Showing 42001 words to 45000 words out of 135096 words

Chapter 15 - Akidata Book 1 Hausa Novel Complete

01 Jan 2025

752

nan ta mayar damu kamar bayi, cin kashi kala kala, ana Wulaƙanta mu muda mahaifiyar mu amma kana neman ta"

Anwar yace  "Amma Mummy....

A fusace tace "ke Amal katse min kiran nan, shashashan banza kawai"

Amal ta katse kiran.

Anwar ya turawa Amal message
"Amal ɗan turomin lambar Widad"

Ta masa reply da  "Taɓɗijan wa kake tunanin ze samu lambar wannan? Duk yadda kake tunanin abun ya wuce haka, ba ruwan ta damu fa"

Jujjuya message ɗin ya dinga yi, babban abunda yake bashi takaici be wuce duk lokacin da ya kira Mummy, ya tambayi ina Widad seta balbaleshi da masifa, duk wanda ya tambaya ya bashi lambar ta kowa se yace bashi da ita, ya rasa meye dalilin hakan.

Yana wannan tunanin Fahad ya shigo ɗakin da sallama, ya kalli Anwar yace  "Man what's wrong ne? Nayi sallama baka amsa ba"

Ɗan guntun tsaki Anwar yayi yace  "Fahad, ni gaba ɗaya na kasa gane kan lamuran nan dake faruwa, duk lokacin da zamuyi waya da Mummy, idan har zan tambayi Widad se taita faɗa, babban abunda yake bani mamaki shine, wai ace duk gidanmu babu me lambar Widad balle ya bani"
Fahad yace
"Widad Widad Widad, kai dai baka da zance se wannan Yarinyar, please don't kill yourself mana, Nifa yadda kake bani labarin ta sam bata Yimin ba, nifa tun tana ƙarama yadda take wannan Share mutanen haushi take bani, kuma gashi da bakin ka ka gayamin tana da taɓun hankali "

Anwar yace " shut up please, tunda ba zaka bani shawara ba ka ƙyaleni, baka san yadda nake ji akan ta ba, kai kana soyayya amma kamar baka san meye son ba, Ni anya ma in baka Ramla zaka iya riƙe ta kuwa? "

Fahad yayi murmushi yace
"Anwar kenan, aini Soyayya ta da Ramla tana sona ina sonta, amma kai banda wahala babu abunda kake yi"

"Kai kaga wahala, ni bangan ta ba, Ni na ƙagu kamar in janyo lokaci in koma gida, gashi seka rigani komawa Nigeria"

"Allah ya baka lafiya Anwar, dan ga dukkanin alamu ta shafa maka haukan"

Shiru Anwar yayi ya miƙe ya bar ɗakin, dan Fahad ya fara baƙanta masa rai.

Widad tana ta shirin fita, wayarta ta fara ringing, hannu tasa ta ɗau wayar tasa a kunnen ta, shiru ta ɗanyi tace 
"Ok, thank you very much, send the address via my email" ta ajiye wayar tana ci gaba da shiryawa.

Maimakon ta fito seta tsaya ta saman bene tana duba lokaci, Yusuf ta hango ya fito da Mota yana ta gogewa dukda a wanke take, abun da ta fuskanta da Yusuf mutum ne meson tsafta sosai, baya son datti sam.

Message ne ya shigo wayar Yusuf ya ɗaga ya duba.

"Ba'a wannan motar zamu fita ba, ka fita waje ka jirani"

Mamaki ne ya kama Yusuf, tabbas Wannan message ɗin daga Widad ne, 'Amma yaushe ta samu lamba ta?' ya tambayi kansa, basarwa yayi ya mayar da motar, yana fita wajen gate yaga wata mota, ba dai me tsada bace dan kamar ma ta ɗanji jiki.
Guri ya samu ya tsaya yana jiran fitowar ta.

Seda yayi kusan mintuna talatin kamar ance ya ɗaga kai ya kalli gate, ganin Widad ne yasa ƙirjin Yusuf bugawa da ƙarfi.

Wani arnen black leg jeans ne a jikin ta, da wata tied pitted blue body hook, tayi stocking ta saka beilt, ɗan ƙaramin baƙin veil ta ɗaure gashin kanta, dukda ƙasan gashin nata ya fito.
Google glass ne a fuskar ta baƙi, ga takalmi me matuƙar tsini, se 'yar ƙaramar jakarta, gaba ɗaya bazaka ce idan Widad ta buɗe baki zata yi hausa ba, duk wani shape da surar jikin ta ya fito.

Tabbas da Yusuf nada damar Mayar da Widad ta canza kaya da tabbas zeyi, dan haka kurum yaji takaicin fitar Widad a haka.

Ƙarasowa tayi ta miƙawa Yusuf key ba tare da tace komai ba, jiji a sanyaye ya karɓa, ya buɗe mata motar ta shiga ya rufe ya zaga mazaunin direba ya zauna, gaba ɗaya ƙamshin turaren da take ya cika motar, ya kalle ta yace
"Ina zamu je?" shiru tayi na ɗan wani lokaci sannan ta miƙa masa wayarta, yasa hannu ya karɓa ya duba.
Adress ɗin inda ze kaita ne, ya ɗago ya kalleta zeyi magana, amma yaga ta ƙara yi masa kwarjini, dan haka ya bata wayar ta ya kunna motar.

Yana cikin tuƙi wayarsa ta fara ringing, Umman Yusuf ne a jikin screen ɗin wayar, ya ɗaga wayar yasa a hansfree ya ajiye ta yace
"Umman Yusuf"

"Ɗan gidan Umman sa, yau zaka dawo da wuri ne, an kawomin wani kifi tun daga Yobe, nayi maka farfesu ka dawo da wuri karya huce, ko kuma in cinye abuna"

Duk da ransa a dagule yake wanda ya rasa dalilin hakan, Amma seda ya maze yace 
"Umman Yusuf, ai bazaki iya ci baki ajiye min ba, zan siyo gurasa yai akwai dinner me kyau"

Hirarsa yake yi da maman sa hankali kwance, se shagwaɓa yake yi kamar yaro ƙarami, Widad kuwa ƙura masa ido tayi ko ƙiftawa ba tayi, dukda ta cikin Glas ɗin idonta take kallon sa amma yadda yake wayar da Mahaifiyar sa ba ƙaramin birge ta yayi ba.

A ranta tace 'dama suma talakawa suna jin wannan shauƙin da ƙaunar na iyaye, inama Ammi na tana raye nima in kwanta a jikin ta in ji daɗi'
Ba tayi aune ba taji hawayen da bata shirya zubowarsu ba. Cire glass ɗin fuskarta tayi tana goge hawayen idon ta, katse wayar Yusuf yayi ya kalleta yace
"lafiya dai?"
"Lafiya cigaba da tuƙinka, ina so muje gurin nan kafin 5"
Ya jinjina kai ya ci gaba da tuƙin, wani katafaren hotel ne, motocine suke shiga suna fita a ciki, kowa harkar gaban sa yake yi, sedai mafi akasari kallo ɗaya zakayi wa mafi yawa daga mutanen dake shiga suna fita, ka gano rashin tarbiyya da ta ido a tattare dasu, musamman matan duba da yanayin irin shigar dake jikin su.

Yusuf yayi parking yana kallon Widad, ta buɗe motar ta tsaya tana ƙarewa harabar hotel ɗin kallo.
Da sauri Yusuf ya fito daga motar yana kallon ta, ta dubeshi tace  "wait for me here"
ta sa kai da nufin shiga cikin hotel ɗin, da yawa mazan dake gurin nan hankalinsu ya dawo kanta, Widad ta haɗu iya haɗuwa, wani takaici ne ya kama Yusuf, ace 'yar musulmi ce da wannan shigar a wannan gurɓataccen gurin.
Bin bayanta ya kuma yi da sauri, ta tsaya ta kalle shi tace 
"I said you should wait me inside the car, don't let anyone to see you here, don't tarnish your image because of me"
Ta sake juyawa, ba zato cikin zafin nama da zafin rai Yusuf ya riƙo Widad gaba ɗaya zuciyar su ta buga a tare, Yusuf ya kalli cikin idon ta yace
"Guri irin wannan be dace da mace me daraja kamar ki ba, Mahaifinki babban mutum ne be kamata aga 'yarsa a irin wannan gurin ba, ke mace ce kuma me daraja bekamata kowane gara ya dinga kallon surar jikin ki haka ba, think about it"
Nutsuwa Widad tayi seda ya gama tsaf sannan tace 
"Cikani tun kan in wanka maka mari a gurin nan, kai waye da zaka gayamin abunda ya dace dani? this is my life style not yours, dalla Cikani Malam kana ɓatamin lokaci ni"

A hankali Yusuf yace  "I am musulm, ina kishin yadda mutane ke ƙare miki kallo a haka, kalli irin mutanen dake gurin nan, da yawan su karuwai ne fa da mutanen banza, shigarki bata da maraba da wanda matan gurin nan marasa daraja suka yi"

Cikin isa tace masa "koba maruwanci ba, Nima shi nazo yi, am prostitute karka ƙara shiga rayuwa ta, na gaya maks"

Ta juya ta shiga Hotel ɗin da sauri, wani baƙin ciki ne ya tokare zuciyar Yusuf, ya koma mota ya zauna yana tunani a ransa
'to wai kai Yusuf banda shisshigi ina ruwanka da ita ne?'
Wata zuciyar ta tambaye shi.

Yana nan zaune a mota kusan mintuna Arba'in, gajiya yayi da zaman motar ya fito ya zauna akan motar yana ƙurawa hanyar da Widad tabi ido.
Ba tsammani ya hangota tana fitowa, sedai fuskarta ɗauke da hawaye tana ta share hawayen da handkerchief, inda motar su take ta nufo idanunta jawur, wani ne ya biyo ta yana ƙoƙarin tsaida ita yayi mata Magana amma bata tsaya ba, tana zuwa ta buɗe motar ta shige.
Yusuf ya zagaya ya shiga ya kunna motar, gaba ɗaya se yaji ya tsargu da yanayin daya ganta, gaba ɗaya hankalinsa ya tashi "Are you ok?"

"Do you have any conscience with me being ok or not?" ta tambaye shi a hasale

"Yes i have" ya bata amsa, tsaki tayi ta ɗauke kanta tace 
"drive very fast please" gudu sosai Yusuf yake amma azalzalarsa take wai ya ƙara gudu, kuma still bata dena kukan ba, kuka take me fallasa da tsantsar ɓacin rai da damuwa.
Guri Yusuf ya samu yayi parking ya juyo yana kallonta, ba tace komai ba tasa hannu a jakarta ta ɗakko wayar ta, ta ɗan daddana sannan ta saka a kunnen ta, tayi shiru na wasu 'yan mintuna sannan tace "Hello Daddy"

Yusuf baya jin me mahaifin Widad ke cewa, cikin kuka tace  "please Daddy I want Flight back to U. K, i regret coming back to Nigeria, please Daddy talk to Bulama ask him to set up my visa"

Shiru ta ɗanyi sannan tace  "Daddy don't take it for granted please, i can't define what happens today, dan Allah kace ayimin visa in koma"

"Daddy why? Kayi shekaru ba tare da ni ba se yanzu zaka ce baka so inyi nesa da kai? Karo na biyu ina neman abu kana ƙin Yimin, shikenan Daddy bayan ciwon Ƙwaƙwalwa am at risk of having cardiac attack" ta saki wayar ƙasa ta cigaba da kuka.

Yusuf ya cika da mamakin meyasa Widad kuka haka? Akwai buƙatar yasan me taje yi Hotel.

"malam kayi sauri ka maida ni gida, ka tsaya kana kallo na"

"Bazan iya tuƙin ba muddin zan cigaba da jin kukan ki" yai maganar fuskarsa ɗauke da damuwa

A hankali ta ɗago idanunta da suka yi jawur, ta saka ana Yusuf tana son gano gaskiyar abunda ya faɗa

"to meye haɗinka dani da kuka na ze dame ka, just drive ba ruwan ka da kukana, kayi abunda ke gabanka"

A hankali ya kunna motar, ya bata wuta ya cigaba da tuƙi, sedai gaba ɗaya hankalin sa baya jikin sa, yana can yana tunani daban daban.

Ihun Widad ne ya dawo dashi hayyacin sa, sannan ya lura da abunda ke shirin faruwa, duk yadda yayi ƙoƙarin kaucewa motar, seda me motar ya daki tasu.

Dafe kai Yusuf yayi yace  "Subhanallah"

A fusace ta kalli Yusuf "Are you out of your sense, see how you ruin my life, kashe ni kake so kayi? Baka gani ne? Dama so kake ka kasheni, an haɗa baki da kai zaka kashe ni ko? Dama na sani"

Kafin Yusuf ya bata amsa tuni me waccan motar ya fito yana zazzaga bala'i, an lotsa masa mota se an biya shi.

Yusuf ya buɗe motar ya fita jiki ba ƙwari, ya kalli mutumin ze kai shekaru Arba'in, Yusuf yace 
"Dan Allah kayi haƙuri, birki ne ya ƙwacemin, kuma kaga traffic ta tsaida hannun ka amma baka tsaya ba, kuma ni na riga na taho da gudu, amma dai kayi haƙuri"

"Shut up my friend, ni zaka gayawa traffic ta tsaida hannu na? Titin naka ne kai kaɗai da zaka dinga wannan gudun, banza shashasha kuma wallahi seka biya ni asarar da kayi min kokuma kaga abunda zan maka"

Tuni mutane suka fara taruwa, suka cika gurin ana ta bawa Mutumin nan haƙuri, dukda zagin da yakewa Yusuf amma haƙuri yake bashi, amma mutumin nan ya rintse ido yana zazzaga masifa yana cin zarafin Yusuf, hakimar kuwa ko fitowa ba tayi ba tana mota a zaune.

Yusuf yace "Amma naga idan laifi ne fa kaine kayi bani ba, Amma se baka haƙuri nake kana cigaba da cimin mutunci a gaban mutane, shikenan Yimin duk abunda zaka iya ka huce"

Yusuf dama gashi a cikin damuwa yake, ga shi ze zagin sa mutumin yake, aikuwa nan da nan temper ɗinsa ta hau zuciyar sa ta shiga tafasa, dan haka se yayi shiru ya dena cewa komai.

Mutumin ya cigaba da zazzaga masifa "Do you know who I am da zaka dingamin magana da gadara,? I will show you what am capable of doing, sena nuna maka ni waye, sena sa an sauke maka wannan rashin ɗa'ar taka mara tarbiyya kawai"

"You are nobody More than stupid Malam, waye kai idan har kai wani ne bazaka tsaya kana ɗaga murya akan wannan banzan gwangwanin motar taka ba, kayi abunda zaka yi an bige motar taka, ina son inga kai waye, kuma me zaka iya?"

Gaba ɗaya suka juyo inda Widad ke magana da jajayen idanunta.

Mutumin ya kalli Widad yace
"Lallai ka ɗakko karuwa a mota, dole ka ɗagamin murya danka birgeta, zanyi maganin ku daga kai har ita"
Ya ciro wayarsa yana waya.

Yusuf a harzuƙe zeyi magana Widad ta ɗaga masa hannu alamar yayi shiru.
Ta ɗakko wayar ta tayi 'yan taɓe taɓe.

Mutane suka ja gefe suna son ganin ƙarshen dramar, mintuna kaɗan sega motar 'yan sanda, suka zo suna wuri wuri, mutumin ya nuna musu Yusuf yace  "gashi nan shine, ku kama shi shida wannan koɗaɗiyar Yarinya me kama da sadakar Yalla"

Tuni ɗaya daga ɗan sandan yaje ya cakumo Yusuf, sedai me ɗan sandan ya jiyo bindiga a jikin Yusuf!!!


SHARE PLEASE 🙏

__Masha Allah nagode da addu'oinku Daddy yana samun sauƙi Alhamdilillah nagode sosai Allah yasaka da alkhairi __

Ayshercool
07063065680

_*AƘIDA TA*_


PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

P. W. A



*Story and written by*

_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_

The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *

I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum




https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=in








ELEGANT ONLINE WRITER'S






PART1
Page 12






Ɗan sandan ya zare ido zeyi magana, Yusuf yayi saurin girgiza masa kai, ya juya ya kalli Widad yaga hankalinta baya kansu.

A hankali ya zura hannu a aljihun sa ya ɗakko ID card ya nunawa ɗan sandan, washe baki ɗan sandan yayi yana niyyar sarawa Yusuf, amma Yusuf ya girgiza masa kai yace

"Dan Allah Yallaɓai ku duba lamarin nan, ni bani da laifi a abunda ya faru, kuma na bashi haƙuri yaƙi haƙura"

Mutumin ya ƙaraso inda su Yusuf suke yace  "kaga Ku tafi da shi ajiyata ne, ku kulle shi har se nazo station ɗin"

Ɗan sandan Ya kalli Yusuf zeyi magana, sega wasu 'yan sandan sunzo, motar da' yan sandan suka zo ze tabattar maka da manyan wanda mutumin ya kirane, nan na farkon suka shiga sarawa wanda Widad ta kira.

Widad tace  "ina so a duba Accident ɗin nan, idan direba nane yake da laifi, zan biya shi kuɗin motar sa uku, idan kuma shi yayi laifin ze durƙusa ya bamu haƙuri, saboda cin zarafi da ɓata mana lokaci da yayi, in kuma yaƙi a tafi da shi, ajiyata ne a kulle shi se nazo"

Nan fa kallo ya koma sama, nan 'yan sanda suka shiga dube duben su, aka tabattar da mutumin nan shine ya karya doka, nan fa mutanen gurin suka ɗau sowa.

Widad taje gaban sa tace " if you are somebody you won't say it yourself, don't ever say you are Somebody when you are nobody, yanzu ka durƙusa ka bawa direba na haƙuri akan cin zarafin da kayi masa"

"Wallahi baki isa ba keɗin banza, in bawa wannan wulaƙantaccen haƙuri, kin san koni waye?"

Ɗaya daga 'yan sandan daya kira ne yaja shi gefe yace  "kai wallahi wannan' yar masu ƙasa ce, idan taso zatasa a ɓatar da kai gaba ɗaya wallahi, kayi abunda tace kota sa a ɗaureka"

"wannan ƙaramar yarinyar 'yar cikina?"

"to karkayi cigaba da taurin kai, wannan' yan sandan data kira muma iyayen gidanmu ne"

Mutumin ya dawo a ƙule ya kalli Yusuf yace  "Yi haƙuri"

"Akan gwiwowinka zaka durƙusa ka bashi haƙuri" cewar Widad

Cikin tsawa wani ɗan sanda yace "ba zakayi bane? Semun tafi da kai?"

A hankali yaja da baya ze durƙusa, Yusuf yayi saurin riƙe shi tare da girgiza kai ya kalli Widad yace  "please Madam ina nema masa Alfarma, kiyi haƙuri dan Allah, ni zan durƙusa in baki haƙurin a madadinsa"

Dama Widad tasan Yusuf baze taɓa yadda hakan ta faru ba, tayi ne dan nunawa Mutumin shi ɗin bakomai bane.

"Shikenan tunda ya haƙura, gobe in Allah kaimu, yaje station ɗinka ya karɓi kuɗin motar sa, na ninka maka masa sau uku, Amma ya kiyaye gaba"

Ta juya ta tafi motar su, Izzar Widad da yadda ta tafi da al'amuran cikin isa da izza, da bajinta suka birge mutane, aka dinga sowa, anawa mutumin nan dariya.
Dare yayi musu a gurin nan saboda wannan incident ɗin, Yusuf yaja motar cikin nutsuwa suka tafi.

Amma still lokaci lokaci tana goge Hawaye a fuskarta, suka ci gaba da tafiya Yusuf na godewa Allah da Widad bata ga bindigar nan ba, tabbas yasan da Asirinsa ya tonu daya gama kaɗewa, ƙarshen ta seta kulle shi me fitar dashi se Allah.

suna zuwa gida Yusuf yayi horn Isa ya buɗe musu gate, Yusuf ya shiga da motar yayi parking, har ya gama abunda zeyi ze buɗe motar ya fita, Widad tana zaune ko gezau ba tayi ba, bata da niyyar fita daga motar.
fita yayi ya zagaya ya buɗe mata ƙofar, yace  "Munzo fa" ɗaga kai tayi ta kalle shi, a hankali ta zuro ƙafafunta da take jin kamar ba'a jikinta suke ba waje ta yunƙuro ta fito, sedai tana fitowa ta tafi luuu zata faɗi, cikin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login