Showing 30001 words to 33000 words out of 135096 words

Chapter 11 - Akidata Book 1 Hausa Novel Complete

01 Jan 2025

741

zuciya? Tabbas babu inda wannan Auden zeje, gara ma karka fara"

"Babu ruwan ki, Insha Allah zasu zauna lafiya"

Miƙewa tayi tsaye tace  "Ai se ayi in gani, ni na haifi abuna ba wani ya haifar min ba, bame Aura masa Mahaukaciya mara tarbiyya"

Ta ɗau jakarta ta bar gurin tana ƙunƙuni.

Yusuf ne zaune ya zubawa sarautar Allah ido, Widad ce take zaga dabbobin gidan, wanda mafi Akasari karnuka ne da maguna se tsuntsaye, Abunda ya bashi mamaki shine yadda tasa aka fito mata da wani jibgegen ingarmar doki, aka ɗaura masa linzami, ta ajiye Wayarta ta da 'yar ƙaramar Jakarta, ba tare da an taimaka mata ba ta haye kan dokin nan.

Kasancewar harabar gidan ƙatuwa ce sosai, hakan yabawa Widad damar yin sukuwa akan dokin nan yadda take so, ba ƙaramin ɗaurewa Yusuf kai tayi ba, yadda take sukuwa akan dokin tana sarrafa akalar sa yadda take so, ze tabattar maka ta saba hawan dokin, kuma ga dukkan Alamu hakan yana bata Nishaɗi.

Seda tayi me isar ta sannan taci birki ta sauka daga kan dokin, ta shiga cikin gidan.
Yusuf yana nan zaune ɗaya daga cikin ma'aikatan gidan wanda Aƙalla ze shakara talatin da wani abun ya ƙaraso inda Yusuf yake zaune shima ya zauna kusa dashi.
Ya miƙawa Yusuf hannu suka gaisa, ya kalli Yusuf yace
"ɗan Samari daga wani gari kake ne?"
Yusuf  ya ɗan ƙura masa ido Sannan yace  "Kano"
Mutumin Yayi Murmushi yace  "Ashema ɗan garin nan ne kai, a wace unguwa kake?"
Yusuf yace  "Me yasa kake tambaya ta ne?"

"Ahh karka damu kawai dai na tambaya ne, Amma idan ba zaka damu ba, dan Allah wani irin aiki kakewa Madam haka da take yawo da kai ko ina? A iya sanina da ita tun shekarun baya bata sake wa da mutane haka, Amma kai gashi tana yawo da kai ko ina"

Yusuf yayi Murmushi yace
"Ita yakamata ta baka wannan Amsar bani ba"

Suna cikin maganar ne Widad ta fito sanye da wasu kayan daban.
Ƙure Yusuf da Saleh tayi ido, tana musu kallo irin na tuhuma, ba tace komai ba ta nufi inda Motar su take, Ma'aikatan gidan suka biyo ta suna mata kirari suna Allah ya kiyaye, bata kula kowa a cikin su ba ta hau motar Yusuf ya ja suka bar gidan.

Suna cikin tafiya yaji tace 
"Me Sale yace maka?"

"Waye Sale?" Yusuf ya tambaye ta, shiru tayi masa tsawon wasu daƙiƙu sannan cikin maganar ta ta isa, tace 
"Kana jin daɗin rainamin hankali a lokuta da yawa, na kan ƙyaleka ne saboda ina jin nauyin hukunta ka a lokuta da yawa, saboda hatsarin da rayuwar ka ke ciki Kasancewar ka tare dani, Amma hakan baze hanani koya maka hankali idan ka saɓawa Yarjejeniyar mu ba, na tambaye ka ɗazu da Safe baka bani haƙiƙanin Amsar tambaya ta ba, ka rainamin hankali, yanzu ma na tambaye ka kana sake tambaya ta, wannan abubuwan da kake kana jawowa kanka zargi ne a gurina, karo na biyu Me Sale yace maka? "

Murmushi Yusuf yayi yace
"Ya tambaye ni Sunana ne, da kuma aikin danake miki, na gaya masa sunana, Amma aikin da nake miki nace ya tambaye ki"

Jinjina kai tayi tace  "Amma kamar na gaya maka duk inda muka je, ba zakayi magana da kowa ba se idan ni nayi maka izinin yin hakan"

Juyowa yayi ya kalli Widad, Yarinya ƙarama se izza da jin kai.

Yusuf ya ɗan rausayar da kai yace
"Allah ya baki yawan rai ya kare ki daga sharrin maƙiyanki, banyi hakan da saɓa dokarki ba, sedai idan nayi hakan mutane zasu ga tamkar wulaƙanci ne, nasan tsoron ki kar a haɗa kai dani a cutar dake, Amma ina tabbatar miki da cewa bazaki taɓa samuna da cin amanar ki ba"

Ba tare da ta kalle shi ba tace
"Zan gani ai"

Sunyi shiru na wani lokaci, can ta jinjina kai tace 
"Lallai Sale, kar nake kallon sa, yana son ganin bayana saboda abunda nayiwa ɗan uwan sa, duk randa na kama shi red handed wallahi se yaje inda ɗan uwansa yaje, babu Amfani zama da maƙaryaci me cin Amana"

Yusuf ya juya yana kallon ta, yana tunanin randa ta gano waye shi, wane irin mataki zata ɗauka akan sa?

****************************
A kwana a tashi Yusuf yayi wata guda cif yanawa Widad aiki, kullum cikin hantarar sa take da wulaƙanci amma sam seya nuna mata ko a jikin sa, duk abunda yayi baze burgeta ba, yayin da Amal keta ƙara tura kai a gurin Yusuf, dan ita nan duniya babu wanda yayi mata kamar shi tana matuƙar ƙaunar Yusuf saboda nutsuwar sa, Yusuf yana ta ganin Abubuwa na ban mamaki a game da uwar ɗakin sa yayin da gefe guda ya kasa gane bakin zare al'amuran gidan nan, gaba ɗaya yanayin yadda mutanen gidan ke gudanar da mu'amalarsa da ban mamaki dan kowa da inda yasa gaba kuma kowa akwai wani boyayyen abu da yake ɓoyewa a ransa.
Har wata ya cika, aka shiga wani watan Widad bata biya Yusuf haƙƙin sa ba, shi kuma bece mata komai ba, sannan duk lokacin da ta buƙaci zuwa wani guri, zeje ya kaita ba tare da ɓata lokaci ba.

Isa me gadi yana ta ƙoƙarin bugun cikin Yusuf yaji wani abu game da shi amma Yusuf yaƙi gaya masa komai.

Gaba ɗaya ma'aikatan gidan suka tsangwami Yusuf suna ganin ana fifita shi akan su.
Shikam ko a jikin sa, shima ya dena shiga harkar su, har gara Murtalah me kuka da shuke shuken gidan suna hira da Yusuf wasu lokutan.

Hajiya Halima na zaune a falo tana aiki a System, gefen ta kuma Amal ce ke cin Abinci, mai aiki ta fito daga sashin Widad, ta durƙusa a gaban Mummy tace
"Hajiya, Anty Widad fa tun jiya ɗakin ta a rufe, na ƙwanƙwasa taƙi buɗewa, tun jiya da safe naje in gyara mata amma ɗakin a rufe"
Tsaki Hajiya Halima tayi tace  "To ina ruwana, yarinya ce ita ƙarama da zan dinga binta, in taji yunwa zata kashe ta ta fito"

Amal tace  "Mummy kina tunanin Yunwa zata saka ta fito ne? In baki wasa ba sedai kiga gawar ta kin san halin ta, idan ta mutu da wani kalamai zaki ƙwaci kanki a gurin me gidan nan? Bama ke kaɗai ba dukkan mu, sannan Burinmu baze cika ba, ƙarshe ma dukkanmu sedai mu mutu a prison"

Ɗan zaro ido Mummy tayi tace  "Kuma fa hakane, tashi muje mu gani"

Suka nufi part ɗin Widad, Amma suka tarar ta rufe bedroom ɗinta, suka yi bugun duniya taƙi ta buɗe.

Rasa abunyi suka yi, suka kira Alhaji Bulama suka sanar masa da abunda ke faruwa, da kiran wayar tasa beyi mintuna Arba'in ba se gashi.

Yaje ya tarar dasu sunyi cirko cirko a ƙofar ɗakin Widad, ya taka yaje gaban ƙofar ya fara ƙwanƙwasawa
"Lovely daughter, Dad ɗinki ne, ki buɗe ƙofa kinji, karkiwa kanki illa"
Still Widad ba tayi responding ba, dan ko motsin ta basaji.

Alhaji Bulama yace 
"Kuma babu wani abu daya haɗaku da ita? Kowani saɓani ko ayi mata wani abun?"

Ramlah tace "waze nata wani abu kuwa? Ita wannan se an mata wani abu? Ai sedai tayi wa wanima,wataƙila haukan nata ne ya motsa"

Alhaji Bulama yace "ku bani mukullin ɗakin ta, a buɗe ɗakin karta"

Mummy tace  "taɓ wake da mukullin ɗakin basarakiya, ita da bata yadda da kowa ba, wa zata bari ya mallaki mukullin ɗakin ta ba wanda yake da mukullin ta"

Alhaji Bulama yace  "to ko maza za'a kirawo su ɓalla ƙofar a gani"

Ramlah tace  "A'a karka jamana Jaraba, a ɓalla mata ƙofa ka samu a tashin hankali da masifarta, a kira Baban ta aji meze ce"

Alhaji Bulama yace  "Keba babanki bane Ramlah"?

Cikin tsiwa Ramlah tace  "Niba baba na bane, kullum bata da gori seba gidan ubanmu bane, dan haka ubanta ita ya haifa bani ba"

Yau Yusuf ya makara dan se sha ɗaya ya tashi na safe, tunda ya koma bacci ƙarfe takwas na safe, dan haka a gurguje ya kintsa ya fito, yayi sa'a Umma bata nan ta fita, dan haka ya kulle gidan ya fita, ya nufi gidan su Widad.

Yana zuwa suka gaisa dasu Nura sama sama,suna masa wani kallon banza

Yusuf ya kalli Murtalah yace "Murtalah Madam ta fito kuwa? Ko tazo nema na naga yau na makara sosai"

Murtalah yace  "ina fa, tana can tun jiya taƙi buɗe ƙofa, ana can anata fama da ita, ba wanda yasan tana raye kota mutu, gashi babu wanda yake da mukullin ƙofar ta, ana tunanin ko ɓalla ƙofar za'ayi

Zaro Ido Yusuf yayi ba tare da yace komai ba, ya tashi da sauri ba tare da tunani komai ba ya tun kari cikin gidan.

Isa ya taɓe baji yace "kalli uban shisshigi, Allah yasa yana zuwa su Wulaƙanta shi su koro shi, banza me rawar kai kawai"

Murtalah yace  "Haba Isa, ka sawa Yusuf ido da yawa wallahi, gashi kullum ƙara samun matsayi yake a gidan nan fiye da kai"

"dalla rabu dani, se kace baka ganin yadda aka fifita shi akanmu a gidan nan, danma mun samu mu Hajiya tana bayan mu, duk yadda muka so samun gindin zama a gurin yarinyar nan muka kasa, Amma shi daga zuwan sa ga yadda ya samu sake yake wani zaƙewa kamar gidan ubansa"

Yusuf kuwa na shiga Babban falo ya gansu a zazzaune suna tattaunawa, Ya durƙusa ya gaishe su.

Alhaji Bulama ne kawai ya amsa, se Amal da tace "Sannu da zuwa"

Hajiya Halima tace  "To Munafuki me ka shigo yi uban iya"

Yusuf yace "Naji ance Madam bata fito daga ɗaki ba yau kwana biyu shine nace.....

Cikin hantara Ramla tace "shine me, mezaka iya? Bama son munafunci malam jeka mungode, Anjima baban ta ze dawo, yasan yadda zeyi da ita uban shishshigi"

Yusuf yace "Amma be kamata a barta har se ya dawo ba, babu wanda yasan halin da take ciki, ta rufe kanta a cikin ɗaki yakamata a duba halin da take ciki"

Hajiya Halima tace  "kai bana son rawar kai irin naku na matsiyata, ka fimu sanin abunda ya dace ne? Dalla ɓacemin daga nan"

Alhaji Bulama yace  "A'a Hajiya Halima, kika san Alaƙar dake tsakanin su?, ki ƙyale shi ya Jarraba mana wataƙila kiga ta buɗe ƙofar, kaga tashi kaje ko zata buɗe"

Yusuf ya miƙe ya nufi hanyar ɗakin ta.

Yana zuwa ƙofar ɗakin ba tare da ɓata lokaci ba, yasa hannu a aljihunsa ya ɗakko mukullayen motocin ta dake gurin sa, ya saka key ya buɗe ɗakin nata, da yake yasan mukullin ƙofarta ta falo da ta bedroom tunda tana aiko shi ɗakin.

"Innalillahi wa inna ialaihi raji'un!!!"

Shine abunda Yusuf ya faɗa



In an karanta ayi share please 🙏


07063065680
Ayshercool

_*AƘIDA TA*_


PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

P. W. A


*Story and written by*

_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_

The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *

I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum

https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=in


                          PART1
                                Page 9




_Asslam Alaikum warahmatullah_da _fari dai zanyi wata magana_ _tun page ɗin farko nayi bayani_, _nace ina da Jarrabawar ƙarshe_, _ina ƙoƙarin cika Alƙawari ne yasa na cigaba da kawo_ _littafin nan ɗaya ga watan October_ _nace bazan samu yin posting kullum ba_ _amma ina iya ƙoƙarina inga nayi duk dan faranta muku_ _amma wasu na ƙorafi hadda gayamin baƙar magana_  _dan bana posting kullum_  _littafin nan dai nina sa kaina_  _kuma nace free ne balle ace siya akayi nake jan rai_ _babu wanda nayiwa dole seya karanta_ kuma ban karɓi kuɗin kowa ba, _ni nake saka data in ɓata lokacina inyi typing sannan inyi posting_  _dan haka wanda baze iya haƙuri ba ze iya dena karantawa_ ba zanyi _typing kullum ba tunda ba siyarwa nayi be_
_Ni bana Wulaƙanta kowa nasan soyayya ce tasa ake karanta littafina

_
_Masoya har kullum ina sake godiya da Comments ɗinku da Addu'oinku_ _zancigaba da ƙoƙarin faranta muku Insha Allah_







Widad ya hango zaune acan ƙarshen gado kamar Mahaukaciya tuburan, rigar jikin ta iya cinyar ta, gaba ɗaya gashin kanta a hargitse, ta sunkuyar da kanta jikin ta se rawa yake tana kuka, ta rufe ko ina babu haske a ɗakin, seda ya buɗe ɗakin sannan haske ya bayyana a ɗakin.

Babban abunda ya bawa mutan gidan mamaki be wuce yadda akayi Yusuf ya mallaki mukullayen ɗakin Widad ba, alhalin su raɓar ɗakin nata ma basu isa suyi ba, balle samun mukullayen.

Da sauri ya ƙarasa gaban gadon ta yana ambaton Subhanallah,tana  ɗagowa taga Yusuf ta gigice ta fara ja da baya tana girgiza kai.

Yusuf yace  "Meya sameki haka? Ki kwantar da hankalin ki, Yusuf ne direban ki fa"

Girgiza masa kai tayi tana kuka tace  "Ni karka kasheni"

"No ba kashe ki zanyi ba"

Ɗaga kai tayi ta kalli su Alhaji Bulama dake tsaye suna kallon su, riƙo rigar Yusuf tayi kamar zata yagata tace  "Suwaye wannan? kace su fita bana son ganin su, kace su fita su bar nan" ta faɗa cikin ɗaga murya da zubda hawaye.

Yusuf ya zauna yace 

"Calm down, kinga fa wancan Dad ɗinki ne Alhaji Bulama, ga Mummy, ga Ramlah ga Amal, sune baki gane ba?"

Alhaji Bulama ya tako yazo inda suke, ya miƙa hannu ze riƙo Widad.

Wata irin ƙara ta saki, ta rirrƙe Yusuf tana ɓuya a bayan sa tana girgiza kai, cikin ƙaraji take cewa
"Ni su fita, su fita su bar nan gurin, kasheni za suyi, kana kallo nima zasu kasheni, bana son ganin su ba wannan ne Daddyna ba kuma bashi ne Bulama ba"

Yusuf yace  "buɗe ido ki kalle su fa, ga Daddy Bulaman nan s tsaye a gaban ki"

Girgiza kai tayi tace "bashi bane ba, na gaya maka bashi bane"
Ta rungume Yusuf gam tana ci gaba da zubar da Hawaye.

Yusuf a ransa yace  "ta tabbata kenan Widad tana da taɓin hankali? In ba haka ba meze sa ta koma haka?"

Alhaji Bulama yace "Karka damu dama tana yin hakan wani lokacin, ciwonta ne ya tashi"

Ihun da take yi ne iya ƙarfinta, kai kace wadda ake yankawa, ba shiri suka bar ɗakin Amal wani irin baƙin kishi ne ya cunkushe zuciyarta, yadda Widad ta rungume Yusuf yafi komai yi mata ciwo.

A hankali Yusuf yace  "Kinga sun fita ba kashe ki za suyi ba, cikani ki ga wani abu"

Girgiza masa kai tayi "tace ni A'a tsoro nake ji, kasheni za'ayi nima an kashe Ammi nima kasheni za'ayi"

Yusuf ya girgiza mata kai cike da damuwa yace "Ai ina nan tare da ke, ba inda zani babu me taɓa ki idan ina nan insha Allah , ba wani abun tsoro fa"

A hankali ta cika Yusuf tana sauke Ajiyar zuciya, hawaye na cigaba da bin fuskarta.

Yusuf ya kalle ta yace  "je kiyi brush se kici Abinci, ance tun jiya baki ci Abinci ba"

Girgiza masa kai tayi Alamar A'a.

"Idan baki abunda nace ba, zan tafi in barki anan suzo su tafi dake"

A firgice ta kalle shi, ya jinjina mata kai alamar eh,  rigarsa ta kuma riƙewa gam ya rakata banɗaki ta wanke baki, ta fito, tana ta binsa da kallo kamar taga wata halitta daban.

Da yayi hanyar fita seta biyo shi tana sake rirriƙe shi, gaba ɗaya tausayinta ya kama shi, ya ɗauki bedsheet ɗin dake kan gadon ta ya ɗaura mata, ya ɗakko hula ya saka mata.

Alhaji Bulama ya kalli Hajiya Halima yace "Nayi mamakin abunda ya tayar da ciwon Widad, na zata tuni ta warke?"

Hajiya Halima ta taɓe baki tace  "to ni ina zan sani, daga ita se ubanta se kuma kai suke sakawa a lamarin su, ta yaya zan san kota warke ko bata warke ba"

"Amma abun da mamaki, Akwai buƙatar ta cigaba da ganin likitan ƙwaƙwalwa kenan?"

"Wannan kuma ya rage shawararka kai da Mahaifinta, ni 'yar kallo ce ai tunda alamu sun nuna haukan yana nan tuburan"

Bulama yace "Hajiya Halima ai ba kyace haka ba ɗa na kowane"

"A'a wannan dai bata kowa bace, ta babanta ce kawi, ka dena wannan maganar nawa' ya'yan dai nawane, itama 'yar wasu ce"

Ƙyalƙyalewa da dariya Alhaji Bulama yayi yace  "Shikenan tunda haka kikace, ni dai na tafi, Munyi waya dashi Megida kafin inzo nan yace yana kan hanyar dawowa, zezo ya dubata idan jikin da sauƙi ya koma, idan kuma da yuwuwar a maida ita ga likitocin ƙwaƙwalwa shikenan, dan be gama abunda yake ba ze yanke ya dawo, kin san idan bata da lafiya baze iya komai ba, Allah ya bata lafiya"

Hajiya Halima tace "Karma Allah yasa tayi lafiyar, Ita da ubanta ya shafa bani ba"

Alhaji Bulama ya girgiza kai ya fice.

Yusuf Ya kira Amal a waya, ta ɗaga tana tura baki, dan gaba ɗaya kishin Yusuf take, Yusuf yace 
"Amal dan Allah ki kawo Abu me ɗan ɗumi a bata taci, da alama tana jin yunwa sosai"

"wallahi Yusuf ba dan kai ba ko zata mutu ba zan kawo komai taci ba, kaima ɗin dai kawai zan kawo ne"

"Yi haƙuri, Nagode sosai da kika min Alfarma"

Amal ta shiga kitchen ta haɗa kayan tea, Mummy tace "Me zakiyi da tea  ranar nan?"

"Widad za'a bawa" ta bata amsa

"ke meye naki a ciki to?"

"Mummy wai so kike se duniya tasan halin da muke ciki ne? Kar hankali ya dawo kanmu, Ai se munayi muna ɓadda sahu"

Mummy tai murmushi tace  "daɗina dake wani lokacin akwai hankali, ɗakkomin Jakata a ɗaki"

Amal taje ta ɗakko mata jaka ta dawo, sannan ta ɗau tray ɗin ta tafi part ɗin Widad.

Yusuf ya miƙe da nufin karɓo kayan tea ɗin, Amma Widad ta riƙe rigar sa tabi bayan sa tana zare ido.

Yusuf ya kalli Amal yace "dama Amal dagaske Widad nada taɓin hankali?"

Amal tace "gashi kuwa kana gani tana yinsa tuburan"

Cikin tsawa Widad tace
"niba mahaukaciya bace, ka gaya musu niba mahaukaciya bace, su suka haɗani da hauka, su suke maida ni mahaukaciya, Amma

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login