallonsa taso ya fadi fiyye da abinda ya fad'a idan ma da hali yace "ya amince da umarninta amman sai sa'banin haka yake furtawa ,ya tsaya a iya hakuri kawai da kin amincewa ."ta rasa wace irin zuciya ga Adam sam idan ya kafe akan abu ya kafe kenan is very hard ya canza ra'ayinsa wannan halin kawai tafi tsana a rayuwarsa tun yana yaro tayi iyakar kokarinta akan wannan hali abun ya cutura sai dai akan wannan lamarin ta rantse ko zai rasa ransa sai ta canzasa Kuma sai yayi abinda take bukata ..
ya d'auki tsawon minti goma yana durkushe yana bawa mahaifiyarsa hakuri wanda ita ba hakuri tafi bukata daga tillon dan nata ba amincewarsa tafi bukata ,naunayen ajiyar zuciya ta sauke da karfi sannan tace "shikenan komai ya wuce na yafe maka amman ka San da sanin bazan taba janye maganata ba tunda na baka lokaci mai tsawo ka kawo min wacce kake so Kaki kullum da dramar da kake bullowa daita ayi mgn kace tru love kake jira ,dan haka bazan zuba maka Ido ba kayita zama babu iyali ba "Kai yanzu sbd Allah baka jin kunya ?duk sa'aninka sunyi aure har da yayansu abun sha'awa ? amman Kai baka wannan kasar baka wancan kasar , Neman kudi kawai kasa a gaba to meye amfanin kudin da Babu magada ? Kai da mahaifinka bai haifeka ba ka gaji tarin dukiyar daya bari ?yayi shiru yana riko tafukan hannuwanta cikin nashi dan bashi da amsar bata " ni dai gaskiya na gaji da zaman ka haka babu iyali Ina bukatar ganin ya'yanka idan Kuma kafi bukatar sai na mutu kayi auren shikenan sai na hakura na daina maka maganar amman fa kasani muddin nayi shiru yana nufi babu ni babu kai har abada ko mutuwa nayi zan bar wasiha kar abarka ka ta'ba ga....."
"Dan Allah Dan girman Allah kiyi hakuri Sweetheart ki daina ambato mutuwar Nan ki rufa min asiri idan kika mutu duniyar fa bazata min dadi ba , kece duniyata, ke kike sakani farinciki idan nayi cikakken awa daya banji muryarki ba Ina rasa gane kaina inaga baki duniyar ...?"kiyi hakuri inshallahu zaki ga aurena nida auta kmr yadda kika ga na saura yanuwanmu amman ki dan bani lokaci zan kawo miki wacce nake so nan kusa ,sai byn da yayi maganar ya fahimci maganarsa ta fito ne ba a yadda ya dace ta fito ba dan ta Ina zai fara ...?
"Wannan lokacin ya Kure Maka Adam har abada Babu wani sauran lokaci da zan sake baka kaje ka fara shirin aurenka da maryam kawai , tana gama fadar haka ta kawar da fuskarta gefe dan idan ba haka tayi ba zuciyarta zatayi sanyi akan tillon danta har ta fasa aiwatar da nufinta akanshi tsam ya Mike ya soma kokarin barin falon zuciyarsa na tafarfasa da tuttukin bakinciki dan yasan tunda ta kafe ta nace Babu wani sausauci baya ga amincewa kudirinta ."
Kai tsaye mota ya shiga muhd bello na ganin haka Shima ya shiga bangaren daya shiga ya zauna suka bar gidan har suka hau kan titi nasiha m b ke masa me kwantar da hankalinli da ratsa zuciya sai dai ko Daya Adam bai jin zai iya saduda da auren maryam gabadaya ya maida idanunshi yana kallon motocin dake gudu akan titi yayinda kwakwaluwarsa ke tunanin neman mafuta dan dole yasan abun yi kafin ayi masa auren dole da yarinyar nan "
"Adam ......"!
M.b ya kira sunansa ko gezau bai yi ba bare ya nuna alamun mutun na kusa dashi bai tsaya jiran jin amsarsa sa ko akasin hk ba ya cigaba da magana "ka kasa fahimtata amman kayi hakuri kasanyawa zuciyarka sallama ,na fahimci yadda kake ji amman me kake son nayi daya wuce na tayaka yiwa mahaifiyarka biyayya ? yayi maganar kmr zai yi kuka dan ya tsani yaga damuwar amininnasa ya dafe kanshi da hannunsa daya yana dukar da kanshi tausayinsa ya kama Adam ya furzar da iska me zafi daga bakinsa sannan ya soma magana .
"MB nima ka kasa fahimtata ne amman Ina da ra'ayina akan mace da nake son na ajiye agidna , muddin na auri Maryam ya zama dole na qara aure abinda bazan so faruwarsa kenan ba bama haka ba ni bani da ra'ayin ajiye mace sama da daya a gidana ."to meye dan ka ajiye sama da daya ? ka Kara mana tunda kana da abinda zaka iya rike mata ko sama da goma ne ba biyu ba ."
tsaki Mr ATA yaja a lokacin da direbansa ya karya kwana yana cigaba da tukinsa ,motar tayi shiru can ya sake motsa bakinsa "mb kasan komai akaina sai dai abinda bakasani ba ni bana son auren farar mace, nafi son mace chocolate colour ita ba fara ba ita ba baqa ba sannan mara kiba wace matakin karatunta iya diploma ne sannan doguwa daidai kafad'ana ba guntuwar mace ba "Kai yanzu me zakayi da doguwa har kafad'arka sbd Allah? " yar daidai fara kmr maryam ai ta isheka rayuwa sannan a matsayinka me zaka yi da mai iya karatun diploma ga mai digree har biyu "
"Zanci master's ne ? yayi masa tambayar a matukar fusace "yariyar nan babu abinda ta iya common ruwan zafi sai an daura mata ga balain son social media ,Kai ni duk bama wannan ba na tsani farar mace arayuwata ni dai chocolate itace type dina kasan Allah dana yi rayuwa da farar mace sol irin yarinyar nan gara na mutu ban yi aure ba saboda na tsaneta "subhanallah ATA ka daina fadar haka dan allah , dukkaninsu halittar Allah ne , da baki da fari duk Allah ne ya haliccesu ya tabe baki kawai yana furzar da hucin numfashi mai zafi haka suka cigaba da tafiya m.b na nusarsheshi ."
Maryam yan'uwa ne da adam, da mahaifin maryam da mahaifiyar adam uwa daya uba daya maryam ce babbar diya agurin iyayenta sai kanwarta Faiza ,islaha manir , Abusufyan , Salman sai auta izzatu wacce suke kira da izza suna zaune a Abuja yayinda adam suka kasance su biyar agurin mahaifiyarsu aunty shahida itace babba Kuma ma'aikaciyar likitanci ce a babban asibitn gwanaty dake jahar lagos a ikeja ,sai aunty khadeja wacce ta kasance maaikaciyar zenith ,sai adam wanda ya kasance dan boko Kuma rikakken dan kasuwar da duniya ke ji dashi,sai aunty zabiba wacce ta kasance lactura ce a lagos state university, sai auta nana hauwa'u wacce tuni itama ta gama karatunta a London tare da maryam akan harkar compurte science , a london akwai tsananin shakuwa atsakanin nana hauwa'u da maryam Hakan yasa sanda suka kare karatu maryam ta kasa zama tare da iyayenta ta dawo suka cigaba da rayuwa gabadaya dangin mahaifiyarsu da mahaifinsa babu baki duk wanda kagani fari ne sol babu mixed ."
Direban mr ATA bai tsaya akoina ba sai a haraban asibinti da aunty shahida ke aiki yana parking ya fito da sauri ya Bude masa murfin mota mr ATA ya yunkura da kyar ya fito yana gyara zaman rigarsa "friend ka bani minti ashiri yanzu zan dawo "na baka awa daya ma har ya juya m.b yace " , dan Allah friend karkayi wata ja inja da aunty kawai kace mata ka amince wani banzar kallo mr ATA ya juyo ya banka masa sannan ya juya cigaba da tafiya ."
m.b yayi murnushi dan daman yasan sai ya samu tsaraban wannan kallon daga gurinsa kai tsaye office dinta ya nufa cikin takun nan nasa mutane sai kallonsa suke saboda hotunansa sun qarade koina na matsayinsa na dan kasuwar da duniya Ke ji dashi wasu kuwa tsananin kamaninsa da yaruwarasa yasa suka dinga kawo masa gaisuwa wasu ya amsa Wasu ya share barin ma idan ya fahimci yanmata ne , ya tsaya a bakin office dinta yayi knowking ta bashi izini ya shiga yana taku da kyar yana furzar da iska ."
ta dago da sauri ta kallesa tana nuna masa gurin zama Dan tasan Halinsa ba karamin aikinsa bane zuciya tasa ya juya ya kama gabansa "zauna na Dan karasa abinda nake zama yayi ya daura kafarsa Daya akan Daya Yana ciza gefen lips dinsa daya zame masa jiki .byn kmr minti biyu ta tsaida abinda take ta sake dagowa ta zuba masa idanunta "Ina sauraronka wani taimako zan maka ?"kisa a fasa auren nan kawai shine babban taimako da zakiyi min ". "me yasa kake kin auren marym? shin kana da wacce kake so ne data fi Maryam komai ?ya gyada mata Kai alamun "eh ! Yana lumshe idanunsa "a Ina take Kuma su waye iyayenta ?wani mataki iyayenta suke dashi a kasar nan ko ....."? Ki tsaya iya haka ma ya isa dan ban San komai daya shafeta ba sbd ban San komai nata ba , Ina take a ina zan ganta duk bansani ba ina dai kan nemanta sai ki tayani da addua Allah yasa na ganta nan kusa kuyi min auren soyayya idan ma soyayyar zanyi kenan ."
"aunty shahida na San idan na fada miki komai zaki fahimceni sbd akwai fahimta a tsakankanimu shiyasa kika ji Ina maganata Kai tsaye dake , a zahirin gsky matar da nake so na aura ni kaina na dade Ina nemanta sai dai har yanzu ban ganta ba ......"nifa ban gane nufinka ba Adam , " I mean matar da nake so ban San Inda take ba ya sake maimaita mata abinda yace "Amman dai ku bani lokaci zan cigaba da nemanta idan na ganta zan kawo muku ita ya karasa maganar tare da fito da pendat din sarka dake makale da wuyansa wanda ke hade da hoton zannen yarinyar ya nuna mata ."
Shiru tayi tana kallonsa da kallon zanen yarinyar kyakkyawa ce chocolate colour " kinganta aunty ita ce rayuwata , ni dai kaina na zanata akanta na koyi Zane , ta miki kyau ko ?yayi mata tmyr yana sakar mata tsadaddaden murmushinsa wanda ba ko yaushe yake yi ba "subhanallah Adam kana hauka ne ko me ?" Taya zaka kamu da soyayyar macen da baka San Inda take ba hasalima baka taba ganinta ba ....?"Haka ne aunty Amman ta shiga zuciyata ta samu kyakkyawa mazauni acikinta shekara goma sha biyar kenan nake nemanta aunty babu Inda ban nemi yarinyar nan ba acikin garin Nan har ma da kasashe da garuruwan da nake zuwa Amman ban sameta ba ,Kai ko me kama daita Bangani ba "shine Kuma Dan hauka ka cigaba da Sonta? "ya lumshe idanunshi tare da cewa "ya zanyi haka tawa qaddarar ta kasance itama ba wai ina sonta bane amman muddin zanyi aure ita zan aura".
"ka manta wannan shirmen dan har abada bazaka ganta ba dan dayawa mafarki ba gsky bane "wallahi aunty jikina na bani tana Nan a duniyar Nan shiyasa kika ga bana son na karbi auren yarinyar Nan mrym gbdy aunty shahida ta dauke maganarsa a matsayin shirme ta cigaba da kallonsa kmr wani sauna ,Taya zai ce yayi mafarki da mace Kuma Yana Saka ran tana Nan acikin