Showing 72001 words to 75000 words out of 168608 words

Chapter 25 - Mar'adam's Book 1 Hausa Novel Complete

masa a saman goshinsa yayi baki tmkr tawadar Allah ."

ahankali zuciyar mr ata  ta soma bugawa da karfin gaske  yana jin tmkr ta kunno masa emotion's din da yake ta qoqarin dannewa acikin zuciyarsa nan da nan idanunshi suka canza kala cikin tunanin da maryam take taji yana  cewa "yarinyar mafarkina ce dana  zanata da hannuna, itace  cikar  burina  ce farincikina ina matukar sonta itace mace ta farko da zuciyata take so  .." jin haka yasa gaban maryam  yayi wani mummunar  faduwa sakamakon jin abinda  ya fad'a ta juyo ahankali ta tsura masa idanunta duk da ba karon farko  kenan ya ta'ba fadar haka agabanta ba amman na yau din yasa taji wani iri a gbdy  ilahirin  jikinta  ta lura baya iya boye fellings dinsa  akan  zanen  ."

ina ma zata ga fuskar yarinyar taga dame tafita da har zuciyarsa ta zabeta alhalin ita din ba gsky bace ?tuna zane ce   yasa ta sauke wani boyayyen ajiyar zuciya mai  had'e da  zallar  kishi "ina  matukar  sonta  auta amamn na rasata a yanzu haka ina son raba rayuwata da tunaninta da duk abinda ya shafeta yana  magana yana  kallon  screen din  wayarsa wanda  Ke  dauke   fuskarta "mun dace da juna ko ?ya tambayi  nana  hauwa'u  yana  lumshe tsumammun  idanuwanshi   dake  cike  da  azaban ciwo ."

Nana  hauwa'u  bata  bashi  amsa  tmyr  da   yayi mata  ba  ta kalli  maryam  dake  tsaye  tana  dubansu   idanuwanta  cike  da  kishi  ajiyar  zuciya ta  sauke  tace "yaya  zamu ce allah ya  baka lafiya "na  tambayeki  baki  bani  amsa  ba ya fad'a a mutukar fusace  yana  watsa  mata  harara "me kace ?" shiru  kawai  yayi  tare  da  tsura  mata idanuwanshi   itama  kallonsa  take  tasan   abinda  ya  tsana  kenan  dan  hk  muryarta na rawa tace "kun..." kun  dace  sosai  kawai  dai  matsalar ita din ba   genuine  bace  wani  dogon  tsaki  yaja  yana  cewa "nonsense !"you  and   this  stupid  girl  should  leave  this  room  right  now "ya fad'a  yana furzar da iska mai   zafi  daga  bakinsa  da sauri ta kamo hannun maryama suka  fice  daga  d'akin ."

Bayan  fitarsu  kwanciya  yayi  yana cigaba da kallon hoton screen  din  wayarsa  dayawa daga cikin hotunta ya  konasu  hatta  tsarka  zanenta dake wuyansa always  yayi  flushing  dinsa  ,kadan ne daga cikin zanenta  suke cikin  d'akinsa   sai  na kan screen  din  wayarsa  suma nan kusa yana sa rai zai rabu  dasu  ya  huta  da  tunaninta  sosai  yake kallonta "muguwa "ya  furta a wahalacce   "kin addabi  rayuwata  kin  hanani  zaman  lafiya  ke  wace  irin  muguwa ce  da  zaki  damun  rayuwata ?ya  tambayi  kanshi  yana  mai  kawar da kansa daga kallonta  yana   tunani "anya  bazan  dinga  zagawa cikin  anguwane  anguwani  ba ko allah zai sa na ganta "? wannan ai hauka ne mr ata  kake  shirin yi ,me  yasa  bazaka  yarda  cewar  yarinyar nan ba  gsky  bace  Kmr  yadda  aka  Ke  fad'a  maka ?
shiru yayi  yana  jin  wani  irin  buguwa  da  zuciyarsa ke  yi  akanta  sosai  yake son raba kanshi da tunaninta  ."

Bangaren  maryam  kuwa   suna  taka  step  tana  maseefa "nifa  shiyasa  bana  son  zuwa  inda yake bashi  da  aiki  sai  maseefa  da  disga  mutun sannan wulakancinsa  baya  qarewa akan kowa sai akaina ko ban shiga  tsabgarsa ba sai ya hada dani ni wallahi bana  son  auren  zan dai  yi  ne kawai dan kun dameni , dan  allah  ku raba ni da aurensa na huta tunda ba'ayin  aure  mutun daya  ." murmushi nana hauwa'u tayi  "na lura kishi kike da zane fa  "babu wani  kishi  sister  amman ka auri mutun zuciyarsa na mafarkin wata aljana can wannan ai sai su shafi  mutun  azo arasa meke damuna "hhhhhhh nana hauwa tayi dariya "yarinya kina da aiki kam dan fasa wannan auren sai dai idan daya daga cikinku ne ya mutu  maryam  taja  tsaki ta  d'auki  hanyar  da  zata kai  ta  d'aki  ta  shige  tayi kwanciyarta dan kar mami  tayi amfani da zamanta  a parlour tayita aikenta  d'akinsa  shi  kuma ya samun damar ci mata  mutunci ."


Mr ata  na kwance akai  knocking kofar falon yana daga kwance ya bawa mai yi knocking din izinin shigowa hisam ne ya shigo cike da kulawa ya qaraso ya zauan yana cewa "a she bakaji dadi ba ? ya amsa da  kai kawai "oh my god  amman dai ba matsalar nan  bace ? "no ! wannan muguwar yarinyar ce "
maganar ta daki kunnuwan hisham ya dan tsaya yana kallonsa  yana nazarin maganarsa "yes  muguwa ce  taki  barin na ganta a zahiri  taki barin zuciyata  ta  zauna  yanzu  ko mafarkinta nayi bata min  magana , bata min murmushi this love is so hurt  wallahi  muguwa ce amman har yanzu ina jin sonta hisham na qasa  cireta  araina  ."

ya sake kallonsa ya girgiza kai cike da tausaya masa ya mike da kyar ya shiga bayin dake ciki ya zubar da yawu ya dawo ya zauna ya sake kallon hisham yaga shi yake kallo fuskarsa da mamaki ya sake  girgiza kai dan gbdy ya fahimci wa yake nufi "gsky wannan yarinyar tana baka wahala " ya langwabar da kanshi gbdy  ya koma kalar tausayi "wallahi yau shekara nawa ina faman da soyayyarta amman sam sam yarinyar nan bata tausayina yayi mgnr duk jikinsa ya sake kana kallonsa kasan bashi da lafiya ."

"da  ba dan baka da lafiya  ba  ai da mun dan dinga zagawaya  cikin unguwani ko zamu ganta ko wanda yasanya  nima  nayi  wannan  tunanina  hisham   amman  bazan  iya  ba  ya  fad'a  yana  lumshe  ido yana  jin  wani  d'aci  a bakinsa wanda ya rasa na meye ,"karka ce haka ata  ka bari  idan  ka samu sauki  kaje  france  ka  dawo  lafiya  sai  mu  fara nemanta " nace bazan  iya  ba  wannan  muguwar yarinyar  kona  ganta  damuwa  zata zame min
a  zuciyata ."

Zuciyarsa  na zafi yace tashi muje ka  d'a zaga gari ko jikinta  zai  rage  nauyin  da  yake "ya fad'a yana jin tsantsar soayyarta na  ratsashi  koina  ajikinsa ya mike da kyar "ata  kayi  zauna  gida  wallahi  jikinka babu  kwari   "karka  damu  muje  kawai tunda kana tare  dani  bani  da  wata  matsala ahankali suka sauko falon  qasa   babu kowa a  falonta   farko da alamun mami  tana  falonta  na  uku yaso sheidawa mami  amman  yasan  zata  hanashi  fita  koina  dan  haka   ta  kofar  baya  suka  fice  dan baya son escourt dinsa su  bishi  ya zauna shiru a gefen hisham dake  tuki  yana ciza lip's  dinsa "ina muka dosa "?cewar hisham ".

muje    gra   dan   ina  ji  ajikina a irin  wuraren  nan zamu  samu muguwar yarinyar nan   "hisham  ya kwashe da  dariya  har da  dukan stearing mota shi  kuwa gogan ya hade rai a she a fili   yayi mgn ba "wai muguwar yarinyar nan wallahi ata baka  da dama
,yanzu  dai  wani gra ne  a kusa damu  ?mr ata yayi  masa  banza  ya maida kallonsa  gefen  titi yana kallon mutane da motocin dake kai  kawo "duk  da kaki kayi mgn bari muje ikeja gra nan ma shiru  yayi  yaki  cewa  komai  "gskiy ata ka iya  bada suna pricess ta tashi da  sarauniya  ta  dawo  muguwa"dan  allah  malam  ban son isknaci ka maida hankalinka ga tuki " ya fad'a  yana nuna masa gaban mota da hannunsa  "naji  amman  yanzu ace taki sa'a   ka ganta  a  zahiri zaka ganeta "wallahi  zan  ganeta ". daga haka bai sake yin magana ba  shiru motar tayi babu wanda ya sake cewa komai  har suka d'auki titin  ikeja ."


Ahankali   Ummah  da  aunty  da maryama  suke  tafiya a hanyar   fitowarsu  titin unguwarsu domin su dauki  hanya zuwa marcaz  duba jikin hafsat diyar aunty  fati , maryamah  ta  hango mlm yahuza ya nufo  hnayar  da  suke  da littafi a hannunsa  da alamar islamiyya zashi  tun daga nesa ya fara raragefen  alamun Kamala ya durkusa har kasa ya gaishe da aunty da Ummah tare da cewa "unguwa zaku né ? maryama ta d'an kallesa ta  d'an  basar dan kar aunty da umma su  fahimci akwai wani  abu atsakaninsu tace" rakiya zanyiwa aunty  tare da umma  zuwa bakin titi ."


" allah sarki ya sake durkusawa har kasa ya  gaidai  umma da aunty duk da yasan tahirin rayuwarta amamn  bai  ta'ba  sanya mahaifiyarta  acikin  kwayar idanunshi  ba  amman ya gane aunty ce mahaifiyarta  dan  ko dan yanayin tsawonsu iri  daya ne , mlm yahuza yayi murmushi yace "dan allah ku dan jirani  minti uku kafin ku isa titi ma na dawo amman dan allah karku tafi a kafa  Ummah  ta d'an yi murmushi tace "kada ka damu dan allah , kada ka wahalar da kanka ba  wani  nisa da inda zamu ba mu gode Kwarai da gaske ."

" a dai min Afuwa ina zuwa  yanzu  Ummah  tace tô shikenan mlm yahuza yayi murmushi ita dai maryama ta bisa da kallon mamaki dan bata san me yake nufi da kafin suje titi ya qaraso ba ummah ta dubeta cikin mamaki "wannan kuma wanene ? wallahi malamin mu né na makaranta islamiyya ummah  tayi shiru domin ta danyi zargin son maryama din yake itama dai marayam taso ta fada mata kasancewar bata boye mata komai amman ganin fadar bashi da wani amfani tunda da zarar ta amincewa mutun ya fara zuwa kwana biyu sai ya gudu batare da laifin komai ba ."

suna tafiya suna hira  har suka karaso bakin titin gwagulori wanda ya dawo sabon titi  a yanzu sakamakon gyaran daaka masa suna tsaye kawai sai ga mota ta nufo inda suke maryama tasha jinin jikinta domin dai tasan bashi da mota amman babu mamaki ko ta abokinsa ce yayi burki agabansu ya fito daga cikin motar "umma  ku shigo na kaiku har inda zaku "maryama shiru tayi mamaki ne ya damu zuciyarta tunda take bata ta'ba jin mlm yahuza ya dan burgeta ba sai yau sosai tayi farinciki da abinda yayiwa mahaifiyarta da ummanta ido kawai ta tsura masa ta cikin nikaf dinta tana kallonsa cikin farinciki shi kanshi ya fuskanci  hakan ."

ya zagaya ya bude masu  mota suka  shiga kafin ya zagaya bangaren direba ya jefa mata wani kallo mai nuna tsantsar so kawai itama ta tsinci kanta da mayar masa da murmushi suka wuce ita kuma ta koma gida duk da  abinda yayi mahaifiyata da ummah  a yanzu bata ji ta  fara jin mlm yahuza acikin zuciyarta ba amman  ta kudirce zata danne zuciyarta ta fara sauraronsa ."

Hud'u  daidai  ta shirya zuwa islamiyya bata tsaya jiran sakina ba  ta  kama  gabanta acikin aji sune na farkon zuwa ita da kawarta subai'a wacce suka qare karatu tare ahankali suke hira fitowar result dinsu kafin malamin da zai daukesu darasin qurani ya shigo sosai taso tayi mata hirar mlm yahuza amman ta kasa har aka cika a ajin mlm abbas ne ya shigo nan da nan suka fara karatu ita dai karatun yau dai tazo makaranta tayisa amman zuciyarta fal da walwala da irin farantawar da mlm yahuza yayi mata dan tana matukar qaunar mahaifiyarta da umma duk wanda yaga girmansu kuma ya mutunta matasu tô lallai zai samu wani babban matsayi acikin zuciyarta most especially mahaifiyarta tana tausayin halin data tsinci kanta ciki yana daya daga cikin abinda yasa ta d'auki komai nata da mahimmanci ."

"ta godewa allah ta kuma ta godewa mahaifiyarta da umman tare da  abban sadam domin sun tsaya akan ganin sun ingata rayuwarta da karatun boko da Arabic tun alokacin da take secondary babu wanda yasa rai zata cigaba da karatunta zuwa jamia sai gashi kwatsam allah ya taimakesu ita da subai'a sun samu scholarship daf da zaa tashi ta shigowar mlm yahuza makaranta  ,taso Kwarai ta gansa tayi masa  Godiya ta fito tana duddubawa ko zata gansa amman bata ganshi ba zuciyarta taso ta gansa farincikin da yasa  iyayenta  take son tayi masa godiya dan tasan dole zai ji dadi acikin ranshi ."



Bayan an tashi daga makaranta bai biyota ba kamar yadda ya saba sai dai kafin ta isa gida kanwarsa nafisa tayi saurin isa inda take daman kuma tasanta sai dai ba aji daya suke ba tana gaba daita sosai suka gaisa tare daita suka cikin gidansu inda suka iske aunty salma a tsakar gida  tana zaune tana waya ganinta tare da nafisa yasa aunty salma kashe wayar suka gaisheta suka wuceta suka shiga bangarensu maryama." suna shiga ta nuna mata wajen zama "nafisa ki zauna ga waje tayi murmushi ta zauna akan kujera ita kuma ta shiga dakin aunty ta duba inda aunty tasaba ajiyar kudi taci saa ta samu naira dari ta dauka ta fito tana cewa nafisa "ina zuwa ."


"nafisa ta mike ta biyota ina zaki bari muje tare maryama tayi dan Jim dan taso ta zauna taje ta siyo mata lamurje ta kawo mata amman bata da choice dole ta barta suka sake fitowa tare kai tsaye bangaren aunty hassana suka shiga tayi sallama ta isketa zaune tare da yaranta babu wanda ya amsa sallamarta bare ya kalli inda take bata damu ba dan ta saba "aunty hassana ina yini akwai lamurje?
"Akwai na nawa zaki tsiya "?amm.. na naira dari ne wani dogon tsaki taja "ai nasan bazaki canza zani ba daga na naira darin babu qari kullum ana waje daya baa cigaba ni  bani kudin ki shiga ki dauka ki bace min da gani ."

Zuciyar  nafisa ta cika da mamakin aunty hassana maryama ta mika mata kudin ta shiga ciki ta dauka suka fito ta mikawa nafisa gashi nafisa babu yawa "kai  haba ai babu komai ai danasan ma kashe kudinki zakiyi da tun farko na hanaki " karki damu ai ba wani abu bane maryama ta fada tare suka shiga bangaren Ummah duk inda maryama tasa kafarta nan nafisa take ajiyewa ta share wa umma gida ta gyara mata koina tare da nafisa suka fito zasu wuce aunty salma ta kirata cike da isa ta isa inda take "kije kiyi min shara "

"Shara !"
Maryama ta furta a hankali?eh ko bazakiyi bane kika tsaya kina maimata min abinda na fada ?zanyi ta fada a taikaice tare suka shiga bangaren aunty salma ta fara shara "aunty maryama kawo na share miki da sauri dan akwai abinda ya kawoni "? itama tashi jinin jikinta dan tunda suke da nafisa  bata taba zuwa inda take ba sai yau "no ki barni na share nima yanzu zan gama ta zauna akan kujera sakina da shukura suka shigo shukura  na ganinta ta washe mata hakora "nafisa yau kece agidanmu ?ta tambayeta murmushi ya sake bayyana akan fuskarta "eh nazo wajen aunty maryama ne "aunty kuma ?ta fada a rude "eh mana aunty ce ai maryama tunda zuciyar babban yayanmu ta kamu da matsanancin sonta dan har wani kirki ya kirkirawa kanshi dan kawai ya aikoni wajenta ta fada batare da wani shakka ba ."

shukura  batace komai ba ta zauna kusa da nafisa " inata son nazo gidanku amman ban samu damar zuwa ba saboda makaranta nafisa tayi murmushi "ai kuwa sai ki arawa kanki lokacin ki dinga zuwa gidanmu tunda yayana ya kamu da soyayyar maryama nasan naki  matsayin sai yafi nawa zance bai yiwa shukura  dadi ba dan haka kawai taji bata son wata halaka a tsakanin maryama da mlm yahuza haka kawai take jin rashin jin dadi aranta ."


Maryama tana gama shara ta fara kokarin wucewa yayinda nafisa take qoqarin mikewa shukura  kuma tana janta  da hira "kinga bari na isar da sakon da aka aikoni gobe ma hadu a islamiyya ta tashi tabi bayansa maryama suka jera har cikin falonsu atare suka zauna akan kujera nafisa na cewa "aunty nah "maryama tayi murmushi "kai nafisa da ki daina ce min aunty kullum fa da sunana kike kirana "ai yanzu komai ya canza baki ji yan karin magana ba sunce idan kidi Ya canza dole ma rawa ta canza nafisa ta fada tana dariya "ya karatu yanzu uzukin nawa ?maryama ta sauya magana dan bata son wata maganar soyayya mlm yahuza yayi mata mutunci Kwarai kuma ta yaba masa amman batu na soyayya bata jin zata iya

yayana ne yace na fad'a miki zai zo zuwa anjima maryama tayi murmushi amman shine tun dazu baki fad'a ba  kika zaunar da kanki "ai ina sane na zauna ina qarewa zabin yayana kallo naga shin haukan da yake akanta ya dace abun mamakin sai naga tafi gaban tunanina ashe da kawai kallonki nake ta fad'a tana dariya "kai nafisa a she haka kike kema?maryama ta fad'a tana murmushi santi nake yi yayana ya iya zabe wallahi maryama nayi matukar farinciki da yaya ya sanar dani Ke yake so kuma har kin amince nan fa yanayin maryama ya sauya daga murmushi da take zuwa mamaki "ita a ina ta amince masa da zai qarar .?

"kun dace da yayana sosai ni daman ina tunani wa yahuza zai dauko mana acikin yammatan dake mutuwar sonshi saboda tsananin kyawunsa da kyawun halinsa uwa uba ilimi kema kuma munyi saa a komai kina dashi taso kwarai ta tsaida nafisa akan yayanta amman kuma sai ta kasa har zuwa lokacin data ciro wata karamar takarda ta bata tace gashi inji yaya in baki hanuna da naki ta fad'a tana shirin tashi daga kan kujerar da take zaune  itama maryama ta tashi ganin tana alamar fita domin rakiyarta da hannunta ta dakatar da maryama "zauna abunki ba sai na wahalar dake ba ki zauna ki karanta sakon yayana cikin tsigar wasa maryama tace "ban son iskanci nafisa naga alamun raini ya fara shiga tsakaninmu ta bude baki "ni kuma  asuwa na raina aunty  amman dai Kiyi zamanki wallahi na gode ?"

Ta koma ta zauna ganin idan ta biye mata sai su kai dare bata gama iskancin ba ta fice ita kuma ta samu waje ta zauna ta bude takarda da nafisa ta bata ."
_Ina son ki takaita kanki  da abinda kikasan zai war gaza farinciki dana gani akan fuskarki ina bukatar ganinki cikin farincikin dana ganinki dashi yau my maryama ina son jin muryarki cikin kunnuwana ina son jin hirarki zanzo yau byn sallah ishai_

Ta sake karantawa ta sauke naunayen ajiyar zuciya ita sam bata jin wata soyayyarsa wata killa da a shekaru biyu da suka gabata yazo lokacin tana shekara shatakwas kuma alokacin maza basu zama abun tsoro a wajenta ba da babu mamaki taji tana sonshi har ma ta iya aurensa amman zatayi kokari ko yaya ta fahimtar dashi illa soyayya gareta ."

ahankali ta jingina

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login