Showing 96001 words to 99000 words out of 135096 words

Chapter 33 - Akidata Book 1 Hausa Novel Complete

01 Jan 2025

774

karkaji komai ku saki jikinku duk abunda kuke buƙata kuyi magana insha Allah baze gagara ba"

Yusuf yace  "Masha Allah, mungode sosai da wannan karamcin naku"

"Karka damu, ai shi ɗa na kowa ne"

Wajejen ƙarfe tara na Safe aka aiko yaro ya kawowa Su Yusuf Koko me zafi da ɗumamen tuwo, Yusuf ya karɓa yace sun gode.

Ya kalli Widad dake zaune tayi shiru, gwanin ban tausayi yace  "ga Abinci an kawo, ki daure kici se Kisha magani"

Kallon kwanon tuwon tayi, sannan ta kalli kwanon da'aka zubo kokon, har ɗan gara kwanon kokon, amma na tuwon dai se a hankali ga warin daddawar nan ji tayi kamar tayi amai, miyar nan baƙa wuluk ga uban tuwo a ido in ka kalli Tuwon nan kasan ze azabar tauri.

Ta kalli kokon tana tunanin ta ina zata sha abun sha a cikin kwano, ta kalli Yusuf tace "janye min wannan baƙin Abincin kar inyi amai"

Kallonta yayi da mamaki, tuwon ne bata sani ba ko kuma tsabar rainin hankali ne? Ta miƙa hannu ta ɗau kwanon kokon, ta dinga juya kwanon sannan ta kai bakin ta, karɓa ɗaya tayi ta dire kwanon ta yamutsa fuska kamar zata yi kuka.

Yusuf yace  "ya dai?"

"Ba daɗi" ta bashi amsa

"to ai badan daɗi zaki sha ba, kinga nan ba kamar gida bane da zakici abunda kike so, ki daure kisha"

Banza tayi masa taƙi kallonsa, ya ɗau kwanon ya zuƙi kokon, kokon dawane kuma gasarar tayi tsami dan ta ɗan fara wari ma, gashi babu ko ɗigon sugar a ciki.

Yusuf yace "kinga babu wani Abincin da zan baki, idan baki sha ba babu wani Abincin da zaki samu kici, ki daure ki ɗauke numfashi kawai kisha"

Da ƙyar ya lallaɓata ta sha kokon nan shima kaɗan ta sha tace ita ta ƙoshi, sannan ya bata magungunanta.

Yusuf yace  "Inaga yakamata inyi musu magana, idan da hali a bani ɗakin da zan dinga kwana, kinga be dace mudinga kwana a ɗaki ɗaya nida ke ba, sannan dole kiyi haƙuri su ɗan dinga temaka miki ko gurin wankan ne da canza kaya, nida nake miki be dace ba, tunda ba muharrama tace keba"

Da sauri ta kalle shi tace "Nikaɗai zan dinga kwana a ɗakin nan? Ni gaskiya bazan iya ba"

"to se a samu a yaran gidan wasu su dinga ta yaki kwana"

Ai tuni ta fara kuka tace  "Ni wallahi ba wanda nasani a gurin nan ba zaka tafi ka barni a ɗakin nan ba, kuma wallahi niba zasu dinga taɓani ba, wannan matar me haƙora tsoro take bani, in ba haka ba kawai ka maida ni gida"

Yusuf ya ƙara kwantar da murya yace "Widad mufa musulmi ne, mun san illar zaman mu a guri ɗaya, bekamata yadda nake kula dake ba bayan ga 'yan uwanki mata a gidan nan ba"

"to ni ka maida ni gida mana, kkme ze faru ya faru amma wallahi ba inda zaka tafi ka barni".

"so kike mu koma gida wani abu
ya sameki?

" Idan ba zamu koma gida ba, to bazaka bar ɗakin nan ba, in ba haka ba ni zan tafi gidan nikaɗai "

"Amma kin san zamana dake a ɗaki ɗaya ya saɓawa shari'ar musulunci?"

Shiru tayi bata ce komai ba, Yusuf yace "kiyi haƙuri, mutan gidan nan suna da kirki kuma duk mutane ne, babu wanda ze cutar dake, kiyi haƙuri zanje in samu me garin muyi magana"

Riƙo rigar Yusuf tayi ta fashe da kuka tace "Wallahi bazan dinga zama a ɗakin nan nikaɗai ba, sedai duk inda zaka in bika"

Shiru yayi yana Kallonta, kuka take sosai har cikin ranta, tabbas yasan halinta da ƙyanƙyami da rashin yadda, ba zata yadda ta zauna da kowa a ɗaki ɗaya ba in bashi ba, kuma gashi hakan ya haramta.

Jiki a sanyaye yace  "shikenan is ok kidena kuka, idan har kina son mu cigaba da zama tare a ɗakin nan inyi jinyarki bisa shari'a mafita ɗaya ce, kuma mafitar nasan me tsaurin gaske ce a gurinki ba lallai ki yadda ba"

Widad ta ɗago idonta tace "Meye mafitar?"

Yusuf yace " Sedai ki amince muyi Aure zuwa lokacin da zaki warke, mu koma gida semu rabu"

Gaban Widad ne ya faɗi ta tsaya tana masa wani irin kallo

Duk yadda me Adda yake tunanin lamarin ya wuce tunaninsa, dan babu wata alama ko sheda da zata nuna maka inda su Yusuf sukabi, suka yi sintiri da neman duniya a dajin nan basu sami su Yusuf ba, me Adda yace  "gaskiya ina mamakin guduwar mutanen nan, tabbas akwai munafiki a cikinmu, wanda ya kuɓutar dasu banda haka yaza'ayi mutanen da ko tashi basa iyawa ace sun gudu?"

"Oga nima dai nayi wannan tunanin, dan tabbas maganar ka haka take, da saka hannun wani a kuɓutar tasu"

Me Adda yace  "Ni yanzu tunanina yadda zanwa wannan mutanen bayanin sun ɓata, dan wallahi babu lallai su ƙyalemu"

"To Oga ko muma sanfewa za muyi muyi ta kanmu"

Me Adda yace  "ƙwarai kuwa, Amma zamu fara kiransu mu gaya musu su san meya dace suyi, sannan muma muyi ta kanmu da ba mutunci mutanen nan suka cika ba"

Suleiman shike zuwa ya rarrashi Maman Yusuf, dan ko Abinci bata iya ci, sedai wataran inzeje yayi mata Nasiha ya sai wani abun ya kai mata.

Yauma bayan Azahar da ya taso daga gurin aiki gidan su Yusuf yaje, yatarar da Umman Yusuf akan dadduma taci kuka ta ƙoshi, idanunta duk sunyi jawur.

Suka gaisa Suleiman yace "Umma har yanzu baki dena kukan ba? Ki sani wannan carbin da kike ja kina masa Addu'a yafi wannan kukan da kike yi, dan Allah ki kwantar da hankalinki, kar wani ciwon ya shige ki"

Umman Yusuf tace  "To Suleiman dangana ta zama dole, yau da gawar Yusuf na gani seta fiyemin kwanciyar hankali akan ɓatansa, ban san a ina yake ba, yaci Abinci? Yayi wanka? Me yake ciki? Yana samun Abincin da yake so duk ban sani ba, Allah ne kawai ya barwa kansa sani, dole in shiga damuwa inyi kuka"

Suleiman yace  "hakane Umma, amma ki kwantar da hankalinki, muna nan muna bincike akan mu gano inda Yusuf yake, very soon zakiji labari me daɗi, kuma kisawa zuciyarki addu'ar nan da kike tana isa ga Yusuf insha Allah muna sa ran jin labari me daɗi akan Yusuf"

Umman Yusuf tace "Nagode Suleiman, Allah ya saka da alkhairi tunda abun nan ya faru kai kaɗai kake zuwa inda nake ka rarrashenin, Nagode Allah yayi Albarka"

Suleiman yace "Ameen Umma, kin san mahaifin yarinyar ma yana can a gadon Asibiti, sedai fatan Allah ya bayyanasu"

Umma ta amsa da Ameen.

Nurat ta kuma satar jiki, mahaifiyarta bata sani ba ta tafi Asibiti duba jikin Baban Widad, koda taje Anwar kawai ta gani a gurinsa, sedai abun mamaki har yana zaune yana cin Abinci da kansa.

Nurat tace  "Alhamdilillah lafiya ta fara samuwa, ya ƙarfin jiki kuwa Daddy?"

Daula yayi murmushi yace "Alhamdilillah, yau gani a zaune ina cin Abinci ma"

Nurat tace "Alhamdilillah"
Ta kalli Anwar tace "Yaya Anwar ina kwana"

Anwar yace  "lafiya ƙalau, ya mutan gidan?"

"duk suna lafiya Alhamdilillah, Amma ina su Anty Ramlah ne?"

Ɗan kame kame Anwar ya fara yace "kin san da yake tunda Daddy ya kwanta itama taƙi lafiya, tana can tana jinya su Amal ke kula da ita"

Nurat tace "Allah sarki, Allah ya sawwake naje in duba ta"

Saleh ne yayi sallama ya shigo, yana ganin Daula a zaune yace "Alhamdilillah Alhajin Allah, kaine a zaune haka kake cin Abinci?"

Daula yayi murmushi yace "Alhamdilillah, tambayi Anwar da kaina na tashi na zauna, sedai bana jin daɗin Abincin sam tunanin 'ya' yana nake, ban san a halinda suke ciki ba"

Saleh yace "Insha Allah suna lafiya, kuma da yardar Allah za'a gansu"

Nurat tayi shiru zuciyarta gaba ɗaya ta tsinke, tausayin Daddyn Widad ya kamata, ji take tamkar ta gaya masa abunda ke faruwa, Amma idan ta faɗa da wani suna za'a kirata, kuma meye hujjarta na cewa da hannun mahaifinta a sace Widad tunda ita kaɗai taji abunda suka faɗa, Mahaifinta yana zaune da nasa iyalin cikin kwanciyar hankali, amma ya jefa rayuwar wannan iyalan cikin fargaba da damuwa.

Tana cikin tunanin Daddy yace  "Nurat, ki koma gida kinji ko, nagode sosai Allah yayi miki Albarka"

Nurat tace "Ameen Daddy"

Ta miƙe tsaye ta fita, Anwar yabi bayanta suka fita, suna fita harabar ta tsaya ta kalli Anwar tace "Yaya Anwar wai meyasa baza'a fita da Daddy waje ba, tunda yana da kuɗin nan ba babu ba? Kana kallon da yadda yake numfashi fa"

Anwar yace "Wallahi Nurat, nayi iya yina amma su Mummy sunƙi Amincewa, wai anan ma ana kula dashi, Jiya Saleh ya bani shawarar ko Asibiti in canza masa basu sani ba, sedai kawai suga an canza amma ina tunanin abunda ze biyo ba idan nayi hakan"

Nurat tayi ajiyar zuciya tace "ya batun taron kasuwanci da'ake yi duk ƙarshen shekara da ma'aikata da 'yan kasuwa kuwa?"

Anwar yace "Ana nan za' ayi jibi insha Allah"

Nurat tace  "babu wanda ze wakilci Daddyn Widad kenan?"

"Nurat ana ta lafiyarsa wake ta wani taron kasuwanci"

"Amma idan da kara, tunda shike jagorantar taron ayi wani abu akai, tunda yana kwance ba lafiya"

"Ayi wani abu kamar me kenan?"

Nurat tace "A ɗaga taron zuwa wani lokacin"

Anwar yace  "kina ganin su saura mahalarta taron zasu yarda da haka?"

"Yaya Anwar, ƙaddara bata wuce kan kowa ba, dan haka babu laifi idan munyi wani abu akai"

Anwar ya gyara tsaiwa yace "to gurin wa zamuje ayi mana wannan Alfarmar?"

Nurat tace "karka damu ina da hanya, duk yadda ake ciki zan kiraka amma wannan maganar da gani se kai, karka gayawa kowa"

"insha Allah babu wanda zan gayawa, Allah ya saka da alkhairi da wannan taimako da zakiyi"

"Babu komai yaya, yiwa kaine inda kara ai bekamata ayi taron nan Daddy na kwance ba"

A ranta kuwa cewa tayi "daka san Abunda ake shirya yi a gurin taron nan, da kaima ka nemawa Alhaji Daula mafita '

Saleh ya kalli Alhaji Daula yace
" Yanzu idan nace maka na san inda Widad take zaka yadda? "

Daula yayi murmushi yace " daka san inda Widad take da baka ƙyaleni ina fama haka ba"

Saleh yace  "Hakane, jikina yana bani Su Widad sun kuɓuta, sedai kasan su dawo cikin garin nan hatsari ne?"

Daula yayi shiru yace "Tabbas, dan mutanen nan basu da imani, Allah kaɗai yasan halin da suke ciki, ina cikin damuwa sosai Saleh"

Saleh yace "Insha Allah nan ba da daɗewa ba zanzo maka da Labari me daɗi a kansu"

"kamar yaya kenan?"

"Kai dai ka kwantar da hankinka Alhajin Allah, kasan retired solder neni, nasan techniques na abubuwa da dama, dan haka ina daf da gano su"

Riƙo hannun Saleh yayi yace "Dan Allah Saleh dagaske kake? Gaba ɗay....

Farinciki yasa Daula kasa cigaba da magana, sema tari daya sarƙeshi.

Saleh yace" ka kwantar da hankalinka, Amma wannan maganar iyani da kaine, ban yadda wani yaji ba, ko Bulama karka sake ka gayawa "

" Insha Allah bazan gayawa kowa ba, Nagode Saleh "

Yusuf ya cigaba da kallon Widad da take masa wani irin kallo, zame hannun ta yayi daga jikin rigarsa yace
" Shikenan tunda baki amince ba, na manta baki da babban maƙiyi kamar Aure, kuma Aure ma kamar Auren maƙasƙancin mutum irin direbanki, bani da wani zaɓi na zama dake inba Aure mukayi ba, kuma niba abunda ze haɗa ni dake har mu gama zamanmu anan mu koma gida, tunda baki amince ba shikenan "

Ya ƙarasa maganar tare da miƙewa ya nufi hanyar fita, jiki a sanyaye Widad tace
"Na Amince!"


Share, share and Share please 🙏🙏🙏

Domin gyara sharhi ko shawara
Ayshercool
07063065680

                    _*AƘIDATA*_
       

PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

*Story and written by*

_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_

The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *

I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum

Haƙƙin Mallaka ⚠ : Littafin nan mallaki nane, tun daga sunan labarin zuwa abunda ya ƙunsa, ban yadda wani ko wata ya sauyamin ko yin Amfani da wani ɓangare na labarin ba ba tare da izinina ba, Nagode

https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends

NOT EDITED

ELEGANT ONLINE WRITER'S

                         PART1
                                Page 30_31

Yusuf ya tsaya cak ya waigo ya kalle ta yace "are you serious kin amince?"

Shiru tayi, taƙi ce masa komai, har yanzu izzar tana nan, abune mawuyaci ta maimaita magana sau biyu, Yusuf yace "Shikenan, idan Saleh yazo zanyi masa magana, kokuma in samu maigari in masa bayanin komai"

Gyara kwanciyarta tayi tace "kuma ranar da zamu koma gida zaka sakeni,gara kasa wannan a ranka"

Yusuf yayi murmushi yace "karki damu, nidai fatana ki samu lafiya komai ya lafa mu koma gida"

Nurat ta koma gida, ta lallaɓa zata silale ta shiga ɓangarenta, "daga ina kike?"

Taji muryar mahaifinta, tsayawa tayi amma takasa cewa komai, cikin tsawa yace "Nace gidan ubanwa kikaje?"

"Amm.. Ammmm. Dama... Damanaje gidansu ƙawata ne shine....

" shine ubanki, yaushe kika fara fita ke kaɗai babu direba? Daga gidan ubanwa kike? Zaki gayamin ko sena kwantar dake na yankaki a gurin nan"

Nurat ta faɗa a Shagwaɓe "Nifa ba inda naje"

"Ubanwa ya kaiki duba Daula a Asibiti ubanki ne?"

A razane ta ɗago ta kalleshi, ta shiga rarraba ido.

"ba magana nake miki ba?"

"Daddy waye ya gaya maka naje duba shi?"

"Ubanki ne ya gayamin" Alhaji Musa ya bata amsa

"Kin san a duniya mutumin nan maƙiyinane, shine kika kwashi jiki kika tafi?"

Nurat tace "Daddy, 'yarsa ƙawatace kuma dukda abunda ke tsakaninku tazo gidan nan birthday na ta bani kyautar mota, yanzu kuma a sace ta mahaifinta a gadon Asibiti in kasa duba shi"

Kafin ta ƙarasa ya ɗauketa da mari, wanda seda ta dena gani na wani ɗan lokaci.

Da sauri Mahaifiyar Nurat ta fito tana cewa "lafiya kuwa? Me tayi maka ne?"

"dole ki tambayi me tayimin mana, munafuka daga ke har ita, wato da saninki ta fita taje Asibiti duba Daula, babban maƙiyina ko?"

Mahaifiyar Nurat tace "haba Alhaji kai waye ya gaya maka can taje"

Alhaji musa yace "Rufemin baki kafin in haɗa dake in muku duka, na wuce duk yadda kuke tunani, duk wani motsinku a waje ina da masu kawomin rahoto, kuma daga yau na saka doka, kada ki kuskura Nuratu ta sake fita daga cikin gidan nan, ban yadda ta sake zuwa ko'ina ba, idan kuwa ta sake sena saɓa muku daga ke har ita"

Maman Nurat taji zafin marin da yayiwa 'yarta, dan ba taga laifin da tayi wanda harta cancanci wannan marin ba.

Taja hannun Nurat zuwa ɗakinta, ta kalleta tace "kema Allah ya ƙara, gobe ma ki sake, gashi nan ya mareki a banza, kin fiye rawar kai Nurat"

Nurat ta share hawayenta tace  "Ni ban san wani tantirin munafikin ne ya gaya masa naje ba, Amma idan harna cika 'ya ta halak inason mahaifina ya dace da rahamar Ubangiji, dole in shiga rusa duk wani mummunan ƙudirinsa, ta haka ne kawai zan huce wannan marin da yayi min"

"kinga karki jawa kanki wani tashin hankalin, ki ɗakko mana magana kin san halinsa sarai"

"Mummy, wallahi zubawa Mahaifina ido yana abunda yaga dama, alhalin nida ke munsan ba dai dai yake ba bamu kyauta ba, babu ruwanki a ciki nikaɗai zanyi komai.

" Na sani, amma Nurat ina jiye miki matakin daze ɗauka akanki, idan ya gane abunda kikeyi "

Nurat tace "ba abunda ze gane, sedai inke zaki gaya masa"

Ta ɗau jakarta ta bar ɗakin, ta nufi nata ɗakin.

Amal ta zama kamar wata me jinya, ta rame sosai dan ko Abinci bata iya ci Sam, sedai abunda ba'a rasa ba, yanzu ma Mummy ce da Ramlah suke cin Abinci suna hirarsu, yayin da Amal juya cokali kawai take, ba ta kai ko loma ɗaya bakin ta ba.

Ramlah tace "wai Abincin ne bakyaci, kokuwa? naga se juya spoon kike"

Hajiya Halima tace "na lura da yarinyar nan, kwanakin nan sam bata walwala ta takure kanta da yawa"

Amal tace "Nifa wallahi ɓatan Yusuf ne ke ɗaga min hankali, wallahi na damu sosai beji ba be gani ba am sace shi, Allah kaɗai yasan wahalar da yake sha"

Ramlah tace "Ai kece 'yar wahalar, dama abunda yasa kike wannan damuwar kenan?"

Hajiya Halima tace " waini Yusuf ɗin nan ko tare mukayi Naƙudarki ne muka haifeki ban sani ba? Ubanki ne shi? Ko haifarki yayi idan baki kiyayeni da maganarsa ba sena fasa miki baki, kije ki kashe kanki saboda wani ɗan iska, Allah yasa su haɗa dashi su kashe"

Zare ido Amal tayi tace "Mummy a kasheshi kuma?"

"Eh a kashe shi, munafikin yaro na tsani yaron nan wallahi ba ƙaramin daɗi naji ba da aka sace dashi"

Ramlah tace "wallahi nima naji daɗin hakan, munafuki yaita sunkuyar da kai kamar na Allah, saboda shi ba irin wulaƙancin da wannan makirar ba tayi mana ba, yanzu da suka ƙara gaba se hutawarmu muke"

Amal ta dire cokalin ta miƙe ta bar musu dining ɗin.

Mummy tace "Allah ya kawo lokacin da burinmu ze cika, ita kuma tana wani shirme daban"

Ramlah tace  "kedai bari Mummy, nifa harna fara tunanin irin bushshar da zanyi, da yadda zan fantama in kece raini a cikin manyan yara, wayyo Allah daɗi"

Mummy tace "kedai bari yarinya, ai komai yana tafiya daidai"
Suka kwashe da wata uwar dariya, hakan yayi daidai da shigowar Anwar, hakan yasa suka ja baki sukayi tsit.

Ganin yadda sam halin da Daula ke ciki baya gaban mahaifiyarsa da 'yan uwansa yasa ya girgiza kai, tunda Daula ya kwanta a Asibiti bata taɓa kwana a gurinsa ba, se tafi kwana uku ma bata je ba.

Hajiya Halima tace  "Allah sarki yaron kirki, Anwar duk ka rame fa, anya baza' a nemi me kula da Alhaji a dinga biyansa ba,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login