Showing 117001 words to 120000 words out of 135096 words

Chapter 40 - Akidata Book 1 Hausa Novel Complete

01 Jan 2025

763

kazarce?"

Widad tace "to waya sani"

Gwaggo dake banɗaki kam dariyarta ta sha, dan yanzu sun saba kusan kullum da rigimar Widad da Hari suke karyawa.

Yusuf da wanine yace masa Widad ta iya neman magana cewa ze ƙaryane, amma yanzu yake ganin zahiri da ikon Allah, haka yaita bawa Hari haƙuri sannan yasa Widad a gaba zuwa ɗaki.

Ya ƙura mata ido sannan yace "da wanine ya cemin kin iya rikici haka cewa zanyi an miki ƙarya, amma gashi da idona ina ganin ikon Allah, kullum sekin nemi magana"

"da da bana yi ancemin mahaukaciya bana son mutane, yanzu kuma kace na fiye rigima"

Yusuf yace "yi haƙuri, amma adinga ragewa kinji queen, waini ya'akayi kika sake da mutan gidan nan, abun ya bani mamaki fa"

"Basu san ni wace ba, dan haka bana tunanin zasu cutar dani, dukda suma bawai yarda dasu nayi ba, amma inajin daɗin yadda suke kyautata min ne"

Yusuf yace "to nifa, an yarda dani?"

Kallon up and down Tayi masa tace "tukuna dai"

"shikenan ni na yadda dake ai, zoki zauna kusa dani muyi hira"

"Baza'ayi hirar ba, idan nazo kusa da kai taɓani zakayi"

Dariya Yusuf yayi, yace "taɓakinne bakya so inyi?"

"Eh bana so, kai kuma sekace dole seka taɓani"

"ba laifina bane, laifin zuciyata ne Gimbiyata"

"kai ka sani kai da zuciyar taka"

Tai maganar tare da kwanciya ta koma bacci, a hankali Yusuf ya dawo kusa da ita ya kwanta, tana yunƙurin juyi akan katifarta taji mutum, ta leƙo kanta daga bargo taga Yusuf.

"wai dan Allah meyasa kake min hakane, tasarmin daga kan katifa"

"Niba taɓaki zanyi ba, ina son inyi bacci ne zuwa ƙarfe goma in fita, Amma cinnaku se cizona suke wuyana ciwo yake saboda kwanciyar ƙasa, haba uwa ɗakina, atemaka a tausayamin mana"

Tura baki tayi tace "to matsa ni in fita tsakar gida in baka guri seka kwanta"

Zaro ido yayi yace "haka kawai inje ki fita ki jawomin magana, ki fita neman rigima, a'a yi zamanki anan"

"toni gaskiya bazan kwanta a kusa da kai ba"

Banza yayi mata ya gyara kwanciyarsa, tare da lumshe ido, yunƙurawa tayi zata fice ya fizgota ya zaunar da ita yace "yi haƙuri, bari in tashi in bar miki katifar, base kin fita kin janyomin magana ba, har mamaki nake yadda kika koyo rigima"

"nifa ba magana zan ɗakko ba, ni kawai zomaye zan kalla"

"Idan kika tsokani Baba Hari, ba zan baki bredin ba"

"aikuwa kuka zanyi in ka hanani" ta miƙe tayi waje abunta.

Hankalin Hajiya Halima ya kasa kwanciya sam, saboda rufe mata ɗa da'akayi, Amal ma duk abun ya dametta, suna ta zaryar station amma abu ya gagara, Yanzu ma Amal ce ta tafi ɗakin Ramlah, ta tarar da ita a zaune tana waya, da Fahad.
Amal ta samu guri ta zauna, ta jira ta kammala sannan ta kalli Amal tace "lafiya kuwa? Kin shigomin ɗaki kin sani a gaba kina ta kallona"

Amal tace "Ramlah waike baki damu bane dan Allah, kwanan Yayanmu Uku a hannun 'yan sanda, Mummy se zarya take anƙi sakinsa, amma kin shigo ɗaki wayarki kawai kike"

"to Amal haukacewa kike so kiga nayi ko yaya? Shima Allah ya ƙara masa waishi ga me mutunci ya zauna yana jiyyar uban da ya tsinta a rana, kinga hakan ze zamo masa darasi gobe baya ƙara taimakao ba"

Amal tace "bekamata ki faɗi haka ba Ramlah? Ta wani fannin in aka duba abunda Yaya yayi beyi laifi ba, ko so kike duniya ta farga da halin da'ake ciki? Ace bashi da lafiya amma babu wanda ya damu a cikinmu? Ni wallahi abun ya fara damuna koba komai Yaya Anwar ɗan uwanmu ne"

Ramlah tayi ajiyar zuciya tace  "kuma fa hakane, ni kaina ta wani fannin inajin ba daɗi rufe shin da'akayi, amma me zan iya akai wanda Mummy ta kasa"?

Amal tace  "Fahad zakiyiwa magana, dan Mummy taje har gidansu ta gayawa mahaifinsa amma yaƙi ɗaukar abun da mahimmanci, ke tunda kuna ɗasawa dashi kisa yayiwa mahaifinsa magana yasa baki a saki Yayanmu"

Ramlah tace "Anya kuwa? Fahad fa akwai lafiyar kafiya mussman yanzu da suke takun saƙa da yaya"

Amal ta taɓe baki tace "ashema ba son naki yake ba tsakani da Allah tunda ze iya barinki cikin damuwa, Allah wadaran wannan soyayyar"

"Amal ni kike cewa Allah wadaran?"

"Na faɗa Allah ya wadaranta, dama wannan banzan Fahad ɗin me fuskar jakai kansa kawai ya sani, in ba soyayyar ƙarya ba, yayiwa mahaifinsa magana yasa baki a saki ɗan uwanmu mana, naga shima dai ɗan uwansa ne"

Ramlah tace "Aikuwa Amal i will prove you wrong, zan nuna miki soyayyar mu ta gaskiya ce"

Amal tace "in gani ƙas, ancewa kare ana biki a gidansu, ƙaryar banza burodi a lefe, ina amfanin soyayyar da baka da alfarma a gun wanda kake so"

Ta tashi ta bar mata ɗakin, tana ci gaba da mita da tsaki.

Nurat ta shirya cikin doguwar riga, tayi rolling ta ɗau wayarta da jakarta ta fito, ta leƙa ɗakin mamanta taga tana bacci, ta taho cikim sanɗa ta fito harabar gidan, da sauri sauri ta tafi bakin gate tace "zoka buɗemin ƙofa zan fita"

Me gadi ya kalleta yace   "ina zaki?"

"ka aikeni ne? Ka buɗemin zan fita"

Ya ɗan sosa kai yace "Madam, me gidan nan yace kar in kuskura in sake bari ki fita, muddin bashi ya bada umarnin hakan ba"

A ɗan hasale tace "ka buɗemin ba nisa zanyi ba, yanzu zan dawo"

Girgiza mata kai yayi yace "dan Allah kiyi haƙuri, wallahi zan fuskanci fushinsa muddin na bari kika fita"

Juya tayi cikin gida, jiki ba ƙwari tana tunanin meye mafita, can wani abu ya faɗo mata, ta miƙe ta fito tace masa  "kazo Mummy na kiranka"

Ya miƙe ya biyo bayan Nurat, yana gaba tana binsa a baya, yana shiga falonsu cikin sanɗa ta dawo baya a hankali, tayi waje tana zuwa tasa mukulli ta buɗe gate ɗin tayi waje abunta.

Gidansu Widad ta tafi, tana zuwa tayi sa'a ta tarar da Amal a babban falo tana karyawa, Amal na ganinta ta buɗe baki tace "Nurat yau kece a gidanmu haka? Abun mamaki"

Nurat tayi murmushi tace "meye na mamakin kuma?"

Amal tace "ni dai nasan koda zaki zo gidan nan saboda Widad zaki zo, kuma duk garin nan ba wanda be san anyi kidnapping ɗinsu ba, kuma dai amma baban ku besan kinzo ba"

Nurat tayi murmushi tace "tabbas nasan an sace Widad da ɗan uwanta, sedai...

Amal tace " ɗan uwanta kuma? Direbanta dai"

Nurat tace "direba kuma kamar yaya direba?"

Amal tace "kamar yadda na gaya miki, ita da Yusuf ne aka ɗauke su, Yusuf kuma direbanta ne"

Nurat tayi shiru, sannan tace "Amma meye alaƙar dake tsakaninta da Yusuf?"

Amal tace "Allah kaɗai yasani, Wallahi Nurat ina cikin matuƙar damuwa ɓatn nan nasu, mussman Yusuf idan nace zan nuna damuwar da nake ciki ma babu me saurarata a gidan nan, Amma duk rashin yardar Widad ta yadda da Yusuf fiye da tunaninki"

"Amma Amal mezesa matashi kamar Yusuf ya ɓige da aikin direba a gidan masu kuɗi?"

Amal tace "bake ba ni kaina ina wannan tambayar, amma kin san da wani aikin gwamnatin gara aiki a gida kamar wannan, dan ba Widad ba hatta me gidan nan ya yadda dashi sosai, Amma a yadda Yusuf ya haɗu kam, bekamata ace aikin direba yake ba, nayi masa zancen ya nemi wani aikin, amma yaƙi yarda, yafi ƙaunar kasancewa a ƙarƙashin wannan uwar izzar, tana hantararsa tana komai amma baya ganin laifinta"

Shiru Nurat tayi kamar ba zata ce komai ba, can tayi ajiyar zuciya tace "Amal ya batun Yaya Anwar kuwa?"

Amal tace "hamm, yana can Mummy tana ta fama anƙi sakinsa, wai har yanzu bincike ake akai"

Nurat tace "wani station ɗinne?"

"Suna state CID shida Likitan"

Nurat tace "Allah ya fidda shi lafiya, Insha Allah zanje in ganshi"

Amal tace "kai amma kuwa mungode sosai Nurat"

Nurat tace "bakomai Amal, se anjima"



Yusuf yayi baccinsa ya tashi, ya buɗe jakarsa ya ɗakko kayan tea daya bada sautu aka kawo masa, ya ɗora tea Widad tana tsakar gida suna hira da Hindu, da hansai.

Yayinda Hanne se wani gyatsine fuska take yi, bata kallon ko inda Widad take, Widad data fita bata taɓa nuna tasan da halittar Hanne ba, abun da Hanne bata sani ba shine, mutanen da suka damu da itama ba kowa take iya shiga sabgarsa ba, balle wanda ya nuna be damu da ita ba.

Yusuf ne ya fito tsakar gida, yaje ɗakin megari suka sake gaisawa  ya zauna suka shiga hira.

Widad na zaune kusa da gwaggo, tana dama koko tana kallon yadda take yi, Widad tace "Mama haɗa kokon nan ma ashe ba wahala, na iya haɗa custard shima zan iya wannan"

Hansai tace "meye kuma kostan?"

Widad tace "wani abune shima sha ake, kamar haka ake dama shi amma suna da ɗan banbanci da wannan, Ai zaki ban watarna nima inyi ko?"

"taɓ za'a sha kwaɓa kuwa, yadda kike a sangarcen nan ba uwar da kika iya, mijinki na fama wallahi, ba uwar da kika iya se zance"

Widad ta ɗaga ido ta kalli Hari tace "Mijinki ne yake fama da ƙazantarki ba nawa ba, kuma karki ƙara cemin sangartacciya"

Gwaggo tace "yi haƙuri Amarya, ƙyaleta"

Gwaggo ta fara rabon koko, ana zuba na kofin megari Widad tasa hannu ta ɗauka tace "wannan nake so, wannan kofin yafi kyau"

Gwaggo ta ɗanyi shiru, Hansai tace "Amarya kofin megari nefa"

Widad ta tura baki tace "toni ina son kofin, wannan nake so"

Gwaggo tace "Hindu, jeki ki duba ƙasan gadona a cikin kwanukan Hanne ki ɗakkon sabon kofi irina Malam"

Hanne tace "kai gwaggo kofin Auren nawa za'a ɗakko?"

Gwaggo tace "eh kema ba Allah ne ya baki ba, a sai miki wani"

Haka aka ɗakko sabon kofin silva, se ƙyalli yake da murfinsa aka zubawa Widad koko a ciki, Hanne ta dinga mita tana kumbura baki, ai Widad bata nuna tasan da zaman Hanne a gurin ba.

Hanne na tsaka da masifar ne sega Yusuf ya fito daga ɗakin megari, ai nan da nan Hanne ta nutsu ta fara murmushi, Yusuf ya harari Widad dan yaji duk abunda ya faru, ita kuwa tayi kamar bata ganshi ba.

Hanne ta durƙusa ta gaida Yusuf, Yusuf ya ɗan saki fuska ya amsa mata, yazo ya durƙusa ya gaida su gwaggo, duk faɗan da Hari keyi da Widad, tana matuƙar girmama Yusuf, dan suna ɗasawa dashi.

Hanne tace "yau ba wanke wanke ne ka kawo ayi?"

Yusuf ya kalli inda Widad take, yaga ko a jikin ta, jujjuya kofin kokonta kawai take.

Yusuf yace "A'a babu na wanke tun Asuba.

Gwaggo tace "kaine kake wanke wanken? "

Yusuf yayi murmushi yace "A'a Mama, wani lokacin ina rage mata aikine kawai"

Gwaggo ta kalli Widad tace "Anya Ɗiyata?"

Widad tace  "Mena yi? Shine yake cewa zeyi fa, kuma idan nace zanyi se yace ban iya ba"

Hanne tace "ka dinga barinsu, da safe se in haɗa in wanke, tunda bata iya ba"

Hansai tace "ikon Allah, toke Hanne dole ne sekin wanke musu kwanukan?"

Widad tace "Yoseef kaga sabon kofinmu, Mama ta bamu"

Yusuf yace "Ahh mama mungode sosai Allah yasaka da alkhairi"

Ya kalli Widad yace "let's go and have a breakfast"

Ta miƙe tayi gaba, suna zuwa ɗaki yace "sannu kinji"

Cikin rashin fahimta tace "aikin me nayi kakemin sannu?"

"yanzu memakon kice in sai miki kofin kina so, kawai seki sa rigima ke se'an baki?"

"ko zaka Ƙwace ka mayar ne?"

Yusuf yace "A'a ni bance ba, na dafa shayi ne kuma gashi kin karɓo koko"

Da sauri tace "dan Allah dagaske?"

Bece mata komai ba, ya wuce ya sauke tukunyar tea ɗin, ya buɗe jakarsa ya ɗakko kayan tea ɗin ya haɗa mata shayi yasa mata madara, tana zaune tana kallonsa, ya ɗauka ya kai ya ɗanɗana yaji in beyi zafi da yawa ba sannan ya bata.

Ta kalle shi tace  "meye kuma seka sha zaka bani?"

"Na duba ne inji in beyi zafi da yawa ba karki ƙone baki"

"to shine zaka sa baki a jikin kofin, toni gaskiya da cokali zan sha tunda kasa baki, ko in canza kofi"

Tsayawa yayi yana kallonta, taje ta ɗakko wani kofin ta juye a ciki, ta ɗau bredin ta gutsura ta koma gefe.

Karon farko da taga fuskar Yusuf ta canza saboda abunda tayi, ta nuna ƙarara tana ƙyamarsa kenan.

Tana kallon yadda ya ɗan ɓata fuska, ya kasa sakin jiki yaci Abincin ma, amma ta basar ta cigaba da cin bredinta, da a gidane ba yadda za'ayi taci bredi babu mahaɗi, amma yanzu se tura shi take kuma tana jin daɗinsa  a haka.

Ƙarshe Yusuf miƙewa yayi yaje yayo wanka, yazo ya fara shirin fita sedai yaƙi cewa uffan, be sake kula ta ba shirinsa kawai yake.

Widad ta matsa inda yake tace "wai naga ka wani yi shiru, lafiya dai?"

Girgiza mata kai yayi, ya cigaba da shirinsa "Amma naji kayi shiru haka? Nasan baka saba zama haka kayi tsit ba"

Still shiru ya kuma yi mata, yana gyara kayansa dake cikin jakar matafiya.

Ɗagowar da zeyi taga idonsa yayi jawur, gaba ɗaya se jikin ta yayi sanyi.

"dan Allah meye ya same ka?"

Raɓata yayi ze wuce ta sha gabansa tana kallonsa.

Ze kuma kaucewa ta kuma shan gabansa, ba tayi tsammani ba Yusuf ya janyota ya haɗe bakinsa da nata.

Mutsu Mutsu ta dingayi tana ƙoƙarin ƙwacewa, amma ta kasa ko ƙwaƙwaran motsi, saboda yafi ƙarfinta nesa ba kusa ba.

A hankali ya cika ta, tayi baya da sauri tana rarraba ido, tare da sauke numfashi.

Tofar da yawun bakin ta ta dingayi, tana goge bakinta tana kuka.

Yusuf ya ƙaraso inda take, amma ta shiga ja da baya, riƙota yayi ya ƙura mata ido, take yayi mata wani irin kwarjini.

Cikin sanyin jiki Yusuf yace "Widad da zuciya zatamin adalci to da ban iya jure duk wulaƙancin da kikemin a baya ba, saboda Yusuf baya Jura wulaƙanci dan shima mutum ne kamar kowa, sedai kash zuciya ta ta fara son abunda tasan yayi mata nisa har abada, wanda be dace da ita ba, zuciyata ta saɓa Alƙawarin da mukayi da ita nayin ban kwana da soyayya har Abada, hakan shine kawai mafita ga irin rayuwar da Yusuf ya tsinci kansa a ciki, Amma ko warkewa banba daga cikin zugi da raɗaɗin da zuciyata ke ciki ba, ƙaddara ta haɗani dake, kuma zuciyata ta shiga begen ki, Auren nan da mukayi har cikin zuciyata nake som Auren nan, sedai nasan dole wataran zamu rabu saboda bamu gina Auren akan tirbar soyayya ba, dan Allah Widad ni bance sekin soni ba, saboda nasan hakan baya cikin tsarin rayuwar ki, kuma tamkar ƙasƙancine a gareki Auren mutumin dabe kaiki a komai ba, nasan yanzu ma kutsen ƙaddara ne ya haɗamu zama inuwa ɗaya dake, ko baki soni ba dan Allah kidena nunamin ƙyama kinji Gimbiya, yi haƙuri na saki kuka" yai maganar yana ƙoƙarin goge mata hawaye

Fizgewa tayi tace "Dalla ni cikani in wuce, the must useless word i hate in my life Love, kaima ka shiga sahun imagination da shirme kenan, ban guri ni zan wuce"

Ta ture shi tayi gaba abunta, ta ɗakko brush da toothpaste ta tafi sake wanke baki, duk dan Yusuf yayi kissing ɗinta.

Jiki a sanyaye ya ƙarasa shiryawa, ya fito ze fita ko kallon inda yake ba tayi ba, ganin ba kowa  a tsakar gidan se Hanne yasa yazo gabanta yace "Zan tafi"

"Jirani inzo in zama mota seka hau ka tafi"

Ya girgiza kai yace  "nasan kina jin haushina, kiyi haƙuri"

Banza tayi masa ta cigaba da abunda take, Hanne tace  "Adawo lafiya Allah ya tsare"

Yusuf yayi murmushi yace "Allah yasa nagode"

Har yayi gaba ya waigo ya kalle ta, suka haɗa ido ya ɗan lumshe ido yace "I love you My queen"

Wata uwar harara tayi masa ta miƙe ta bar tsakar gidan.


Nurat tana zaune a reception, da ƙyar aka bari taga Anwar, fuskarsa duk ta ɗaga yayi wani iri, a gigice tace "Yaya Anwar me kayi aka kama ka haka?"

Anwar yace "wallahi Nurat ban saniba, wai ana tuhumata da haɗin bakina akan sace Daddy, kuma wallahi ban san komai ba, na gyara masa jiki na bashi abinci, likita yace inje in karɓo wani magani, ina komawa se cemin yayi wai ya shiga ɗakin amma be ganshi ba"

Nurat tace "kamar yaya, ta yaya za'a sace mutum a Asibiti mutumin dako motsin kirki baya iyayi"

Anwar yace  "wallahi bam sani ba Nurat, ni yanzu ba kamanin da'akayine damuwa ta ba, sanin inda Alhaji Nasir yake shine babbar damuwa ta, ba shi da lafiya waye ya sace shi? Waze kula dashi? Waze bashi magani na rasa wacce irin masifa ce tasa ake bibiyarsa haka"

Shiru Nurat tayi tana zancen zuci  'Anya kuwa babu sa hannun mahaifina a sace Alhaji Nasir?'

Ta ɗago ta kalli Anwar tace "Yaya Anwar baka yi laifi ba dan baka banga dalilin da zesa a kama ka ba, dan haka ka kwantar da hankalinka, akwai wani cousin brother ɗina, barrister Abdallah zan masa magana ya shiga cikin case ɗin"

Anwar yace "bakya ganin akwai matsala? Kar a sashi a matsala fa, sunce in suka gama bincike za'a sakeni"

"babu wata matsala insha Allah, ka kwantar da hankalinka, Insha Allah zak bar gurin nan"

Anwar yace "Nagode sosai Ƙanwata, Allah yasaka miki da alkhairi"

Nurat tace  "you deserve it dear" ta ɗau jakarta tayi waje.

Ramlah ce zaune a motar Fahad, ta murtuke fuska yana ta surutu amma tayi shiru, kallonta yayi yace "beb, ya inata magana amma kinyi shiru, lafiya kuwa?"

"Fahad yanzu ace brother na yana ɗaure, amma koka jajantamin talk less of kace zaka kai masa ziyara"

Fahad yace "ni inje state CID no i can't tarnish my image"

"Amma fa kaima ɗan uwanka nae"

"Yeah really, you are right dear but zuwa gurin nan se masu manyan crimes da manyan terrors, kuma kinga daddy na sanannen mutum ne, ace anga mutum kamar ni a irin wannan gurin is not fair at all, it will tarnish our family image"

Ramlah tace 'but your dad can bale him out, so you don't care about my

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login