Showing 15001 words to 18000 words out of 168608 words

Chapter 6 - Mar'adam's Book 1 Hausa Novel Complete

duniya Kuma zai aureta sai Kuma tayi tunanin ko aljanu sun shafesa ne a take agurin tace "Adam ka sausarareni da kyau mafarki baya zama gsky ..."no aunty wannan zai zama gsky yayi mgr a fusace .... "
jikinta yayi mugun mugun sanyi ta ajiye nata damuwar ta fara lallabashi dan taga alamun idan ta cigaba da mgn komai zai iya faruwa dan ya zurfafa soyayyar yarinyar sosai ya mike tsaye "ki taimakeni ki fahimtar da sweetheart ku tayani da adduar samota "aikuwa zan fada mata, a ranta tace babu adduar da zamu tayaka tunda mun san abinda muke yi har ya bar office din bata dauke idanunta akansa ba ...."

Washegari aunty shahida ta shirya ta samu hjy zulai "ta Koro mata duk halin da adam yake ciki" mu tashi da addua mami saboda Adam yayi nesa cikin wata duniya ,hjy zulai ta gyada Kai cike da matsanacin fargaban tace "Allah kyauta inshallahu zan tashi tsaye da addua da Kuma sadaka lallai da alamun aljana ta auresa idan ba haka ba ga lafiyyayar yarinya me zai Yi da wata a mafarki "shine abinda nayita kokarin na fahimtar dashi yaki yarinyar Nan tunda ta taso bata da matsala ke din mahaifiyarta ce zamu shiga gidansa a duk sanda ranmu yaso, Kuma zamuyi abinda muka ga dama tunda ta muce ita ."
"Allah yasa ya gane alkhairi ake binsa dashi "Ameen aunty shahida ta fada tare yiwa mami sallama har wannan lokacin Babu Wanda ya sanarwa Maryam batun aurenta da adam ana jiran sai ya amince sannan a tunkareta da batun cikin saa da jajicewar mahaifiyarsa da yayarsa mr ATA ya amince a wanni yammaci sun dade a dakin suna tautaunawa ya numfasa idanunshi a runtse ya cigaba da magana "Amman fa duk sanda na samu yarinyar da nake nema zan Kara da daita "ai wannan ba wata damuwa bane inji cewar aunty shahida ta fadi haka ne sbd tasan da wahala ya samu yarinyar mafarkinsa ita kuwa mami shiru tayi tana kallonsa a karshe ta girgiza Kai tana masa addua acikin ranta ."

aunty shahida ta fito daga dakin mami tare da Mr ATA dake faman cika Yana batsewa da cicci magani bai tsaya ba ya nufi kofar fita aunty shahida tace "adam Dan Allah bari na fito ku saukeni a gurin aiki Bai ce mata uffan ba ya wuce sannan ta Kalli Inda maryam dake zaune tare da nana hauwa'u suna kallo da wayar maryam tace "Maza Maryam dauko mayafinki kizo muje kiyi min rakiya zuwa asibiti Nan take ta mike daman a shiryenta take mayafi kawai ta dauka suka fito tare , Kai tsaye Inda motar mr ATA yake suka nufa limoxin ta bude gidan baya ta shiga maryam ma tayi kokarin bude dayan bangare ,aunty shahida tayi saurin cewa "zauna a tsakiya kusa da adam maryam taji maganar wani iri ta dan saci kallon aunty shahida tana mamakin jin furucinta" zauna a tsakiya kusa da adam to me hakan yake nufi?Tana son tai tmby babu hali dan haka  jikin a sanyaye ta bude ta shiga ta zauna nesa dashi kamar wata tsuntsuwa ta kame Kanta tana jin mummunar faduwar gaba from no where " .

Direban mr ATA ya ta-da motar suka soma kokarin fitowa daga cikin gidansu "Ina muka nufa ma kika ce ? ita Kuma wannan ina zaki daita nifa bana son kwashe kwashe a motata? asibiti ta bashi amsa duk da tasan yaji abinda tace , bai sake cewa komai ba har suka iso asibiti ,yaki fitowa Yana jiran aunty shahida ta karasa fitowa dan maryam tuni ta fito "adam muje akwai sakon da zan baka yayi shiru yana maimata maganarta yaji Kmr yace ta bawa mrym ta kawo masa Amman Kuma baya son abinda zai hadashi da yarinyar "a hankali ya fito ransa a bace Kai tsaye office dinta suka nufa aunty shahida ta bude office dinta dukkaninsu suka shiga Yayinda mr ATA ya tsaya daga bakin kofa yana jiran ta bashi sakon da tace aunty shahida tace "bismilla mana ranka shi dade mr ATA shigo ka zauna  ga guri nan yayi mata wani irin kallo yana bukatar qarin bayani akan abinda ta keyi "ta gyada masa kai "shigo mana ." da kyar mr ATA ya shigo office din ya zauna yana hura hanci sannan itama maryam ta samu guri ta zauna tana satar kallon fuskarsa kwata kwata babu digon annuri ,"


" Maryam tashi ki bude fridge ki dauko masa ruwa dan nasan bai fiyye shan lemo ba ,ta mike a hankali ta karasa ta dauko masa ta ajiye a gabansa ta koma ta zauna gabanta na faduwa "ka bani minti goma kawai zan duba wani fayal ne yanzu zan gama sannan ta soma aiki tsaki yaja a ransa dan dai tana da matsayin aunty shi ce if not bai ga dalilin da zai yita batawa kanshi lokaci ba akaron banza ba ."baka sha ruwan ba ?ta dago ta tambayesa cike da kulawa "no need !ya bata amsa ataikaice
byn kmr minti biyu ta mike ta fita tace "kanina ina zuwa "zuciya ta sake kawo masa wuya sakamakon barinsa da zatai yi shi da wannan guntuwar yarinyar mai siffar aljanu yaja tsaki yana dafe goshinsa da hannunsa ."
Zamansu daga ita sai shi acikin office din baqaramin tashin hankali maryam ta shiga ba ,gbdy duk ta rude sai zufa take fitarwa da zarar tayi kamar zata dago ta kalleshi sai  ta kasa dan gbdy ta nemi natsuwarta ta rasa ji take kamar zuciyarta zata buga allah allah take Aunty shahida ta shigo domin bazata iya cigaba da irin wannan zaman ba ,minti biyar kawai Aunty shahida tayi  da fita amman ganin take Kmr awa biyar tayi da barin office din ,shi kuwa  mr ATA banda tsaki babu abinda yake yana qarawa domin ya fara gajiya da zamansa tare da abinda yafi tsana arayuwarsa ."

Aunty shahida na fita ko cikakken minti goma batai yi ba sai ga nuzla ta shigo office din bakinta dauke da sunan Aunty shahida,turus tayi sakamakon ganin maryam zaune gefe guda kuma mr ATA ne zaune kallon tsoro tayi masa ta dauke kanta tana gaishesa bai amsa mata ba kamar sauran lukuta ta qarasa ta dafa maryam "marsi ina Aunty shahida ."?
"ta dan fita amman tace bazata jima ba ki jirata ,
"okay da ido tayi mata tmby me ya Adam yake yi ? itama da kwayar idanunta ta bata amsa da bata sani ba dan babu damar ayi magana mai sauti kasamcewar sun san baya son hayaniyar komai saurin ciro wayarta tayi ta maida silet ."


sadiya wacce ta kasance me koyon aiki ce a asibiti ta shigo bakinta dauke da sallama "Assalamu alai...... kasa karasa sallamar tayi sakamakon gani mr ATA zaune idanunshi na kallon screen din wayarsa sanye cikin kanan kaya ,gbdy ta rikice akansa madadin ta karasa ta ajiye file din dake hannunta ta kasa ko daga dan yatsan kafarta garin kallonsa ma har file din hannunta ya subuce daga hannunta ya fadi kasa da sauri ta tsugunna ta dauka jikinta na rawa ta karasa ta ajiye fayal din akan table ,tana faman kallonsa  sai lokacin ta lura da maryam dake zaune  tana kallon yatsun hannunta yayinda nuzla ke tsaye a gefenta "sannuku da hutawa ta furta a hankali ."
maryam ta dago tana murnushi tace "yauwa ya kokari ? alhamdulillah sadear ta bata amsa tana kallon nuzla sannan ta fita tana waiwayen Mr ATA tana yaba kyawunsa acikin ranta shi kuwa Mr ATA ko ajikinsa dan iskar ma data debota bai gani ba idan da sabo ya rigada ya saba  da irin kallon da suke masa haka ma kallon da mrym da nuzla Ke masa bai sa ya dago daga duban wayarsa da yake ba .

Nurse sadiya na fita daga office suka ci Karo da husaina itama maakaciya ce "ke lafiyarki kika fito a hargitse Kmr wacce aka koro ?"uhm ke dai bari husseina wani matashi na gani a office din doctor shahida mutumin yayi min kyau matuka ya dauki hankalina wallahi irin mijin da nake nema kenan mijin duniya Mijin novel ya hadu sosai da gani yana da kudi yana da tarin ilimin boko da Arabic uwa Uba kyau "ke sadear raba kanki da wahala, kina diyar talaka dake naci ma da kyar kuke samu kullum Kuna yawo a gidan haya , yayanki ma da kyar yake daukar dawiniyarki Amman kin kashe kanki da mugun buri  , ki roki Allah idan yaga dama zai Baki ki Daina zafafa burin akan auren me kudi ."
sadear ta Dan turo mata karamin Bakinta tana yatsina fuskar ,jikin Sadia yayi sanyi sosai husaina taja tsaki ta wuce ta barta Nan tsaye tana maganar a fili ."

Wayar hannunsa da yake ta faman daddanawa ce ta dauki qara ya manna a kunnensa tare da zamowa kad'an daga Kan kujerar da yake zaune yana lumshe idanunshi "na barota a gida ne ,okay suna bukatar  new design's da kaya ?shikenan ki  bawa kwararrun wadan da suka iya domin  bana son a samu matsalar komai aikinsu  dan last time sunyi complain okay may be tomorrow  yana magana yana lumshe idanuwa yana lasar lip's dinsa  na kasa ."
uzla,maryam duk suka zuba masa idanunsu suna kallonsa kowacce da abinda zuciyarta take saqawa jikinsa ya bashi  kallonsa  suke dan haka ya tsaida  lumtsatsun idanunshi akansu  yana masu wani irin kaskantacce kallo  sannan ya dauke kansa ya cigaba da waya a daidai lokacin da husseina da sadiya suka shigo tare ita kanta husseina ta jinjinawa kyawunsa dan sai da tabawa idanunta abinci suka dauki abinda ya shigo dasu suka juya ."


Ya sake tsaida idanunshi akansu ganin still shi din suke kallo har lokacin Kmr basu san shi ba wani irin taikaci ya kamashi dan baya son yawon kallo arayuwarsa wani abu ya hadiye mai daci a makoshinsa kafin ahankali yaja tsaki yana cigaba da kallonsu yayinda su kuwa a matukar firgice suke kallonsa cikin tsananin tsoro da firgici sam basuyi tsamanin zai sake  kamasu suna kallonsa ba irin kallon da yake masu yasa suka sake shiga rudani dan basu san abinda zai biyo bayan kallon da yake masu ba sannan basu abinda zasu fad'a dan kare kansu ba nuzla ta kalli maryam itama ta kalleta gabadaya jikinsu ya kama rawa nuzla tayi saurin durkushewa kasa bisa gwiwowinta dan tasan na lahira zai fisu jin dadi idan bata hanzarta bashi hakuri ba dan taga maryam bata da alamar bada hakuri "ka..! kayi hakuri ya Adam magana yake son yi amma ina  jin isa acikin ransa yasa ya gagara furta komai illa kafarsa daya daya shiga jijigawa yana takaici ."

ganin har kusan minti talatin aunty shahida bata dawo ba yasa mr ATA ya Mike a fusace ya tura hannunsa daya cikin aljihunsa ya bar office din dan jikinsa ya fara bashi so take ta hadasu da Maryam ta fayyace mata komai a gabansa,yana fita nuzla  ta nufi kofa cikin sand'a itama mrym ta biyo bayanta, nuzla  na gama bude kofar turus  sukai yi sakamakon ganin sadiya da husseina tsaye rungume  da file suna kallon byn mrs ATA suna magana can kasa kasa sakamakon mutanen dake kai kawo " ai wannan ba bakon fuska bane sadiya matashin dan kasuwan nan ne  da duniya Ke ji dashi  sannan kani ne ga sister shahida  yana zuwa lokaci zuwa lokaci ke baki ga kamarsu ba "?lallai kam sai yanzu na ganesa ko dan na rikice ne amman yafi kyau a fili km suna matukar kama sosai da Sister shahida sai dai har ya fita kyau ,wallahi husseina mutumin nan ya shiga raina sosai ban ta'ba ganin halittar daya dauki hankalina ba  kamarsa komai nashi irin mafarkina "uhm uhm sadiya na sha gaya miki ki daina irin wannan hange  ki tsaya matsayinki kin kasa fahimtata ."kisani babu abinda allah bayayi bansan dalili  ba gani daya nayi masa amman na kamu da matsanancin soyayyarsa  " wallahi wannan yafi karfinki Ke ko yaronsa yafi karfinki bareshi  idan zaki dawo haiyacinki ki dawo taja hannunta sukai wuce  sadiya na juya bayanta ."


Naunayen ajiyar zuciya nuzla da maryam suka sauke atare suna dafe qirji "marsi wallahi ba qaramin tsorata nayi ba ,koni kusan nafiki tsorata wallahi kadan ya rage ban saki fitsari ajiki ba qaramin saa muka ci ba da yau mun sha maruka suka kwashe da dariya "kinga bari na wuce bazan iya jiran Aunty shahida ba daman nazo karban test din hjyrmu ne nace nazo mu gaisa kinga wucewata sai mun hadu a gida ta zame hannunta dake cikin na maryam ta wuce tana daga mata hannu , maryam ta koma cikin office zaman jiran Aunty shahida ."
Bai Dade da wucewa ba doctor shahida ta dawo ta ga wayam bashi Babu alamunsa "sarkin zuciya halan ya gaji ya wuce "eh Maryam ta fada muryarta a sanyaye "okay ta shiga tattara kayayyankinta muje kou daman akwai maganar dana so muyi mu uku Amman zanzo gobe inshallahu idan na tashi daga aiki muyi a gida "magana kuma aunty.?"ta tmbyeta a tsaro ce .
"Eh!
" wacce magana ce haka Kuma har da ya adam zaayi ?aunty shahida tace ",magana ce me mahimmam ci , dan girman Allah aunty shahida wallahi bana son duk abinda zai hadani dashi nifa tsoro yake bani culmdown my sister ki cire wannan tsoro ba wani Abu bane face alkhairi shiru mrym tayi tana nazarin maganar aunty da tunanin wacce magana ce wannan da har sai anyita da ya Adam Kuma tace alkhairi ne ...?
suna fitowa haraban asibinti suga direbansa na jiransu "a ruwa Ina mai gidanka ? sai daya rusuna mata sannan yace "ya kira anzo an daukesa da wata motar aunty shahida ta girgiza Kai ta shiga mota ita da maryam inda take fad'a mata zuwan nuzla "Ayya kanwata ai kuwa na gode sosai itama kuwa ina son ganinta nan hankalin maryam ya dan kwanta jin har da nuzla sai dai har sanda a ruwa ya sauke aunty shahida a kofar gidanta zuciyar mrym bata bar Saka da warwara ba Allah Allah take gobe tayi taji ko meye .."


washegari da misalin karfe goma na safe sakon mutuwar sadiya ne ya riski doctor shahida, tayi matukar firgita da Jin wannan mummunar labari saboda cewar da akayi yankar rago akayi mata ta zabura ta mike daga zaunen da take jikinta na rawa ......."

Mmn sudais

💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
Book one
Free page

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
Arewabooks username
Ayshabagudo

bismillahirrahmanirrahim


Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a tura 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.

Page4

"Wani  irin   gumi  ke tsatsafowa   ajikin  aunty  shahida   yayinda zuciyarta  ta  dinga bugawa da  karfi  fiyye  da  kaida ,nan  take ta mike tsaye ta shiga zariya  a office   ta kasa  zaune ta kasa tsaye  tana  sake jin wani sabon tashin hankali   tana cikin wannan halin sai ga doctor  sa'a   ta shigo  a  rud'e  ta tsaya  suna  kallon  juna  yanayin  doctor  shahida  ya  tabbatar  mata taji abinda  ya  shigo daita office  din  dan  duk ta fita  haiyacinta ,a matukar  tsorace  aunty  shahida  take kallonta qirjinta  na  dokawa  "nasan  kinji  abinda  ya  shigo dani ? wai  an yiwa  sadear  yankan rago a gidansu."
har  lokacin  fargaba da  tashin hankali bai bar gangar  jikin  aunty  shahida  ba ,da kyar  ta iya motsa labbanta  "yanzu   doctor zinnira  ta kirani   take  fad'a min wannan mummunar tashin
hankali alamarin nan ya  d'aure  min Kai  matuka ,
hakika  mutuwar  sadear  ya gigitani  jiya  fa  iwar haka muna  tare  daita  har  tana  cewa  zatayi magana mai mahimmanci  dani yau idan mun
had'u ko me  zata  fada  min ? ta   k'arasa  maganar idanunta na ciccikowa da ruwan  hawaye "gbdy  mutuwar  mubina ce ta dawo  min , Allah sarki rayuwa , Allah  ya  jikansu ya  tona asirin duk wanda yayi  sanadiyyar  barinsu duniya  , "duniyar  nan ma guda nawa take da zaka kashe dan'uwanka ?cewar  doctor sa'a  "ya  kamata  muje gidansu   yanzu ko ? "Eh ! wannan  gaskiya  ne ya kamata muje " da sauri aunty  shahida ta tattara abubuwanta dan bata   Jin  zata dawo asibiti  daga can gidan hajiya  zata  wuce doctor sa'a  ta  nufi  kofar  fita itama  aunty  shahida ta biyo bayanta da s auri ta rufa mata baya suka jera tana kokarin neman number doctor  zinnira  suje tare ."


"Kai  tsaye gidansu sadear    dake  ijora olopa
suka  nufa   a kofar  gidan  suka  iske 'yansanda   suna tambayar  aminu   yayan   sadear  yadda  abun ya kasance  "to ni dai bazan qarar da komai  ba , kawai  dai na  tashi da asuba  na shiga d'akinta  Inda take kwana tare da yarana guda  biyu  domin suyi sallah kawai   naga gawarta   cikin   jini  amman  babban yarona  sadi  yace  yaga  bayan matar Kuma ya ganeta   duk  da   jikinta lullube yake da  bakin  kaya  ba'a iya  ganin  komai   nata ".ya qarasa maganar Idanunshi  na  sauya kala." yauwa haka muke so yanzu    Ina  yaron yake ?  police  officer ya tambayi aminu yana gyara tsayuwarsa "  kan aminu  na kasa  hawaye  na tsiyaya daga idanunshi  cikin rawar murya  yace "yana  ciki   gida  " girgiza Kai  aunty  shahida  tayi  cike da  tausayawa masa   ,."

a tsanake  suka   gaisa   sannan     gbdy   suka had'a  baki  da doctor sa'a  da  dr   zinnira sukai masa gaisuwa   "aminu  ya  qarin  hakurinmu  Allah  ya  jikan sadear Allah  yayi  mata  rahma halinta na gari ya bita  "Ameen  ya   Allah , na gode  Allah  ya  bada  lada  "Allah  ya  tona 

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login