Showing 69001 words to 72000 words out of 135096 words

Chapter 24 - Akidata Book 1 Hausa Novel Complete

01 Jan 2025

766

ta kira lambar Daddy, ya ɗaga suka gaisa yace "Lovely meyasa wayarki bata shiga?"

"Jinyar Roux nake, bata da lafiya"

"To Allah ya bata lafiya, dama munyi waya da Daddynki yau baƙonki zezo"

"waye baƙona?"

"Fahad mana, zezo ya ganki ku gaisa dan Allah Lovely banda wulaƙanci ko makamancin haka, shima ɗanuwankine Yayan Ramadan ne, yana nan tafe Anjima Insha Allah"
Nan da nan dukkan annurin fuskarta ya ɗauke ta dire wayar tace

"Ina nan ina jiran zuwan sa, yazo ya sami Widad Nasir Daula, yazo yaga mahaukaciyar da'ake shirin ƙaƙaba masa"

Ayshercool
07063065680

                     _*AƘIDATA*_
       

PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

*Story and written by*

_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_

The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *

I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum

Haƙƙin Mallaka ⚠ : Littafin nan mallaki nane, tun daga sunan labarin zuwa abunda ya ƙunsa, ban yadda wani ko wata ya sauyamin ko yin Amfani da wani ɓangare na labarin ba ba tare da izinina ba, Nagode

https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends

ELEGANT ONLINE WRITER'S

                         PART1
                                Page 18





Binta da Kallo Yusuf yayi, ganin yadda ta canza lokaci ɗaya annurin fuskarta ya ɗauke, tabbas akwai drama yau.

"Jeka anjima zamu fita" ta faɗa ba tare da ta kalli Yusuf ba

Miƙewa yayi ya fito daga ɗakin ya nufi hanyar fita, ba zato Amal tasha gabansa wanda ya tilasta masa tsayawa.

"Yusuf ka fara ƙoƙarin tsallake iyaka, Yusuf meyasa baka tsoron Allah ka dinga nuna kai na Allah ne amma baka kyautawa rayuwarka, Yusuf kai mugune mara tausayi baka da tausayi baka tausayina, ko kaɗan soyayyata bata da daraja a idonka, na rasa meye a tsakaninka da Widad, wallahi akan Son da nake maka banƙi komai ze faru ya faru ba, wallahi akanka koni ko Widad "

Girgiza kai Yusuf yayi yace " keya dace a nemawa maganin mahaukata ai, nayi iya ƙoƙarina in ganar dake amma kin kasa ganewa, bana Soyayya bani da ra'ayinki, ba abunda ya kawoni nan kenan ba, ki ƙyale rayuwar Yusuf ta huta, tun kafin in nuna miki ainihin kalata na gaya miki"

"Haka kace?"

"Eh haka nace, ko baki da kunne ne?"

"bayan ƙalubalen dake gabanka saboda Kasancewar ka da wannan mahaukaciyar, ka shirya ƙalubalen da zaka fuskanta daga gareni"

"duk wanda ya dogara da Allah, to ya isar masa"

Yusuf ya bata amsa yasa kai ya fice, ya barta tana mamakin wannan taurin kai irin na Yusuf.

Bayan Suleiman ya gama nazarin abunda Yusuf ya tura masa, yayi mamakin jajircewa da kuma ƙoƙarin da yayi, tabbas Yusuf jajirtacce ne me kuma hikima da iya aiki, amma meye dalilin da yasa Abbas yakeson lallai a ƙwace aiki a bashi? Lallai akwai wata a ƙasa Abbas yana da fuska biyu.

Yusuf yana nan zaune yana ganin yadda aketa aiken su Murtalah, anata shirye shirye da alama akwai baƙon da gidan zasu tara yau, shi dai yana guri ɗaya nasa ido.

Ƙarfe biyu na rana Yusuf ya dawo daga masallaci sallar Azahar, wata dalleliyar mota ta shigo gidan, wani matashi ne ya fito daga motar, jikinsa sanye da ƙananan kaya kallo ɗaya zaka masa kasan ɗan hutune, ya ɗaga kai ya ƙarewa gidan kallo tsaf, su Isa mai gadi suna gaisheshi yana ɗaga musu hannu ba tare da ya amsa ba.

Shidai Yusuf be kula shi ba, sema ɗauke kai da yayi kamar bega Matashin ba, ba zato suka jiyo muryar Ramla ta taho da gudu tana faɗin "Oyoyo my heart beat"
Ba kunya suka rungume juna a gurin.

Fahad yace  "I miss you so much Baby"

"I miss you too mine" Fahad yayi kissing ɗinta a forehead yace 
"kin ƙara kyau my Ramlat"

"Kyau ai kaine ka ƙara kyau, mutanen Amurka muje daga ciki ko"

Suka shige hannunsu saƙale da juna.

Nura direba yayi tsaki yace  "ƙaryar banza burodi a lefe, waisu a dole turawa ba kunya taje ta rungume ƙasurgumin gaddi tana ce masa Baby tir da wannan hali"

Shidai Yusuf bece musu komai ba suka ci gaba da gulmarsu.

A babban falon dake ɓangaren Hajiya Halima aka sauki Fahad, suka dinga hira yana basu labarin Anwar shima ya kusa dawowa.

Fahad ya ɗan ɓata fuska yace  "Hajiya wai ina Yarinyar take ne? Ance inzo in ganta karta ƙullamin wani sharrin a gurin father ta jamin magana, danni sam ba'a kyautamin ba da'akace zan Aureta"

Ɓata rai Ramla tayi ta miƙe ta bar falon, Hajiya Halima tace  "Aikuwa dai an gama da kai, dan yarinya ce ba tarbiyya ga kuma uwa uba hauka"

"wallahi Hajiya na rasa wani irin tunani Daddy yayi haka, da yasa yake son illata rayuwa ta, nazo ne dai kar'ace banzoba amma sena tabattar da na mata rashin mutunci yadda ko ganina tayi ba zata nuna ta sanni ba"

Amal ta kalleshi a yatsine, sam Fahad haushi yake bata yana ta wani iyayi shi lallai ya dawo daga Turai, indai Widad ce ze gane kurensa ne.

Ba kunya Fahad ya miƙe yace  "Hajiya bari inje gurin Ramla, naga tayi fushi"

"Shikenan kunfi kusa ai"

A ɗakinta ya sameta tayi kicin kicin da rai, ta haɗe fuska, ya zauna kusa da ita ya janyota jikinsa yace  "haba Baby, meye abun damuwa nifa danke nazo gidan nan, ba dan wata banza ba meye na ɓata rai, ki tsaya kiga matakin da zan ɗauka yau akanta"

"Fahad inajin tsaro fa, su Daddy suna san Auren nan naku, zasu iya tursasa maka fa"

"waye ya gaya miki? Kamarni aina wuce ajin amin auren dole, calm down Baby" ya faɗa yana jan hancinta

Murmushi Tayi tace  "bari in shirya maka Abinci a dining, na maka girki"

Kafin yayi magana wayarsa ta fara ringing yace "excuse me Daddy ne"

Ya ɗaga wayar yasa a kunnensa yace  "hello Daddy"

"Fahad kaje gurin nata kuwa?"

"Amm.. Eh ina gidan amma ban ganta ba"

"to ka tsaya ku gaisa, sannan yarinyar nan ka bita a hankali bata da cikakkiyar lafiya, kabi a sannu ka kwantar mata da hankali"

Tura baki Fahada yayi yace  "Haba Daddy sekace uwata, yarinyar ma ashe mahaukaciya ce"

"ba zakayi ba kenan?

" Naji zanyi "

" idan naji wani abu na rashin kyautawa daga ɓangarenka sena saɓa maka, shashasha wanda be san halacci ba, aiko wani kaga ze Wulaƙanta 'yar Nasir Daula kai me tare matane"
Bulama yayiwa Fahad tatas sannan ya kashe wayar

Fahad yace  "kar wannan abun ya ɗaga miki hankali kinji babyna, ina tare dake, nasan matakin da zan ɗauka"

Ta jinjina masa kai suka fito babban falo, Fahad yace  "kiramin ita".
Ramla ta nufi part ɗin Widad, a falonta ta tarar da ita tana kwance a ƙasa ta ɗora ƙafafunta akan kujera, mageneta na kan cikinta a kwance, itakuma tana danna waya.

Ramlah tace "Fahad yazo, yana falo yana jiranki"

Ai kamar da kujerun gurin Ramla ke magana ba da Widad ba, dan ko motsi ba tayi ba.

"Magana fa nake miki"

"And then? Ko bayan hauka kuma inada larurar kurmanta ne? Kinyi magan na jiki kin cigaba da tsayawa a kaina, ki matsa daga kaina"

"Amma se ki bani amsa ai, tunda keba kurma bace"

Miƙewa Zaune Widad tayi tace barmin falo.

"Amma...

" ki fice nace, ko Bulama ne yazo da kansa be isa ya tursasani in saurare shiba, kije ki gaya masa ya cigaba da jira idan ze iya daga nan zuwa lokacin da zan fito, idan baze iyaba ze iya komawa ya tambayi Bulama tsarukana, idan ya shirya ɗauka ya sake dawowa, fita ki barmin ɗakina"

Buɗe baki Ramla tayi tabi Widad da kallo, wato ita kullum rashin mutuncinta ƙara ta'azzara yake, ina ita ina zuwa ta Sanarwa da Fahad wannan baƙin saƙo, mussman shi dabe san kan Gimbiyar ba.

Ramla ta juya ta fice ta koma main falo tace  "Baby naje yanzu ta tashi daga bacci zata shirya ta fito"

Ramla ta zauna a kusa da Fahad suka shiga hirarsu, tun Fahad yana tsammanin fitowar Widad harya fara ƙulewa.

"Ramlah wai yarinyar nan ba zata fito bane?"

"Fahad baka ga komai ba, indai akan wannan Yarinyar ne, idan ka kuskura ka aureta taka ta ƙare wallahi"

"zan saita mata zama kuwa, dan nafi ƙarfin wata banza ta Wulaƙanta ni, bari inje akwai wani friend ɗina a quarters ɗin nan, inaso mu gaisa ina dawowa"

"to ka fara cin Abincin mana"

"karki damu yanzu zanje in dawo"

Ramlah ta rakashi har gaban motarsa, kallo ɗaya Yusuf yayi musu ya ɗauke kai, Fahad yace  "Baby wai waye wannan ne?"

Yai maganar yana nuna Yusuf, yamutsa fuska tayi tace  "Direban wannan sakaryar ce"

"yanzu wannan ne direba?"

"direba ne, sedai ya samu gindin zama fiye da duk wani me aiki a gidan nan, shiyasa har wani jin kansa yake"

"ku kuka ƙyaleshi baku saita masa zama ba"

"ni yanzu ba shine a gabana ba, kaje kayi sauri ka dawo kaci Abinci"

Suka yi sallama Fahad ya tafi, se bayan ƙarfe huɗu Yusuf yaga message ɗin Widad, ya miƙe ya shiga part ɗinta.

Yau dogon skirt ne a jikinta baƙi, da wata riga me dogon hannu ta ɗora ɗan ƙaramin veil akanta, tayi kyau sosai kayan sun zauna cif a jikinta sedai ana ganin duk wani shape na jikinta.

Tunda Yusuf ya shigo ba tayi magana ba, se sabgar gabanta take yi.

"Ya jikin magenki?" ya tambaye ta

Abunda Yusuf ya faɗa ne yasa ta ɗagowa da sauri tace  "i think she got better now, she's able to play"

"Allah ya bata lafiya, na ɗauka mutuwa zata yi ashe da sauran kwananta a gaba"

Harar Yusuf tayi ta ɗau jakarta tayi waje, binta yake a hankali baya sauri yana tafiya kamsr kazar da ƙwai ya fashewa a ciki , ta juyo ta kalle shi tace  "wannan wace irin tafiya ce kuma?"

"Nifa gaskiya Yunwa nake ji, tun safe ban kuma cin komai ba, kuma kince kar inje ko ina ban samu na fita naci Abinci ba"

Hararasa tayi tai gaba abunta, suna fitowa falo taga an shaƙe kan dining da Kulolin Abinci, wani murmushi tayi ta kalli Yusuf tace  "jirani anan"
Ta juya ta koma part ɗinta, fitowa tayi hannunta ɗauke da magenta ta nufi dining.

Alama ta yiwa Yusuf da hannu yaje, ya nufi kan haɗaɗɗen dining ɗin da'aka shaƙe da kayan Abinci.

Tai masa alama da ya zauna, yaja kujera ya zauna tace  "buɗe duk abunda kake so a gurin nan kaci"
Kallonta yay yace  "Amma ranki ya daɗe, naga kamar baƙo aka shiryawa teburin

" bana son musu ko jayayya, umarni na baka ba shawararka nake nema ba" ta faɗa cikin faɗa da bada umarni.

Yusuf ya shiga buɗe Kulolin, Abinci ne kala kala kamar ba'asan zafin nema ba, yasan duk tsiya wanda aka shiryawa Abincin baze iya cinyewa ba.

Widad ta zuba kifi akan plate  ta miƙawa magenta, Taja plate itama ta ɗiba ta zuba, dama Yusuf yunwa yake ji ga Abinci yayi daɗi nan ya dinga zurawa
(samun guri direba a dining 🤣🤣🤣)

Ramla ce ta fito itada Amal suna magana, me zasu gani Widad da mage ga direbanta suna cin Abincin da'aka shirya karɓar baƙon Ramla sannan baƙon Widad, Amal tayi saroro tana kallon Ramla.

A fusace Ramla ta ƙarasa dining ɗin kamarta fashe da kuka tace  "Widad wane irin wulaƙanci ne wannan, ta yaya za'ayiwa baƙo girki ki zauna kina ci naga dai idan munyi Abinci ba ci kike ba, dan kawai ki muzgunamin kika yi haka? Saboda wulaƙanci kuma ace harda direbanki saboda tsabar tozarci"

Shidai Yusuf bece komai ba, Widad cikin ko in kula tace  "Ramla me direban nan nawa yayi miki ne haka? Naga kuna takun saƙa sosai dashi, kina yawan manta wani abu Ramla, duk wanda yake aiki a ƙarƙashina matsayinsa ɗaya da duk wanda yake zaune a gidan nan ƙarƙashin kulawa ta, dan haka babu laifi dan na bashi Abinci ko?"

Cike da ɓacin rai Ramlah tace "Amma fa baƙo nayiwa, ta yaya zaki min haka? Ina laifin kice inda saura in zuba masa"

Widad tace "waini wannan baƙon gurina yazo ko gurinki?"

Ras gaban Ramla ya faɗi jin tambayar da Widad tayi mata,
"naga alamar gurinmu yazo nida ke, nasan kina tunanin me zakice masa ne, idan baki da abunda zaki gaya masa kice kinyi masa girki, 'yar masu gida tayi yadda take so dashi"

Hajiya Halima da ta fito ta riski rigimar tace  "Amma Widad baki kyauta ba, ya za' ayi kidinga nuna direba yafi 'yan gida"

"Ni bana abu dan in kyauta dama, bana abu dan in birge kowa, muddin zan cigaba da saka doka ana watsi da ita nikuma zan cigaba da ɗaukar matakin daya dace, if i can recall a falon nan nayi kashedi akan a dinga bawa direbana Abinci, akayi fatali da dokar aka barshi da yunwa tun safe, nayi abunda ya dace ne, ga ragowa nan mun bari idan baƙon naki yana buƙata seya ci dan naga ƙirarsa ta mayuntace dama kamar baya ƙoshi"

Tai maganar tana kallon Ramla, tare da goge hannunta da tissue.
Da gudu Ramla ta bar falon tana kuka, ita kanta Amal ba taji daɗin abunda Widad tayi ba taji haushin hakan.

Yayi parking ɗin motarsa a harabar gidan ya fito daga motar, yana rufe motar tare da amsa waya, kamar an ce ya ɗaga kai ya hangota tana fitowa, fara ce sosai fari me ɗaukar ido, tana da matsakaicin tsayi sannan tana da shape me kyau.

Tabbas idan ba gizo idonsa ke masa ba wannan itace Yarinyar da Anwar yake kallo a hoto yana nuna masa, kenan itace Widad ɗin daza'a haɗa shi Aure da ita? '

Cigaba da Ƙarasowa Widad tayi, Yusuf na bayanta da jakarta a hannunsa, tana kallon Fahad suka zo zata wuce shi
"Widad Nasir Daula" Fahad ya kira sunanta.

Ta tsaya cak bata juyoba tace  "Fahad Bulama"

"Amma kin san gurinki nazo kina kallona zaki wuce ki tafi"

A hankali ta juyo cike da izzarta ta ban mamaki, ta ƙare masa kallo sannan tace  "banyi tsammanin kaine Fahad ɗinba ai, na ambaci sunan ne dan tabattar da kai ɗinne ko ba kaiba, dan abun da mamaki ace kaine Fahad ɗin, ina jinka faɗi abunda ke tafe da kai"

Fahad ya jinjina kai yace "tun ɗazu nake gidan nan ina jiranki, meze hana mu shiga daga ciki mu samu guri mu zauna se muyi magana"

"bani da wannan lokacin, yi maganar ka anan inajinka" ta faɗa tana kallon Idon Fahad.

Fahad be taɓa zaton haka Widad take ba, ta kai mace har mace sedai tana da girman kai da izza.

Ya kalli Yusuf yace  "Amm ko zaka iya bamu guri, zamuyi magana"

"Ko da Bulama zanyi magana agabansa ake yi, dan haka cigaba da maganar ka" ta faɗa cikin isa

"Amma kin san Aure zamuyi, meyasa zaki dinga gayamin magana haka ba respect, har ki dinga kiran sunan mahaifina kai tsaye"

"Anƙi ayi respecting ɗin naka, Babana ma ina faɗar sunansa balle wani Bulama, kai a tunaninka  kai namijin daze tunkareni a matsayin wadda ze aurane?, ɗan sake kallon kanka mana sannan ka kalli da wadda kake magana kasan niba ajinka bace, haka Bulaman be gaya maka yadda mukayi da shi bane? Bana soyayya ban yadda da ita ba kuna ba zanyi Aure ba, ana ƙoƙarin cusamin kaine kawai kuma bani da ra'ayin Auren namiji irinka, dama ka kai Namiji ne zan iya maleji, amma sam baka da ƙira da zatin da za'a kalleka a kiraka Namiji balle ace mijin Widad, ka sani koda ace Widad nada ra'ayin Aure bazan taɓa zaɓarka a matsayin miji ba, banga alamar nagarta da kamala a tare da kai ba, idan kana da zuciya kaje ka gayawa Babana Bulama baka son haɗin Auren nan, 'yar tasa bata sonka, in baka da ita kuma kace masa kana son Auren kaga yadda zamu ƙareta da kai "

Aiba Fahad ba hatta Yusuf jikinsa yayi sanyi da wannan mummunan cin zarafi da'akayi wa Fahad, koba komai ɗan uwansa ne namiji.

Gaba ɗaya Fahad kasa magana yayi, be taɓa tunanin haka Yarinyar nan take ba, duk wadda za'ayi sedai ayi amma seya auri Widad, sedai hakan yayi sanadiyyar ɓatawarsa da Anwar, ze tabbatarwa da Widad shi Namiji ne, Namijin ma irin wanda kowace mace keda burin samu, be tsaya ba ya shige motarsa ya fice.

Yusuf yana diving ya kalli Widad data cika tayi fam yace  "Madam amma kamar abunda kikayi wa wannan bawan Allah be dace ba, bakya tunanin ya Alhaji zeji idan yaji labarin abunda kika yi, baki kyauta ba

"Yoseef!!!"  karo na farko da Widad ta kira sunansa cike da gargaɗi, koda wasa bata taɓa attempting kiran sunansa ba, danshi be zaci tasan sunan nasa bama, sannan yadda ta faɗi sunan nasa yasha banban da yadda ake kiran sunan nasa, dukda Wasu lokutan hausa bata isheta ba, idan ta faɗi wani abun yasha banban da yadda ake faɗa.

"karka kusakura in dawo kanka, meyasa kake son shiga rayuwata, ban taɓa ganin mutumin da nake ɗagawa ƙafa kamar kai ba, shiumrun da nake maka Albarkacin mahaifina kakeci, kar in ƙara yin abu kace zaka yi challenging ɗina, duk abunda kaga nayi inada dalili karka ƙara challenging ɗina if not i will teach you a lesson you never forget "

Tai maganar a matuƙar fusace cike da gargaɗi.

" Allah ya huci zuciyarki, Allah ya baki haƙuri insha Allah ba zan sake ba"

Ya kaita gurin saloon kaman yadda ta buƙata.

Ramlah tayi kuka sosai akan wannan wulaƙanci da Widad tayi mata, seda idanunta sukayi jawur saboda kuka, ƙanwar bayanta dan kawai suna zaune a gidansu ake musu wannan wulaƙancin haka.
Mummy ta tako tazo gaban gadon Ramla ta zauna ta dafata tace  "Am sorry daughter nasan....

"Mummy dan Allah ki ƙyaleni wallahi wannan karon sena ɗau mataki, haba abun ya isa haka wace irin rayuwace wannan muke a gidan nan se kace zamanin Bayi, wallahi sena ɗau matakin daya dace"

"A'a Ramla tynda kikaga na haƙura ban ɗau mataki ba kema haƙuri zakiyi,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login