Showing 129001 words to 132000 words out of 135096 words
Hindu ne suka iya zaman rarrashin Widad.
Hari tace wai ke Wudas daga miji na zazzaɓi seki zauna kita mana kuka, memakon ki masa Addu'a "
Ko kallon Hari ba tayi ba, ta miƙe ta tafi ɗakinsu tayi kwanciyarta tana cigaba da kuka.
Nurat suka dinga communicatinga da cousin ɗinta akan yadda za'ayi belin Anwar.
Yanzu ma tana kwance akan gadonta hannunta ɗauke da waya, tace" Brother ya ake ciki ne? Yakamata a gaggauta fitar da Anwar bashi da laifin komai fa"
"Nurat, kince bakyason asan muna ƙoƙarin belinsa, dan haka nake taka tsantsan, sedai abunda na gano shine tsare Anwar da akayi da manufa akayi shi, idan muka matsa tabbas za'a gano ke kikasa ayi belinamsa, tunda an san alaƙar dake tsakanin mu"
Cikin karaya Nurat tace "yanzu Brother babu abunda zaka iyayimin, Anwar be cancanci ya zauna a gurin nan ba"
Yace "Nurat, lawyan mahaifiyarsa ma yana ta ƙoƙari, amma har yanzu sun hana belinshi bansan meye abunyi ba, amma meyasa kika damu ya fita bayan kin san munin Alaƙar dake tsakanin mahaifinki da Daula?"
"Brother, idan akazo batun gaskiya da adalci ba'a kawo maganar alaƙa, an cutar da Anwar fiye da yadda kake zato, shikaɗai ne akan lamarin rashin lafiyar Alhaji Nasir, amma kalli abunda ya biyo baya, kodai an masa hakane dan a tozarta shi, ko kuma wanda ya sace shine yake son wanke kansa ta hanyar sawa a kama Anwar "
Barrister yace "Amma abun da mamaki ta yaya za'a iya sace mutum Attajiri kamar wannan a gadon Asibiti, kuma babu wani ƙwaƙwaran bayani, abun da mamaki fa"
Nurat tace "Brother, dan Allah idan kana da dama ina son kazo in ganka, ina son mu tattauna wani zance da kai dan Allah"
Barrister yace "Fara gayamin mana"
"A'a Brother, nidai so nake ina ganka, akwai magana ne a bakina"
"shikenan karki damu, Insha Allah idan ma samu lokaci zanzo insha Allah"
"Yawwa brother nagode sosai"
Ta kashe wayarta ta ajiye, shiru tayi abubuwa da dama suna damun zuciyarta, har yanzu bata ji alamar labarin inda su Yusuf suke ba, har yanzu bata sake jin wani magana game dasu ba, ta shiga tuna hirar da suka yi da Amal akan alaƙar Widad da Yusuf, ji tayi tana gumi dukda sanyin AC dake ɗakin nata, amma ta shiga haɗa gumi, miƙewa tayi ta tafi toilet da niyyar ta watsa ruwa ta rage damuwa.
Har bayan magariba babu labarin dawowar su Yusuf, nan fa Widad ta sake gigicewa, ta shiga sintir a gidan nan tana "Allah ka duba Yoseef ka bashi lafiya, Allah ka bashi lafiya ba danni ba"
Gaba ɗaya tausayin ta ya hana Gwaggo nutsuwa, se aikin rarrashin Widad take, ita kuwa Hari harta ƙule saboda ganin abun na Widad take kama harda shagwaɓa dan taga ana lallaɓata, kawai dan mutum yana zazzaɓi ta cikawa mutane gida da ihu.
Dukda Hanne itama tana cikin damuwar rashin lafiyar Yusuf, amma ji take kamar ta make Widad, gaba ɗaya ta hana mutane sukuni, se wani kuka take se kace wadda akace ya mutu.
Gwaggo ta zauna tasa Widad a gaba taci Abinci, amma ta gagara ci, Gwaggo tace "Amarya kiyi haƙuri, kici Abinci kinji, ki cigaba dayi masa Addu'a"
Cikin kuka Widad tace "Mama idan wani abu ya samu Yoseef sanadina ne, ba danni ba ba dan yasanni ba da duk baze shiga wannan halin ba"
Gwaggo tace "A'a kiyi haƙuri, Allah ne ya ɗora masa, kuma ze yaye masa"
Har dare basu dawo ba, ba Saleh ba dalilinsa, hankalin Widad ya sake tashi, yanzu take sake ganin Amfanin Yusuf a tare da ita, dare yayi tace bazata iya zama a ɗakin ita kaɗai ba, Gwaggo tace taje ɗakinta ta kwana, amma Widad fafur taƙi, ƙarshe Hindu ce tabi Widad ɗakinsu ta tayata kwana.
Har yanzu hankalin Umman Yusuf yaƙi kwanciya, rashin Yusuf a tare da ita ba ƙaramin abu bane a gurinta, sam rayuwa kawai take ba dan tana jin daɗin rayuwar ba, Yusuf shine ɗanta ɗaya tilo, yau a sanadin aikinsa yayi nesa da ita, bata san inda yake ba, gashi a hukumance babu wanda yace mata komai, se Suleiman da yake sintirin zuwa ganinta yana kwantar mata da hankali.
Wataran a ɗakin Yusuf ɗin take kwana, taita kuka gwanin ban tausayi, tana matuƙar ɗan nata rabuwarta da shi ji take kamar ta rasa komai na rayuwarta.
Bacci kam Widad ba tayi shi ba, Hindu tun tana rarrashin ta harta gaji tayi bacci, Widad kam kwana tayi tana Addu'a, Allah ya bawa Yusuf lafiya.
Se washegari sannan Ila da suka tafi kai Yusuf Asibiti tare yazo gidan, Widad na ganin shi a gigice tace "Ina Yoseef ɗin? Yana ina?"
Ila yace "ki kwantar da hankalinki, kwantar dashi akai, can cikin garin Bauchi muka kai shi, ya ɗan samu sauƙi Amma yaji jiki fa, kafin muje har Suma ya dinga yi a mota, amma ya farfaɗo, baza'a sallameshi yau ba"
Hanne dake gefe tace "Alhamdilillah"
Gaba ɗaya suka juya suna kallonta, banda Widad da tace "dan Allah dagaske kake ya tashi?"
Ila yace "kwarankwatsa dagaske nake, dan yace in gaidaki, Saleh na baro a gurinsa"
Se a lokacin Widad ta ɗanji hankalin ta ya ɗan kwanta, harta samu tayi wanka, megari ma yayi ta mata Nasiha akan wannan kukan data dingayi.
Ramla kam a kusan buge ta dawo gidan nan, Hajiya Halima bata ga dawowarta ba, Amal ce taga wucewarta kamar tana tangaɗi, binta tayi da sauri ɗakinta, ta tarar tayi cilli da jakarta da takalmanta ta zube akan carfet tana bacci, Amal tace
"Innalillahi wa inna ialaihi raji'un, Ramla me zan gani haka, meya same ki?"
Ramla kasa magana tayi se ɗaga hannu da take, cikin maye tace "ke.. Keee.. Nace ina ruwank.... Ki dani neeeee.. Ki fita nace"
"Ramla, shaye2 kika fara ne?"
Shiru Ramla tayi mata, ta cigaba da baccinta.
Gaba ɗaya hantar cikin Amal ya kaɗa, tabbas Ramla shaye2 take, dan maye take yi, ta tuna yadda take bacci ba ƙaƙƙautawa, da tayi kamar taje ta gayawa mahaifiyarsu, se kuma ta tuna dama a ƙule take da Fahad da mahaifinsa, muddin ta gayamata za'ayi ɓatacciya ne.
Kwanan Yusuf uku a Asibiti, gaba ɗaya Widad ta rame, idanunta duk sun kumbura, jama'ar ƙauyen duk sun san rashin lafiyar Yusuf, dan shike jansu Sallar Asuba da magariba zuwa isha'iyanzu, kuma ga karatu da yake koya musu suna jin daɗinsa.
Widad ta zuba ido, taga ta ina Za'a dawo mata da Yusuf, dan Ila ya gaya musu ranar za'a sallameshi.
Gwaggo tasa akayi Abinci, aka dama Fura saboda Yusuf.
Ila ya shigo gidan da Sallama yace "ku kintsa, mun dawo maƙota sun baibaye mota zasu shigo da shi"
Da ƙyar Gwaggo ta janye Widad zuwa ɗakinta, saboda maza zasu shigo, dukda damuwar da Widad ke ciki be hana Widad kallon Ɗakin Gwaggo ba, yasha jeren samiru da fanteku, ga gadonta na ƙarfe me rumfa da mudubi, ginin tsurar ƙasane ɗakin amma yayiwa Widad kyau nesa ba kusa ba, ga ƙwarya da'akayi wa itama nata jeren, ƙwaryar ta sha zane mekyau, ga wasu a cikin ragaya, Widad bata taɓa ganin irinsu ba"
Idan ba gizo kunnuwanta suka yi mata ba, to tabbas a cikin muryar mazan da suka yi Sallama hadda Yusuf.
Zumbur ta miƙe tsaye, Gwaggo tace "aikuwa ga muryar ɗana nan, Alhamdilillah lafiya ta samu"
Kasa jurewa Widad tayi, kawai se gani Gwaggo tayi Widad tayi waje, kai tsaye ta nufi ɗakinsu, ga mutane maza a ciki, wasu na ƙoƙarin fitowa, haka ta kutsa ta shiga, ta hango Yusuf yana zaune yana murmushi, sedai yayi rama sosai, yayi haske.
Da gudu ta ƙarasa ta rungume shi, ta kasa magana kawai ta fashe da kuka.
Ɗaya bayan ɗaya suka zame suka bar ɗakin, yau suka ga taɓara, ba kunya bakomai ba kara tazo ta rungume Yusuf a gabansu.
Suna fita Yusuf ya ha&a hannayensa ya rungumeta shima yace "Queen kin rame, duk kinyi wani iri"
Maimakon ta bashi amsa se sake kwanciya da tayi a jikinsa tace "Ya jiki ka warke?"
" Na warke amma ina ganin yadda kika rame naji zata dawo"
Hanne ce tayi sallama da kayan Abinci a hannunta, sedai me taga Yusuf da Widad rungume da juna, take taji jikinta ya hau rawa, bata taɓa ganin hakan a zahiri ba, sannan ga wani kishi daya taso mata, take ta saki kwanon dake hannunta.
(Gobe insha Allah, zan kammala book 1,Ashirin ga wata insha Allah zan fara book 2&3, tuni an fara biyan kuɗin, kuma zaku iya hanzarta biya ta wannan hanyar dake ƙasa "
Normal group duka littafi biyun ₦300
Idan kuma ɗaya zaki siya ₦200
VIP ₦ 500
Inkuma sena gama zaki sai complete document ₦700
Account Number
Aisha Adam
0009450228
Ja'iz Bank
Ko katin MTN banda VTU please
A turo evidence of payment ta 07063065680
Duk Wanda ya biya yayi min magana ta what's app number ɗina inyi adding ɗinsa a group ɗin Nagode
Domin gyara sharhi ko shawara
Ayshercool
_*AƘIDATA*_
PERFECT WRITERS ASSOCIATION
(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)
https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*Story and written by*
_*AISHA HUMAIRA _
(Daddy's girl)*_
The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *
I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum
Haƙƙin Mallaka ⚠ : Littafin nan mallaki nane, tun daga sunan labarin zuwa abunda ya ƙunsa, ban yadda wani ko wata ya sauyamin ko yin Amfani da wani ɓangare na labarin ba ba tare da izinina ba, Nagode
https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends
NOT EDITED (BANYI EDITING BA)
ELEGANT ONLINE WRITER'S
PART1
Page 44_45
Yusuf ne yayi saurin ɗagowa ya kalli Hanne, Yusuf yace "Subhanallah, garin yaya kika ɓarar da Abinci?"
Widad kam ko motsawa ba tayi ba balle ta tashi daga jikin Yusuf.
Cikin rawar jiki Hanne tace "Tuntuɓe nayi shine ya zube, bari in samo in kwashe"
Ta juya ta fita da sauri, tana fita tsakar gida Gwaggo ta kalleta tace "ke meye haka, ba dai Abincin da nace ki kaiwa mara lafiyan kika zubar ba?"
Cikin inda inda tace "Amm.. Mm... Tuntuɓe nayi shine ya zube"
A fusace Gwaggo tace "kekam kamar mara hankali wani lokacin, kije ki kai Abinci kawai seki zubar dan shirme"
Hanne ba tace komai ba ta tafi ta ɗau tsintsiya da abun kwashe shara ta tafi gyara inda ta ɓata musu, cike da zullumin me zata je ta sake tararwa.
Gwaggo tace "Hindu tashi ki duba sauran kunu a ɗakina ki kai musu ba'a bar mara lafiya da Yunwa ba"
Sukam Maƙota da suka rako Yusuf ne suka dinga jinjina rashin ta ido irin na Widad, a gabansu ba kunya taje ta rungume mijinta.
Wani da'ake kira da Lado me Jakai yace "to ai kunsan su ba namu ne na nan ba, jama'ar birni ne baku ga matar tasa bama kamar balarabiya, su sun saba irin wannan bakomai ne ba"
Ɗayan da'ake cewa Liti yace "Aradu amma ai kunya wani abuce, tunda nasan duk abu Hausawa ne"
Lado yace "ku kuga haka, su a gurinsu ba wani abun bane ba"
Liti yace "Sumi sumi dashi haka, Amma ta rungume shi ya wani basar abunsa, memakon ma ya ɗanyi mata tsawa ya hanata"
Wani me shekaru a cikin su yace "Kai waye ya gaya maka suna hantarar matansu, lallaɓasu suke yi, ni wallahi birgeni ma suka yi"
Kwashewa sukayi da Dariya gaba ɗayansu, harda ƙyaƙyacewa.
Hindu tayi Sallama, da kofin kunu tace "gashi inji Gwaggo, tace dan Allah kuyi haƙuri Hanne ta zubar da Abincin"
Yusuf yace "bakomai Hindatu hakanma mungode"
Hindu tace "Amarya yau za'a ci Abinci, tunda me gidan ya dawo"
Yusuf yace "Ai naga alama bata cin Abinci ta rame sosai"
Hindu tace "bata ci, Gwaggo taita fama da ita sedai tayi ta kuka, ko bacci bata iyayi"
Widad ta yatsine baki tace "Akanme zanƙi bacci, in kasa cin Abinci toni ƙiba ma nayi, ci nake in ƙoshi"
Hindu tayi dariya tace "bari a kirawo Gwaggo a tambaye ta"
Sukayi dariya, Hindu tayi waje, Yusuf ya kalli Widad yace "bani kunun insha dan inajin Yunwa"
Widad ta miƙe ta ɗakko kofin kunu, tazo ta zauna tana bawa Yusuf, Saleh ne yayi Sallama ya shigo ɗakinsu.
Kallon Widad yayi yai murmushi yace "Allah me iko, Allah ba yadda be iyaba, wai Gimbiyar Daula ce ke bawa direbanta Abinci a baki, abun da mamaki"
Banza tayi masa ta cigaba da bawa Yusuf kunu, Yusuf yace "Saleh ƙaraso ka zauna mana"
Saleh yace "to bari in ƙaraso, ina fatan hankalinki ya kwanta ban gudu dashi ba, gashi na dawo miki da shi, kuma Alhamdilillah jikinsa yayi kyau"
Shiru ta kuma yi bata ce komai ba, Yusuf yace "Ana magana fa"
Widad tace "me zance?"
Saleh yace "base kince komai ba kam, Malaria me ƙarfi da typhoid ne suka kama Yusuf, sannan ulcer na damunsa, ga rashin sabo da wasu abubuwa da yake yi, wanda be saba ba, dan haka shine damuwa gajiya da pressure ga kuma zazzaɓi gaba ɗaya suka dameshi, amma Alhamdilillah mun samu an ceto miki shi, yasamu sauƙi Alhamdilillah, na samo Net guda ɗaya, yace min ba guri ɗaya muke kwana ba, dan haka ga guda biyu nan ke ɗaya shi ɗaya, likita yace 'ya dena zama da yunwa, ya dena barin sauro yana cizonsa, sannan a kula ya shanye magungunansa"
Widad tace "Aishi zaka gayawa bani ba, tunda ze iya kula da kansa ko"
Mamkine ya kama Saleh, ya tuna yadda ta dinga kuka ranar da zasu tafi da Yusuf, amma yanzu tana faɗar wata magana daban, shi kansa Yusuf beji daɗin hakan ba, amma ya basar.
Saleh yace "koma dai menene, Zan zauna zuwa jibi in Allah ya kaimu zan koma, nayi muku siyayya wajen gobe in Allah ya kaimu za'a kawo muku"
Yusuf yace "Mungode sosai da ɗawainiyar da kake mana, Allah ya saka da alkhairi, Allah ya biya ka"
Saleh yace "Ameen"
Ita kuwa madigar, miƙewa tayi tai waje abunta, ba tare da ta sake tanka musu ba.
Amal na kwance akan gadonta tayi shiru sosai take tunani, tayi zurfi sosai a tunani, Mummy ta shigo ɗaki Amal ta tarar a kwance tayi shiru tana ta tunani"
Mummy tace "ke meye haka? Tunanin me kike yi? "
Amal ta ɗan tura baki tace "lafiya ƙalau Mummy"
"Amma kika zauna kika yi shiru haka? Kina ƙarama dake kike tunani haka"
"Mummy ina ɗan zancen zuci ne kawai"
"to idan waccan uwar baccin ta tashi ki gaya mata zan fita, ni na rasa gane kan wannan baccin banzan dat take yi sekace wata kasa"
Ita dai Amal bata gayawa Mummy abunda Ramlan keyi ba.
Bayan fitar Mummy kwanciya Amal ta sake yi tana cigaba da tunani, kuma ba tunanin kowa take ba face Yusuf, tun tana dannewa yanzu abu yavfara gagara, bata iya ɓoyewa sam, Bata iya cin Abinci ba tayi zaton ƙaunar Yusuf haka tayi mat wannan mugun kamun ba, gaba ɗaya yanzu haushin samarin ta take ji, gani take duk cikinsu Yusuf yafi su komai dukda Kasancewarsa talaka, amma ya haɗu gashi nutsatse babu Hayaniya a tare da shi, ji tagi inama a sako Yusuf a riƙe Widad, dama itake hana ta rawar gaban hantsi, dan ta rasa wace irin Alaƙace ke tsakanin su, Widad bata da yadda kamar me, bata yadda kowa ya raɓe ta ba, amma ta yadda da Yusuf ya shiga jikinta sosai da sosai, Yusuf yasan abubuwan dasu da suke zaune da ita basu sani ba.
"Ke Amal! Tun ɗazu nake miki magana amma se kace wata kurma, kinmin shiru"
Firgigit Amal ta kalli Ramlah, tayi ajiyar zuciya tace "Meye nayi min ihu kuma?"
"na dole inyi miki ihu ba, tun ɗazu nake kanki ina magana amma kinyi shiru"
Amal ta miƙe zaune ta kalli Ramlah tace "ban san kin shigo abane, dana san kin shigo ai zanyi responding"
"Wai nikam wane irin tunani haka kike yi?"
"Ramlah tunanin komai ma inayi, Abubuwa da yawa sun dameni, Amma Ramlah jiya fa maye kike kika dawo"
"Maye kuma?"
"Eh mana, wallahi jiya a buge kika dawo gidan nan, Mummy kuma a ƙule take dake, fitar da kikayi da Fahad"
Ramlah ta ɗan ɓata rai tace "ba wani maye da nake, na gaji ne kawai, sannan me Fahad ɗin kuma yayi?"
Amal tace "Eh to, kin san sunyi faɗa da ɗan uwanta akan belin Yaya Anwar, shiyasa"
"to kuma shine seya shafi Fahad, laifin meyayi? Kuma shima bakiga yadda yake ƙoƙari akan lamarin ba, amma kin san halin babansu da kafiya"
Amal tace "wani tabacci kike da shi na yana ƙoƙarin nan, nifa kallon Fahad ɗin nan kawai nake, bakin maƙaryata ne dashi"
Ramlah tace "zaki fara ko? Karki kusakura kici masa mutunci"
Amal tace "ke niba wannan ba, nifa naji tana cewa za'ayi uwar watsi idan ba'a fito mata da Yaya Anwar ba, karta yi wani abu daza'a zo ana da nasani daga baya"
Ramlah tace "kuma fa hakane, kin san bata iya fushi ba, bari inje ɗakinta in sameta"
Amal tace "to ai ta fita"
"ta tafi ina?"
"Nima ban sani ba, ni dai tacemin zata fita"
Ramlah tace "Shikenan, bari inje kitchen in samu ɗan abunda zanci, da yamma zanje gurin wani birthday na 'yar gidan IG na ƙasa, na tura a ɗakkomin wata sabuwar motar megidan nan daga kamfani, da ita zanje, kin san gurine na manyan yara fa"
Amal tace "Mhmm yakamata kam"
"waini meke damunki ne Amal, bakya walwala fa"
"Ramlah wace walwala zanyi? Yaya Anwar a rufe, hankalin Mummy yaƙi kwanciya, ga uwa uba wallahi Ramlah Ji nake kamar inyi me saboda rashin Yusuf, na shiga damuwa wallahi ko bacci na kwanta yanzu mafarkinsa nake yi, na rasa inda zan saka raina, tun ina iya dannewa yanzu na kasa "
Wani uban dogon tsaki Ramlah taja tace " Aikin banza, shine zaki kashe kanki saboda wannan jakin"
"Karki sake kiransa da Jaki, Inda wanda za'a kira Jaki to tabbas Fahad ne, dan kunnuwansa ma irin na jakaine ga ƙaryar tsiya".
Haka abun nasa ya koma faɗa, ƙarshe sukayi baran Baran.
Widad ta fita tsakar gida, ta ƙarasa inda Gwaggo take tana murmushi, Hari tace "ohh ni Harira, se wangale baki kike miji ya dawo, kin