Showing 81001 words to 84000 words out of 168608 words

Chapter 28 - Mar'adam's Book 1 Hausa Novel Complete

kame akan daya daga cikin kujerun falon ,mami ta dawo inda maryam take tsaye tana kallonta "sannuki maryam gsky kinyi kokari sosai yau kin aikatu da kyau haka ake so, maryam tayi murmushi kawai tana jin dadin yabon da mami tayi mata "na gode sosai ai nan gaba zan kware na zama professional ta bangaren girki bazan ta'ba baki kunya ba ."

mami tayi murmushi tace "da alama zaki wanke zuciyar mamnki ta gyada mata kai alamun "eh !"
"To ni zan hau sama na dubo adamcy Idan kin kammala komai ki shirya dinnig kije kiyi sauri Kiyi wanka ki shirya ki dawo Kiyi saving din sarkin zuciyar Kiyi komai a natse  kin dai san halinsa dan oya oya ne yafi son komai cikin sauri sauri bare yau  din nan sai ahankali ."mami dan allah ki zuba masa da kanki mana"idan kunyi aure nice zan dinga zuwa gidanku ina zuba masa ?"dakewa zakiyi  maryam ai ya kamata ace kin saba da halinsa "wallahi mani babu mai iya sabawa da halinsa sai ke nifa mugun tsoro yake bani idan na gansa hatta kayan cikina karkarwa suke mami tayi murmushi tana cewa ni na wuce "To mami sai kin fito ta fad'a cikin murmushi mami ta fito zuwa parlour'n."

hindu na ganinta ta saki fuskarta sosai tare da gaishe da mami cike da sakin fuska mami ta masa tana tmbyrta mutanen gidansu ta amsa da lafiya lau kowa yake "mami ina ya adam ne ko har yanzu bai tashi ba ?"eh!hindatu ina tunanin bai tashi ba amman yanzu haka ma samansa zani na taso shi dan yace idan ya wuce tara bai tashi ba na tashesa rausayar da kwayar idanunta tayi tana jin wani zazzafan sonshi ."

Mami ta nufi saman dakinsa tana mamakin hindu su dai yaran zamani basu da ta ido akan nmj so na mugun rufe masu ido shiyasa har kullum take ganin girma da kimar maryam, a dai barta da son social media dinta amman rawan kai akan maza sam bata dashi dan tasan bancin itace ta hadata da adam to har abada bazata iya bude baki tace tana son shi ba ."

Maryam ta kammala komai a natse ta fito a yatsine hindu ke binta da kallo tana shirya dining ,ita kuma tana tunanin yadda zasu buga kishi daita idan tai nasara shigar gidan ya adam dinta dan dole ta fita ta bar mata gidan ta zauan ita kadai ,dan idan bata kaita lahira ba lallai zata raunatata dan irin son da takewa ya adam ba na wasa ba so ne wanda bazata iya sharing dinsa da kowa ba ."

Marayam ta sha jinin jikinta da irin kallon wulakancin da hindu Ke mata dan duk lokacin data kallo bangarenta sai taga kamar hararata take wanda ta rasa dalilin faruwar hakan ,sai da maryam ta tabbatar da komai yayi neat babu abinda mr ATA zai gani yayi complain sannan ta wuce ta nufi dakinsu cikin sauri still tana mamakin hindu ."

tana shiga dakin bathroom ta shiga ta fara wanka sai dai matsalarta bata iya wanka cikin sauri ba idan ta shiga wanka a qalla tana daukar awa daya a bayi amman kasamcewar zatayi saving din mr ATA yasa ta tsakaita tayi wanka ta fito ta dauki man shafa warta wanda shima shafa man kanshi aiki ne domin tana daukar a qalla mintuna talati bare aje ga make up ta shirya cikin doguwar rigar shadda bazin har kasa bata gama kammala shiri ba taji sautin muryar mami na kiranta da d'an sauri ta fito zuciyarta na rawa kuma har lokacin hindu na zaune a parlour'n tayi shiru tana yi masa kallon tsab komai nashi yayi mata irin wanda take so nmj ne sai kallonsa take yayinda mami ke qoqarin jawa mr ATA kujera baya"

Wani abu mai mugun daci ya hadiye tare da zama yana mai runtse idanunshi ganin mami na son bawa maryam umarnin saving din mr ATA hindu tayi sauri ta mike tsaye tana cewa "mami bari nayi saving din yayana ta fad'a tana mai sunkuyar da kanta alamun kunya "amm...! "Sweetheart bari tayi kawai ya fad'a atakaice mami ta kallesa na second biyu dan sam bataji dadin hukuncinsa ba dan tasan da wata manufa hindu ta fadi hk shi kuma gudun karyaci daga hannun maryam ya fadi haka dan tasan shi tasan halinsa baayi masa gwaninta ranta ya baci sai dai danne damuwarta ."

Madadin mami ta zauna kusa dashi kamar yadda ta saba sai ta koma kan kujera ta hankince ta nunawa maryam kusa daita"maryam zauna anan kinji  yar albarka ta maida hankalinta kan tv mr ATA yaji babu dadin yadda mami taja jikinta amman sanin dan maryam tayi haka yasa ya share ya dauki wayarsa yana duba sakonin dake shigowa yayinda hindu ke zuba masa abinci acikin wani haddaden plet ta matso daf dashi Sannan ta ajiye plet din a gabansa."

cike da girmamawa ta kira sunansa"ya adamccccyy...!yadda ta kira sunan cikin slow voice yasa daga maryam har mami suka waigo suna dubanta murmushi ta sakar masu wanda ke nuna tana cikin farinciki sannan ta dauke kanta ta maida kanshi wanda shi gogan har lokacin bai daina abinda yake ba bare ya dago ya kalleta sai faman ciza lips din yake yana kallon screen din waya ."

kira ne ya shigo wayarsa ya dauka a natse "ok but I think kasan nan da 1week zan wuce france ya aikin gunka ina fatan akwai nasara ya hade rai sosai haba hisham you should know me by now ka ta'ba ganin inda akayi haka ?kawai dan na tattara hankalina zuwa wani waje kawai su kamawa yiwa mutane barna ,ka kuwa san adadin kudaden da mukayi asara kuwa ?kowa acikinsu kanshi kawai yasani ba cigaba AGC bane agabansu well sai na shigo dai hindu ta marairaice murya sosai tace "ya adamcy ga abincin ka dan ajiye waya kaci abinci ".

Banza yayi mata ya cigaba da wayarsa "a lokacin zuwa office muke gashi naji ya sultan yace yau kuna da zama na mussaman "bai kalli inda take ba bare ma ta samu matsayin ya bata amsa hakan kuwa yayi wa maryam dadi sosai ,sauran kadan ta fashe da dariya amman ta danne ,ta kalli mami wacce itama ita take kallo suka sakarwa juna murmushin jin dadi sai daya gama wayarsa ya ajiye sannan ya fara cin abinci babu irin kwarkwasan da batayi masa ba da jansa da magana amman bai ce uhmm ba bare uhmm uhm ba illa ma mikewa da yayi tsaye yana gyara yar saman suit dinsa ya dan qarasa kusa da mami muryarsa a dake yace "ni zan wuce kuma kai tsaye daga nan AGC zani "to Allah ya tsaye sai ka dawo yace" Ameen!
"har ya juya ta kirasa "adamcy ! ya dan tsaya yana saurareta "kabi komai a hankali dan Allah karka dauki zafi dayawa ahankali ake bin komai ka tsaya ku fahimci juna da yanunwaka".

Kai kawai ya gyada mata ba dan zai yi abinda tace din ba dan yau kusan sai ya tashi rabin mutanen kamfanin kuma daga aiki wanda dayawa yanuwa ne a natse ya juya ya fice yana fita hindu tabi bayansa har tayi taku biyu mami tace "amm...hindu yau yayanku baya cikin moon mai kyau ba kin kuma san halinsa bare idan yana jin miskilancinsa idan kika nemi ki tsaida shi komai zai iya faruwa ko kina son wani abu ya faru ne ?"

Hindu ta girgiza mata kai alamun a'a daman ba tsaida shi zanyi ba gida zan wuce "to shikenan sai anjima sai data fice mami ta dawo da kallonta kan maryam "mami me kika karanta akan hindu ni yau gani nayi tana wasu abubuwa kamar son ya adam take mami ta tabe baki "wai son shi take amman shi har yanzu bai sani ba dan dayasani bazai bari tayi saving dinsa ba" maryam ta dan ware kananun idanunta sanna tasa dariya tana cikin dariya sai ga nana hauwa'u "sister yi sauri kizo kije wani sabon rigima da sauri ta qaraso tana cewa "bani na sha matar yayana "wai hindu Ke son ya adam wace hindu kuma ?"

Wacce hindu mike dashi a gidan nan data wuce ta gidan baba qarami wallahi har na tausaya mata dan idan ya kirani guntuwa ita km fa me zai kirata ?"
gabdaya suka sa dariya har mami "wanna kam gsky ne ina zai kaita ? ga wani cream na organic tasha duk ya canza skin dinta ta dawo farar karfi da yaji ,shi daaka bashi farar mace sol yace bai so ina ga mai shafa cream? ni wallahi da zai karbeta ma ya barni da naji dadi anan ne mami tasa baki "kar na qara jin kin fadi haka ai babu wacce zaki barwa shi da sannu zai koyi sonki dan nasan you are so different daga sauran mata ai shiyasa nace a saka sati uku ayita ta qare burina ki rage media ki janyo hankalinsa cikin kankanin lokaci ku zo juna ."

"mami kina ganin komai zanyi ya adam zai soni ?"
Mai zai hana maryam zai soki mana aure nawa akayi irin naku km a karshe ya zama soyayya mai karfi ,ni dai ina ji ajikina aurensa zai sa ku rasani da wuri tun lokacina bai yi ba." maryam ta fad'a idanuwanta na kan Mami "ki daina irin wannan tunani babu abinda zai faru sai alkhairi zai soki ki so shi babu abinda zai rabaku sai mutuwa shiru maryam tayi tana jin mami ."

Motocinsa na tsayawa a haraban AGC escout dinsa suka firfito daga cikin motocinsu mutun biyu na qoqarin bude masa murfin mota ya bud'e ya fito fuskar nan tashi sam babu annuri yana miqawa na hannun hangunsa wayoyinsa ya nufi cikin kamfanin kallo daya zaka yi masa zaka qara jin tsoronsa fiyye da yadda kake ji ."

tunda ya samu information barnar daake yi a kamfanin walwalarsa ta ragu sosai babu inda zaka kalla a fuskarsa kaga rahma ganinsa yasa kowa ya shiga hankalinsa domin a irin wannan ziyarar da yake kawowa yake korar mutun daga aiki yana tafiya ana gaishesa cike da girmamawa yayinda sectary dinsa some na biye dashi abaya hannunta rike da files wanda ake bukatar saka hannunsa duk cikin wad'an da suke gaishesa babu wanda ya masawa daya daga cikin escout dinsa yayi saurin bude masa kofar office dinsa ya shiga a natse yana duba agogon rolex din dake daure a tsintsiyar hannunsa ."

ya qarasa mazauninsa ya zauan ransa a matukar bace, cike da girmamawa some tace "good morning sir ?kanshi kawai ya gyada mata batare daya amsa ba "sir ana bukatar saka hnnunka acikin wadan nan file's din ta fad'a muryarta na rawa dan ta tsorata da yanayinsa na yau gabansa ya nuna mata alamun ta ajiye cike da girmamawa ta ajiye tana rusuna masa "ya tsurawa file's din ido kawai yana kallo kafin a hankali ya dauki daya ya rabashi gida biyu a matukar tsorace ta dinga binsa da kallo har ya gama yagasu gabdaya ya watsasu sama suka tarwatse yana hura hanci sannan yace "are you crazy some ?


Mmm sudais
💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗


*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan  littafin  na kudi ne mai bukatar karantashi   byn na kammalashi zai  biya 1000 ta wannan  account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura  domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina  (Hausa bakwai ) a YouTube.


Page 17


" are you crazy some "?ya furta a zafafe yana hura hancinsa har zata girgiza masa kanta alamun "a'a ! sai kuma tayi sauri ta gyada masa kanta alamun "Eh! dan ko giya ta sha bata isa tace masa "no ! ba bare tana cikin hankalinta "what's wrong with mr ata I did not do anything wrong ? tayi maganr acikin ranta tana mai sake kama kanta dan karta yi wani kuskuren da zai dakatar daita na wasu satittuka koma ya dakatar daita aiki gabadaya ."


" ahankali ya mike tsaye ya kamo lip's dinsa na kasa yana cizawa ahankali ahankali !! magana yake son yi amman ko ya bud'e bakinsa maganar bazata fito ba , daga can bakin kofa akayi knowking tare da cewa "may I coming sir ?". shiru yayi yaki cewa komai sannan yaki kallon kofar , some dake tsaye cikin tsananin tsoro da fargaba ta kalli glass din kofar taga prosper ne tsaye hannunsa rike da file mai cover green wani yawu ta hadiye sannan ta saci kallon inda mr ata yake tsaye taga baya kallonta ta sake juyawa tayi wa prosper alama da hannunta ya koma da sauri ya juya ya bar bakin kofar ."


Mr ata yasa hannu ya d'auki wani file mai white cover dake ajiye akan makeken table dinsa yana dubawa , lokaci me tsawo ya d'auka yana dubawa yana shawagi acikin makeken office din nasa zuciyarsa na tafarfasa yayinda wata irin zufa ke tsatsafo wa some akan goshinta kamar an watsa mata ruwa .duk lokacin da taga mai gidan nata cikin damuwa itama sai ta tsinci kanta ciki dan kusan duk abinda yaje ya dawo akanta zai
qare tunda itace sectary dinsa duk abinda zai shiga ya fita ta sani ."


Ya sake kamo gefen lip's dinsa. na qasa yana cizawa hannunsa dake rike da file ta zubawa ido tana tausayawa duk matar datai ganganci aurensa , tana goge zufan goshinta dake ta tsatsafo mata duk da karfin sanyin ac dake ratsa office din ."Cikin kulawa da girmamawa tace "sir !" ko zan iya kiran metting a yanzu ?"
"ahankali ya lumshe lumtsatsun idanuwanshi da suka d'an canza kala alamun tarin 'bacin rai yake ji acikin ransa "sir !ta sake kiransa a karo na biyu ahankali ya motsa lip's dinsa "go !" ya fad'a atakaice batare daya kalleta ba da sauri ta juya ta fice daga cikin office din tana sauke naunayen ajiyar zuciya ."



Cikin kankanin lokaci ta dawo ta tsaya a gefe cike da kamewa da girmamawa tace "sir komai ya Kamala kai kawai ake jira." a natse ya goya hannuwansa duka abayansa ya soma daga kafafunsa dake cikin hadadden black canvers tana biye dashi abaya hannunta rike da wata takarda mai bango ja , tafiya kad'an sukai sai ga hisham da yaya Ibrahim tare da wasu manyan maikata guda biyar suka marasa baya suna takawa ahankali har zuwa qasan kamfanin madadin yabi hanyar da zai kai shi comference room sai suka ga ya karya yabi wata doguwar hanya , nan take some tayi gaba da sauri domin ta fahimci inda yake son zuwa kafin ya shiga conference room yayinda sauran suke take

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login