Showing 120001 words to 123000 words out of 135096 words

Chapter 41 - Akidata Book 1 Hausa Novel Complete

01 Jan 2025

747

feelings, ɗan uwana yana rufe kaikuma abunda ya dameka daban ko? "

"Ai na miki bayani, ban san me kike so ayi ba kuma"

"ina son ka saka baki, Daddynka yayi magana a sake shi"

"Amma Ramlah kin san ba abune me sauƙi yin hakan ba ko, yaynki an haɗa baki dashi an sace Daula, me zesa Daddy yasa baki"

A fusace  Ramlah tace "shut up Fahad, ta yaya Anwar ze hakan, tare kukayi school room ɗinku ɗaya, you know what he can do and what he cannot do, dan haka ina jiran kaje kayi magana da mahaifinka a fito da shi, that's the only way you can prove to me that you loves me"

Tana gama maganar tayi waje ta bar motar, ɗan taɓe baki yayi ya kunna motarsa yayi tafiyarsa.


Yau da Yusuf ya dawo a ɗaki ya tarar da widad, kamar tana cikin damuwa ya kalle ta yace "Na dawo"

Jinjina masa kai kawai tayi, amma ta kasa magana, se ya zata tun abunda ya faru da safe ne yasa take jin haushinsa.

"Meke damun kine? Ko har yanzu fushin kike dani?"

A kasale tace "Bakomai fa"

Haka ya fita yaje yayi wanka ya dawo ya sameta a inda ya barta, yau dambun tsaki Hansai ta girka ta aiko musu, amma taƙi sakin jiki taci, ya kaɗa ya raya amma tace lafiyarta ƙalau, sedai ya lura buni buni seta tafi toilet ta dawo.

"Gimbiya ko cikin kine ya ɓaci?"

Girgiza masa kai tayi tare da kwanciya, haka taita yi har washegari gaba ɗaya kamar bata da sukuni, kuma taƙi gaya masa abunda yake damun ta, haka ya fita ya barta ya ɗauka dai fushi kawai take, Da Azahar ya dawo sedai ya tarar da tun Abincin safe bata kuma cin komai ba.

Yaje gabanta ya durƙusa yana ƙare mata kallo yace "dan Allah idan fushi kike dani kiyi haƙuri, kin sani a damuwa fa"

"Nifa ba fushi nake ba, ka ƙyaleni kawai"

"baki da lafiya ne?"

"lafiya ta ƙalau"

"but you look so much restless"

Shiru tayi bata ce uffan ba, ya miƙe yana duba kwanuka yaga abunda aka kawao, se yaga tana ta dube duben abun shimfiɗar dake kan katifarta.

Yana zuwa ya ɗagata cak daga kan katifar, meze gani jini ne a jikin ta, ya ɓata mata jiki da katifar.

A gigice yace "Subhanallah, Widad meya same ki haka?"

Take ta fashe da kuka tace "Period yazo min tun jiya bani da pad"

Cike da damuwa yace "shikenan is ok, kwantar da hankalinki"

Yasa hannu ya naɗe bedsheets ɗin, ya ɗora ruwa yayi ɗumi ya haɗa mata ruwa, ya rakata banɗaki, ya dawo ya haɗa abun shimfiɗar da kayan data cire ya zubasu a bokiti.

Tayi wankan ta fito ta dawo ɗakin, har yanzu bata dena kuka ba, Yusuf yace "jeki zauna bari inje gurin Mama inga inda wani taimako da zata bamu"

"Idan na zauna ɓata gurin zanyi"

Yusuf yace "bakomai zauna, idan ya ɓaci zan gyara"

Ya zaunar da ita ya fita da sauri.

Yana fita tsakar gida Hanne ta kalle shi tayi murmushi tace   "kana buƙatar wani abune?"

Yusuf yace "gwaggo zaki kira min dan Allah"

Tace "to"

Ta tashi ta shiga ɗakin gwaggo, gwaggo ta fito ta kalli Yusuf tace "lafiya dai malam Yusuf?"

Cike da kunya, Yusuf yayi mata bayani, Gwaggo tace "to mudai yaranmu da tsimmane suke amfani, ban sani ba ko zata iya amfani da shi"

Yusuf yace "bakomai Gwaggo, zata iya insha Allah"

Gwaggo ta shiga ɗaki ta ɗakko sabon turmin Atamfa, da sabuwar reza, da ƙyar Gwaggo ta iya shiga ɗakin nasu saboda kunya.

Widad na zaune da towel se vest a jikinta, Gwaggo tace "Sannu Amarya ya jiki?"

Widad tace "lafiya ƙalau"

Tasa reza ta yanka Sabuwar Atamfa ta gwadawa Widad yadda zata yi.

Widad tayi shiru taƙi cewa uffan, Yusuf yace "Mama nagode sosai da taimakonki, Allah ya saka da alkhairi"

Gwaggo tace "bakomai Malam Yusufa"

Gwaggo ta fita, tana fita Hari tace "Yaya wai Wudas ɗince bata da lafiya?"

Gwaggo tace "Eh"

"meya same ta?"

Gwaggo bata amsa mata ba, Hanne tace "waini Gwaggo meye na yanka sabuwar Atamfarki, wallahi kin fiye zaƙewa akan wannan fitsararriyar"

Gwaggo a fusace tace "wallahi kika kuma magana sena kwaɗa miki mari, ina kallon ki duk abunda kike yi, ɗa na kowa ne, meye dan na yanka Atamfa? Abum duniya fararre ƙararre"

Haushi Hanne taji, dan da wuya kaga Gwaggo tana faɗa se an ɓata mata rai sosai, Amma yau akan wannan koɗaɗɗiyar tana ta mata masifa.

Yusuf ya kalli Widad yace "gimbiyata nasan baki saba amfani da irin wannan ba, amma kiyi haƙuri gidanmu babu mata nikaɗai ne shiyasa nima ban san kan wannan abubuwan ba, da tuntuni nasa an nemo miki abunda zaki yi amfani dashi"

Da ƙyar Yusuf ya lallaɓata ta saka ƙyallen nan, sam she's not comfortable with this thing, gaba ɗaya ta takure kanta, Yusuf yana kallonta ta kwanta ta zauna gaba ɗaya ta kasa zama.

Ya kwashi kayan data ɓata yaje ya wanke su tsaf, taga ya dawo ɗaki yana goge hannu ta kalleshi tace "wai me kayi?"

"kayanki na wanke"

"Kayan jinin?"

"Eh mana, nasan idan na bar miki ba zaki iya wankewa ba"

Shiru tayi ta bishi da kallo, tuno abunda ya faru da safe tayi, yadda tay masa wulaƙanci amma har ya manta yana tarairayarta, yasa hannu a kayanta na jini ya wanke.

Ganin da yayi ta kasa zaune ta kasa tsaye yace  "Gimbiyata meya ke damunki yanzu?"

"ƙafafuna ne kamar ba nawa ba, babu daɗi marata ma ciwo takemin"

Yazo ya zauna a kusa da ita, ya kamo ƙafafunta ya ɗora akan cinyarsa yana matsa mata a hankali, lumshe ido ta dinga yi.

Ta ɗauke ƙafafunta daga kan cinyarsa, ta ɗora kanta sannan ta miƙa masa hannunta, tana masa nuni daya ja mata yatsun, haka Yusuf ya riƙe yatsun ta yana matsawa a hankali, babu daɗewa kuwa bacci yayi gaba da ita.



Seda Nurat ta tinkaro komawa gida sannan gabanta ya shiga faɗuwa, dan se yanzu ma ta tuna taɓargazar da tayi.

Kanta tsaye tana ta Addu'a ta fara buga gate ɗin, me gadi yazo ya buɗe mata bece mata uffan ba, ta shiga cikin gidan, sedai me a harabar gidan idonta ya sauka a cikin na mahaifinta yana zaune yana kallonta.



SANARWA! SANARWA!! SANARWA!!!

(Ina ma'abota karatun littafin AƘIDATA, a fari nace zan bada littafin kyauta ba tare da ko sisi ba, amin Afuwa wani dalili zesa zan saida book2 and 3,dukda nima ba hakan naso ba, gaba ɗaya kyauta nayi niyya bada littafina, Amma dalilin me ƙarfi zesa in saida ƙarashen in na gama book1 ina fatan zaku fahimceni)





Domin gyara, sharhi ko shawara
Ayshercool
07063065680
                  _*AƘIDATA*_
       

PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

*Story and written by*

_*AISHA HUMAIRA _
(Daddy's girl)*_

The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *

I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum

Haƙƙin Mallaka ⚠ : Littafin nan mallaki nane, tun daga sunan labarin zuwa abunda ya ƙunsa, ban yadda wani ko wata ya sauyamin ko yin Amfani da wani ɓangare na labarin ba ba tare da izinina ba, Nagode

https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends

NOT EDITED

ELEGANT ONLINE WRITER'S

                         PART1
                                Page 40_41

Gaban Nurat ne ya shiga bugawa da sauri da sauri, ta shiga zazzare ido be kula ta ba bece mata komai ba, tazo ta tsaya tana kallon sa, taga harta wuce bece mata uffan ba.

Ta shiga ɗaki ta nemi guri ta zauna, tayi shiru tana tunanin yadda zata samu Anwar ya kuɓuta, babu zato  taji an murɗa ƙofar ɗakin nata.

Mahaifinta ne ya shigo yana rarraba ido, gadan gadan yayo kanta yana faɗin "gidan ubanwa kika je?"

Miƙewa tayi a gigice ta shiga ja da baya tana faɗin "babu inda naje Daddy"

"ƙarya kike munafuka, harni zan saka doka ki sa ƙafa kiyi fatali da ita? Uwarki ta ɗaure miki gindin kiyi rashin mutunci ko? Ni da Daula waye ya haifeki?"

"Daddy niba gurinsa na je ba, Ai an ɗauke shi daga Asibiti"

Sekuma yayi sak, "Ubanwa waye ya gaya miki?"

"wallahi Daddy a gari naji"

"to gidan ubanwa kikaje? Zaki gayamin ko sena yanka ki a gidan nan?"

Girgiza kai take, takasa magana ya cakumo wuyanta yana zazzare ido, kakari ta dinga yi tana kuka tace "Wallahi Daddy ba inda naje, kawai gajiya nayi da zaman gidan na fita, dan Allah kayi haƙuri"

"se naci ubanki yadda idan na sake saka doka ba zaki takamin ba"

Cikin kuka Nurat tace "Wayyo Allah Mummy, ki temakeni karya kasheni"

Maimakon ya saketa sake shaƙeta yayi, yana kuma zaro mata ido kamar tsohon maye.

Kakarin Nurat ne yasa mahaifiyar ta, ta sallame salar da take, a guje ta rugo ɗakin Nurat, ta tarar ya shaƙe Nurat kamar ya kama sa'ansa ko kuma wani shahararren Ɓarawo.

"Kayi haukane, ka cikamin 'yata ita kaɗai ce dani, kana gani duk yaranmu mutuwa suke, ita kaɗai Allah ya barmin ka ƙyalemin' yata"

Juyowa yayi a fusace ya mangare mahaifiyar Nurat yace "itama ɗin gara in aikata inda waɗancn suka tafi, muddin zata dinga takemin doka, tasan a duniya bani da maƙiyi sama da Daula, danme zata dinga zuwa inda yake, akan me?"

Yai maganar tare da wurgi da Nurat, wadda tuni ta fara fita a hayyacinta, dan daya jefar da ita ko motsi ba tayi, se kokawa take da numfashi.

Da sauri Maman Nurat ta nufi kan Nurat, yayin da Alhaji Musa ya cigaba da banbami, ta ɗago Nurat sedai bata numfashi.

Cikin kuka tace "wallahi idan ka kashe min 'ya se nayi shari'a da kai, Kai kanka kawai ka sani, buƙata in ba ta kaba baka damu da kowa ba"

A fusace yace "Maza karki fasa yin shari'a dani, idan na kashe ta na kashe banza, duk son da nakewa mutum muddin ze bujiremin to zega ba dai dai ba tabbas"

Banza tayi masa, Taje ta buɗe fridge ta ɗakko ruwa me sanyi ta shiga shafawa Nurat, a hankali ta dinga sauke Numfashi, tana buɗe ido ta fashe da kuka tace "Mummy anya Daddy ne ya haife ni? Kalli yadda yayi yunƙurin kasheni me nayi masa haka?"

"kema da halinki Nurat, kin fiye taurin kai, na hana ki wannan abun da kike amma kin kasa ganewa, gashi ze kashe ki a banza"

Shiru Nurat tayi, tabbas tunda mahaifinta yake yunƙurin kashe ta akan taje inda Daula yake, to tabbas wani mummunan abu yake aikatawa, kuma na abunda baze iya aikatawa akan kowa ba.
Lumshe idon ta tayi tana jin yadda ƙirjinta yayi nauyi, wani irin baƙinciki ya mamaye zuciyarta.

Shikuwa Alhaji Musa yana komawa ɗaki ya shiga sintiri, kamar yadda ya zame masa jiki a 'yan kwanakin nan, ba shi da nutsuwa sam, musamman da' aka ce su Widad sun gudu daga inda aka sace su, gashi sunsa a nemo su a ko'ina suke amma abu ya gagara.

Gashi yanzu wata maganar rainin hankali da ta taso, wai an sace Daula akan gadon Asibiti, 'Anya ba wani rainin hankalim su Alhaji Haruna suke shiryawa ba?'

A hankali Widad ta buɗe ido daga baccin da yayi awon gaba da ita, taga Yusuf ya jingina da jikin bango ya lumshe idanunsa, hannunsa ɗaya yana wasa da gashin kanta, a hankali tayi miƙa tare da hamma, da sauri ya buɗe ido yana jera mata sannu.

Ba tace komai ba se jinjina masa kai da take.

Miƙewa tayi zaune, se kuma yaga ta yamutsa fuska.

Kallon ta yayi da sauri yace "lafiya dai?"

Ɗan tura baki tayi tace "am not confortable at all, ji nake kaman am stain"

Yusuf yace "kiyi haƙuri insha Allah, zan san yadda zanyi a samo miki wancan da kike amfani da shi"

Widad tace "baza a samu wanda nake amfani da shi ba, sedai a siyomin kowanne ne, bana son wannan abun da nake using dashi yanzu, is so much irritating"

Yusuf yace "Shikenan, Insha Allah zan san abunyi"

"Sannan kuma..." se kuma tayi shiru

"sannan kuma me?" Yusuf ya tambaya

"Nasan baza'a samu shaving cream ko powder ba, a siyomin shaver please"

Cike da son ya kunnata Yusuf yace "shaver kuma, me zakiyi da shaver?"

"Abunda kake yi da ita" ta bashi amsa cike da tsiwa

Yayi murmushi yace "Aini gemuna nake askewa da ita"

Ta kalle shi ta ɗan tsuke baki tace "Nima nawa gemun zan aske"

Aikuwa Yusuf ya kwashe da dariya, sosai yadda tayi magana da abunda ta faɗa ɗin ya bashi dariya, kallonsa take yi yadda dariyar tayi masa kyau.

"wallahi idan ka ƙware ba ruwana"

Tai maganar tana shirin Miƙewa, ya kalleta yace "Ina zaki?"

"tsakar gida nake son fita"

"Amma kin manta halin da kike ciki ne?"

"To zama zan tayi ina kallonka, ni na gaji da kwanciyar ma, zan kula sosai"

Yusuf yace "Aini bana gajiya da kallon kyakkyawar fuskar nan taki, muyi zamanmu a ɗaki nima na iya hirar se in miki, kuma baki ci Abinci ba, ko kin manta?"

'ƙyale Abincin nan, ni idan ina period bana son Abinci sosai "

Yusuf yace " dama can haka kike, ina lura dake tarkace kawai kike ci ba Abinci ba, so nake ki ƙara Ƙiba ki daure kici ko kaɗan ne mana"

"Ni gaskiya, ba irin wannan nake so ba"

"wanne kike so" ya faɗa cike da kulawa.

Ɗan tsura masa ido tayi, sannan tace
"Bari dai inci kaɗan"

Ya ɗakko kwanon dambun ya ajiye mata, tasa cokali ta fara ci, dambun tsaki ne amma yaji gyaɗa da zogale yayi daɗi Sosai.

Widad tace "tunda nazo ƙauyen nan, ban taɓa cin Abinci me daɗin wannan ba"

Yusuf yayi murmushi yace  "harda bredin jiya?"

Widad tace "hmm dan dai kar kaji haushi ne, amma gaskiya bredin nan ya daɗe a ajiye, se marmashewa yake ba daɗi"

Yusuf yace "dagaske ba kya son inji haushi?"

Ɗan kallonsa tayi tace "No i mean banyi niyyar magana ba lokacin shine kawai, ka ɗakko spoon muci Abinci mana"

Yusuf ya girgiza kai yace "A'a kici kawai, idan kin rage se inci"

Widad tace "meyasa? Ai ze ishemu"

Yusuf yace "bana son in samiki yawuna a jiki, naga bakya son hakan"

Ɗan tura baki tayi, cikin ƙunƙuni tace "na nawa kuma, ƙarewa ma ai Yawun naka ka samun a bakina jiya"

Yusuf yace "ai bazan manta wannan moment ɗinba, nayi kissing ɗin gimbiyata the most memorable moment in my life"

Widad tace "tabbas kam, ka kafa tarihi, kayi abunda wani mahaluki be taɓa gangancin gwadawa ba, kayi min abunda ban taɓa zaton wani zemin in ƙyaleshi ba, hmm ban san meyasa kake min abubuwa son ranka ba, ƙyaleka kawai nake"

"Are you sure babu wanda ya taɓa kissing ɗinki seni?"

Watsa dambu tayi a bakinta, ta ja wasu seconds sannan tace "Idan an taɓayi kana tunanin zanji tsoron ka ne? Ban taɓa shan yawun Ƙato ba se a kanka, kuma bashi ka ɗauka, tunda kasa na haɗiye yawunka"

Murmushi Yusuf yayi yace "Yaushe ne ranar biyan bashin?"

Banza tayi masa taƙi ko kallon inda yake, can Yusuf yace "Amma meyasa kike zuwa Clubs da kuma Hotel?"

Jin tambayar tayi a bazata, take taji tana kokawa da dambun dake bakinta, gaba ɗaya Mood ɗinta ya canza a hankali tace

"ai tun a lokacin na gaya maka me nake zuwa yi, na gaya maka ni karuwa ce kamar yadda matan gurin suke"

Haɗe rai Yusuf yayi yace "Kamar yadda bakya son ƙarya, na tabbata kema bakya aikata ta se bisa kuskure, meyasa zaki gayamin haka? Ko kina son zuciya ta ta buga ne?".

"Tunda baka yarda ba shikenan, amma kasan dai bazan zauna ina rantse maka dan ka yarda dani bako?"

Ta ajiye spoon ɗin Abincin ta je ta sha ruwa, tayi waje abunta ta bar Yusuf a gurin a zaune.

Roƙon Allah ya shiga yi akan Allah yasa abunda Widad ta faɗa ƙaryane, dan ba ƙaramin kishi yaji ba, kuma yasan halin ta ko meye zata yi ƙoƙarin gaya maka gaskiya, ko ta maka daɗi ko akasin hakan'

Tana fitowa Gwaggo tace "Amarya kin ware kenan?"

Widad tace "eh Alhamdilillah"

"Masha Allah, haka nake son ji"

Hari tace "Wai meya same ki ne?"

Widad tace "Kaji Baba Harin nan, sekace kin damu dani, bayan ko gani kika yi zan mutu murna zaki yi, to ciwon yara nake bana tsofaffi ba dan haka base kinji ba"

Aikuwa a fusace Hari tace "karki ƙara cemin tsohuwa, ta ina nayi miki kama da tsohuwa? Da ƙuruciyata dudu shekarun nawa ba zasu gaza Ashirin da shida ba, amma kike kiramin tsufa"

Ai gaba ɗaya wanda ke tsakar gidan ba wanda be dariya ba, Widad tace "A'a kin manta a zanin goyo kike ma ƙarewar yarinta, harfa jikokine dake amma kice shekarar ki Ashirin da shida, shekarar ki biyar akamiki Aure kenan"

Hari tace "koma yane dai, niba tsohuwa bace ba ehee, dan jina nake garas kamar 'yar shekara goma sha shida"

Widad tayi dariya tace "dama zaki dinga gayune, za kiga yadda zaki koma yarinya sharaf, amma indai baki dena ƙazanta ba, to tabbas wataran za' a kalle ki ace shekararki sittin da 'yan kai"

Hari tayi kicin kicin da Fuska, dan Widad ta fara kaita bango, idan ta cigaba da biye mata to tabbas za suyi ba daɗi, dan haka tayiwa Widad banza.

Widad ta ƙarasa inda Hindu ke tsinke zogale ta zauna tace "Hindatu, ya ki keyi? bari in tayaki"

Hindu Ta gwadawa Widad yadda ake tsintar zogale, ta zauna suna yi tare.

Can Widad tace "Hindu, wai kuma idan kuna period bakwa amfani da pad ne? Se tsimma"

Hindu tace "meye kuma firiyios?"

Widad tace "A'a ba kije makaranta bane? Me yasa Common things idan na faɗa, seki ce baki sani ba?"

Hindu tace "bari Amarya wallahi muna son karatun nan, amma ba yadda muka iya ne, kinga inda muke zuwa makarantar furamarai can wani ƙauye ne, kusan ƙauyuka biyar duk ita muke zuwa, to guri ba kusa ba nisa kafin kaje duk anyi wani abu baka nan, lokacin damuna kuwa bama samun zuwa, sannan akayi ruwan Sama me ƙarfi ya kwashe kwanon

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login