Showing 141001 words to 144000 words out of 168608 words

Chapter 48 - Mar'adam's Book 1 Hausa Novel Complete

iska yanayin yadda yay mgnr kamar yana cikin damuwa."

"Me za'a kawo maka? "coffe " to maza mrym tashi ki kawo masa" badan ranshi yaso ba yayi shiru dan ko yace zai yi mgn damuwa kawai zai qarawa kanshi."ranar da nuzla ta cika kwana biyar aka kira ATA daga police station bayan yaje aka tabbatar masa an kammala duk wani bincike kuma ansamu bambamci a wajen gwajin zanen hannu ,dan nuzla da hannun dama take amfani yayinda mai kisan da hannun hagu, bugu da qari ba zanen hannunsu daya ba dan haka zai iya tafiya daita "to shikenan a fito daita ya fad'a lokacin daaka fito daita shi kansa ya tausaya mata tana ganinsa ta durkushe a gabansa ta kamkame kafafuwansa ajikinta saurin dauke numfashi yayi sai dai tausayinta ya hanashi zareta kafafuwansa ajikinta duk da dottin da jikinta yayi ."

Murya cikin kuka ta soma mgn "yaya na fad'a maka ban aikata komai ba wallahi bani bace kasa aka kawo ni nan kalli jikina yaya ni kaina bana son ganin kaina haka dan allah karka barni anan ka tafi dani gida ka tausaya min kafin na mutu da kyar ya samu ya zare kafafuwansa yana sauke numfashi ya mike tsaye yana mikewa dpo hannu "na gode sosai idan na koma gida zan kira akwai maganar da zamuyi "okay yalla'bai sai najika zumbur nuzla ta mike tsaye tana kuka "dan allah yaya karka barni wallahi bani bace dpo yayi murmushi yana cewa "ai ki kwatar da hankalinki yau a gida zaki kwana wani irin naunayen ajiyar zuciya ta sauke tana masa godiya ATA yayi gaba ta biyosa da sauri ."

Suna shiga cikin estate dinsu kai tsaye hanyar gidansu suka nufa sukai parking masu tsaronsa suka firfito shima ya fito suka nufi cikin gidan a parlour'n suka iske hjy salema da wasu yanuwanta mutun biyu da gudu nuzla ta qarasa ta fad'a jikinta tana kuka itama tana kuka ta rungume diyarta tana shafa bayanta ganin irin kukan da suke yasa ATA ya juya ya kama gabansa alkwari ne kuma ya cika ranar kam murna wajen hjy salema da yanuwanta baa magana sai da kira doctor domin lafiyar nuzla tare da allurar."


Kwanci tashi babu wuya a wajen Allah kullum kwanakin bikin ATA da maryam qara matsowa yake har yau ya rage sauran kwana bakwai kuma har lokacin zuciyar ATA bata rusuna ba salim da mb har ma da hisham ango suke yin duk abinda ya dace dan shi dai ATA yace bazai bata kudinsa akan auren maryam ba kuma babu abinda zai yi na event duk kuma wanda ya kashe kudinsa kar yace dan shi yayi ,dan bai aike kowa ba duk sun jisa amman babu wanda ya tankasa mb da hisham sunyi rabon iv sun kai duk inda ya kamata ace sun kai sosai shirye shirye yayi nisa amman babu ruwan ango dan ko tautaunawa baya yarda suyi dashi da zarar sun soma mgn zai bar wajen ."


Yau tun safe maryam ta tashi jikinta a sanyaye ji take kamar zata rasa rayuwarta komai take gabanta na faduwa abu na tashin hankali dana farinciki duk sai taji gabanta ya yanke ya fadi har kasan mararta take jin ga zuciyarta dake tsinkewa shiru kawai tayi kwance har zuwa lokacin da mami ta shigo "maryam bacci kike yi ne ?ta tmbyeta tana shigowa dakin sosai ta yunkura ta tashi daga kwanciyar datayi tana cewa "a'a mami ba bacci nake ba na dai dan kwanta ne ."akwai abinda zan miki ne ?mami tayi murmushi tana dubanta dan ta lura tunda aka shiga satin bikinsu take cikin damuwa ."

"akwai abinda ke damunki ne ?
Ta girgiza mata kai alamun a'a "ki sanar dani idan akwai abinda Ke damunki ni din tmkr mahaifiya ce agareki ? ta sake girgiza mata kai alamun a'a sai dai kallo daya zaka mata ka fahimci akwai damuwar dake damunta ,ki cire damuwa aranki kinji maryam babu abinda zai faru sai alkhairi ta lumshe mata idanunta alamun ta gamsu "maza tashi ga mukulin mota kije gidan shahida yanzu ta kira wai kije tana son ganinki anya kuwa zan iya tuki nan mami ? bana jin zan iya dan bani da kuzari ajikina ,to shikenan bari nayiwa nura direba mgn ya kai ki ."

"to mami amman bari naje nayi masa magana da kaina tare suka fito maryam ta fice ta bar mami da nana hauwa'u a parlour'n zuwa haraban gidan akan idanun hindu ta fito dan haka tayi adduar samun nasara da aiwatar da nufinta akanta domin kusan wata guda kenan tunda aka saka lokacin aurensu take neman hanyar da zasu samu kebewa ."

bayan maryam ta fad'a masa zai kaita gidan aunty shahida ta juya ta koma ciki domin ta qara shirya kanta a parlour ta tsaya kusa da nana hauwa'u "sister muje ki shirya ki rakani." a'a babu inda zani maganarku ta matan aure zakuyi ina ni ina rakiya kinga je ki kawai sai kin dawo allah ya tsare hanya" ganin mami zaune a wajen yasa maryam bata sake cewa komai ba ta shige ciki .yayinda hindu ta qaraso inda nura yake zaune tana cewa "mlm nura ina son na dan aike ka ko akwai abinda zakayi ne ?tayi masa tmbyr dan tasan me zai yi adaidai lokacin "hajiya mryma zan kai unguwa okay to shikenan karka damu allah ya tsare ta juya zata koma ciki ,kina bukatar wani abu ne ?


Ta tsaya cak ta dan juyo fuskarta a sake "daman abu nake son a karbo min anan bakin titi amman tunda fita zakayi karka damu ,aa baa yi haka ba kawo nayi sauri na karbo miki kafin ta fito ta mika masa kudi dan cake zaka amso min amman mai chocolate ya karba kudin ya nufi babban get din estate din da dan saurinta ita kuma ta shiga gidansu domin ta shirya ."akan idanunta still maryam ta fito kafadarta makale da jaka tana neman nura direba tayi sauri ta fito tana cewa "mrym amarya fita zakiyi ne ?ta waigo bayanta a hankali ganin hindu ta saki fuska sai dai mgnr datai mata yau din ya dan bata mamaki dan sam batayi tsammani ba dan ba abokiyar maganarta bace domin dai kusan duk kallon mai girman kai suke mata kasancewar ta girmesu km bata shiga cikinsu "

"Eh wallahi fita zanyi nura direba ne zai kai ni gashi na fito ban gansa ba ko ina ya shiga ,Allah sarki okay muje na saukeki mana nima fita zanyi ta fad'a tana qoqarin shiga motarta da kamar bazata shiga ba amman sai tayi tunanin karta ga Kmr tayi mata wulakanci dan haka ta yanke shawarar shiga idan yaso direban aunty shahida ya dawo daita ta bude dayan bangaren ta shiga ta zauna hindu ta tada mota suka fice daga gidan koda nura direba ya dawo kai tsaye gidansu hindu ya nufa ya bada sakonta ya dawo zaman jiran fitowar maryam ."

Ahankali suke tafiya hindu na jan mrym da hira "Maryam amarya adamcy kenan gashi yazo amman naga baki fara shirin komai na amare ba, wallahi ban fara ba dan bana cikin natsuwata "to me kuma Ke damun amarya ko fargaban kasancewa da angonki ne ? maryam tayi murmushi kawai "Ke kuwa me zasa kiyi fargaba alhalin auren soyayya zakuyi ?ko auren soyayya ne dole kaji wani iri dan aure ba wasa ba, kenan gskyr labarin danake ji daga bakin mutane daban daban na kina son adamcy gsky ne ? zuciyar maryam a dake tace "eh hk ne muna son juna ."

"Na tambayeki ?
"Ina jinki ! mu ajiye maganar wasa zaki aure adamcy ne saboda kina son shi ko kuma zaki auresa ne dan biyayya wa mahaifiyarsa ? "zan aureshi ne dan ina son shi "akan wani dalili kenan zaki so shi ? tambayar tabawa maryam mamaki amman sai ta kawar da mamakinta tace "akan dalilai masu yawa ."ko Kinsan akwai wacce ta fiki son shi da son mallakarsa wacce zata iya komai akansa ?

"Eh nasani "!
"Wacece ?ke mana na samu labarin kina mutuwar sonshi Kmr Kiyi hauka afirgice hindu ta juyo gareta tana cewa "tabbas bakiyi karya ba ina mutuwar son shi irin son da zan iya yin komai akanshi dan haka abinda zan iya ce miki ki rabu dashi ki kuma fasa aurensa saboda adamcy raina ne akanshi babu abinda bazan iya yi ba ".

"ni kuma akan na rabudashi na bar miki gara na rasa raina." shine nima abinda na gani kenan, kuma nake tunani akai, kmr mutuwar ce zata fiye miki sauki akan ki cigaba da rayuwa a doron duniya , dan zan kasheki tun wa'adin kwanakin mutuwarki bai cika ba, zanyi sanadin rasa ranki batare da kin shiryawa hakan ba, ta karasa mgnr cike da matsanancin zafin rai tana fitar da hucin kishi.


"wai meye haka ne hindu kike kokarin aikatawa ruhin da bai d'aukar miki laifin komai ba? "gsky zan gayawa mami . "ba sai kin rayu ba tukun zaki gaya mata ina tabbatar miki daga nan sai kabarinki, domin kuwa zan miki aika aika ,zakiyi mutuwa mafi muni da rad'ad'in azaba wanda ko makiyinki yaga gawarki sai ya koka miki "aikin banza kawai daman da wata manufa kika daukoni a motarki ?

"Yes of course da wata manufa na dauko ki mana ,amman da yake Ke jaka ce kika qasa ganewa tana gama fadar hk taja wani irin wawan birki sannan taja motar aguje ta soma hajijiya da motar akan titi bata tsaya akoina ba sai atsakiyar titi , ta fito da hanzarinta, kafin maryam tayi wani yunkurin fitowa daga cikin motar , tuni har hindu tayi lock din motar gbdy , ta tsaya rike da kugunta tana dubanta tana murmushin mugunta ,"wai meye hk ne hindu ?

"mutuwa kenan !"

"ki budeni karki kasheni da wasa nake miki wallahi bana son shi nima zan auresa a dole sbd mahaifiyarsa "hhhhhhhhhhhh karyarki yarinya ai wasan ya rigada yazo karshe sai ki jirasa a lahira har zuwa sanda zai iso gareki so that kwa auri juna acan inda wata katuwar tanka mai ta nufo motar gadan gadan a matukar tsorace maryam ta saka wata razananniyar k'ara me sauti "tana toshe kunnuwanta duka tare da runtse idanunwata .......


Mmn sudai

💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗


*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan  littafin  na kudi ne mai bukatar karantashi   byn na kammalashi zai  biya 1000 ta wannan  account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura  domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina  (Hausa bakwai ) a YouTube.


Page 26

hankalin maryam ya qara tashi Kuka take sosai da iyakacin karfinta tana furta duk wata adduar data zo bakinta domin neman cikawa da imani dan gabadaya ta sadaukar da rayuwarta akan mutuwa zatayi yayinda hindu ke tsaye rungume da hannuwanta duka a qirji tana sakar mata murmushi farinciki tana kallon yadda motar ke tahowa wajen motarta da maryam ke ciki ."

maryam ta kamkame jikinta sosai tana mai sake fashewa da wani gigitaccen kuka jira kawai take taji saukar motar akanta amman sai taji shiru sai ma jiniyar motar ' yansanda ta jiyo dan haka da sauri ta ware idanunta dan tabbatarwa kanta gaske ne ?ganin motar yansanda ta sha gaban motar yasa ta sauke wani naunayen ajiyar zuciya da numfashi atare ,yayinda mutumin dake ciki motar ya soma qoqarin fitowa domin ya tsire amman cike da hanzari yansanda suka samu nasarar damke bala ,cikin tsananin tashin hankali yake masu bayanin komai dan gabadaya ya gama rud'ewa "

Yayinda hindu ke tsaye awaje kamar an dasata tsabar firgitar da tayi zufa ce kawai ke karyo mata dan kana kallonta zaka fahimci yadda hankalinta yayi mugu mugun tashi , gashi tana son guduwa kamar yadda bala yayi qoqarin yi amman ta kasa aiwatar da hakan har sanda ' yansanda suka samu nasarar daba masa ankwa a hannuwansa tana tsaye kikam kamar mashi ."

Zuciyar hindu ta shiga bugawa da matsanancin karfi nan take ta shiga sake sake hade da jerowa kanta tmby "wa yasan shirinta ?wa ya turo 'yansanda ?"yaakayi suka san inda zata aiwatar da shirinta akan maryam ?ita dai tasan daga Allah sai bala da zasu yi aikin tare suka san komai dan hatta babanta bata bari ya sani ba ."

shiru tayi kawai har zuwa lokacin da yansanda suka qaraso zuwa inda take tsaye suka tsaya a gabanta
a wulakace ta d'aga kanta tana kallonsu d'aya bayan d'aya tare da bude bakinta zata soma zazzaga masu ruwan bala'in 'bata mata shirinta da sukayi amman sai taga daya daga cikin police din dake tsaye a gabanta ya ciro I'd card daga gaban aljihunsa yana nuna mata kasancewar babu uniform ajikinsu da alamun cid ne ."


wani dogon tsaki taja tana cewa "ai ni ba makauniya bace, ko baka fito da I'd card dinka ba nasan ku din yansanda ne "? dan sanda ya gyada mata kai kawai yana kallonta a tsanake kafin daga baya ya soma magana "da fari ki miko mana key motar hannnunki a fito da wacce kikayi yunkurin kashewa " furzar da iska mai zafi tayi daga bakinta kafin daga baya cike da maseefa tace "bazan bayar ba ,dan tunda nayi niyyar kawar da maryam daga duniya a yau din nan sai nayi babu fashi idan yaso nima daga baya akasheni tana qarasa maganar tabi gefensa zata wuce har tayi taku biyu taga wata gajeruwar macen yansanda ta harde mata kafafu sai gata dim a kasa ta zube bisa gwiwowinta inda key'n hannunta ya fadi kasa ."


Macen yansanda ta qaraso inda hindu take wargaje a kasa cikin azaba ,kallo daya zaka ma macen yansanda kasan babu rahma a fuskarta ta d'auki keyn daya fadi ta mikawa d'ansandar dake tsaye a kusa daita"ungo naziru maza ka fito da yarinyar" ya karba keyn daga hannunta da sauri ya nufi inda motar take ."

Macen yansanda ta fito da ankwa daga cikin aljihunta tana duban hindu a tsanake kafin daga bisani ta soma qoqarin kamo hannunta domin da'ba mata ankwa amman hindu ta fixge tana zabga mata harara "ki miko hannunki na saka miki ankwa ko kuma na harbe kwakwaluwar kanki yanzu ." wani murmushin bakinciki ya bayyana akan fuskar hindu "bazan so faruwar haka ba ,dan bazan so na bar duniyar nan batare dana kawar da mutun biyu din nan a duniya ba,wannan hatsabibiyar yarinyar da kuma wanda zai aureta, duk da na shiga hannu amman ban yi nadama ba ,dan ni kadai nasa me nake ji a zuciyata yadda zan rasashi dole itama ta rasashi ."



Ta sake yin murmushi wanda kana gani na takaici da bakinciki né da rashin cimma buri "duk da na shiga hannun amman nasan zan fito dan mahaifina zai yi iya qoqarinsa sannnan zai kashe ko nawa ne akan yaga na fito tana gama fadar haka ta mika mata hannuwanta duka , sai da suka kalli juna da sauran yansanda nan take suka fahimci yanayin cewar hindu bata cikin hayacinta ,ta daba mata ankwa a hannuwanta tana cewa "duk abida kike taqama dashi wanda yasa muka bibiyi rayuwarki har zuwa yau din nan ya fiki kuma yafi mahaifinki komai ."

"idan taqamar mahaifinki nada kudi ya zartashi dan haka kisani matsawar bashi ne ya lamunce ki fito ba ubanki bai isa ba ,kuma bashi da kudin da zai fito dake oya muje ."ta qarasa mgnr alokacin da aka qaraso da maryam wacce ke kuka har lokacin ga wata zufa dake tsatsafo mata a dukkanin ilahirin jikinta kallo daya zaka wa maryam ta baka tausayi ."

Wani wulakantaccen kallo hindu tayiwa maryam sannan ta yunkura ta mike tsaye cike da d'agawa da isgilanci ta kalli macen yansanda tace "koma waye shi ina mai tabbatar miki mahaifina yana da karfin ikon da zai sa shi ya lamunce a fito dani ta qarasa maganar tana sake watsawa maryam mugun kallo "Ke kuma ki jira fitowata wallahi karon mu bazai yi kyau ba, bazan ta'ba barin kiji dadin rayuwarki ba, baqar makira wallahi nice ajalinki ki rubuta ki ajiye ."


wasu hawaye masu zafi suka gangaro acikin idanun maryam hankalinta ya qara tashi fiyye da lokacin da take cikin mota ,yayinda zufa ke sake karyo mata muryarta a raunane. tace "police kunji abinda take fad'a wai zata kasheni itace ajalina "ki kwantar da hankalinki babu abinda zata iya miki daga hannunmu sai kotu zaa kaita daga kotu kuma sai gidan kurku kinga babu wata hanyar data sauran mata "karya kake munafukin Allah bani ce zani kurku ba uwarka ce zata kurku shegu matsiyata kawai tass tasss!! taji saukar mari har

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login