Showing 123001 words to 126000 words out of 135096 words
da'aka rufa azuzuwa, ai kuwa akace mu dena zuwa se an gyara, dan haka tun aji huɗu furamarai nidai na dena zuwa har yanzu "
Widad tayi shiru, ita ko a tatsuniya bata taɓa jin wannan al'amarin ba, ace a Nigeria akwai 'yan ƙasa wanda basa samun ilimi, ina wakilansu? Meye amfanin shugabannin da suka zaɓa suka wakilta dan suyi musu aiki? Ace ƙauyuka huɗu su dogara da primary ɗaya, kuma shima se sun sha baƙar wahala kafin suje, dole abun ya fita daga ransu'
Widad tace "gaskiya banji daɗi ba Hindu, ai Ilimi shine mutum, tabbas da'a bakin wani naji cewa zanyi ƙarya ne labarine kawai"
Hindu tace "aikuwa gashi a zahiri kinji, shiyasa duk muka haƙura wasu suka kama talla har zuwa lokacin da mace zata samu miji tayi Aure, dama idan kana karatun wasu kallon ɗan iska suke maka, muka koma zuwa ta Allo ta Allonma gata nan dai nidai na samu nayi izu biyar na haddace itama munyi yawa, babu wata kulawa yadda yakamata, dan anan wajejenmu makarantar Allo ɗaya ce"
Widad ta jinjina kai tace" to sauran litattaafai fa, kamar Ahlari, fiqhu hadisan manzon Allah salallahu alaihi wassalam, suma ana koya muku? "
Hindu tace" Taɓɗijan, Al'qur'ani kawai ake koya mana a makarantar Allo, kuma shima mun dena zuwa, se Baffanmu ne dai da yana koya mana Alhadisin Auwwalu, shima yace mana Babansa ne ya koya masa, kuma ma yanzu duk mun manta tunda shekarun da yawa "
Widad kawai tayi tagumi tana sauraren Hindu, tana jin kwamacalar da ko a Film bata taɓa ganin irinta ba, yanzu dama da irin wannan mutanen suna rayuwa a haka, amma ake samun mutanen da suke wawashe dukiyar al'umma, a 'ya' yan sanatoci akwai wanda tasan ana biya musu ku&in makaranta na secondary naira milyan uku, duk term miliyan ɗaya, iya 'yan tsirarin' ya'yansa, amma ga dubunnai zaune a gida babu arabi babu boko, irin wannan ne idan suka faɗa harkar ta'addanci basa imani sam.
Hindu ta kalli Widad tace "ya naga kinyi shiru ne?"
Widad tace "Mhmm bakomai"
Hindu tace "Yawwa, dan Allah meye Firiyas ɗin da kika ce?"
Widad tace "Period nace, ina nufin jinin Al'ada"
Hindu tace "Auho ai ban gane ba, seki cemin baƙon wata, ai mu da tsumma mukeyi, mu yayyanka tsumma semu dinga amfani dashi, duk wanda muka cire se mu wanke mu ninke"
Widad ta kalleta da sauri tace "ku wanke me?"
"tsimmar mana, idan ɗan kamfan mutum ɗaya ma haka ze haɗa duk ya wanke, ya ɗan jira ya bushe seya sake mayarwa"
Dafe kai Widad tayi, tayi shiru ta shiga duniyar tunani, ta tuna yadda take fantamawa a cikin kuɗi, babu abunda ta nema ta rasa a rayuwar ta, Kama daga Abinci, sutura abun hawa gurin kwana, har wasu kuɗi ne da ita na musamman wanda take kula da dabbobinta kawai, tayi kyautar mota, tayi kyautar gida ta bada kuɗi kamar aikin banza, ashe akwai bayin Allahn da sun fidda rai da samun wani jin daɗi.
Hindu tace "Amarya, Allah yasa ba wani abun na miki ba, naga kin ɓata rai?"
Widad tace "bakomai Hindu, mu cigaba da aikin kawai"
Widad bata iya tsinkar zogalen ba, dan haka wani yanayi wani kuma harda kararen jiki take zubawa, Hindu bata damu idan Widad ta zuba a haka se tabi tana gyarawa.
Hanne ce ta taho a fusace tasa hannu ta ɗauke robar da suke tara zogalen tace "Aikin banza, ke Hindu kin san ba abunda ta iya kawai kin ɗauki abu kin bata kinsa se ɓatawa mutane take, tana mayar mana da aiki baya kin zauna se surutan shirme ki keyi, da yanzu an wanke an ɗora amma duk ta ɓata mana"
Hindu tace "Haba Hanne, to ba a hankali zata iya ba, kuma ai tayani take tana yi ina gyarawa, meye a ciki dan munyi tare"
Tsaki Hanne Tayi, tai gaba da robar zogalen, Widad ko ɗaga kai ba tayi ba balle ta kalli Hanne, tayi shiru ba tace komai ba.
Cikin damuwa Hindu tace "dan Allah Amarya kiyi haƙuri, ni ban san meyasa take wannan abubuwan ba"
Widad tayi murmushi tace "Ni banyi fushi ba ai, bakomai"
Saleh ya ɗau waya ya kira Abbas, sedai har tayi ringing ta katse be ɗaga ba, tana katsewar ne Abbas ya biyo kiran, Saleh ya ɗaga tare da yin Sallama Abbas ya amsa, Saleh yace
"Malam Abbas, kayi gaba ko waiwaye baka yi, kana da labarin an sace amininka kuwa tare da 'yar gidan Daula?"
Abbas yace "ƙwarai kuwa na sani, dan nine ma na gayawa mahaifiyarsa"
Saleh yace "Wani tunani kayi akai kuwa?"
"wani tunani zanyi kuwa, maganinsa kenan ai, shegen shishshiginsa da rawar kai yaja masa, ni Allah ne ya dube ni, dani naso in maye gurbinsa da dani za'a ɗauke, Amma kuwa an karɓi files ɗin daga hannunsa?"
Shiru Saleh yayi sannan yace "basu karɓa ba tukuna, ni suke jira, har yanzu basu san cewar Yusuf ne jami'in tsaron ba, zancen da nake maka yanzu haka Yusuf sun tsere daga inda aka ɓoye su"
Abbas yace "haba dai, garin yaya akayi suka tsere? Kai Yusuf fa ba ƙaramin hatsabibi bane ba"
Saleh yace "babu wanda ya sani, kuma har suka gudu ba'a samu karɓar abun nan daga hannun yarinyar ba, yanzu maganar da nake maka, shi kansa Daulan an ɗauke shi a gadon Asibiti, babu wanda yasan inda yake"
"Innalillahi wa inna ialaihi raji'un, garin yaya, yanzu shikenan munyi biyu babu, nifa ba wanda yake tuntuɓata yanzu tunda akamin transfer"
Saleh yace "karka damu, ina son ka saurareni da kyau, duk abunda ake ciki zan dinga sanar da kai, karka kusakura wani daga cikin su yayi yunƙurin haɗa kai da kai, dan yanzu gaba ɗaya kawunansu a rarrabe yake, duk wanda ya tuntuɓeka koya tambayeka wani abu game da wanda aka bawa binciken nan kace baka sani ba"
Abbas yace "to aini basu sanni ba, kai suka sani me zesa su nemeni?"
"Abbas mutane ne masu wayo matuƙa, yanzu haka a manyanka na gurin aiki wani ze iya bugun cikinka ya tambayeka wani abu, karka kuskura ka gaya wani, wani abu akan harkar nan, na gaya maka kansu ya rarrabu, wasu zasu iya zamewa suyi harkar nan babu mu, bayan wahalar da mukayi "
Abbas yace " bakomai na fahimce ka, Insha Allah babu wanda zeji wata magana daga bakina, dama kai ka jawoni cikin harkar "
Saleh yace " Good nagode "
Sukayi Sallama, Saleh ya jinjina kai yanzu ya sake jinjinawa Widad, lallai bata da laifi naƙin yadda da mutane, ƙir ƙiri Abbas na jikin Yusuf ne, amma saboda kuɗi yake masa zagon ƙasa, tabbas mutum abun tsoro ne, kuma da alama Abbas Soko ne, dan haka yi masa wayo ba wani abu bane me wahala.
Saleh yana son sake komawa gurinsu Widad, dan haka yana ta ɗanyi musu siyayya.
Alhaji Musa ne ya kira shi a waya yace 'lallai yana son ganinsa a guest house ɗinsa'
Haka Saleh ya bar abunda yake yi ya tafi gidan Alhaji Musa.
Yaje ya tarar dashi a lambun dake gidan, suka gaisa Alhaji Musa yace "Saleh ina cikin damuwa fa"
"wace irin damuwa kuma ranka ya daɗe?"
"Na fuskanci Nurat tana ƙoƙarin fara yin shisshigi ga al'amuran Daula, gashi yanzu ina ɗari ɗari da su Haruna, ina tsoron Ayi Amfani da ita a cutar da ita koni, yanzu babban abunda ya sake bani mamaki be wuce yadda Daula yayi ɓatan dabo ba, ko kusa ko alama an rasa inda yake, zargina yana ƙara tabatta akan ana min maƙarƙashiya, kodai su Alhaji Haruna suke cuta ta suke al'amuran su suka ɗai, kokuma akwai wani a gefe daya ke harin abunda muke hari, ko kuma yasan siriinmu yake son temakawa Daula"
Saleh yayi ajiyar zuciya yace "banƙi ta taka ba, Amma ko waye wannan tabbas na jikin ku ne, amma abun da mamaki ace an nemi Daula ko sama ko ƙasa an rasa sekace wata takadda"
"Shine abunda ya ɗauremin kai ai, ni yanzu gefe zan koma in nemawa kaina mafita, idan abun nan ya samu shikenan, in be samu ba shikenan, suma har yanzu da suka gudu babu wanda ya sake jin ɗuriyarsu, dan haka ni inaga tunda babu wanda yasan inda Daula yake, zan fito takarar Senate ne kawai "
Da sauri Saleh ya kalle shi yace " Amma ta yaya kake tunanin mutane zasu yarda su zaɓeka? Bayan Daula ya riga ya ɓata siyasarka a idon duniya? "
Alhaji Musa yace " shiyasa nima na ƙuduri aniyar kota wane hali, sena Wulaƙanta Daula a idon duniya, sannan malamai zan shiga a rufemin bakin jama'a, akwai yarana da suke aiki a wasu daga kamfanunukan Daula, zamu haɗa kai dasu mu karkatar da wasu kuɗaɗe inyi amfani da su, niba kuɗin Daula ne sjka dameni ba, yadda zan Wulaƙanta shi in ɗaiɗaita shine ya dameni, amma ko yanzu na rage raɗaɗin dake zuciyata, kuma zan cigaba da bibiyarsa se naga babu inda ya rage wanda ze jingina yaji daɗi, sannan in dawo kan su Alhaji Munir"
Yadda Alhaji Musa ke maganar babu alamun tausayi ko imani a tare da shi, har zuciyarsa yake faɗar wannan maganganun.
Saleh ya ɓoye duk mamakinsa, ya dinga ziga Alhaji Musa, Alhaji Musa ya kawo kuɗi ya bawa Saleh, Saleh a ransa yace "ka bada kuɗin da zanyiwa maƙiyan ka siyayya, kuma nima zancigaba da bibiyarku, ɗaya bayan ɗaya sena ɗau fansar cin amanata da kuka yi, da saɓa Yarjejeniyar da muka yi daku"
Widad gaba ɗaya hirar da suka yi da Hindu ta tsaye mata a zuciya, ta tuna yadda haka siddan se ɗan kasuwa yayiwa ɗan siyasa kyauta motar miliyoyi, ko biliyoyin nairori, Amma al'ummar su suna tagayyara, da yunwa da rashin kyakkyawan mahalli.
Yusuf yaga gaba ɗaya Widad tayi wani iri, seta zauna tayi shiru tana tunani, dukda shima zuciyarsa ba daɗi, Amma sam baya son ganinta a damuwa dan haka yace "Ran gimbiyata ya daɗe meke damunki ne?"
Jiki a sanyaye tace "Abubuwa da yawa"
Yusuf yace "Kamar me? Ko har yanzu fushin kike dani"?
Jiki a matukar sanyaye ta bashi labarin hirar da suka yi da Hindu, daga ƙarshe tace "tabbas ƙaddarar data sameni na zuwa ƙauyen nan, ishara ce Allah ya nunamin, na rayu cikin gata wanda nake ganin babu wani abu da zan iya nema in rasa a rayuwata, ranar da kace min akwai mutanen da Naira ɗari take gagararsu, gani nake kawai ka faɗane dan ka rainamin hankali saboda a lokacin, abun da ke cikin asusun bankina ya ninka ɗari sau ɗari, bani da wata damuwa ko matsala, Amma ace a rayuwa akwai tarin 'ya' ya mata da suke zaune ba ilimi? Akwai tarin mutanen da suke rayuwa da gurɓataccen ruwan sha? Akwai tarin yara manyan gobe da rayuwarsu ta lalace saboda rashin gurin samun ilimi, Yoseef yaran masu kuɗi na Almubazzaranci da dukiya, da yawanmu bamu san yadda aka tara kuɗin ba... Kasa ƙarasawa tayi gaba ɗaya jikinta yayi sanyi, wani irin ɓacin rai ke taso mata, yadda ake ɓarnar kuɗi gurin bukukuwan birthday dana Aure, da makamantan su.
Yusuf ya taso daga inda yake, yazo ya samu guri ya zauna kusa da ita yace "Widad baki ga komai ba, a yanzu haka a cikin ni'ima muke, a gidan megari muke a zaune, kuma gidansa da rufin Asiri, ya kike tunanin gidajen sauran talakawa da suke garin nan? Wanima abunda zasu cin ma babu, Widad talauci gaskiya ne, shiyasa Wulaƙanta mutane bashi da kyau "
Widad tace" tabbas wulaƙanta mutane bashi da kyau, nasan mutane dayawa sunamin kallon mace me izza da Wulaƙanta mutane, sedai...
Se kuma tayi shiru, Yusuf yace "sedai me?"
"Bakomai" ta bashi amsa tare da basar da zancen.
Da Asuba bayan Yusuf ya dawo daga sallar Asuba yazo ya tattara kwanuka zeje ya wanke, Widad tace "ka bari zan wanke"
Yusuf yace "No ki huta kawai, bari in wanke ai ba yawa kwanukan"
Widad tace "ce maka akayi ban iya wanke wanken bane?"
"Ni na isa ince gimbiya bata iya wanke wanke ba?"
Widad tace "gashi nan kuwa ka faɗa"
"A'a ni ban faɗa ba, taso muje muyi tare"
Widad ta tashi tabi Yusuf suka je suka wanke kwanukan tare, ta tattare duk kwanukan wanke wanken da'akayi fatali dasu na Abincin dare a tsakar gidan, ta haɗesu a guri ɗaya, Yusuf yasa tsintsiya duk girman tsakar gidan yana sharewa, Widad ta dinga kallon ikon Allah, yadda Yusuf yake sarrafa tsintsiya kamar mace.
Widad tace "dan Allah dagaske kai ka ɗaine a gidanku?"
Yusuf yace "Eh nikaɗai ne Mamana ta haifa, ni nake mata aikin gida, shara, wanke_wanke hadda girki duk ta koyamin ni nake yi, idan ta tafi unguwa kafin ta dawo nayi komai"
Widad tace "shiyasa ka iya aiki sosai, nima nasan da tare na girma da Ammi na da duk na iya aiki, da baza'a dinga kallon ban iya komaiba"
Yusuf yazo kusa da ita ya tsaya, ya kalleta yace "karki damu gimbiyata, Insha Allah muna tare zaki iya komai kafin mu koma gida"
Widad ta kalle shi tace "dagaske har girki zaka koyamin? Nafa iya girki amma ba sosai ba"
Hannu yasa ya ɗago haɓarta yace "zaki iya komai insha Allah, duk zan koya miki, amma bana son taurin kai, dan nasan halinki"
"Nice me taurin kai?"
Yusuf yace "eh kina dashi amma kaɗan"
Murmushi Widad tayi tace "Ni dai in zaka koyamin zanyi duk abunda kake so"
Yusuf yace "dagaske?"
Widad ta jinjina masa kai, ya matso daf da ita yace "to shikenan, Yimin kiss a goshina ma ba'a baki ba, se in koya miki kunna risho yau"
Tureshi tayi tace "Baza'ai wannan ɗinba"
Matseta yayi a jikin bishiyar ya riƙota, cikin sigar magiya yace "please Gimbiyata, ko sau ɗaya ki nuna kin damu dani please"
Cikin tsiwa tace "to Jaririne kai? Ko goya ka zanyi?"
Kwantar da kansa yayi a kafaɗarta yace "to goyanin mana, ko daga nan zuwa ɗakine"
"Eh ba shakka, ba kunya wai in goya ka, sakeni ko in cijeka yanzun nan"
Hanne ce ta fito daga ɗakinsu, tana fitowa idonta ya sauka akan Yusuf da Widad dake tsaye a jikin bishiyar ceɗiya dake tsakar gidan, kamar zasu shige jikin juna.
Da ƙyar ta haɗiye wani irin mugun yawu a wuyan ta, ta koma cikin ɗakinsu tana fesar da numfashin baƙin ciki.
Hindu ce ta Kalle ta tace "Hanne lafiya kuwa?"
Hanne tace "wallahi Hindu na tsani matar Yusuf, ji nake kamar in shaƙeta"
Cike da mamaki Hindu ta kalle ta tace "kamar yaya kin tsane ta?"
Hanne tace "Hindu dan Allah kina ganin Yusuf ze iya Aurena?"
Wani mugun kallo Hindu tayi mata tace "Anya kina kallon kanki a mudubi kuwa? Kina ganin mace jawur, kalle ki kice kina son mijinta, matar nan fa tana miki kawaici akan Mijinta, kiyi ta mata wulaƙanci amma tana ƙyale ki, karki kuskura Gwaggo taji wannan maganar da kike"
Hanne tace "ba zaki gane ba Hindu, wallahi Yusuf ɗin nan yana da kirki sosai, ita ba abunda ta iya se rashin kunya, gata bata da tarbiyya sam gata a wani taɓare, ga tsbar iskanci da rainin hankali, komai se tace bata sani ba"
Hindu tace "A'a wallahi tana da kirki, niba abunda tamin da zan zageta, kije kiyi ke kaɗai, Allah ya yaye miki wahala, dan tabbas yana da wannan matar babu abunda ze dake"
Yau kam Widad ta ɗan rage yiwa Widad rashin kunya, dan tare suka ci Abinci saboda tana son ya dinga koya mata aikin gida, dan tana jin zafin gorin da'ake mata, wai bata iya komai ba.
Bayan sallar la'asar Widad ta fito daga ɗakinsu, dama gyara ɗakin baya mata wahala da gyara gado duk wannan ta iya.
Hari ta hanga a inuwar bishiya tana saƙa mafici, Widad ta ɗakko kujera ta zauna a kusa da ita tace "Uwata ta kaina"
Hari ta harareta tace "Allah ya kiyaye in haifi 'ya irin ki, na haifi fitinanniya kamarki ai se ince ko sa kamun hannu akayi"
Murmushi Widad tayi tace "ba wannan ba, ɗan koyamin wannan abun da kike yi mana, idan na iya se in dinga ta yaki"
"Lallai nasan ba iyawa zakiyi ba"
Widad tace "Allah zan iya"
Hari tace "Keɗin ce zaki iya, taɓ"
Widad tace "ni zaki wulaƙanta dan zaki koyamin abu? Shikenan"
Hansai tace "Amarya ba wahala, nima na iya zan koya miki"
Widad tace "Yawwa ummu Sani, thank you very much, May Allah subhanahu wata'ala bless and unite your Family"
Hari tace "kekam wudas akwaiki da tsirfa, meye hakan kuma kika faɗa? Ke ba zaki iya magana ba sekinyi yaren Yahudawa, kiyi ta zagin mutane"
Widad tace "aini kona rasa abun zagi, bazan zageki ba"
Hindu tace "Nidai dan Allah amarya ki koyamin turanci, ina son inga na iya"
Widad tace "Shikenan, zan koya miki insha Allah, amma nima zaki dinga koyamin abunda ban iya ba"
Hindu tace "duk abunda kika ce zan koya miki"
Gwaggo na gefe tana jinsu, tana murmushi, sam Widad bata da girman kai idan bata iya abuba, zata yi ta magiya a koya mata.
Da Yamma aka kawo manyan Ayaba daga gonar megari, aka raba aka bawa kowa, Widad se murna take dan tana son Ayaba, ajiyewa taje tayi a ɗaki tace, se Yusuf yazo zasu raba.
Yau Yusuf se gefin magariba ya dawo gidan, ya gaji sosai.
Tunda ya samu ya watsa ruwa ya dawo ɗaki ya kwanta, salla ma a gida yayi.
Widad tace "Yoseef ga Banana, an bamu daga gonar megari aka cirota, nace in ka dawo semu raba dan idan na fara ci, bazan iya rage maka ba"
Murmushi yayi yace "bani guda ɗaya kawai ta isa, kici Abunki"
Ta ɗan ɓata fuska tace "saboda me bakaci? In ajiye maka abu kace ba zaka ci ba"
"i don't have appetite, that's why"
Ta kalle shi tace "kamar yaya?"
Rungume ta yayi a jikinsa, ya kwantar da kansa a kafaɗarta yayi shiru.
Widad ta kalle shi da sauri tace "Subhanallah, ai baka da lafiya jikinka yayi zafi sosai fa"
Yusuf yace "karki damu zan warke insha Allah"
Yana nan rungume da ita, yana ta juya kansa a jikin ta, tana jin yadda jikinsa yake tsuma jikinsa na ƙara ɗaukar zafi.
Widad cike da damuwa