Showing 12001 words to 15000 words out of 135096 words
AUGUST, KATSAM AKA ƊAGA JARRABAWA AKA MAIDA ITA 20 GA WATAN SATUMBA, AMMA TUNDA NI NAYI MUKU ALƘAWARIN CIGABA DA KAWO MUKU WANNAN LITTAFI A WANNAN WATA, NA SHIRYA TSAF DAN CIKA ALƘAWARIN KU 'YAN AMANA, WATTANI HUƊU KUNA SAURARE NA, INSHA ALLAH BAZAN BAKU KUNYA BA, KU SHIRYA DOMIN SALON NA DABAN NE, AKWAI TUFKA DA WARWARARA ME MATUƘAR SARƘAƘIYA A WANNAN LITTAFI DA KUKA DAƊE KUNA JIRA.
KARA ƊAYA ZAKUYI MIN, SHINE NUNAMIN JIN DAƊIN KU TA HANYAR YIMIN COMMENT TARE DA SHARE, LITTAFIN NAN KYAUTA NE DOMIN JIN DAƊIN KU MASOYA NA, AMMA A DALILIN RASHIN COMMENT ƊINKU KOMAI NA IYA CANZAWA, GA MASU MANHAJAR WATPAD KU GARZAYA KU NEMENI
@AYSHERCOOL7724
KU NEMI LITTAFIN A FACEBOOK A
GROUP ƊIN PERFECT WRITERS ASSOCIATION
ƘOFA TA A BUƊE TAKE DOMIN GYARA SHARHI KOKUMA SHAWARA
AYSHERCOOL
07063065680
YADDA NA FARA LAFIYA ALLAH YASA IN KAMMALA LAFIYA
Haƙƙin Mallaka ⚠ : Littafin nan mallaki nane, tun daga sunan labarin zuwa abunda ya ƙunsa, ban yadda wani ko wata ya sauyamin ko yin Amfani da wani ɓangare na labarin ba ba tare da izinina ba, Nagode
BISMILLAHIRAHMANIRRAHIM
ELEGANT ONLINE WRITER'S
*PART1*
_Page 4_
Babu alamar sassauci fuskar Widad, yanayin fuskarta ze tabattar maka da gaske har cikin zuciyar ta zata aikata abunda ta faɗa, ta juya ta koma cikin gidan da hanzari.
Jinjina kai Isa ya dinga yi yana kuma sake shafa kumatunsa yadda yske masa raɗaɗi, tare da tausayawa wulaƙancin da Yusuf ze fuskanta.
Ramla kam cikin sassarfa ta nufi ɗakin mahaifiyar ta, tun daga waje take kiran "Mummy"
Hajiya Halima tace "Ramla wannan wane irin kira ne haka? Ke kam bakya girma"
Ramla ta ƙarasa kusa da mahaifiyar ta ta zauna tace "wai nikam nace me akayiwa 'yar gwal ne? Naga kaman ciwon nata na ƙoƙarin tashi fa? Kuma ga dukkanin alamu yau ta kwaɓe mata itada uban tane"
Ɗan tsaki Mummy tayi tace
"sakani yake cikin sha' aninsa shida 'yar sa ne? Ai sedai inga suna lamauran su ta yaya zan san meya sameta?"
Ramla ta sake gyara zama "hmm kinsan dai halin ciwon ta, a corridor ɗin ƙasa na haɗu da ita, tana ta surutai, wai Daddy Aure zeyi mata, se safa da marwa take tana zufa"
Zaro ido Mummy tayi tace "Aure kuma? Wane irin Aure ana zaman lafiya? Waye ze Auri mahaukaciya mara tarbiyya kamar wannan Yarinyar? Shi mijin da haukan zeji ko kuma da rashin tarbiyya?"
Ramla tace "waya sani musu?, sedai ki jiyo mana kanun Labaran muma ki fesa mana, Amma ina tunanin wanda ze kwashi wannan Mahaukaciyar"
"To nidai a iya sanina bata yadda da mutane ma, to ta yaya ta samo wanda ze Aure ta?"
Ramlah tace "Ai samun miji ba wuya ze mata ba, ko dan wannan haɗaɗiyar Daular, dan haka ko'a turu take dan hauka, za'a iya samun me sonta yace ze aureta a haka"
Mummy tace "hakane, Amma ya zama dole musan waye ze Aureta, dole in gano"
Haka Suka ci gaba da tattauna wa akan lamarin.
Yusuf kam kashe wayoyin sa yayi ya shiga sabgoginsa, duk yadda Isa yaso kiran Yusuf a waya ya gaya masa Saƙon Widad abu ya gagara wayar sa taƙi shiga, ƙarshe se haƙura Isa yayi.
Widad kam baranda ta samu ta kwanta, akan tiles ga sanyin tiles na ratsa ta amma sam bata ji, tayi ruf da ciki tana jin yadda zuciyar ta take mata raɗaɗi, kamar ta tsaga ƙirjinta ta fito, Babban Abunda ya ƙara bata mamaki shine yadda mahaifin nata be biyo sahunta ba balle ya rarrashe ta kaman yadda yake yi abaya, shima kamar yayi fushi da ita karon farko ya barta cikin damuwa, lallai wannan karon mahaifin nata dagaske yake.
Washegari Yusuf ba shida Niyyar zuwa gidan su Widad Sam, da ya tashi da safe ma shirin tafiya Office yayi abun sa, ya shirya ya fito Umman sa ta kalle shi tace
"Ya haka kuma? Yau ina zakane?"
Murmushi yayi yace "Yau Office zanje Umma"
"Kacemin kuma, an turaka aiki gidan Alhaji Nasir Daula, yanzu kuma kace min zaka gurin aiki ya haka?"
Yusuf yace "hakane Umma, an turani aiki gidan Alhaji Nasir Daula, Amma dole zan dinga leƙawa Office, ina documenting findings ɗina sannan indinga presenting sakamakon bincike na"
"shikenan a sauka lafiya, Allah ya tsare ya kiyaye hanya"
"Allah yasa Umma, dan Allah yau ki mana dambu kinji Umma na"
Umma tace "banyi Alƙawari ba, ka bari ranar da kake nan se kayi"
Noƙe kafaɗa Yusuf yayi yace "dan Allah Umma, ni gaskiya idan ba dambu kika yi yau ba bana cin Abincin"
"kar kaci ɗin, ai cikin ka ba nawa ba"
Haka yaita zolayar umman nasa sannan yai mata sallama ya tafi.
Da yaje Office ɗin ma Ayyuka sun ɗanyi masa Yawa, ya duƙufa sosai yana ta shigar da ayyukan sa cikin system.
Sallamar da'akayi a office ɗin ne ya sashi ɗagowa yaga me Sallamar, kamar yadda ya zata sakine ce ta shigo.
Kallo ɗaya yayi mata, ya Amsa sallamar ya maida kansa ya cigaba da danna system ɗin shi.
Yauma cikin baƙaƙen suit Sakina take, amma skirt ga ƙaramin hijjabi da ta saka, gaba ɗaya kayan sun bayyanar da surar jikin ta.
Kujera ta ja ta zauna tana facing ɗin sa.
"Yusuf sannu da Aiki"
Ba tare da ya kalle ta ba yace "lafiya kalau Alhamdilillah"
"kwana biyu baka shigowa Aiki, lafiya dai ko?"
Ɗan ɗagowa yayi yace "Eh an bani wani Assignment ne"
Cikin iyayi da lumshe ido tace "to Allah yaba da sa'a"
Ya amsa da "Ameen"
"Can i offer you something to eat?"
Ba tare da yace komai ba ya girgiza mata kai, Alamar A'a.
Miƙewa tayi ta zagayo inda yake tace
"ko Akwai abunda zan taya ka ne?"
Ɗagowa yayi ya kalleta a hankali yace "dan Allah ki fitar min daga Office inada Ayyuka da yawa kina takuramin fa"
A Shagwaɓe tace "Yusuf meyasa kake son yi mun wulaƙanci ne?"
"ba wulaƙanci bane, gaskiya ce, Aikine ya kawo ni gurin nan ki barni inyi aikina mana"
"Amma Yusuf meyasa zaka maida Soyayya ƙiyayya, tunda na nuna ina sonka kake wulaƙantani haba Yusuf"
"Sakina niba wulaƙantaki nake ba, yanzu lokacin aiki nane, dan Allah ki tashi ki tafi, bearable in shiga lokacin aiki ba"
"Yusuf" ta kira sunansa, ɗaga mata Hannu yayi ya dakatar da ita tare da faɗin
"Sakina dan Allah ki barmin office, kalli shigar jikin ki, kuma kinzo kin sani gaba, dan Allah ki tafi"
Suna cikin Jayayyar ne Abbas ya shigo, Sakina ta miƙe ta bar office ɗin a fusace.
Abbas ya kalli Yusuf yace
"Anya Sakina bata fara kama zuciyar ka ba Yusuf?"
Ɗan girgiza kai Yusuf yayi yace
"Abbas kenan anyi na farko, baza'ayi na biyu dani ba, bana son yi mata wulaƙanci ne amma taƙi ganewa, Soyayya kam sedai inga anayi, bazan sake ba, in Allah yayi zanyi Aure shikenan, Amma na gama Soyayya"
Abbas ya jinjina kai yace "shikenan Allah ya kyauta, na kiraka tun jiya bata shiga ya labarin mutuniyar ne?"
Shafa Aljihun sa Yusuf yayi, sannan ya jingina da jikin kujera yace
"Aini tun jiya dana dawo na kashe waya ta, bana son a dameni ne sam"
Abbas yace "kayi mata aikine jiya?"
"Eh munfi ta, na kaita wani gida, inaga gidan ɗan uwan mahaifinta ne ko makamancin haka"
Abbas yace "babu dai wata matsala ko?"
"Babu wata matsala, ba tayi min dai wulaƙanci ba, Amma fa naga izza wadda ban taɓa ganin makamanciyarta ba, dan cikin isa da gadara take wa kowa magana, bata shakkar kowa bata girmama kowa, kai ko Dariya banga tayi ba Jiyan nan, magana ma aiki ce a gurin ta"
Abbas yace "taɓ, aishi yasa nace bazan iya ba, saboda na samu labarin yarinyar, shikenan ka dai kula sosai akan abunda muke son ganowa"
Jinjina kai Yusuf yayi, tare da cewa "Insha Allah, komai ze tafi dai dai"
***********
Ƙarfe goma na safe Yusuf ya bar gurin aikin, ya koma gida seda yayi wa Umman sa cefane, ya kai mata markaɗe ya kama mata Ayyukan gida sannan ya sauya kaya, ya nufi gidan Alhaji Nasir.
Yau da yaje ya tarar da Isa mai gadi dashi da wani, Suka gaisa, Isa yayi farat yace
"Yusuf ga Nura shine direban megidan nan, lokacin da kazo yaje garin su ne, amma gashi ya dawo, shike kai Alhaji unguwa"
Yusuf ya miƙa wa Nura hannu suka gaisa.
Isa ya nisa yace "Yusuf kayi gangancin tafiya jiya, nan ta fito a birkice jiya kaman mara hankali tazo nan tana neman ka wai ka fita da ita, baka ga shigar jikin ta ba, daga tambayar ta a haka zaka fita da ita ta mareni, wallahi har yanzu ko ƙuda bana so ya taɓa fuskata dan ba ƙaramin shiga marin nan yayi min ba"
Zaro ido Yusuf yayi yace "mari kuma?"
"Wallahi Yusuf mari na tayi"
Nura yace "aiba abun mamaki bane, dama wani lokacin haka take birkice wa, kun san abunka dame rangwamen Ƙwaƙwalwa, aini tunda naji zata dawo naji aikin gidan nan ya fita daga kaina, Allah ya temakeni aka samo mata nata direban"
Kallon su Yusuf yake dan be fuskanci inda zancen nasu ya dosa ba.
Isa yayi ƙasa da muryar sa yacewa Yusuf
"wani lokacin birkicewa take kaman hauka hauka, shiyasa kaga bata son mutane suje inda take, tana da larurar ƙwaƙwalwa shiyasa....
Yusuf ya katse shi ta hanyar cewa
"Shikenan shikenan, Allah ya bata lafiya be kamata a dinga yayatawa ba, Addu'a ya dace ayi mata, faɗar bashi da Amfani sam"
Widad ce ta fito ƙaton falon gidan, ta tarar da matar gidan da yaran ta Suna ta ciye ciye suna hira, tana fitowa suka yi tsit suka shiga taitayin su, suka dena hirar.
Ta dube su ɗaya bayan ɗaya, kamar me nazari, sannan ta yatsuna fuska tace
"Amal jeki kira min wancan matsiyacin talakan direban, yau in fara gwada masa wacece ni"
Sam Amal ba taji daɗin kalaman da Widad tayi amfani da su akan Yusuf ba, Amma babu yadda ta iya ta miƙe ta tafi kiran sa.
Tunda Amal ta fito ta hangi Yusuf yana hira da su Nura, yayi kyau sosai komai nasa gwanin sha'awa, kamar ba direba ba.
Amal Ta ƙaraso inda suke bata kula su Isa dake ƙoƙarin gaishe ta ba, ta dubi Yusuf tace
"barka da rana Yusuf"
Fuskarsa ba yabo ba fallasa yace
"Yawwa barka, ina uwa ɗakina?"
Bata jin daɗin yadda koda yaushe yake taƙaita magana da ita, Amma ta basar tace
"itace tace in kira ka ma"
Yusuf ya miƙe yace "shikenan muje"
Yabi bayan Amal, tsananin kwarjinin Yusuf ne yasa Amal sam ta kasa kuma ce masa komai, se ƙamshin turare yake fitarwa me daɗin ƙamshi kaman ba direba ba.
A falon suka tarar da hakimar ta harɗe da alewa me tsinke a bakin ta, tana danna waya tareda kaɗa ƙafafuwan ta.
Kamar kullum yanzu ma kanta babu ɗan kwali, ta baje gashin ta, Amma yau anyi sa'a skirt ne dogo a jikin ta da wata 'yar ƙaramar riga shara shara.
Tunda Yusuf ya shigo ɗakin ƙamshin turaren sa ya daki hancin ta taji ya saukar mata da wata muguwar kasala, a duk lokacin da Yusuf zezo gidan nan taji wannan ƙamshin turaren a jikin sa se kasala ta saukar mata.
Kallo ɗaya Yusuf yayi mata yaji ƙirjin sa ya buga da ƙarfi, da sauri ya ɗauke idon sa daga kanta, Sam fuskar ta babu alamar afuwa.
Ya kalli matar gidan yace
"barka da yamma Hajiya"
"Yawwa barka sannu ya aikin?"
"Alhamdilillah"
Ya juya ga Widad yace "sannu da hutawa ranki ya daɗe"
Dama be zaci zata amsa ba, dan haka be kuma cewa komai ba se sunkuyar da kansa ƙasa da yayi.
Ya shafe mintuna Arba'in a durƙushe a gaban ta ba tare da tace komai ba, shi kuma ko kansa be ɗaga ba.
Amal ji take tamkar ita ce a durƙushe a gurin, gaba ɗaya taji kaman ta cewa Yusuf ya tashi yayi tafiyar sa.
Ba zato ba tsammani ya tsinkayi maganar ta
"Waye ya baka iznin tafiya jiya?"
"ba kowa Ranki ya daɗe"
Seda ta kuma jan wasu mintunan sannan tace
"meyasa ka tafi?"
Ba tare da ya ɗago kansa ba yace
"na zata na gama aikina na jiyane shiyasa, Amma hakan ba zata sake faruwa ba Insha Allah, kiyi haƙu....
Cikin tsawa tace
"Shut up, what the hell are you trying to say? Do you sign my conditions based on Assumption? Don't you read what is in that paper? Why are you trying to applogise? Talaka baze canza hali ba, baku da Alƙawari baku san ƙa'idar Aiki ba, se an jima ku buɗe baki kuna zagin shugabanni da masu kuɗi, waye kai da zaka karyamin doka? Me kake taƙama dashi da zaka nemi ka raina min hankali? Ɗan uban waye kai? Ko ban gaya maka lokacin aiki nawane ba? Har da zaka fara da rainamin hankali"
Tunda Widad ta fara zazzaga rashin mutuncin ta Yusuf be ɗaga kai ba, dukda yadda zuciyar sa ke harbawa jijiyoyin kansa suka miƙe saboda ɓacin rai, Amma ya dake.
Amal kaman ta ɗora hannu akai tayi ihu, ji take tamkar ita Widad ke ciwa mutunci, ita kuwa matar gidan da Ramlah ko a jikin su dan babu wanda Widad ta bari a rashin mutunci.
"kasan tsanani baƙin cikin da na shiga zama na a gidan nan bayan an ɓata min rai, daka nan ka fita dani da ban shiga damuwar dana shiga ba, tun jiya nake fama da damuwa saboda sakacinka, nayi kwanan baƙin ciki da ɓacin rai, this is my last warning to you, idan makamancin haka ya kuma faruwa, sena nuna maka wace ce Widad"
Risinawa ya kuma yi da kai
"zan kiyaye ba zana kuma ba insha Allah"
Jefo masa key tayi fuskar sa tare da faɗin
"Car Number 8, to bulama's residence"
Yaji zafin yadda ta jefa masa key a fuska, da maganganu marasa daɗi da tayi masa, amma yasa hannu ya ɗauka, kaman wanda ƙwai ya fashewa a ciki ya nufi hanyar fita.
Fakar idon Widad Amal tayi ta biyo bayan Yusuf, wajen ƙofar fita ta cin masa, yana ta sauri fuskarsa babu Annuri, Amal ta kira sunan sa, dan tsayawa yayi ya waigo yana kallon ta
"Dan Allah kayi haƙuri da abunda Widad tayi maka, haka halin ta yake muma duk haƙuri muke da ita, dan Allah kayi hakuri"
Ga mamakin ta se taga murmushi akan fuskarsa yace
"aini banji haushi ba, tabbas laifi nane da banbi komai a ƙa'ida ba, bayan nasan hakan ya saɓawa Yarjejeniyar dana sakawa hannu, kuma nasan yana daga AƘIDAR uwa ɗakina girmama Alƙawari, ya kamata in nemi Afuwa ne ba jin haushi ba"
Ɗan zare ido Amal tayi "yanzu duk abunda tayi maka kana nufin ba kaji haushin hakan ba?"
Jinjina mata kai yayi alamar eh tareda faɗin,
"bari in hanzarta in fito da motar karta fito ta sameni anan ranta ya kuma ɓaci" yayi gaba abun sa yayin da shi kaɗai yasan me yake ji a ransa.
Yaje ya fito da motar da ce masa, ya buɗe ya shiga ya zauna ya kifa kansa akan sitiyari, tabbas badan duk cikin aikin sa yake wannan abun ba to da ko Gidan su Widad gold ake sarrafawa baze kuma aiki a gidan ba.
Jin ƙamshin turaren ta yasa shi saurin ɗagowa, ta buɗe gaban motar ta zauna, tace "jeka falo inda na zauna ka ɗakko min wayata"
Ikon Allah wayar ma bazata fito da ita ba seya ɗakko mata? Bece komai ba ya fita daga motar ya koma cikin gidan, yana zuwa ya tarar falon ba kowa wayar tana kan center table, ya ɗakko ya fito ya kawo mata.
Tasa hannu ta karɓa ba tare da ta kalle shi ba tace "A ina kaga wayar"
"Akan center table"
Murmushin gefen baki tayi tace "let's go"
Kamar yadda tace gidan Bulama ya kai ta, ya samu guri yayi parking ya fito ya buɗe mata ƙofa ta fito, ƙafarta sanye da takalmi me tsini sosai shigar nan tata baka ce musulma ce ba, kayan sun kamata tsam a jikin ta a hankali ta furta "do not accept any gift from anyone"
Gyaɗa mata kai yayi yace "Insha Allah"
"Follow me"
Haka yabi bayan ta, cikin hanzari take tafiyar yau.
Yau kai tsaye bata nemi iso ba cikin gidan ta nufa, Yusuf na bin bayan ta.
A babban falon dake gidan suka ga wata budurwa da wannan matashin da suka tarar jiya, da wata babbar mace da alama itace matar gidan.
Maimakon Widad tayi Sallama se tace "Hi how are you doing guys?"
Matar tace "Widad dama kina garin nan amma ko ganin ki ba'ayi"
Budurwar tace "Wallahi Mum Ramadan yace tazo jiya amma taƙi shigowa" Yusuf dai bece komai ba saboda jan kunnen da tayi masa jiya.
Ramadan ya kalli Widad yace "you look so Cute in this outfit Dear"
Ba ta amsa musu maganganun su ba tace "Is Daddy Around?"
Yusuf ya kalli kayan dake jikin Widad, da kuma abunda Ramadan yace kawai ya girgiza kai
Ramadan yace "yeah yana nan"
Ƙoƙarin hawa bene Widad take yi, budurwar tace
"hey Baby who is this gentleman with you?"
Aiko tsaya ba tayi ba balle bada amsa, ta haye saman benen da sauri, Yusuf bashi da zaɓin daya fi yabi bayan ta.
Wata ƙatuwar ƙofa ta buɗe, ta kutsa kai Yusuf yabi bayan ta, shima wani haɗaɗɗen falo ne me girman gaske, sanyi Ac ke rasa ko ina na ɗakin.
Alhaji Bulama ne ke zaune akan ɗaya daga cikin kujerun falon, yana shan tea tareda dannan system, Yusuf ne yayi sallama, Alhaji Bulama ya ɗago ya kalle su.
Murmushi yayi ya amsa sallamar Yusuf, yana ƙarewa Widad kallo, guri ta nema ta zauna tana fuskantar Bulama.
Bulama yace "Daughter wai shi wannan duk inda zaki se tare da shine? Ina direba ne kawai? Kodai Allah ya karɓi Addu'armu kin fara sakin jiki da mutane?"
Haɗe rai tayi tace "my policies remain constant, babu abunda ya canza, babu ruwan ka da dalilin da yasa duk inda zani yake bina"
Alhaji Bulama ya murmusa yace "shikenan Allah ya baki haƙuri"
Ya kalli Yusuf yace "Sannu ɗan Samari, daughter ɗin tamu seka na haƙuri, muma lallaɓata muke"
Da ido ta kalli Yusuf, dan haka Yusuf bece komai ba se ɗan murmusawa da yayi.
Alhaji Bulama ya maida kallon sa ga Widad yace "ina jinki?"
"Meyasa ka turawa Daddy na ra'ayin ayimin Aure?"
Ɗan girgiza kai Bulama yayi tareda murmushi "yaro yaro ne, Widad