Showing 63001 words to 66000 words out of 135096 words

Chapter 22 - Akidata Book 1 Hausa Novel Complete

01 Jan 2025

754

ita Madam bata jiran izinin kowa kafin ta yanke hukunci, dan haka wannan maganar a tsakanin ku ya kamata ku tattauna ta"

Har Hajiya Halima ta buɗe baki zata yi magana se kuma tayi shiru, waiwaya wa yayi yaga Shigowar Widad ce tasa ta yin shiru, bata kula su ba tayi part ɗinta, shima Yusuf ya silale ya bar falon.

*******************************

"Maman Yara ina cikin farinciki Ɗana ze dawo, yakamata ayi dukkanin wasu shirye shirye da suka dace domin tarbarsa, yasuhe rabon sa da ƙasar nan? Sannan ya dawo ya tarar da kyakkyawan Albishir"

Haɗe rai Hajiya Sarah tayi tace  "nikuma takaici ne fal raina wallahi"

"Saboda me takaici fal ranki, kamar ba ɗanki me ze dawo ba?"

"Eh ɗana ne, amma abunda kake shirin yi kaima kasan be kamata ba, ta yaya yarona lafiyayye zaka haɗa shi Aure da mahaukaciyar da bata san girman kowa ba, ga bata da tarbiyya"

Alhaji Bulama yace  "Easy Madam, Sarah shifa ɗa na kowane, bekamata ki cigaba da aibata Widad ba, itama kamsr 'ya take a gurin mu duba da yadda mahaifinta yayi mana halacci a rayuwa, muna ƙoƙarin yin abunda zesa ta dawo hayyacin ta ne, kuma kinga mu munsan larurarta, Fahad ze iya haƙuri ya zauna da ita, saɓanin a bawa wani a waje Auren ta"

"to kai kaɗai ne yakamata kayi tamakon? Ina sauran mutanen gari? Nidai gaskiya aka haɗa Auren ɗana da wannan tantiriyar mara mutuncin an cucemu, kai kanka da kake matsayin uba a gurin ta cin zarafin ka take, inaga ɗanka kuma?"

"Sarah, bazan zaɓawa yarona abunda ze cutar da shi ba, Aure yana gyara mutum, wuyarta su zauna a guri ɗaya ze iya canza ta"

"A'a canza halin wannan yarinyar banga ta inda ze yuwu ba Sam, kawai ka canza shawara da tunani"

Tai maganar tare da miƙewa ta bar masa ɗakin

************************************

Yallaɓai Suleiman na dawowa, Abbas ya miƙe ya tafi Office ɗinsa, ya shiga ya gaida Sulaiman cikin girmamawa irin ta masu ɗamara, se da yayi masa izini sannan ya zauna, suka sake gaisawa.

Abbas yace "Yallaɓai, lokaci fa na ƙurewa, game da aikin nan daka bawa Yusuf, bana tunanin abunda aka sashi yake yi, ɗazu yazo gurin nan, na ɗanyi masa tambayoyi akan aikin, Amma Amsoshin daya bani sam basu gamsheni ba, da alama dukiyar dake gidan da alherin da suke masa yasa ya bar aikin da 'aka sashi "

" Amma a iya sanina Yusuf mutum ne me hazaƙa, nasan shi da ƙwazo da himma akan aiki, ba shida kwaɗayi sam"

"Yallaɓai mutum na iya canzawa a kowane lokaci, Yusuf abokina ne, amma ba yadda zanyi, bana son inci amanar aiki ko' a samu matsala akan harkar aikin mu kimar mu ta zube a idon duniya, Amma ya kamata kayi wani abu yallaɓai"

Suleiman ya ɗanyi shiru sannan yace  "idan kuwa hakane, to tabbas Yusuf ya bani mama, sedai zan kira shi muyi magana, zan bibiye shi idan har na gano maganar da kake gayamin gaskiya ne, zan ɗau mataki na musamman akansa"

Abbas yace "Yallaɓai idan har ka kira shi kuyi magana ai zaka ɓata komai, zeyi duk me yuwuwa ya kare kansa koda kuwa ƙarya ze maka danka yarda da shi, tunda shima jami'in tsaro ne yasan duk hanyar da zebi ya kare kansa"

Suleman yace  "Abbas base ka nunamin aikina ba, Nagode da wannan bayani naka zan bincika, ka ciji jami'i nagari tunda har kishin aikin ka be hanaka ɓoye laifin Abokin ka ba"

Abbas ya miƙe ya sarawa Suleiman sannan ya fice.

Koda ya bar Office ɗin Suleiman Office ɗinsa ya koma yana tunani, tunani yake akanme zeyi wanda zesa gaba ɗaya aikin da Yusuf yayi ya lalace kowa ma ya huta?

************************************

Gaba ɗaya Nurat ta rasa abunda yake mata daɗi, ta shiga damuwa rashin samun wayar mutumin da ko  sunansa bata sani ba, dama Widad ta dena ɗaga wayarta gaba ɗaya, tun ranar da tazo birthday ɗin ta, abun nan ya faru, ta fara shawarar ko gidan su Widad zata je don ta tambaye ta wannan wanda suka zo taren.
Sedai kuma tayi wani tunani, aiki ne me matuƙar sauƙi a gurin Widad ta sa aka mata a ɗaure, bata da tabbacin Abokinta ya gayawa Widad abunda ya faru kokuma A'a, gaba ɗaya ta rasa abunda yake mata daɗi, komai ya dena mata daɗi se tunanin wannan bawan Allah, me matuƙar kirki, a farko tayi zaton shima mugu ne lokacin da ya ritsata har yayi mata barazana, amma yanzu ta gane ba haka abun yake ba, ranar da yazo gidan yanayin yadda ya mu'analance ta da kyakkyawar ma'amala.

************************************.

Fahad ne da Anwar tsaye a tashar jirgin Sama, Anwar yace "Fahad ina taya ka murnar kammala karatun ka, Allah ubangiji ya kaika gida lafiya, sena taho nima in next couple of weeks Insha Allah"

Fahad yayi murmushi yace  "to baban Soyayya, kaima ina taya ka murna, tsiran namu befi sati biyu, ina maka fatan Nasara ɗan uwana seka taho".

Suka rungume juna suna murmushi, sannan Fahad yaja trolley ɗinsa yayi gaba.

"Amal kin san wani abu kuwa? Munyi waya da Yaya Anwar yace min Fahad yau ze dawo Nigeria, baki ji daɗin da nake ji ba, dan Allah me ya kamata inyi wanda zan sake kama zuciyar sa, yaji in ba niba se rijiya"

Wani banzan kallo Amal tayi wa Ramlah tace  "Ban sani ba, kije kiyi abunda kika ga ya dace"

Cike da mamaki Ramlah tace  "lafiyar ki kuwa? Me yayi zafi daga neman shawara zaki hayayyaƙomin?"

"dole kice haka mana, da yake matsalarki itace damuwa kawai, ni ina lokacin da nake cikin tawa damuwar ziga Mummy kikeyi, kuka haɗemin kai kuka dinga hantara ta, har dena kulani kukayi saboda kawai nace ina son Yusuf, Ashe ke kaɗai kika san So, ni ban sanshi ba ko? Can ta mulmule miki gara tun wuri kema ki cire shi daga ranki, dan in kin manta bari in tuna miki, 'yar masu gida akace ze aura kuma kinsan baki isa kice kina da matsala da hakan ba, danke ba mutum bace a kanta, kuma kinsan baki isa kiyi takara da ita ba, akan haka ba' aƙi a baki red card daga gidan nan ba, you better go back to your senses "

Tana gama faɗin haka ta miƙe ta fice daga ɗakin, wani zazzafan gumi ne ya shiga karyowa Ramla, dan gaba ɗaya ta manta ds batun ance za'a haɗa Auren Widad da Fahad.
Gaba ɗaya kanta ys kulle dan bata san wama yakamata ta tunkara ba, Mummy ba abunda zata iyayi, shiru tayi tana tunanin meye mafita? "

************************************

Widad ta dudduba Aiken da Yusuf ya kawo mata, ya siyo komai kamar yadda tace, harda receipt ya kawo mata, tana duddubawa taci karo da wata leda, ɗakko ledar tayi ta buɗe me zata gani, wasu tsala tsalan Abaya ne kala biyar, kowacce da kalar ta sunsha stones se ƙyalli sukeyi, ta ɗauka ɗaya bayan ɗaya tana jujjuya su.
'me wannan gayen yake nufi?' ta tambayi kanta

'harni ze saiwa kaya ya bani? Meya maida ni ko nayi masa kalar saka wannan kayan?'

Tattare kayan tayi ta fito falo a fusace, da watsasu akan kujera, part ɗin su Amal ta nufa tana huci, babu ko sallama ta banka ɗakin su Amal, gaba ɗaya seda suka razana, mussman Amal dan a tsorace take tun ranar da Widad ta gansu tare da Yusuf.

Ta kalli Amal tace  "Kije bakin gate, ki kiramin wancan sakaran direban yanzun nan" tana gama maganar ta juya ta fice

Ramalh na ganin a yadda Widad ta shigo tayi magana, tasan akwai matsala dan haka ta miƙe ta fita dan ganin me ze faru,
Jikin Amal na rawa ta miƙe tayi waje kiran Yusuf.

Koda saƙon Kiran Widad ya riski Yusuf yasan a rina, yasan ze fuskanci wulaƙanci, Amma ya dake ya shiga cikin gidan.

A falo ya tarar da ita a tsaye, tana wani irin huci, haɗi da sauke numfashi, Tabbas Widad Yarinya ce ƙarama Amma Allah yayi mata kwarjini na musamman.

Yaje daf da ita ya tsaya ya sunkuyar da kai ba tare da yace komai ba.

"Kalleni nan"

A hankali ya ɗaga idonsa yasa a nata, dukda bugawar da ƙirjin Widad yayi be hanata cewa
"Nayi maka kama da matsiyaciya ko me neman temako?"

Kallon ta yayi bece komai ba
Cikin tsawa tace  "magana nake maka"

"temako ana yinsa ga kowa, duba da rayuwar gaba ɗaya taimakon juna mukeyi, dan haka ba fuska ake gane...

" Shut up!!! "
Tai maganar tare da ɗaga masa hannu

"waye kai? Me kake da shi? Me kake taƙama dashi wanda har yasa kake ganin kana da abunda zaka ɗauka ka bani? Me kake da shi? Ni zaka bawa wannan banzayen Abubuwan na maka kama da wadda zata saka wannan tarkacen, shara? Ka taɓa ganin na saka irin wannan kayan? Ko na ce maka ina da buƙatar su? "

Te Ɗebo kayan dake kan kujera ta watsa masa a fuskar sa tace " don't you ever try to make this mistake again, ka nemi mabuƙata ka basu  Widad tafi ƙarfin saka wannan tsumman"

Idon Yusuf jawur ya ɗago ya kafe ta da ido, ko ƙyaftawa baya yi, dukda hucin da take hakan be hana ta tsayawa tana kallon sa ba itama.

Ba zato ba tsammani suka ga Daddy ya ƙaraso cikin falon, ya durƙusa ya tsince rigunan, yazo gaban Yusuf ya kamo hannun Yusuf yasa nasa yace
"Yusuf wannan kyautar ni kayi wa, ba Widad ba, lokacin da zanyi tafiya ka kawo alheri ka bani kace in ƙara a guzuri, kuma ka nemi da kar in gayawa kowa, yanzu ma ka ɗakko kyauta ka bawa 'yata ɗiya tilo da nafiso, Tunda Allah yayi min Arziki babu wanda ya taɓa ɗaukar alherin naira biyar ya bani, saboda kowa gani yake ni me wadata ne bana buƙata, sedai ma kullum a nema a gurina, idan kuwa kaga anmin kyauta to wani abu ake nema a gurina, Mutum na farko da yayi min kyauta har sau biyu kuma saboda Allah, nagode sosai Yusuf, nasan kana haƙuri Amma ka ƙara zaka ga ribar sa, Widad ta gode da wannan kyautar"

Tabbas ba dan Alhaji Nasir ba, ko duniya yake samu a gidan nan baze sake zuwa ba, da babu abunda ze hana ya miƙa file ɗin aikin a ɗora wani dan ya gaji.

Yusuf bece komai ba, ya jinjinawa Alhaji Nasir kai ya fice, zuciyar sa na ƙuna dan gaba ɗaya jijiyoyin kansa sun miƙe saboda ɓacin rai.

Alhaji Nasir yayi wa Widad wani irin kallo, ya wuce part ɗinsa da kayan a hannun sa.
Se a lokacin ta sha jinin jikin ta, bin bayan Daddy tayi da sauri zuwa part ɗinsa.

Ramla tace  "Allah ya ƙara, maganin me shishshigi kenan, da haka da haka wataran zata sallameshi kowa ya huta"

Amal tace  "kema kiji da abunda ke damunki mana, aikin banza kawai"

A ɗaki Widad ta riski Mahaifinta, tace "Daddy are you angry?"

Shiru yayi mata yana ƙoƙarin ninke rigunan.

"Daddy am talking to you, why will you be angry? Am I wrong?"

Shiru ya kuma yi bece mata komai ba.

"Daddy magana fa nake maka"

"Me kike so ince miki Widad? Yaron nan yana matuƙar ƙoƙari da haƙurin zama dake, Amma kalli yadda kike treating ɗinsa, yana miki biyayya yadda ya kamata amma bakya gani, can you remember when last someone offer you a gift, for the sake of God? Meye laifin sa dan ya baki wannan kayan, irin wannan rigunan Amminki take sakawa, sunfi mutunci akan wanda ke kike sakawa, bana son takuramiki saboda yanayin halin da kike ciki, Amma ba kya tausayin kanki, meye aibu da wanda yake ƙasan ka ya baka kyauta, dukda muzguna masa da kike da wulaƙanci amma ya miki alheri, meyasa zaki Wulaƙanta shi, Widad ko baki yadda da abunda na gaya miki kwanaki ba? "

Shiri tayi tana nazarin maganganun Mahaifinta.

"baki ga yadda ya fita ransa a ɓace ba? Baki kyauta ba sam"

"to yanzu ni me kake so inyi?"

"ki karɓi wannan kayan kiyi amfani da su"

"Over my death body, gaskiya Daddy bazan iya saka wannan kayan ba"

Daddy ya jinjina kai yace  "As you wish, zanje ganin likita gobe in Allah ya kaimu, sannan baƙonki yana nan zuwa da weekends ɗin nan"

"Waye baƙona kuma?"

"Fahad, mijin da zaki aura!!!"

Widad ji tayi tamkar Daddy ya watsa mata wuta me matuƙar zafi.

(MASHA ALLAH NA KAMMALA JARRABAWA ALHAMDILILLAH, INA GODIYA DA ADDU'OINKU NAJI DAƊI NAGODE SOSAI NA GAMA JARRABAWA YAU ALHAMDILILLAH)

Domin gyara sharhi ko shawara feel free to contact me
Ayshercool
07063065680

                     _*AƘIDATA*_

      
PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

P. W. A

*Story and written by*

_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_

The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *

I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum

Haƙƙin Mallaka ⚠ : Littafin nan mallaki nane, tun daga sunan labarin zuwa abunda ya ƙunsa, ban yadda wani ko wata ya sauyamin ko yin Amfani da wani ɓangare na labarin ba ba tare da izinina ba, Nagode

https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends





ELEGANT ONLINE WRITER'S

                          PART1
                              Page 16_17


(Ayimin afuwa jiya nayi mistake ɗin pages)

Ko kallon inda Daddy yake bata kuma yiba ta fice ta bar masa ɗakin.

Komawa ɗakinta tayi, tana jin yadda zuciyarta ke wani irin bugu kamar zata fasa ƙirjinta ta fito 'kenan har yanzu Daddy be janye maganar nan ba? Daddy why?'
Tayi maganar da ƙarfi, tana sauke numfashi a hankali ta zube a ƙasan carfet, gaba ɗaya kanta ya kulle ta rasa abunyi, tabbas wannan karon Daddy dagaske yake, idan kuwa har Daddy ya dage a wannan ƙudurin nasa to tabbas zata bijre, koma hakan yayi sanadiyyar ya rasa ta gaba ɗaya, kuma seta shata babban layi tsakanin ta da Bulama.

Ramla tunani take me zata yi wanda zesa a janye maganar Widad da Fahad, ya za'ayi mutumin data daɗe tana tararirayar soyayyar sa lokaci ɗaya a wargaza mata komai, sam hakan bame yuwuwa bane, dole tasan abunyi dan yiwa wannan tufkar hanci.

************************************

Kallo ɗaya zakayi wa iyalan kasan suna cikin farin ciki, gaba ɗaya sun hallara a katafaren falon gabansu shaƙe da nau'ikan Abinci kala kala, kowanne fuskarsa ɗauke da farinciki.

Ramadan yace "Wallahi broz Fahad gaba ɗaya kaima ka zama kamar Bature, kaga yadda skin ɗinka tayi fresh kamar wani jariri"

Alhaji Bulama yace "Wannan Ƙaton ne fatarsa kamar jariri, kai dai Ramadan ka fiye shiririta"

Hajiya Sarah tace "Haba Daddy, ka kalli yadda ya wani murje yayi ƙalau dashi"

Iman tace "Nikam banga abunda ya canza ba sedai yayi haske ya ƙaro iyayi, ko hausarma bata fita sosai se kace Widad"

Ɗan ɓata fuska Hajiya Sarah tayi jin an ambaci Widad.

Alhaji Bulama yace "se suje can su cigaba da gwarancinsu"

Sam Fahad be fahimci abunda mahaifinsa yake nufi ba, haka suka ci gaba da ciye ciyensu suna hira cike da ƙaunar juna.

Yusuf kuwa tunda ya baro falon nan ransa a ɓace kai tsaye gida ya wuce, zuciyar sa nata faman tafasa, tabbas ƙarshen wulaƙanci yau Widad tayi masa, banda dalilin aikin sa da kuma mutuncin mahaifinta da baze sake komawa gidan ba.

Nurat bata da aiki se tunanin Yusuf, ko bacci ta kwanta mafarkinsa take, gaba ɗaya zuciyar ta ta kasa samun nutsuwa, ta kira lambar Yusuf harta gaji, ta koma kiran ta Widad, amma itama bata tafiya, abun duniya duk ya ishe ta.

Tana zaune tana wannan zaman tunanin mahaifinta ya shigo ɗakin ta, da sauri ta miƙe daga kwanciyar da take.
Ya kalle ta yace "ke meya ke damun ki ne?"
Girgiza masa kai tayi tace "bakomai Daddy"
"to naga Maman ki bata nan, gobe in Allah ya kaimu zamuyi baƙi ki gaya mata, za'ayi mana girki bana son na masu aiki fa"

"To zan gaya mata insha Allah"

"shikenan sena dawo"
"Adawo lafiya Daddy"
"Allah yasa"

Gaba ɗaya ɓacin rai ya hana Yusuf bacci, kamar shi dukda yasan ba wata uwace da shi ba amma Widad ta dinga gaya masa wannan baƙaƙen maganganun gaskiya idan ya ƙyaleta tabbas taci bulus.
Tunani ya shiga yi me ze mata wanda ze nuna mata mahimmancin ɗan Adam.
Da ƙyar bacci ya ɗauke shi cike da ɓacin rai.

Da gari ya waye so yayi yaje gurin aiki amma ya fasa, yayi zamansa a gida se bayan azahar sannan yaje gidan.

Nura da Isa se wani kallon banza suke masa, Yusuf bashi da lokacin su dan haka bebi ta kansu ba.

Be daɗe da zuwa ba Alhaji Nasir ya fito, yana ganinsa kamar babu abunda ya faru Yusuf ya miƙe ya nufi inda yake.
Cike da girmamawa kamar kullum suka gaisa, Alhaji Nasir yace "Yusuf kaga yau ma tafiya ta kamani, kar a gaji dani dai ga Amanar tilon 'yata nan, Fahad zezo gurin ta a satin nan Insha Allah, dan Allah a samin ido akan ta, sannan ka cigaba da haƙuri"

Yusuf yace "Insha Allah, Allah ya kaika lafiya ya dawo da kai lafiya"

"Ameen Yusuf"

Ya shiga mota, Nura yaja suka fita.

Larai me aiki ce ta fito ta samu Yusuf tace "kaje inji 'yar masu gida"

Yusuf yace "Ina zuwa"

Yai zaman sa kamar bashi akace ana kira ba, Isa yace "da alama Yusuf ka raina Yarinyar nan, badan kaine ba akwai wanda ya isa yayi mata haka ta ƙyaleshi, turowa fa tayi tana kiran ka, amma ka basar kana shagalinka"

Ko gezau Yusuf beyi ba, balle Ya nuna yasan me Isa yake faɗa.

Isa yace "da kai fa nake magana"

Still be tanka masa ba, Isa yace "eh da alama kaima ta koya maka baƙin halin, kadai bi a hankali tunda kaima ɗan uwa talaka ne, inka ɗau wannan rayuwar ba inda zata kaika"

Yusuf be kula shi ba ya miƙe ya bar gurin.

Yusuf na tafiya sega Abbas yazo, Isa na ganin shi ya washe baki yace "Sani dama kana nan? Kwata kwata wayarka ta dena shiga"

"ina nan wallahi, na koma ƙauye ne, ya kake ya aikin?"

"Alhamdilillah, ya ka baro mutan gidan?"

"Lafiya ƙalau Alhamdilillah, ina Yusuf kuwa?"
Isa ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login