Showing 60001 words to 63000 words out of 168608 words

Chapter 21 - Mar'adam's Book 1 Hausa Novel Complete

maimakon tai concentrate akan  karatunta da kullum yake yin baya   sai ta maida hankalinta ga tara  samari  marasa amfani , tare suka  shiga  jss one  ,sukai  jss1 tare, sukai  jss 2 tare  sukai exam na zuwa  jss3  ta barta suka  wuce ss 1  ita  da sakina itama sakina lokacin  da zasu shiga ss2 tayi fail ta  wuceta  sai dataje ss3  sannan  kaulat   taje  ss1 sakina taje ss2   gashi  ita  yanzu daga rubuta jarabawar karshe ta fito  amman  ita  kuma har kullm cikin repeating take a qalla a tunaninta tayi repeating  ya kai sau hudu   allah yayi  mata jarabawa ta rashin ilimin  dan  babu  abinda tasani  daga bokon  har islamiyyar zero ce amman  ita da mahaifiyarta kullum cikin cin zarafin mutane suke barin ma ita  da tarasa dalilin dayasa suka  tsaneta suka tsani ganin wani  tare daita  duk wanda zasu gani tare daita wala mace wala nmj sai  sunyi qoqarin rabasu "


"Wai bilal meye haka ne ? ka wani karkace  kai kana kallon maryama gbdy ma ka manta ina tare da kai idan kasan ba wajena kazo ba na qara gaba dan na fahimci duk sanda kaga wucewarta sai ka maida attention dinka wajenta ko zuciyarka na kanta ne sai kayi min bayani  nasani ba wai ka raba hankalinka gida biyu ba alhalin ina tare da kai  "?

"wallahi da tun  asali ita na fara gani  to da babu abinda zai kawoni wajenki  yayi mgnr  acikin zuciyarsa  amman a zahiri cewa yayi  "meye laifi dan kalli halitta mai  natsuwa  ?  ta zaro idanuwata waje  tana masa wani irin kallo kafin  daga baya cikin d'aga murya cike  da  maseefa tace "ko zaka koma  wajenta ne ko me kake nufi da wannan maganar ?da zan samu haka  wallahi da naji dadi sosai "ya sake  fad'a acikin ransa "ai daman haka halinku maza yake da zara kunga mata sai kama 'bare 'bare  to du ka gama 'bare 'barenka ka hakura dan ita wannnan dai ko ka  koma wajenta ma dole ka gudu da kafarka dan idan kasan akanta matsalar  duniya ta qare, kana fara soyayya  daita  komai  daka mallaka  zai  qare idan kayi sa'a ma wani  mummunar bala'i bai sameka ba  tayi samari day day sun kai guda hud'u kuma duk da aure suke sonta amman da zarar sun fara zuwa zance wani mummunar bala'i Ke samunsu ganin ta inda take shiga ba nan take fita ba yasa ya matsota sosai ya rage murya ya soma magana  ."


"Haba kaulat banda sharri fa dan kawai mutun yace yana sonta sai wani mummunar bala'i ya samesa sai kace wata annoba ,wannan ai tafi annoba "to  ko zaki hadani daita kawai ina son naga tasirin bala'in dake tattare daita ?tayi shiru kawai tana nazarin maganarsa idan zata kintata daidai son maryama yake cikin karayar da murya kaulat tace "me kake nufi da wannan mgnr ?ya tsura mata idanunshi kawai "kaga bilal banason wannan maganar karka qara min  hk da kuka ta qarasa maganar dan duk cikin samarinta tafi qaunar bilal "ya salam !meye kuma abun kuka anan daga wasa ?kuka kaulat take sosai ganin haka hankalinsa ya tashi sosai "kinga wallahi ni wasa nake ya ciro hankacip ya mika mata "wip your tears karki min asarar hawayenki da kyar ya samu ya rarrasheta ta daina kuka ."

Da sallama  maryama ta shiga part dinsu inda ta iske habib na  zaune akan wata tsohuwar kujera mai zaman mutun uku  yana ganinta ya saki fuska yayinda aunty ke zaune akan daddumar sallah  , " heartbeat sannu da zuwa "yauwa after dad  ta fad'a tana  cire  nikaf din fuskarta da hijab din jikinta " yau baka fita bane na ganka a gida ?"wallahi na fita ban dai  jima  bane  saboda  ranar  daake  yau  tayi zafi da  yawa "gsky  kam  yau  an zuba   rana ga doguwar tafiyar  mun   kwaso  wallahi a matukar gajiye   nake  da kyar na  qaraso  gida , kasan tun daga dopemu da kafa  muka  shigo agege ya zaro ido yana cewa "halan matsalar mota ?ta gyada masa kai tana rausayar da kwayar idanunta ."

Ya mike  tsaye   ya  qarasa inda  d'an  qaramin fridge dinsu  thermocool yake wanda ya gaji dan murfin ma ya balle idan an bud'e da kyar ake maidashi a rufe ya ciro pure watar mai sanyi ya ajiye akan hannun kujera ya maida murfin  fridge  din da kyar ya qaraso inda take "heartbeat ga ruwa ki sha  "yauwa after dad  na gode  sosai  ya koma Kan kujera daya tashi yana cewa "ya exam din fatan yazo da sauki ?sai data zuke ruwan sannan tace "babu wani sauki amman muna fatan samun nasara daga Allah bata sake cewa komai ba sannan bata zauna ba ta qaraso bayi ta dauro alwala ta fito ta d'auki wani dadduma sallah daga inda suke ajiyewa ta shimfida kusa da mahaifiyarta dake zaune har lokacin tana kaiwa allah kukata akan yaranta most especially maryama wacce ta fita jarabawar karshe ta tada sallah a natse ."

Bayan ta idar da sallah  ta mike tsaye  tana  ninke sallayar ta samu waje ta zauna kusa da habib tana sauke numfashi "kai wallahi ban ta'ba gajiya irin na  yau ba wannan hanyar ta yanoba akwai matukar wahala alhamdulillah  daga yau dai mun huta bata gama  rufe  bakinta   ba taji an bako kofar shigowa falon nasu  da  karfi atare suka kallo kofar kaulat ce tare  da mahaifiyarta tsaye suna huci Aunty hassana tace "yauwa gara da Allah yasa na sameku  gbdy uwa da ya marasa  mutunci  to wallahi na gaji  ki jawa wannan tantariyar yartaki mai  suffar  manufukai kunne ta shiga  hankalinta  bata tashi dawowa  gidan nan daga yawon karywancinta  sai yamma tayi lokacin  da manema  auren yarana suke zuwa ta dinga wannan yar iskar tafiyar tata  simi simi kmr macijiya dan kawai ta dauki hankalin samarin  ya'yanmu to wallahi kinyi kadan  bake  ba hatta uwar  data kawoki  duniya ga tanan tayi kad'an bare Ke karan  kada miya ,ko su sukayi koba dinki?

" ko su sukace maza su dinga gudunki  ?ko Kuma su suka sanya mugun balai ajikinki da maza ke gudunki ? babu daya da sukayi aciki dan haka daga yau banason sake ganin gyallinki idan bilal yazo gidan nan  aikin banza  kawai kyau  har kyau amman bashi da amfani , ana  fakewa da karatu ana  yawon karuwanci "tana kawo nan habib ya zabura ya mike jikinsa na rawa  tare da daga hannu zai zabga ma Aunty hassana mari...."

aunty  wacce ta mike tsaye tun fara maganr Aunty hasana tayi  saurin rike masa hannu tana cewa " qul  habib  karka fara ko ka manta wacece ita da matsayinta agurinka?  "amman male  bakiji kalmar da take fad'awa heartbeat ? "an fada Kuma an sake fada dan uwarka da ubanka kayi duk abinda zakayi karya na fada ba yawon karuwanci take ba ?" idan bashi take ba me yasa samarinta suke gudu su barta ?idan baka sani ba kasani daga yau ai raba masu kanta take kmr MTN shiyasa suke gudu suna barinta  jairi kawai da wani katon kanka can shegu marasa mutunci jinin marasa mutunci ai da bakayi haka ba bazansa kayi gadon dangin uwarka ba masu arziki amamn matsiyatan mutane  ."

Tunda ta fara magana hanakalin maryama yay  kolowar tashi sosai ta firgita da kalaman aunty hassana  ba idanuwanta suka cika da ruwan hawaye ta kalli inda kaulat take da kyar ta bude baki cikin sanyayyar muryarta mai tsananin kashe jiki "mama Ke kanki sheida ce akaina Kinsan bazan ta'ba aikata wani abu da zai 'bata sunan ahlina ba ,walalhi bana aikata komai karatu kawai nake zuwa  sannan mama ko babu komai ni din diyar d'anuwanki ce kuma abar tausayi a irin wannan rayuwar da muke wacce babu wani yanci acikinsa sai tsabar kaskanci kece mutun ta farko da daya kamata ki cetomu amamn sai gashi kece mutun ta farko dake bibiyarmu da mugun alkaba'i  ta sake kallon inda kaulat take tsaye tana zabga mata harara."

"ga kaulat nan idan zata fadi gsky babu wani abu danayi hassalima ko magana banyi ba ta gefensu na raba zan .." dakata dan Allah malama  banson manufarci bangane atambayeni ba ta fad'a cikin zafi rai kafin daga baya  ta dawo gabanta ta tsaya "duk abinda mama ta fad'a gsky ne kisa kunnen baseera ki  ji abinda aka fad'a miki ,ki tsaya iya matsayinki ki kiyaye shigowa alokacin da bilal yake zuwa tana magan tana nuna maryama da yatsan hannunta "idan karuwanci zakiyi sai ki san inda zakiyi ba ..." tas tas !! habib ya dauketa da gigitaccen mari "da uban wa kike wannan maganar ?da ubanka nake banza kawai mara kunya  ta fad'a tana dafe kuncinta .

  "idan kika sake zagina ko zagin yaruwata wallahi sai nayi miki jina jina anan shegiya yar iskar banza kakar  ubanki ce karuwa..."ai bai gama rufe baki  ba Aunty hassana ta sauke masa nashi mari ji kake tas tas !! sau biyu ajere "dan uwarka a gabana zaka mari yata ?" jakar gidan uwarka ce da zaka mareta ?"
habib ya bude baki zai sake yin  magana aunty ta sake dakatar dashi" karka Kara cewa komai wannan idan da sabo tuni princess ta saba  dan haka komai hassana zata fada akanta  banason ka  sake cewa  uhm bare uhm uhm dan yarta ce halak malak idan karuwa ce ita tayi silar zuwanta duniya ."



aikuwa ransa yayi massefar bacci ya dinga Jin wani tuttukin bakinciki na taso masa "ke ai da kin kuskura ya sake ta'ba min lafiya 'ya wallahi da yaga aika aika da yau mun kwashi Yan kallo dake dan kece saar yina basu ba habib bai daddara ba  yace "allah Aunty  ki kama girmanki Kafin na miki abinda bakya tunani koda yake ai ba girma atare dake mahaifiyarmu tafi karfinki sai dai Kiyi damu ba arabi ba boko shiyasa baki san haramcin abinda kikeyi ba "da uwarka da dangin uwarka kake ba dani ba tana gama fadar haka taja hannun kaulat suka nufi kofa tana cewa"dan kutumar uba kawai ."


Kuka  maryama  take  sosai  a wajen  tamkar ranta zai fita  aunty  ta qaraso  wajen da take tsaye  tare da dafa maryama  me ye kuma na kuka  bayan wannan ba sabon abu bane ? Kuka taci gaba dayi  habib ya matso "dan allah heartbeat ki daina kuka idan ba haka ba nima zanyi kuka tana kuka habib na kuka nan da nan aunty ta samu waje ta zauna ta d'aura kanta a hannun kujera itama kukan take da karfi
A hankali suka qaraso suka durkushe kasa kusa da kafafun Aunty tare da daura kansu a saman cinyarta  suna  cigaba da rera Kuka    wanda har  umma ta shigo   basu saniba" umma  ta qarasa shigowa da sauri  tare da dafe qirji  bilkisu  me ya faru Kika tasa yara gaba kuka ? Kuka  suka  ci gaba dayi ba tare da sun bata amsa   ba..."Ke maryama taso muje ki gayamun me yafaru da ke  da mamanki da kaninka haka  kuke kuka ? ."


hannunta umma  ta riqo suka nufi bangarenta Aunty salma  dake tsaye taga wucewarsu maryama na goge kwalla tasan ba lafiya ba  ta biyo bayansu da sauri umma   ta zaunar da ita  a Kan kujera ,a lokacin kukan nata ya fara raguwa"me ya sameku  haka kuke wannan uban kuka haka maryama ? Jin shirun da tayi ne yasa aunty  Salma   ta tunzura "wani mahaukacin tsawa ta sakar mata wanda sai  da ta burkice  "wai  ba magana ake miki ba ne?sai lokacin umma tasan da shigowarta ta dago tana kallon tana mamakin hali munafurci irin nata ko wa ya kirata data shigo ? umma ta hade rai tana cewa    "a'a salma   ba haka akeyi ba ki barni daita kawai karki hargitsa mata lissafi ki barta zatai magna."

"uhm ina jinki maryama fad'a min damuwarki cikin sheshekar kuka ta zayyanewa umma komai da ya faru naunayen ajiyar zuciya ta sauke "gsky bata kyau ba , amman  Kiyi  hakuri ita rayuwa ta gaji haka komai da  kika gani  kafin a samu nasara sai anyi  hakuri   in sha allahu wata rana zai zama labari ,ku ya kamata ku dinga kwantar wa da mahaifiyarku hankali ba wai ku dinga tayata kuka ba yi hakuri kinji maryama   Ki bar komai a wajen Allah in sha allahu sai kin zama madubi abar dubawa acikin gidan nan masu takaki wata rana sai  sun zama fadawanki "wallahy aunty aseeya  har da laifinki wajen iskanci yarinyar nan kawai daga yar wannan mgnr zasu zauna suna kuka Kmr mutuwa akayi ke km   sai  ki zauna kina  bata lokacinki ."

" babu ruwanki dole na rarrashi diyata  mikewa tayi ta fice cikin fushi umma tabi bayanta da kallo karki qara damuwa da sharrinsu idan kina kuka suna ganin rauninki to kin shiga matsala dan kullum da abinda zasu dinga miki amman idan kika jajurce kece zaki ga rauninsa ta fad'a hk tana goge mata fuska da gefen zaninta  "kin ci abinci ma kuwa ?ta girgiza kai alamun a'a to maza jeki ki rarrashin mahaifiyarki da danuwanki ki dawo ga abinci kizo kici ta mikar daita ta rakata har bakin kofar fita  da kyar ta fito zuwa bangarensu wanda lokacin tuni aunty ta daina kuka suna zaune da habib  tana gama shigowa taji  saurin muryar Aunty  "my princess taho kici abinci nasan kina tattare da yunwa."

Babu yadda ta iya ta sakar mata murmushin gefe baki  tana dubanta tace  "kamar kin sani Aunty gbdy suka qarasa  zuwa Kan kujerun roba dake zagaye da qaramin table wanda shima din na roba ne aunty na zaune tare da yaranta suna cin abinci amamn ita  tayi shiru tana tunani  ta kasa cin abinci "male kici abinci mana ta dago ta kalli habib maryama ta ajiye spoon din hannunta ta soma magana a tsanake kamar ba yanzu ta gama kuka ba."

"kiyi hakuri aunty akan duk abinda Ke faruwa a gidan nan wani lokacin  Allah yana gwada mutane ya gwada imanin bawa kinsan al'imanu yazidu wa yankus imani na raguwa yana qaruwa to Ke aunty a mizanin da kike allah yana son ya gwada imaninki ne Kan wasu abubuwa dake faruwa damu  duk duniya bani da abar yabo da koyi da hali mai kyau sama danaki sannan kowa yasan ke din mutuniyar kirkice hatta makiyanki suna fadan hk a bayanki to me yasa abubuwanki sukaki  daidaita duk wannan hakuri naki da juriyar amman ba komai bane  kawai Allah yana son ya gwada imaninki da jin tsoronsa ne dan duk allah yana sane ya tsara  haka  hk ."

"Mu  qara hakuri hakuri ne kawai zai kawo mana sauki kuma Allah yace annan nasara maasabarin duk wani nasara na rayuwa yana tare da hakuri ,
hakuri da kike dashi yana cikin tsani da zai kai  mutun zuwa aljanna, hakuri halin manzon allah ne  wal hilmi wal sabri duk kina dashi aunty kina da dauriya kina da juriya kina da tawakkali kina da imani kina da ibada so duk wani abu da kike ganin yana samunki mara kyau ko yana shirin faruwa dake to wallahi jarabawa ce km kina ta cinye jarabawar sai kiga allah ya tsara bazakaji dadi anan duniya ba sai a lahira ,wallahi aunty da ace kana da rabo a duniya baka dashi a lahira wallahi gara ace kana dashi a lahira  baka dashi a duniya ."


"sai abu daya  da nake   son ki fad'a mana" ta dago da rinannun  idanunta ahankali tana duba kyakkyawar  diyarta son kowa kin wanda ya rasa  abar tinkaho  kuma yar baiwa domin samun irinta sai an tona "aunty idan bazan takuraki ba  ina son ki fad'a mana inda danginki suke muna son musani domin na fara tunanin akwai wani mummunar abu daya faru a baya dake ,dan idan babu komai bazai yuwa kana  da dangi kuma kuna gari daya amman bakwa ziyar juna"tunda maryama ta fara magana idanun aunty  suka sake  cika da hawaye basu samu nasarar zuba ba sai data kawo karshen mgnrta "ki fad'a mana mu yaranki ne  bazamu taba juya miki baya ba duk runtsi duk wuya muna tare dake koda kuwa kice kika batawa yan'uwanki zamu kasance dake  domin kece karfin gwiwarmu  ta qarasa mgnr tana riko hannun mahaifiyarta ."


Mmm sudais

💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗


*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan  littafin  na kudi ne mai bukatar karantashi   byn na kammalashi zai  biya 1000 ta wannan  account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a tura 09136918331 alert domin tabbatar da an tura  domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina  (Hausa bakwai ) a YouTube.

Page 14


"Shiru aunty tayi tana jin fad'uwar gaba mai tsanani tafi mintuna ashirin bata ce qala ba habib ya kai hannu ya d'ago ha'barta yana kallon cikin kwayar idanunta dake kwance da ruwan hawaye "male kece karfin gwiwar dake tafiyar da rayuwarmu Kinyi mana komai arayuwar mu ,kin nuna mana tsantsar soyayya ,kin nuna mana daidai da ba daidai ba kin bamu gatan da ba kowa yake samun irinsa ba wato ilimin addini dana boko , kin inganta rayuwarmu mun yaba miki kuma mun jinjinawa qoqarinki garemu da taimakon Allah da taimakon heartbeat gashi har heartbeat ta kammala karatunta kalamai soyayya iri iri dana sanyaya zuciya yake furtawa gareta wanda yake sake tsuma zuciyarta da soyayyarsu "wannan alfarma ce ki fad'a mana ."


Duk   yadda   habib  ya  d'auki lokaci   yana magana sai dai har zuwa wannan lokacin aunty  ta Kasa furta komai garesu   illa numfashin da take  janyowa ahankali tana fitarwa da kyar
sun sake d'aukar tsawon awa d'aya a wannan yanayin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login