Showing 57001 words to 60000 words out of 135096 words
to kidnapped her?"
Kamar Nurat zatayi kuka tace "bafa laifi na bane, Daddy ne"
Yusuf ya ɗan ƙara matsowa yace "Amma me tayi wa Daddy haka da zesa a saceta?" yai maganar yana kallon idon Nurat, Yarinya ce dan haka yake binta a sannu cikin hikima
Ɗan shiru tayi sannan tace "Nifa ban sani ba"
"Haba me sunan manya, Haske maganin duhu, baki kama da maƙaryata ba, ni ya akayi ma kika san Widad har kuke hulɗa bayan bata son mutane?"
"Nifa ba wani hulɗa mukeyi sosai ba, da tun ina ƙarama, gidan su na U. K yana kusa da namu daga baya suka dawo Nigeria shine... Sekuma tayi shiru tana satar kallon Yusuf.
"Shine me? "
"Dad ɗina sunyi faɗa da Daddynta akan Siyasa, shikenan abunda nasani, Amma dan Allah karka gayamata Daddy nane yasa ayi kidnapping ɗinta idan ta sani, zata sa a kai Daddy na prison ne"
"bazan gaya mata ba, ai kin gayamin gaskiya, amma naga Daddynta ɗan kasuwa ne ba Siyasa ba me zesa suyi faɗa da Daddynki akan siyasa"
"to ainima bakomai na sani ba, muna yara lokacin Amma tabbas sunyi faɗa ne shine yake son ya rama akan Widad, amma ni ban san me yake so yayi mata ba"
Yusuf yace "shikenan nagane, gaskiya you are so kind dear, Insha Allah bazan bari taji ba, Amma dan Allah karki bari a cutar da ita, kinga marainiya ce ita abun tausayi, ke kina da Mum da Dad ɗinki ita kuma she's orphan"
Jinjina masa kai kawai tayi.
Yusuf yace "Bani wayarki in sami ki lambata, se mudinga gaisawa ni daga yau nayi ƙawa, ni zan maye miki gurbin ƙawancen ki da Widad"
Kallon sa tayi ta ɗanyi murmushi yadda yake magana ya burgeta, bashi da hayaniya, ya iya tsara magana daki daki, se yanzu ta gane ranar da yayi mata wannan barazanar ne ya koma kamar wani mugu amma ba haka yake ba, ta miƙa masa wayar sannan tace
"Amma ni ban sanka a Family ɗinsu ba, waye kai a gurin ta?"
Yusuf yayi murmushi yace
"i don't belong to her family, but a very important person attached to her destiny"
Kallon sa tayi cike da rashin fahimta za tayi magana ya kashe mata ido ɗaya, gaba ɗaya seta sunkuyar da kai ta kasa maganar, ya daɗe yana daddana wayarta, ita kuma ta kasa cewa komai.
Seda ya gama abunda yake sannan ya miƙo mata wayar yace
"Nagode sosai ƙawata, Allah ya bar zumunci, ni zan koma naji daɗin kasancewa dake da wannan hirar da mukayi"
Murmushi tayi tareda sunkuyar da kai tace "baka gayamin sunan ka bafa"
"Sunana Abokin Nurat, Just call me Aboki or any name you like, good night Nur"
Ya ƙarasa maganar tare da nufar hanyar fita yana addu'a Allah ya shiga lamarin sa akan wannan aiki me hatsarin gaske da yake yi, yasa hanyar da ya ɗakko ta zama mafita ga al'amuran.
Yayinda Nurat ta rakashi da ido har ya fice
Nurat tana komawa cikin gida Maman ta tace
"Ke lafiya kuwa? Waye wannan yazo kika daɗe haka?"
"Abokina ne yazo muka gaisa" tai maganar cike da basarwa ta shige ɗakin ta tana tunanin Yusuf
(Masha Allah, daga wannan posting bana tunanin zan kuma wani posting se Allah ya kaimu ranar Asabar insha Allah, gobe in Allah ya yadda zan fara jarrabawar ƙarshe ta makaranta, ku sani a addu'oinku please 🙏 🙏 🙏
Dana kammala exams insha Allah zanyi ƙoƙari ku dinga samun update akan lokaci, comments ɗinku zesa kudinga samun update kullum, idan kun shirya yanzu aka fara wasan, ba'a fara komai ba thank you for being with me 😍 😍 😍)
Domin gyara sharhi ko shawara, feel free to contact me
Ayshercool
07063065680
_*AƘIDA TA*_
PERFECT WRITERS ASSOCIATION
(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)
https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
P. W. A
*Story and written by*
_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_
The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *
I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum
https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=in
PART1
Page 14
ELEGANT ONLINE WRITER'S
Sosai Yusuf yake ƙara samun haske akan lamarin binciken da yake yi, Sam babu specific lokacin da Widad take bawa Yusuf albashi, duk lokacin da ta bushi Iska sedai yaga alert ɗin kuɗi, kuma kuɗi masu yawa, sannan be isa yayi magana ba.
Yana ta tattara bayananan daze gabatar a gurin aiki na sakamakon binciken da yake yi.
Tunda Yusuf ya tafi Nurat take tunanin, ko ta gayawa Mahaifiyarta yadda suka yi da Yusuf, wata zuciyar ta gargaɗe ta akan hakan.
********************************
Gaba ɗaya Widad ta takura kanta, sam ko Babban falo bata fitowa, tana iya sashin ta daga ita se magenta, duk da haka Yusuf kullum se yaje koda baze ganta ba kuwa.
Lambar wani abokinsa likita ya dubo a wayarsa ya kirashi, se da ta kusa katsewa sannan ya ɗauka.
"Yusuf kana da kirki kuwa? Ace ka ɓata ko neman mutane baka yi?"
Yusuf yace "Amma ka tsaya mu fara gaisawa, sarkin ƙorafi"
Nan suka gaisa suka taɓa hirar yaushe rabo, sannan Yusuf yace "dama doctor Hamza ina da wata 'yar tambaya ne, dukda nasan tambayar da zan maka ba a fannin daka karanta kenan ba, amma na sanka da shige shige"
Hamza yace "shikenan ina jinka, Allah yasa nasan amsar tambayar taka, in babu amsar ma se'a nemo"
'Masha Allah, dan Allah Hamza wace irin larurar ƙwaƙwalwa ce take sa mutum ya dinga gudun mutane? "
Doctor Hamza yace
"Anthropophobia kenan, is a mental disorder, masu irin wannan larurar suna jin tsoron taron mutane, idan abun ya tsananta ma ko ahalinsu basa son su raɓe su, sedai wasu tsirari daga mutane, basu fiye son taron jama'a ba, ko shiga cikin mutane basa so"
Yusuf yayi ajiyar zuciya yace "to me yake haddasa ciwon"
Hamza yace "eh to, abun da yake haddassa wannan larurar ga wasu, idan an taɓa cin amanarsu, mussaman wanda suka yadda da shi, ko kuma wani abu da ya taɓa faruwa dasu mara daɗi a rayuwarsu, wasu kuma hormones ne suke haddasa musu excessive fear ya danganta dai, zakaga wataran suna lafiya ƙalau ga wanda ciwon be tsananta a gare su ba, amma idan ya tashi zaka ga basa son haɗa ido da mutane, basa son suga ana kallonsu, kosu kasa bacci, ko yawan ciwon kai, bugun zuciyar su ya canza, wasu numfashinsu har ɗaukewa yake, ko su dinga karkarwa in sunga baƙo, ko wanda basu yadda dashi ba, ko kuma su dinga wrong perception akan abubuwa, ko su dinga ganin duk wanda ya raɓesu ze cutar da sune"
"Ok magana, nagode sosai Hamza amma meye maganin ciwon?"
"gaskiya babu wani sahihin maganin ciwon gaskiya, rehabilitation ne a dinga kwantar musu da hankali tare da ƙoƙarin canza musu tunani daga mummuna zuwa kyakkyawa, dan wasu in damuwar tayi musu yawa suna fara shaye2, ko dinga wasu tunani wanda ya saɓa da abunda yake a zahiri, ayi ƙoƙarin samar da wani abu daze dinga ɗebe musu kewa, koya ɗauke musu hankali daga damuwarsu, in kaga an basu magani mafi akasari sedai a basu magani akan sauran matsala, kamar bugun zuciyar, ko daidaituwar hormones ɗin ko makamancin hakan...
Shiru Yusuf yayi yana tunani, meye alaƙar ƙwayar daya gani a ƙasan kofin shayin da za'a bawa Widad da ciwon nata, Doctor Hamza Yana cikin yiwa Yusuf bayanin ne ya hango Widad ta fito, tana nufo inda yake zaune, gaba ɗaya fuskarta a haɗe kamar kullum, yauma shigar tata da ta saba ita tayi, jikin nan a tsuke a cikin ƙananan kaya.
Da sauri Yusuf yace "shikenan nagode sosai doctor, nagane Allah ya saka da alkhairi" ya katse wayar
Ya shiga wani tunanin, "to wace irin Allura akewa Widad haka? Amal tace masa ana mata wata Allura, ga kuma abunda likita yace"
Ta ƙaraso ta kalle shi a yamutse tace
"ɗakko mota, zamu airport ne yanzu"
Ya kalle ta yace
"me zamuje yi a Airport?"
"ban sani ba" ta bashi amsa
Ƙasa yai da idonsa yayi mata wani irin kallo sannan ya miƙe yai gaba, gaba ɗaya kasa gane kalar kallon tayi meya ke nufi da haka?
Ya ɗakko mota ya kunna suka fara tafiya, suna tafiya yana satar kallonta yana tunanin, me zeyi wa Widad wanda ze temaka gurin canza tunanin ta mara kyau zuwa me kyau, kamar yadda doctor Hamza ya gaya masa.
Yana cikin tunanin wayarsa ta fara ringing, sedai lambar ba suna, kuma yana tsoron ya ɗaga yaje a cikin abokan aikinsa ne, wani yayi masa kwaɓa, sekuma ya tuna halinta, yanzu yana ƙin ɗaga wayar zata masa wata fassarar, haka ya basar ya ɗaga wayar yasa a kunnen sa tare da yin sallama.
Siririyar muryar mace ce ta amsa tace
"Aboki ya kake?" se yanzu ya gane muryar Nurat, murmushi yayi yace "lafiya ƙalau, light ya kike?"
Wani murmushi ne ya suɓuce mata tace "lafiya ƙalau friend, dama cewa nayi bari in kiraka mu gaisa"
"Amma gaskiya kin kyauta Light, ina fatan kina lafiya ba kya cikin kowace irin damuwa? Kin san damuwa da yawan haɗe rai yana sa mutum ɓacin rai da saurin tsufa, kuma duk kyansa ya koma kamar wani abun tsoro"
Da sauri Widad ta juyo ta kalle shi, amma ya basar ya cigaba da wayar, yayin da Nurat tayi murmushi tace "Ni lafiya ƙalau nake, bani da wata damuwa ko matsala ina Widad?"
"tana gidansu, ko ince kina gaishe ta ne?"
Kamar Yusuf yana ganinta ta girgiza kai tace "Kamanta kace kar in gaya mata muna abota? Na tambayane kawai dan inji ko tana lafiya"
"Eh kuma fa hakane? Amma yaushe zakizo ki ganta?"
"Ai ban san wane irin kallo za tayi min ba idan nazo gidansu, inajin tsoror"
Tsaki Widad tayi ba tare da ta kalli Yusuf ba tace
"Malam ka isheni, ka cikamin kunne"
Murmushi Yusuf yayi yace
"light, se anjima Madam tace na cika mata kunne"
Jiki a sanyaye Nurat tace "Madam kuma? Dama kana da Aurene?"
Yusuf yace "Babba dani kice bani da Aure, ina da Aure mana muna tare da ita ma, munɗan fita ne, se anjima kar in sake ɓata mata rai"
Wani irin wulaƙantaccen kallo Widad tayi masa, dama yasan a rina
"ni kake cewa matarka? Baka da hankaline, ni ka kalleni ka cemin matarka"
"waye cemiki dake nake ne? Am just kidding idan ba haka nayi mata ba zata ga kamar na mata wulaƙanci ne, kuma babu daɗi ka Wulaƙanta mutum it hurts a lot, Yusuf baya Wulaƙanta mutane"
Wani tsakin ta kuma ja ta ɗauke kanta, yayin da shi kuma yayi murmushi, a ransa yace 'Insha Allah, sena canza miki dukkanin wannan gurɓatattun tunanin naki kafin in kammala bincike na"
Gurin wani restaurant sukabi, tace masa ya tsaya ai kuwa yayi parking, tana yi tana duba agogon hannunta, ta buɗe motar ta fita, shima ya fito yabi bayanta.
Cikin restaurant ɗin ta shiga ta samu guri ta zauna, Yusuf be jira unarninta ba shima yaja kujera ya zauna.
Aka kawo musu menu
(jadawalin Abincin da suke available)
Ta karɓa tana jujjuya menu ɗin, ɗan ɓata fuska tayi ta zaɓi Abunda take so,
Aka bawa Yusuf ma, ya kalli Menu ɗin ya girgiza kai yace
"Ni ban iya cin irin wannan Abincin ba gaskiya, Umma ta cika min ciki da ɗumamen tuwo dan haka ni ba abunda zanci"
Kallonsa tayi ta ɗauke kanta, yayin da waiter ɗin tayi murmushi ta karɓi menu ɗin ta tafi.
Karon Farko da Yusuf yaga Widad tana cin normal Abinci, sam bata damu da Abinci ba, sedai yaga tana 'yan ciye ciye, ta yaya mutum zeyi lafiya ba tare da cin cikakken Abincin da ze gina masa jiki ba, ko duk cikin rashin yardar ne oho mata.
Yanzun ma ba wani cin Abincin take ba, ɗan cakala take a jikin spoon, kamar wata ƙaramar Yarinya kamar me wasa da Abincin tana kaiwa bakin ta .
Yusuf ya ɗan ƙura mata ido yace "Madam are you really Hungry?"
Cigaba da cakalar Abincin ta tayi ba tare da ta kula shi ba.
Ko ɗaya bisa ukun Abincin bata ci ba, ko naman kai bata taɓa ba, ta ture Abincin ta ɗau tissue tana goge bakin ta, 'Iko se Allah, Abincin naira dubu huɗu akayi wa wannan cakalar aka barshi, wani yana nan yana fama da Yunwa'
"wai Harkin ƙoshi?"
"wai ina ruwanka dani ne? Ta yaya zan iya cinye wannan Abincin duka?"
"Amma kin san bazaki iya cinyewa ba kika sa aka kawo miki? Akwai dubban marasa ƙarfi da Abincin naira ɗari ma gagarar su yake a rana, kalli uban Abincin da kika bari, wataƙila yanzu wannan da kika rage sedai a zubar, ba kyau Wulaƙanta Abinci, wataran kema ze iya Wulaƙanta ki"
Ko kallonsa ba tayi ba, ta ɗauke kanta tana kallon wani gurin, amma tayi shiru tana saurarensa, gefe guda kuma ta shiga tunanin maganar sa, dagaske akwai wanda suke rasa Abincin naira ɗari ya gagare su? To wani irin Abinci ma mutum zeci da naira ɗari, se a samu mutum yace bashi da naira ɗari?.
Yusuf Yaja plate ɗin Abincin gabansa ya ɗau spoon ya fara cin Abincin da Widad ta rage.
Kallon Yusuf take, sosai mamaki yake bata shi sam be ɗau komai da zafi ba, Abincin data rage yake ci, ko dan dai shi talaka ne oho.
Yusuf ba ƙaramin mamaki yake ba yadda take ɗaga masa ƙafa, dan shi kansa yasan wasu lokutan yana wuce gona da iri, tana ƙyaleshi ne kawai
"ya naga kina kallona ko nayi wani abun ne na rashin yadda?"
Ɗauke idonta tayi daga kallonsa zuwa wani gurin daban.
Yusuf ya ciko spoon yace
"Kinga yadda ake cin Abinci a ciko cokali da Abinci, se mutum ya ƙoshi ba yadda kike yi ba, kamar kina wasan yara, koda yake yarinyar ce ai"
Ɗago ido tayi ta kalle shi, amma ya cigaba da cin Abincin yaƙi kallonta, lallai Yusuf ya samu dama a kanta ya fara rainata, tunda harya samu damar gaya mata maganganun da yaga dama, ita kanta Widad tana mamakin yadda take ƙyale Yusuf, ba yadda za tayi dashi wata ƙaddara me ƙarfi ta shigo dashi cikin rayuwarta, wanda ko dan albarkacin hakan yaci ta dinga ɗaga masa.
Seda ya kammala sannan ta ajiye masa ATM ɗinta, ta miƙe ta nufi hanyar fita, Yusuf kuma ya nufi gurin biyan kuɗin, kafin Widad ta kai ga ƙofar fita wani mutum da tunda suka shigo yake kallonta yabi bayanta.
Yusuf yace "ashe akwai mini Drama yau"
Ya biya kuɗin ya fito, sedai yana fitowa ya tarar tana zazzagawa Mutumin masifa.
"Kalle ka ni zaka biyo kace in baka lambata? Bazan bayar ba shashsasha an gaya maka kowa sakaraine irin ka?"
"Ni kike cewa sakarai?"
"Na gaya maka ko akwai abunda zaka iya ne?"
Yusuf ya ƙaraso da sauri gurin yace "haba bawan Allah, ya zaka biyo matar Aure kace kana so?"
Mutumin ya kalli Yusuf yace "Matar Aure kuma? Da wannan shigar tata?"
"koma wace irin shiga ce tayi ina ruwan ka? Haka muka tsara rayuwar Aurenmu, haka muka ga damar yi, idan har kasan shigar da tayi bata dace ba meye na biyo ta? Kana gurin nan muka zo tare mu kaci Abinci, danme zaka biyo ta kace kana so?"
Mutumin yace "Amma indai wannan matarka ce gaskiya kayi dacen Auren kyakykyawar mace, sedai bata da ɗa'a kuma bata san darajar Auren ta ba"
"bakomai a haka nake son a bata, sannan karka kuma gangancin kiran ta da wasu miyagun kalamai, ka gode Allah da ban ɗau mummunan mataki akanka ba"
Ya juya ya kalli Widad da mamaki ya hana ta magana, A fusace ta juya ta tafi mota ba tare da tace komai ba
Yusuf ya juya ya koma motar shima yana shiga ya zauna, ya kunna motar suka fara tafiya, ba tace komai ba se tafasa da zuciyar ta take yi
Ba zato ba tsammani, Widad ta Ƙanƙance ido tace
"i thinks you drunk something abusive today, kasan me ka faɗa kuwa? Which type of Weed did you take today? Wane irin rashin hankali ka aikata? Meye hakan kake ne dan me zaka dinga danganta kanka dani a matsayin mijina, kai ko Auren zanyi zan auri talakan mutum kamar Kane?"
Dukda yadda kalaman Widad suka daki zuciyar Sa haka ya daure, yayi parking ɗin motarsa, ya matsa Kusa da ita ya matsa yace "Abunda kika ci dai shi naci, dukda baki san meye So ba, ƙarewa ma kince baki yadda dashi ba, amma the magic behind Love is that, ba ruwan sa da talaka kome kuɗi, sannan wannan abunda nayi shine kaɗai mafita daze hana kowane kare da biri binki, da kuma ƙarewa surar jikin ki kallo, please Dress decently to avoid such type of people, dukda ina matsayin me miki aiki, aikin ma na direba, I have to tell you something, you have an attractive beauty Widad, stop exposing it anyhow yana taɓa zuciyata a duk lokacin da kika fito da wannan shigar naga wasu na ƙarewa wannan kyakykyawar halittar kallo, your beauty suppose to be only for your husband, duk wata mace me tsadace jikinta ma me tsada ne meyasa zaki dinga bari ana ganin naki?"
Ɗaga ido tayi tana kallon sa, gaba ɗaya Yusuf ya rufe mata baki, ya kulle mata kai, gaba ɗaya ta nemi izzar da jin kan da zata masa wulaƙanci ta rasa, yau wani irin kwarjini yayi mata data kasa cewa komai, shi kuma ya samu damar hakan yake ta abunda yaga dama, a baya zata iya rantsewa baze aikata haka ba, ganin yadda ko magana baya son yi.
Haka suka cigaba da tafiya kamar kurame, kowa da abunda yake saƙawa a zuciyar sa, gaba ɗaya tunanin rashin mutuncin da zata yi wa Yusuf take.
Har suka ƙarasa airport bata iya cewa komai ba, parking yayi amma bata buɗe murfin motar ta fita ba, shima zaman sa yayi yaƙi fita, ya sauke glasan suka cigaba da zama, lokaci2 ta dinga duba agogon hannun ta.
Buɗe ƙofar tayi ta fita, shima ya buɗe ya fito, Alhaji Nasir ne yake tahowa da brief