Showing 72001 words to 75000 words out of 135096 words

Chapter 25 - Akidata Book 1 Hausa Novel Complete

01 Jan 2025

751

karki ja mana Asara goma da Ashirin, kin san taɓa wannan yarinyar dai dai yake da kawo ƙarshenmu a gidan nan"

"Niba ita zan taɓa ba, wannan sakaran zan nunawa kuskurensa, se yayi dana sanin zuwa gidan nan, zega abunda zan masa"

******************************

Alhaji Munir, Musa, Haruna se kuma Sale ne zaune a katafaren Falon suna tattaunawa, kana ganin fuskokinsu zaka san abunda suke tattaunawar yana da matuƙar mahimmanci a gurinsu.

Nurat ce ta shigo falon bakinta ɗauke da Sallama tana ɗauke da manyan kuloli a hannunta.

Gaba ɗaya suka bita da ido, kanta a ƙasa ta ƙaraso cikin falon ta durƙusa tana gaishesu, Amsawa sukayi gaba ɗaya Alhaji Munir yace  "wai yanzu Nurat ce ta girma haka, gaskiya babu zumunci yakamata ace yaran nan suna zumunci suna a tsakaninsu"

Alhaji Haruna yace  "gaskiya kam danni banda yanzu ma ban santa ba"

Nan sukayi ta surutunsu, yayin da Saleh yake gefe yaƙi cewa komai, Nurat ta gana hada hadar kawo musu Abinci ta juya bar falon.

"Wai kai Saleh bazaka saki jiki damu bane? Akwai fa riba a harƙallar nan" cewar Alhaji Musa

"Niba ribar ce a gabana ba ɗan uwana ne a gabana, yana gadon Asibiti kunsa an bashi guba ku kuma kuna nan kuna cin Abinci"

Alhaji Haruna yace  "to kuka kake so muyi? Wallahi idan asirinmu ya tonu dagamu harshi sedai wasu bamu ba danme zamu bari ya fallasamu"

"shikenan a rayuwa kenan kowa kansa ya sani"

"ƙwarai kuwa ka bari harƙallar nan ta faɗa, idan ta faɗa ka samu kasanka seka fiddashi"

Alhaji Musa yace  "Wasan yana dab da zuwa ƙarshe indai abunda muka tsara ya tafi daidai"

Alhaji Haruna yace  "ƙwarai kuwa"

Suka maida kai suka cigaba da hirarsu yayin da Saleh gaba ɗaya abun duniya ya dameshi.

***********************************

Gaba ɗaya a sukwane Fahad ya koma gida, se huci yake kamar wani fusataccen kumurci, a falo ya tarar da mahaifiyarsa da ƙannensa, yazo ze wuxe fuuu Hajiya Sarah ta miƙe da sauri tace  "lafiya kuwa Fahad?"

Ya daki kujera yace  "harni za'a kalla ace ban kai namiji ba? Me take taƙama dashi ne haka? Ni Fahad Bulama har akwai Yarinyar da zata kalleni taci zarafina, dan kawai tana da kuɗi, toni na ganta kuma ina sonta sannan zan nuna mata ni cikakken namiji wanda mata je rububin samu!!! Meta taka da harta ke wannan izgilin da cin zarafi ga mutane?  "

"kuɗi yaro wanda hausawa kance masu gidan rana, tabbas Widad ko ba ran Mahaifinta tana da kuɗin da zata taka wanda taso, kar ka manta da bazarsu muke rawa Fahad, ina son saka alkhairi ne da alkhairi shiyasa nake ƙoƙarin haɗaka Aure da ita, karka kusakura inji kayi mata wani abu wanda ze ɓata ranta kona mahaifinta, bazaka taɓa gujewa wannan Auren ba"
Alhaji Bulama ne tsaye a ƙafar benen dake falon, yana wannan maganar

" dan tana da kuɗi, kuɗin banza kuɗin wofi, akanta aka fara arziki? Aiko da ance a gujewa Auren bazan guje masa ba ina sonta tayi min, amma wallahi na aure ta she must pay for what she did, kai kafin in Aureta ma zan Wulaƙanta ta wulaƙanci mafi muni wallahi ni za'ayiwa cin zarafi irin wannan bata isa ba Wallahi "

Ya juya ya bar falon a matuƙar fusace

Hajiya Sarah cikin masifa tace " Alhaji seda nace maka bana son wannan haɗin, kawai ka kaimin yaro ana Wulaƙanta shi daga dawowarsa yaje gurinta zata ci zarafinsa haka, yarinya babu tarbiyya babu ta ido, na gaji da wannan abu"

"maza ki ziga shi, wallahi duk wanda yayi yunƙurin kawowa auren nan cikas zega matakin da zan ɗauka, sannan kija masa kunne, wallahi idan yayi yunƙurin yi mata wani abu ta ɗaureshi wallahi ba zan sa baki a sake shi ba, kinji na gaya miki ku bar komai a hannuna nasan matakin da zan ɗauka"

Yai maganar tare da barin falon ya koma benensa

Yusuf kam tunda aka masa warning yaja bakinsa ya tsuke har sukaje suka dawo be kuma cewa komai ba, amma yana jinsa a ƙoshe saboda garar da ya kwasa yau.

Se bayan isha'i ya baro gidansu Widad, yanata sauri ya koma gida

Ba zato kawai yaga an saka masa wuƙa a saitin Ƙirjinsa, tasayawa yayi cak ba tare da yayi yunƙurin guduwa ba.

Kamar waccan ranar mutanen da suka tareshi ne suka sake tareshi.

"munzone dan mu cigaba da jadadda maka har yanzu muna bibiyarka, muna jiran karɓar wannan abun daga hannunka muna nan muna cigaba da sa maka ido da duk wani motsinka"

"Wai wani abune wannan kuke son karɓa? Ku gayamin in karɓo in baku ku ƙyaleni"

"An gaya maka bamu da lissafi ne? Ba zamu gaya maka menene ba, amma da zarar ka samu abun zamu sani, kuma zamu biyoka mu karɓa"

Suka koma cikin motarsu suka tafi, sedai sunyi ganganci dan tuni Yusuf ya ɗauke lambar motar akansa.

Yau yaci sa'a basu dake shiba suka tafi suka barshi, gida ya tafi yana tunanin meye wannan abun da'aka damu se an karɓa a gurin Widad.

A haka har ya ƙarasa gida, Seda ya zauna sukayi hira da Ummansa dukda abubuwa sun cunkushewa ƙwaƙwalwarsa.

Ya gama cin Abinci ya tafi ɗakinsa, dole zeyi tracking ɗin lambar motar nan ya gano motar waye.

Da ya koma gida Ummansa taita mita akan daren da yake kaiwa a waje, yaita bata haƙuri yana rarrashinta sannan ya tafi ɗakinsa, ya nutsa a duniyar tunani sosai wayarsa ta fara ringing.
Lambar Sakina ce kamar kar ya ɗaga, sekuma ya ɗaga yasa a kunnensa tare da sallama.

"Yusuf baka yi bacci ba?"

"Eh banyi ba" ya bata amsa a taƙaice

"dama magana nake so muyi"

"Amma kinsan dare yayi ko?"

"eh nasani, maganar tana da mahimmanci ne a gareka"

Yusuf yace  "to ina jinki"

"Yusuf akwai buƙatar ka dinga taka tsantsan da wasu abubuwan, akwai mutanen da suke nuna suna tare da kai amma a bayan idonka suna cin dunduniyarka, ba kowane mutum ne aboki na gaskiya ba"

Yusuf yace  "nifa bana son irin wannan ƙananan maganganun, ni ina zaune da kowa lafiya"

"ba ƙananan maganganu bane ba, ka dai yi a hankali sannan karka yadda wani yasan sakamakon binciken da kake komai kusancinka dashi in ba yallaɓai ba shawara ce yakamata ka kula"

"Shikenan nagode" Yusuf ya faɗa cike da ƙosawa, shi sam baya san abunda ze haɗa shi da Sakina baya son mace mara kamin kai sam.

Amma nazarin maganganun ta  ya shiga yi, wayarsa ce ta sake ɗaukar ringing har yayi tsaki ze kashe wayar yaga lambar Alhaji Nasir.

Cikin ladabi ya ɗaga wayar suka gaisa da Baban Widad, Alhaji Nasir yace  "Yusuf meyefaru ɗazu da Fahad yazo gurin Daughter"
. Cikin kame kame Yusuf yace  "Amm.. Yallaɓai yazo sun gaisa"

"Yusuf karka kareta, ka gayamin gaskiya me tayi masa? Wace irin karɓa tayi masa?"

"da alama dai beyi mata bane, ta ɗan dai nuna masa bata sonsa ne"

"Yusuf karka fara ƙarya saboda ka kare uwar ɗakinka, Bulama ya tabattar min da wulaƙanci tayiwa Fahad, kuma nasani zata aikata na kiraka ne dan in tabattar, saboda zan ɗau mataki na ƙarshe daya dace da ita, duk abunda nake dan gyaran rayuwar ta nake amma ta kasa ganewa, dan haka zan ɗau matakin da bata taɓa zata ba akanta wanda ze kasance hukunci na ƙarshe da zan yanke akanta "

Domin gyara sharhi ko shawara, feel free to contact me
Ayshercool
07063065680

                       _*AƘIDATA*_
       

PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

*Story and written by*

_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_

The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *

I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum

Haƙƙin Mallaka ⚠ : Littafin nan mallaki nane, tun daga sunan labarin zuwa abunda ya ƙunsa, ban yadda wani ko wata ya sauyamin ko yin Amfani da wani ɓangare na labarin ba ba tare da izinina ba, Nagode

https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends

ELEGANT ONLINE WRITER'S

                         PART1
                                Page 19_20

Gaba ɗaya Yusuf ya dirircei yace  "Amm... Amma Yallaɓai wani mataki zaka ɗauka haka akanta, ina fatan ba wanda ze mata tsauri bane?"

"Yusuf kenan, ka damu da al'amarin Widad haka nan naji na yadda da kai, shiyasa har nake saka a cikin abunda ya shafi rayuwar mu, na yanke shawarar tsayar da ranar Aurenta a ƙarshen wannan watan zuwa farkon wata me kamawa"

"Amma yallaɓai baka ganin hakan ze sake jefa rayuwarta cikin hatsari, duba da yadda babu Aure a tsarin Rayuwar ta?"

"Yusuf, Widad fa mutum ce kuma lafiyayyiya tana ƙin Aurene saboda wasu dalilanta da suke masu rauni a gurina, bana so in mutu in barta cikin kaɗaici, nasan Bulama baze taɓa barin ɗansa ya Wulaƙanta Widad ba ko bayan raina, dan Allah ka cigaba da yimana addu'a, Amma insha Allah ko ba taso zan ɗaura mata aure karo na farko a rayuwata da zan ɓata mata rai, amma ina fatan hakan ya zama alkhairi a gareta, Insha Allah gobe zuwa jibi zan dawk"

"shikenan Yallaɓai, Allah ya tabattar da alkhairi ya dawo da kai lafiya"

"Ameen Yusufa nagode sosai"

Tunda sukayi Sallama da mahaifin Widad abun duniya ya damu Yusuf, ji yake matakin da mahaifin Widad ke shirin ɗauka tamkar ƙarasa rugurguza rayuwar uwar ɗakinsa ne gaba ɗaya, matakin yayi tsauri sosai, haka nan yaji wani irin matsanancin kishi na taso masa game da Widad ɗin.

Dafe kansa yayi tare da faɗin "Innalillahi wa inna ialaihi raji'un, Allah ka tsareni da sake faɗawa hatsarin Soyayya, Allah yasa tausayinta kawai nake ji, tabbas idan na fara son Widad zan shiga matsala fiye da wadda nasha a baya"

Bacci kam se Ɓarawo ne ya kama Yusuf.

Kwana biyu a tsakani Yusuf yana zuwa gidansu Widad amma ba wani aiki da yake yi, kuma sam baya ganinta.

Abubuwa sun ƙara cakuɗewa Yusuf, tunani kala kala a zuciyarsa amma zuciyarsa tafi fargaba akan hukuncin da Daddy ya yanke ɗauka akan Widad.

Ya ɗakko wayarsa yana ɗan duddubawa kawai yaga message ya shigo wayarsa, anyiwa ma'aikata canjin gurin aiki ciki harda Abbas, an maida Abbas aiki a kudancin Nigeria, abun ya ɗaurewa Yusuf kai sosai, mafi akasari anfi yin wa mutum wannan canjin aikin ne, kodai dan wani mahimmin bincike, ko ƙarin girma kokuma dan hukunci ga wani laifi da ya aikata, sedai shi a ganinsa babu ɗaya da Abbas yayi wanda zesa ayi masa wannan transfer.

Ba shiri Yusuf ya bar gidansu Widad ya tafi gurin aikinsu, kai tsaye ofishin Oga Suleiman ya wuce, gaje suka gaisa Suleiman yace  "Yusuf naga aikin daka turomin, kayi ƙoƙari sosai Yusuf sannan ina taya ka murna da sabon muƙaminka"

Yusuf cikin rashin fahimta yace  "Yallaɓai nida ban fahimci abun nan ba, me Abbas yayi za'a ɗauke shi daga gurin nan akaishi wata uwa duniya?"

"Nima ban san meyasa hakan ta faru ba, sedai daga sama ne akayi wannan transfer sannan ka samu ƙarin matsayi"

Yusuf ya dafe kai yace  "Yallaɓai babu yadda za'ayi a bar Abbas a gurin nan ne? Bekamata a raba shi da iyalinsa ba zuwa wata uwa duniya ba, ni dai banji daɗin hakan ba, zanyi kewar abokina kuma ɗan uwana"

Suleiman ya jinjina sauƙin kai irin na Yusuf yace  "ya za'ayi se haƙuri haka sha'anin aiki yake"

Jiki a sanyaye Yusuf ya baro office ɗin Suleiman ya nufi na Abbas, se sarawa Yusuf ake ana masa murna amma shi sam hankalinsa yana kan wannan transfer da'akayiwa Abbas.

Da sallama ya shiga Office ɗin ya tarar da Abbas yana ta tattara kayansa dake Office ɗin.

"Abbas ya akayi haka? Me yasa akayi maka transfer haka ta gaggawa?"

Abbas yace  "nima ban sani ba Yusuf, jiya aka sanar dani kuma akace lallai gobe in Allah ya kaimu in tafi"

"yanzu babu wani abu da zamu iyayi a fasa wannan transfer ɗin?"

"Yusuf nayi duk ƙoƙarin da zanyi amma abun ya gagara"

Gaba ɗaya Yusuf ya rasa abunda yake masa daɗi, dan har cikin ransa yake jin rabuwa da Abbas ɗin, dan yana jin Abbas tamkar wani ɗan uwansa.

Wayar Yusuf ce ta fara ringing, ya ɗakkota daga aljihunsa ya ɗaga.

"Yusuf mai gida ya dawo yanzun nan, yace a kiraka"

"Shikenan gani nan zuwa"

Yusuf ya kashe wayar yace "Abbas zanzo gida insha Allah, zan ganka muyi sallama"

Abbas yace "Yusuf na ta yaka murna, an ƙara maka matsayi"

Yusuf yace  "Abbas sam bana murna da wannan ƙarin matsayin, ni tafiyarka ce damuwa ta, bari inje wannan kiran zan nemeka Insha Allah"

Sukayi musabiha, Yusuf ya juya ya fita, Abbas ya raka bayan Yusuf da harara tare da yin ƙwafa.

Tun daga harabar gidan Yusuf yaga manyan motoci da alama bayan dawowar maigidan anyi baƙi a gidan.

Kansa tsaye ya nufi cikin gidan, a falon ya tarar da Alhaji Nasir, Bulama, Fahad Hajiya Halima da iyalanta.

Yusuf ya ƙaraso yana gaishesu, Alhaji Nasir yace  "ƙaraso kusa dani Yayana, nace a kiraka aka cemin ka fita ne"

Yusuf yace  "eh naje wani uzuri ne"

Fahad se wani hararar Yusuf yake, shiko Yusuf ya basar kamar be gani ba.

Tsit falon yayi na wani lokaci, Yusuf ya rasa dalilin hakan, yana ɗaga kai yaga gimbiyar ta fito daga ƙofar part ɗinta, da alamu wannan zaman fitowarta ake jira, seda ta tsaya ta ƙare musu kallo ɗaya bayan ɗaya sannan ta ƙaraso cikin takunta na isa, ta samu kujera ɗaya ta zauna ba tare da ta kula kowa ba.

Alhaji Nasir yace "daughter"

"Na'am Daddy"

"waye wannan?" ya nuna mata Bulama

"Alhaji Bulama"

"kin san matsayinsa a gurina?"

"Just a long time business partner to you"

"he is more than that to me, kuma kin sani danme zan baki umarni kiyi fatali dashi? Duk abunda mukeyi munayi ne dan rayuwarki, danme zaki ciwa Fahad mutunci? A gaban Yusuf komai ya faru, daughter nasan duk abunda kike yi, ina ƙyale ki ne saboda nasan halinda kike ciki na maraici, amma kina zarce ƙa'ida wasu lokutan, daughter farincikin ki muke fata shiyasa muke son aurar dake"

Gaba ɗaya Widad ta ɗauke kai daga kallon Daddynta zuwa wani sashin daban, tanajin ɓacin ran saboda wannan daƙiƙin talasurun Fahad ɗin yau Daddynta ke mata faɗa, ze gane bashi da wayo.

"dan haka whether you like it or not, i have took the final decision, ending of this month zuwa farkon wata na gaba zan ɗaura Auren ki da Fahad"

Zare ido Ramlah tayi, taji zuciyarta kamar zata faɗo.

Fahad ya wani gyara zama ya kalli Alhaji Nasir yace  "sannan Daddy gaskiya yakamata ayi mata magana akan tasan yadda zata dinga gayamin magana, ta tauna ta kafin ta faɗeta dan sam bata da ɗa'a"

Miƙewa Widad tayi tsaye a fusace tace  "Over my death Body Daddy, wallahi da in auri wannan mara amfanin gara in kashe kaina, kai ka isa ka kalli tsabar idona kace a koyamin yadda zan magana, waye kai"

"Widad!!!"  mahaifinta ya kira sunanta tare da Miƙewa kamar ze kai mata duka.
Cikin zafin nama Yusuf ya miƙe ya shiga tsakanin Widad da mahaifinta ya girgiza kai yace  "Yallaɓai ayi mata afuwa dan Allah, baka saba yi mata magana haka ba karka fara yanzu karkasa zuciyarta tayi rauni, kowa ya juya mata baya, ka sauraretaba zata rasa dalilinta na ƙinsa ba"

Alhaji Nasir yace  "Amma Yusuf yakamata Widad tayi min haka a gaban mutane ta nuna ban isa ba?"

Girgiza kai Yusuf yayi yace "ba tayi haka dan Wulaƙanta kaba, ta tashi a environment ɗin da kowa yana da 'yancin faɗan abunda yake ra' ayinsa, karka ɗau hakan a matsayin ta Wulaƙanta ka, kayi haƙuri dan Allah kasan bata da lafiya"

Tuni hawaye ya wanke fuskar Widad ta kalli Daddynta karo na farko a rayuwar ta da yaƙi bin abunda takeso, hannayenta biyu ta haɗa tareda duƙar da kanta alamar neman afuwa, daga nan ta juya ɗakinta.

Alhaji Nasir ya nemi guri ya zauna, Bulama yace  "lamarin daughter se haƙuri, Allah ya shirya mana"

Hajiya Halima ta gyatsine baki tace  "wannan direban ne yake hure mata kunne take iskancin data ga dama, na rasa wace irin alaƙace tsakaninsu banda haka ana mata faɗa meye na tsoma baki? Kaima Yallaɓai harda kai da kake saka bare a al'amuran gidanka"
  Alhaji Nasir yace  "ba ruwan Yusuf, a irin taurin kai na Widad da irin haƙuri na Yusuf be isa ya hure mata kunne ba, sedai haƙurinsa ne yasa suke tare har yanzu, dan haka karki ƙara aibata shi ko ɗora masa laifi, kaimu Fahad zan shawo kan komai insha Allah"

Yusuf ya miƙe yayi musu sallama ya fice suka cigaba da tattaunawa.

Cakwakiyar gidan nan akwai sarƙaƙiya da ban mamaki, yana nan zaune ya dafe kai yayi shiru Bulama da Fahad suka fito zasu tafi, Bulama ya shiga motarsa direbansa ya ja suka tafi.

Fahad ya tako zuwa gaban Yusuf ya zauna yana fuskantar Yusuf yace 

"kaine direban Widad ko?"

Yusuf yace
"Eh nine"

"Naga kamar matsayinka a gidan nan ya wuce matsayinka na zahiri, zan ja maka kunne ne idan har kana shishshigi da iyayi ka kiyayi Fahad, dan bana barin duk wani abu daze kawomin cikas, matsiyaci kawai kalli rigar wuyanka wai har kaine zaka shiga maganar da bata shafeka ba"

Yusuf yayi murmushi ya miƙawa Fahad hannu yace "Assalamu Alaikum warahmatullah"

Fahad ya kalleshi yace "ni zaka miƙowa hannu kace mu gaisa, kasan koni waye?"

"haka Addini na ya koyamin, ban saniba ko zama a cikin turawa yasa ka manta hakan, rigar wuyana zata iya fin taka daraja in har da gumin halak na sameta, sannan nafi kowa sanin ko kai waye, ɗan adam ne da'aka samar daga Najasa wanda ƙarshena ni da kake kira matsiyaci da kai da kake ganin kanka wani ƙarshen mu ɗaya wato turɓaya kuma Abincin tsutsa, kana fuffukar ban san waye kaiba, kamar ba'a gabana mace ta keta ka ba ta Wulaƙanta ka, wulaƙanci mafi ƙasƙanci shine yadda ake cusa mata kai tana cewa bata sonka "

Galala Fahad yayi yana kallon Yusuf, sam be zaci Yusuf ya iya yanka baƙaƙen magnganu haka ba, Yusuf ya miƙe yace " ka kiyaye gaba,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login