Showing 3001 words to 6000 words out of 135096 words

Chapter 2 - Akidata Book 1 Hausa Novel Complete

01 Jan 2025

737

tambaya ta kana ina?"

Yusuf yace "wa kenan?"

"kafini sani ai, wacece in ba Sakina ba"

Tsaki Yusuf yayi yace "dan Allah Abbas ka dena sa kamin wannan yarinyar cikin lamurana, ni tun abunda ya faru dani duk wata harka da mata gudun ta nake yi, wannan aikin ma da kuka bani kaida yallaɓai dan ba yadda zanyi ne harka ce ta aiki, balle wata Sakina, ni ina tsoron mata nafi ƙaunar tsira da mutunci na da kuma tsayawa matsayin da Allah ya ajiye ni, nayi darasi akan abunda ya faru dani"

Abbas yace "hakane kana da gaskiya Yusuf, Amma ka sani idan har mukayi nasara a Aikin nan cigabanka ne, sekafi kowa benefitting gaba kaɗan in aikin ya kankama zan ƙara sanar da kai wasu abubuwan"
Abbas ya ci gaba da kwantarwa da yusuf hankali tare da lallaɓa shi har ya ƙara gamsuwa ya Amince Amince akan zasu je gidan Alhaji Nasiru Daula da weekends domin a tantance shi in ze iya zama direban Wannan yarinya me muguwar AƘIDA sannan a gabatar da Yusuf  a matsayin Sabon direban wannan 'yar Hamshaƙin Attajiri Me murɗaɗiyar AƘIDA!!!.

Tun bayan da Abbas ya tafi, Yusuf yake ta tunani akan wannan gagarumin Aiki, yana ƙara duba kyawawan hotunan wannan yarinyar da ko sunan ta be sani ba, she has an innocent face a hoto, gata very young and beautiful amma ya akayi take da halaye marasa kyau haka?
Idan har ya kasance da gaske tana da duk wannan halaye da'aka faɗa masa anya ze iya aikin kuwa?
Amma meyasa Abbas be warware masa yadda aikin yake ba gaba ɗaya yace se ya fara yi wa yarinyar aiki ze gaya masa?
"Allah yasa ba cikin wata cakwakiyar zasu jefa ni ba" yai maganar a fili tare da miƙewa ya tattare kayan da ya baza a kan Katifar sa ya fito daga ɗakin nasa.
Kasancewar Yamma ce bashi da gurin zuwa da yake shi bame yawan shiga sabgar mutane bane, ya shiga ɗakin Umman sa ya ɗakko kayan wankin ta ya wanke tsaf, ya share ko ina, ya ɗora girki se kace mace, cikin nutsuwa yake Al'amuran sa ya kammala dafa shinkafa da miya ya zuba a flask, lokacin ana ta kiraye kirayen sallar magariba yayi Alwala ya fice Masallaci.




Ayshercool
07063065680
                       _*AƘIDA TA*_

             

     *PART1*         
                  _Page 2_

*written and edited by*

_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_

The experience writer of
*ABDUL JALAL*

Bismillahir rahmanirrahim, da sunan Allah me Rahama me jin ƙai, Wannan littafi ƙirƙirarren labari ne banyi shi dan cin zarafi ko cin fuska ga wani ko wata ko wata ƙabila ba, idan har wani ko wata yaga wani abu daya yi kaman ceceniya da rayuwar sa ko ƙabilar sa Amin Afuwa banyi dan cin zarafin wani ko wata ba.
    Wannan littafin mallaka tane, ban yadda a juyamin labari ta kowane fanni ba ba tare da izinina ba.

What's App : 07063065680
Watpad : Ayshercool7724
Gmail : [email protected]

************************************

Wata Babbar Mace ce Zaune a cikin wani katafaren falo me girma sosai, cike yake da kayan more Rayuwa, Aƙalla zata kai shakaru hamsin, Amma kaman 'yar shekara talatin da biyar saboda hutu idonta sanye da glashi ta nutsu sosai tana danna Computer tana shan tea.

Wata matsashiya ce ta shigo falon a ƙalla za ta kai shekaru Ashirin da bakwai, tazo ta zauna a kusa da Matar.
Ba tare da Matar ta ɗago ba tace "Ya a kayi ne? Nasan akwai damuwa tunda na ganki yanzu meya faru?" ta ƙarasa maganar tana kallon matashiyar.

Ta ɗan yatsuna fuska tace " Mummy kin san wani abu?"

"A'a sekin faɗa" matar ta bata Amsa

Cikin shagwaba tace "Mummy ki duba girman gidan nan da cikar sa, kalli dukiyar dake cikin gidan nan, Amma mota ɗaya tak na mallaka, ko ɗan direba ma ba'a sama min ba, Amma kalli 'yar masu gida motocin ta nawa? Direbobi nawa ta wulaƙanta ta sallama a dawowar nan tata? Har motocin me gidan nan take hawa in ta ga dama gaskiya ana nuna mana wariyar launin fata, banda cin fuska da wulakanci da muke fuskanta seka ce wasu Bayi"

Matar ta cire glashin fuskarta tace

"Ramlah me kike so inyi? Alhaji Baya jin magana ko ganin girman kowa sena 'yar sa, abunda take so shi yake yi, Sannan duk abubuwan nan da suke faruwa na ɗan lokaci ne, Amma me kike so ayi? "

"Mum Mota nake so a canzamin sannan nima a ɗaukar min direba, bama mota ba motoci nima in dinga kece raini yadda yakamata, kalli daular da muke ciki, Amma a ce se abunda yarinya ƙarama take so akeyi, Mummy ina son inyi birthday ina buƙatar kuɗaɗe masu yawa fa wanda zan burge ƙawaye na dasu, Sannan naji labarin Akwai filayen da gwamnati za ta yi gwanjonsu a GRA ya kamata ace  kin mallaka"

"Hmm Ramlah kenan samun wannan abubuwane masu Sauƙin samu a hannun me gidan nan, Amma kin san seda izini kokuma ince yaddar 'yarsa ko?"

Ramlah tace "Amma Mummy ba yadda za' ayi in samu kuɗin a hannun ki? Kina matarsa amma ace se Abunda 'yarsa take so haba dan Allah, yakamata ace Akwai wata Dama da zaki dinga mallakar kuɗaɗe bayan wanda yake baki"

"babu wannan damar, dan duk kuɗin dazan fitar seda sanin Lawyern sa, dan haka ba yadda zanyi, Karki manta muna da kyakkyawan shiri a ƙasa shiyasa sam bana damuwa, ni yanzu so nake in lallaɓa shi Amal me ta tafi turkey ta ci gaba da karatu a can"

Ramlah tace
"shikenan Amma yakamata kiyi wani abu akai kar wannan damar ta wuce mu, Amma kafin wannan ya batun canza motarfa?"

Mummy tace "Wannan kuma sekin yi tsani da 'yar masu gida, tana magana ko mota goma kike so kamar kin samu, batun kuɗi kuma zan tura miki kuɗi Account ɗinki base munjira ba, Amma ki same ta in ta yadda za tayi masa magana a baki wata motar"

Ramlah ta yamutsa fuska tace
"A' a Mummy ke zaki mata magana, kin san ba shiga sabgarta nake ba, bana son wulaƙanci da rainin hankali, kin san bama shiri da ita"

Mummy tace "ke kina tunanin idan nayi mata magana zata saurare nine? Yau kwana biyar rabon da in sata a idona fa yarinyar nan barta kawai"

Ramlah tace "bari in kira miki ita dan Allah ki mata magana ko zata sa baki, ni kin san bama jituwa da ita"

Mummy ta ɗan jinjina kai tace "shikenan Allah yabada sa'a"

Tana zaune akan stool a gaban dressing mirror ɗin ta wanda yake shaƙe da kayan shafe shafe na mata, towel ne a jikin ta tana ta ƙoƙarin tsane gashin kanta.
Ƙofar ɗakin aka turo aka shigo, wata matashiyar budurwar ce ta shigo ɗakin ba tare da tayi sallama ba ko wata doguwar maganaba tace 

"Mum nasan ganin ki a cikin gida, zakuyi magana"

Wadda akewa maganar se kace da gini ake, ko gezau ba tayi ba ta ci gaba da abunda take yi,  bata kalli me mata maganar ba ta cigaba da abunda take yi .
Cikin ƙosawa da fushi matashiyar wadda aƙalla ta girmi wadda take wa maganar nesa ba kusa ba tace

"wai ba kyaji ina miki magana ne? Kin min banza kaman baki san na shigo ba?"

Cikin isa yarinyar ta Ajiye Ƙaramin Towel ɗin hannun ta, ta miƙe ta nufi wardrobe ɗin ta, Subhanallah koda ta buɗe wardrobe ɗin sutura ce a ciki kaman shara, kamar inji ne ya shirya kayan ba hannu ba, kai in akace suturar mutum ɗaya ce seka riƙe baki tareda tunanin ina mamallakin suturar ze kai ta?

Ta saka hannu ta janyo wata 'yar riga ja mara hannu, tana ƙoƙarin sakawa ba tare da ta waigo ba cikin ƙasaita tace

"Ramla ki koma ki gayawa wadda ta aiko ki banyi budget da lokacin da zan bata ba a yanzu, ko menene idan ta damu tazo da kanta ta sameni in gani ko zan iya saurarta, idan kuma bame mahimmanci bane zata iya haƙura har se lokacin da Allah yasa na shigo cikin gidan, you can go out i need privacy"

Cikin ɓacin rai Ramla tace "Waike wace irin mara ɗa'a ce haka? Mahaifiyar tawa ce zata zo ta same ki? Kika san me yasa ta kira ki? Se kace sa'ar ki?"

"koma me zesa ta kira ni nasan baze wuce biyan wata buƙata tata ba kokuma ta 'ya' yan ta, ni kuma da ku da ita bani da lokacin ku a yanzu, ɗan fitar min daga ɗaki, zan kaɗaice inyi tunani"

Ramla tace  "Amma baki da kirki, a gabana kike faɗan maganganu akan uwata, ke har Abada girma da shekarun mutum baya sa ki bashi girma, Ko ance miki rayuwar Turai hauka ce? Rayuwar turai fa  ta saɓa da Al'adunmu, Ko kuma akanki aka fara Arziki?"

"Enough Ramlah" Yarinyar ta katse ta  ta nuna Ramlah da yatsa ta ɗora da cewa

"Amma kamar kin san ba'amin shouting ko? You know the consequences of doing that. Mahaifiyar ku, ku ta haifa, ni kuma Babana take Aure bata haifeni ba, what's the meaning of respect according to you ne Ramla? Your mother is just a human being like everyone, she don't deserve any special respect, i will treat her the same way i treat every human being,  and mark you This is my father's house,  if you are tired of what am doing, go back to your father's house, nan gidan mahaifina ne ina da right inyi abunda nake so, and no one should stop me from doing what I want, if you are tired of what am doing park your things and go, madam get out from my room, kaina ya fara ciwo ki fitar min daga ɗaki "

Cikin faɗa take maganar, hannun ta ɗaya riƙe da kanta, tana nunawa Ramlah ƙofar fita

Ramla ta ƙulu matuka ta fice a fusace tare da buga ƙofar ɗakin da ƙarfi.

Falo ta koma inda tabar mahaifiyar ta, kallo ɗaya Mummy tayi mata ta ɗanyi murmushi tace "yana ganki a fusace?"

"Mummy wallahi yarinyar nan bata da mutunci, kinga rashin mutuncin da tamin kuwa, wallahi badan ina gudun abunda ze biyo baya ba sena shaƙeta kowa ya huta"

"hmm Ramla kenan, baki ga komai akan halin ta ba, ni da nake tare da ita ni nake ƙunsar takaici da baƙin ciki, Amma ina jiran lokaci ne wanda...
Bata ƙarasa ba tai shiru tareda yin murmushi ta dafa kafaɗar Ramla tace "karki damu daughter, saura ƙiris komai ya canza, na sama ya koma ƙasa, na tudu ya koma ruwa, a wannan lokaci da dariya zata gagari kare, hmm kiyi hakuri ni da kaina zan canza miki mota, in ɗaukar miki driver kinji?"
Shiru Ramla tayi ba tace komai ba se faman huci da take yi. kaman an mintsine ta tace

"wallahi na tsani yarinyar nan Mummy, bana ƙaunar ganin ta ji yadda aka maida ke da mu kaman wasu bayi ko 'yan Alfarma a gidan nan, ai ko Albarkacin kina Auren mahaifinta ya kamata ace muna da matsayi na musamman"

Mummy tace
"nifa nace kiyi hakuri ko? Komai ya kusa zama tarihi"

********

Yusuf Yana zaune har Bayan sallar isha'i yana kallon labarai, yaji anyi Sallama amsa sallamar yayi tareda ɗan ɓata rai.
Me sallamar ta shigo falon ta ajiye jakarta da mayafi ta ɗan kalli inda Yusuf yake tace
"fushi kuma ake dani, ko a kalli inda nake? Ai gani na dawo"

Yusuf yace "haba Umma tun azahar kika fita se yanzu bayan isha'i duk kaɗaici ya dameni"

Umma tace "kai tafi can, sekace wanda nake shayarwa ba damar in ɗan fita, ka dinga damuwa kenan"

Cikin shagwaba yace "wana keda shi inba Ummana ba? Dole in shiga damuwa duk lokacin da kikayi nisa dani ummana, daga Allah seke se kuma Aikina ku kenan nake da su, niba Abokai ba ko wasu mutane na musamman ke ɗin ce dai, Allah ya jiƙan Abba na, tun abunda ya faru Umma ke kaɗai nake da yaƙinin ƙaunar ki a gare ni baza ta gushe ba, shiyasa bana son kiyi nisa dani"

Tausayin Yusuf ne ya mamaye ta, har zuciyar ta ta karaya hawaye na ƙoƙarin fita daga idon ta, da sauri ta fice ta bar ɗakin da nufin yin Alwala.

Bayan Umman Yusuf ta idar da sallar isha'i suka ci Abincin dare tare suna hira, Yusuf yana ta so ya sanar da Umman sa batun Aikin da'aka bashi a Office amma ya kasa, dan yasan idan har ya gaya mata ranta zata ji babu daɗi, ace ɗanta Yazama direban yarinya, Yarinyar ma mara tarbiyya wadda bata san darajar ɗan Adam ba, dan haka ya bar abun a ransa be gaya mata ba.

Haka ya kwana yana tunanin wace karɓa ze samu a gurin yarinyar nan? Ya aikin ze kasance? Haka yaita tunani har bacci ya ɗauke shi.

Washegari ma Yusuf yayi ƙoƙarin yiwa Umman sa zanncen amma ya kasa, haka yai breakfast ya tafi gurin Aiki.

A office ma kasa wani aikin kirki yayi, wayar sa ya ɗakko yana kuma duba hotunan wannan tsaleliyar yarinyar, ya kuma tuna irin halayen ta da Abbas ya bashi labari. Ɗan tsaki yayi ya ajiye wayar ya jingina da kujera ya dafe kansa yana tunani.

Sallamar Abbas ce tasa ya ɗago kansa, Abbas yace "Yusuf dama ka shigo yau baka nemeni ba?"

"na shigo tun ɗazu ina aiki ne shiyasa ban neme ka ba"

"OK tashi muje, Yallaɓai Suleiman na son ganin mu yanzu"

Yusuf ya miƙe yabi Abbas suka fice, suna zuwa suka gaisa cikin girmamawa, yai musu umarni suka zauna.

Yallaɓai Sulaiman yace "Yusuf nace kuzo tare da Abbas ne dan tabattar da cewar aikin da muka ɗora muku zaku iya, mussman kai Yusuf nasan kana da kula da aiki kuma kana da haƙuri matuƙa"

Cikin girmamawa Yusuf yace "Insha Allah Yallaɓai baza'a samu matsala ba"

"Good kayi taka tsan2 kabi a hankali, karka kuskura wani yasan bincike ne ya kaika gidan, kasan aikin ka base na gaya maka ba, samun matsala a wannan aikin gagarumin hatsari ne da kuma Asara ina fatan kun san hakan"

Yusuf ya risinar da kai yace "Insha Allah ba zamu baka kunya ba sir"

"kai kuma Abbas ku kula yadda ya kamata"

Abbas yace "Insha Allah sir za muyi iya ƙoƙarin mu"

Haka suka ci gaba da tattauna wa akan harkar aiki, sannan Yallabai Suleiman ya sallame su.

Bayan fitowar su Abbas yaita bawa Yusuf ƙwarin gwiwa tareda bashi shawarwari, suka tsara yadda tafiyar tasu zata kasance ranar Asabar zuwa gidan Alhaji Nasir Daula.

Tunda gari ya waye Asabar gaban Yusuf yake faɗuwa, ya rasa dalilin da yasa tun da'aka gaya masa Aikin daze yi yaji gaban sa na faɗuwa a duk sa'ar daya tuna, har seda Umman sa ta fuskanci ya rage walwala, ta tambayeshi yace mata "bakomai" haka Yusuf yaci gaba da Adduo'i.

Yana nan zaune a ɗakin sa ya rasa abunda yake masa daɗi, misalin ƙarfe sha ɗaya na safe Abbas yazo, ya tsaya a tsakar gida suka gaisa da Umman Yusuf sannan ya shiga ɗakin ya same shi.
Abbas ya kalleshi daga sama har ƙasa yace

"gaskiya Yusuf wannan kayan naka ba suyi kama da wanda zeyi aikin direba ba, gaskiya ka canza kaya, ni baka ga kayan da na saka ba"
Se lokacin Yusuf ya lura da koɗaɗɗen Yadin dake jikin Abbas, Yusuf ya ɗanyi murmushi yace "Taɓɗijan, wannan wane irin kaya ne?, ni ban san wani kaya zan saka ba"

Abbas ya buɗe wardrobe ɗin Yusuf, duk kayan Yusuf masu kyaune, da ƙyar ya ɗakko masa wasu ƙananan kaya ya bashi ya saka suma dai basu ji jiki ba, Yusuf ya karɓa ya saka, yace "Allah yasa kar Umma tayi min magana akan kayan nan"

har zasu fita Abbas yace "ɗan tsaya idan muka je gidan Sunana Sani me mangwaro ba Abbas ba "

Yusuf ya jinjina masa kai sannan suka fito, Yusuf ya kalli Ummansa dake kwashe kayan wanke2 yace "Umma zamu fita"
Umma tace "to Yusuf, Abbas ka gaida gida sekun dawo"

Har zasu fita Umma ta kira yusuf tace "Yusuf zo nan"
Dawowa yayi tace "Wannan wace irin shiga kukayi, kalli kayan jikinka be kamata ace ka fita da su ba, Allah ya rufa maka Asiri amma kasa wannan kayan kana yawo a gari"

"Umma shima hakan cikin harkar Aiki ne, idan na dawo zan miki bayani Insha Allah"

Umma tace "Amma harkar aiki shine zaka fita da wannan suturar kamar mara galihu"

"haba Umma wallahi kayan nan da kyansu, kiyi min Addu'a sena dawo"

Ɗan girgiza kai tayi yayin da Yusuf yayi waje da sauri.

Napep suka tara suka hau zuwa gidan Alhaji Nasir, yayin da gaban Yusuf keta faɗuwa.
Tun daga bakin layin shiga rukunin gidan jam'ian tsaro ne ke kaiwa suna komo wa, seda aka musu tambayoyi kafin su wuce da yake sun gane Abbas yana zuwa, aka barsu suka wuce.

Koda suka je gidan Abbas ne ya sallami me Napep ɗin, tun daga waje Yusuf ya fara ƙarewa gidan kallo tirƙash lallai mamallakin gidan yaci ai masa inkiya da Daula.
Suka ƙarasa ƙofara katafaren gate ɗin suka tsaya, Abbas ya ɗakko wayarsa ya kira Isa me gadi, yace masa suna waje.
Befi mintuna uku ba aka buɗe ƙaramar ƙofar dake jikin gate ɗin ya leƙo yana ganin su Abbas ya washe baki yace

"bismillah ku shigo Ashe kaine"
Suka shiga suka tsaya suka gaisa da Isa.
Isa yace "Sani wannan ne ɗan uwan naka daze aikin?"

Abbas yace "Eh shine"
Isa yace "Ya sunan shi?"

"Sunana Yusuf" Yusuf ya bashi amsa

Isa yace  "masha Allah to Allah yaba ka iko, dan seka yi haƙuri aikin akwai samu amma babu sauƙi, bari inje in sanar wa da Alhaji zuwanku"

Abbas yace "shikenan babu laifi"

Bayan tafiyar Isa, Yusuf ya kalli harabar gidan, wasu irin motoci ne masu rai da lafiya a tsaye a gefe ɗaya, yayin da ainihin ƙofar shiga katafaren gidan se kayi wani gajeren tattaki daga gate ɗin kafin ka kai ga ƙofar.
Yusuf ya numfasa yace

"wai ni Abbas ya aka yi rukunin gidajen nan jam'ian tsaro ke gadi, Amma kuma nan gidan naga

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login