Showing 126001 words to 129000 words out of 135096 words
tace "Yoseef jikinka zafi yake sake ɗauka fa"
Kasa magana yayi, sosai jikinsa yake rawa, da sauri ta miƙe ta ɗakko bargo ta rufa masa.
Haƙoransa se karkarwa sukeyi, ta ɗebo ruwa ta duba kayan ta, ta ɗakko wata vest ɗinta, ta shiga shafa masa ruwa a jikinsa, amma kamar tana ƙara rura masa wuta, jifa tayi da abunda take jiƙa masa jikin ta rungume shi ta fashe da kuka.
Share, share and share please 🙏 🙏
(insha Allah ranar 20th ga wata zan fara posting ɗin book 2&3, befi saura page biyu ba in kammala book 1, nagode ga wanda suka fahimceni, wanda suka zageni ma nagode, wanda suka shirya siya zasu iya tuntuɓata ta wannan lambar 07063065680 nagode ƙwarai dagaske, a nunamin ƙauna ta hanyar siyan littafin akan farashi me rahusa, Akwai garaɓasa ga mutum biyar ɗin farko da suka fara siya, cakwakiya da warwara suna book 2&3 don't missed it guys sena jiku"
Domin gyara sharhi, ko shawara
Ayshercool
07063065680
_*AƘIDATA*_
PERFECT WRITERS ASSOCIATION
(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)
https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*Story and written by*
_*AISHA HUMAIRA _
(Daddy's girl)*_
The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *
I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum
Haƙƙin Mallaka ⚠ : Littafin nan mallaki nane, tun daga sunan labarin zuwa abunda ya ƙunsa, ban yadda wani ko wata ya sauyamin ko yin Amfani da wani ɓangare na labarin ba ba tare da izinina ba, Nagode
https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends
NOT EDITED (BANYI EDITING BA)
ELEGANT ONLINE WRITER'S
PART1
Page 42_43
Sosai Widad ke rusa kuka, Yusuf kasa magana yayi sedai ya ƙanƙameta a jikimsa, yana dukan bayanta da sigar rarrashi.
Can ta miƙe cikin hanzari ta fito waje, tana ta goge Hawaye ta samu Gwaggo tace "Mama Yoseef bashi da lafiya"
A gigice Gwaggo tace "Subhanallah, meya sameshi?"
Maimakon Widad tayi magana seta fashe da kuka, Hanne da take wanke wanke take ta dire kwanukan ta miƙe tsaye.
Gwaggo tace "Yi shiru, muje muga jikin nasa"
Hansai ma da Hari gaba ɗaya jikinsu yayi sanyi, ɗaki gwaggo tabi Widad ta tarar da Yusuf yana ta karkarwa a cikin bargo.
Gwaggo tace "Subhanallah, sannu Yusufa Allah ya baka lafiya"
Be iya magana ba se jinjina mata kai da yayi, Hari tace "Yaya meya abunyi yanzu, ga Malam baya nan yaje taronsu na masu sarauta"
Hansai tace "ina sauran saiwoyin nan, a jiƙa a bashi mana, kan malam yazo asan abunda yakamata ayi"
Widad ta koma kusa da Yusuf, tana ci gaba da share Hawaye, Hansai tace "Kidena kuka in Allah ya yadda ze samu lafiya"
Hanne ce ta shigo ɗakin itama, ta leƙa taga yadda Yusuf ke rawar jiki, gaba ɗaya se taji jikin ta yayi sanyi, a ranta tace 'dama wannan kinibabbiyar zazzaɓim ya kama'
Suka dinga rarrashin Widad, yayin da Yusuf ko iya ɗaga kansa ba yayi, Hansai ce ta kawo wasu jiƙe jiƙe wai a bawa Yusuf, Widad ta kalli kwanon ta girgiza kai, cikin kuka tace "A'a wannan abubuwan suna da hatsari ga lafiya, nidai a kai shi Asibiti kawai"
Hari tace "Asibiti, ai kuwa ya mutu ba'a jeba, dan daga nan kafin aje Asibiti har mutum ya mutu akai gawarsa ba'a isa ba"
Sake rushewa Widad tayi da kuka tace "In Allah ya yadda baze mutu ba, semun koma gida tare, dan Allah Yoseef kaji sauƙi"
Gwaggo tace "Hari kina da matsala wallahi, wace irin magana ce haka ba tsari, kalli yadda kika sake tayar mata da hankali fa"
Hari tace "Wallahi Yaya ni bada wani abu na faɗa ba, misali dai na bata, amma Wudas kiyi haƙuri, Insha Allah ze warke amma Asibiti kam kafin aje shi sedai idan amalanke za'a samo a ɗorashi, a fita can wajen gari sannan...
Hansai tace" haba Hari, ana rarrashin ta kina ƙara Sakata kuka, Amarya karki damu insha Allah za'a kai shi Asibiti bari Malam yazo "
Widad ta riƙe hannun Yusuf tana ci gaba da kuka, Hanne tace " Sannu Allah ya baka lafiya "
Har magariba sannan megari ya dawo, ya tarar da zancen rashin lafiyar Yusuf, megari yace " me aka bashi na magani? "
Hansai tace " Na jiƙo tazargade nace a bashi, matarsa tace baza'a bashi ba sedai akai shi Asibiti"
Megari yace "Kin san mutan birni, basu fiye amfani da irin wannan magunguna namu ba, Amma yadda za'a kai Yusuf Asibiti nake ji, kafin Aje ya ƙara galabaita, dan miƙaƙiyar tafiya ce ta gaske"
Widad tace "Yanzu duk garin nan babu Asibiti, ko chemist babu?"
Hindu tace "kamis ɗayane a garin nan, shima a cikin kasuwar yamma da gari yaje, ba'a buɗeshi se ranar kasuwa"
Dafe kai Widad tayi tana faɗin "Innalillahi wa inna ialaihi raji'un, wane irin abune haka, gari kamar wannan me ɗauke da al'umma suna rayuwa a ciki, ace babu gurin shan magani, Yasalam sannu Yoseef Allah ya baka lafiya"
Bece komai ba, se riƙe hannayenta da yayi, da hannu yayi mata nuni da zeyi alwala, Gwaggo ta bada ruwan ɗumi, Widad ta sirka masa, se a ɗaki yayi alwalar dan ko tsakar gida baya iya fita, saboda azabar sanyin da yake ji.
A zaune Yusuf yayi salla, Widad idanunta har sunyi jawur saboda kukan da tayi, ta kalle shi tace "me zaka ci? Kaga tun safe baka ci Abinci ba"
Girgiza mata kai yayi, alamar baya son komai "
Ya nemi guri ze sake kwanciya, Widad tace " kwanciyar nan zata ƙara kashe maka jikine, ka bari gobe in Allah ya kaimu duk yadda za'ayi za'a san yadda za'a kaika Asibiti kaji, sannu Allah ya baka lafiya "
Ta ƙarasa maganar idonta fal hawaye.
Murmushi Yusuf yayi, ya kai hannunsa dake rawa fuskarta ya goge mata hawaye tare da girgiza mata kai, alamar ta dena kuka.
Haka Widad ta raba dare ba tare da tayi bacci ba, data motsa sedai tayi ta shafa masa ruwa, amma jikinsa kamar wuta.
Tun tana yi da ƙarfinta, har bacci ya mamaye idonta ta kife a gurin tana bacci, a haka ya janyo ta jikinsa, yana kaɗe mata sauro yayin da ya kasa bacci saboda azabar ciwon gaɓoɓi da zafin zazzabi.
Da Asuba Widad ta farka, tana buɗe ido tace "Yoseef"
Da Mm ya amsa mata.
"baka yi bacci bane?"
"Nayi ya faɗa a hankali"
"ya jikin naka?"
"Naji sauƙi, samomin ruwan Alwala"
Ta miƙe ta fita waje, ta kawo masa ruwa yayi alwala yayi sallar Asuba.
Gwaggo tayo kunu ta aikowa da Yusuf, kasa sha yayi saboda yana jin jiki, amma saboda kukan da Widad take, ya karɓa ya sha kaɗan, haka nan ya amayar da shi gaba ɗaya, nan fa abun duniya ya ishi Widad, ta kasa cin Abinci se kuka.
Megari ya tashi ɗansa, yace "yaje can gaban su, ya aro babur azo a tafi da Yusuf Asibiti"
Har wajen ƙarfe sha ɗaya Widad tana tare da Yusuf, ko tsakar gidan ta kasa fita, ta kama yatsunsa tana ja masa a hankali kamar yadda yake mata, sam taƙi cin komai.
Wajen sha biyu na rana Saleh yazo gidan, zuwan Saleh ba ƙaramin daɗi yayi mata ba, Megari yace "Alhamdilillah, kazo a dai dai, dama Yusuf yana kwance babu lafiya na aika azo ds babur a kai shi Asibiti, tun jiya ko magana baya iyayi"
A gigice Saleh ya tafi ɗakin su Widad, Hindu da Hanne dasu Gwaggo suka bishi dan a yanke shawarar ƙarshe game da rashin lafiyar nasa, Saleh yayi Sallama Widad ta amsa, ya shiga ɗakin ya tarar da Yusuf ya ɗora kansa akan cinyar Widad, idanunta sunyi ja har sun fara kumbura.
Seda Saleh ya ɗanyi turus dan tabattar da abunda yake gani, wanda ko a wasan kwaikwayo akace Widad zata yi hakan baze yadda ba.
Ya ƙarasa cikin ɗakin, ya kalli Widad yace "meyasa me shi haka?"
Tsuke Fuska tayi sannan tace "zazzabi yake"
Ya kalli Yusuf yace "Sannu Yusuf, bari inje wannan sedai ko mota a samu, ba zaka iya hawan babur ba, se inzo akaika Asibiti"
Yusuf be iya cewa komai ba, se jinjina masa kai da yayi, tun a hannun wanda suka sace su Widad ta jinjinawa jarumta irin ta Yusuf, tunda harta kai ga baya magana to tabbas ta tabbatar yana jin jiki ƙwarai.
Saleh yace "Ranki ya daɗe bari inje a duba motar ko, se a zo a tafi dashi"
Cikin isa da take nunawa ma'aikatanta tace "ina fatan kaga halin da yake ciki, dan haka bana buƙatar ɓata lokaci, duk inda abun hawa yake a nemo azo a kai shi Asibiti, kar ya sake galabaita"
Mamaki ne ya kama su, Yadda Widad take wa Saleh magana cikin isa da gadara, dukda irin taimakon da yayi musu, ga kuma tarin tazarar shekaru da ya bata, amma take masa wannan isar haka, se suka ga ta canza kamar ba Widad ɗin dake magana sanyi sanyi ba.
Saleh ya ɗago ya ɗan ƙurawa Widad ido na wani ɗan lokaci.
Cikin tsawa tace "Kamar na gaya maka bana son ɓata lokaci, ka tsaya kana kallona, he's condition is getting worse, ko nawa za'a kashe ayi a nema masa lafiya" tai maganar tana wani sauke wahalallen numfashi.
Cikin harshen turanci Saleh yace "You are under my care now, why are you still shouting at me like this, so you are still rude up to now"
"My name remains Widad Nasir, Nothing will make me change, No matter what you did to help me, my policies remains constant, nothing has change"
Cikin rawar sanyi Yusuf ya shiga girgizawa Widad kai alamar tayi shiru.
Sudai mutan gida se binsu su kayi da ido.
Hanne ce taja wani uban tsaki tace "Aikin banza, ace mutum baya ganin girman kowa, se tsabar wulaƙanci da rashin ta ido"
Da sauri Saleh yace "Ke dawa kike? Idan kika kuma gangancin yin wannan mummunan furicin akanta duk abunda ya biyo baya ke kika siya, ko dan kin ganta zaune a gidanku, kin sam wace ita?"
Gwaggo tace "ayi haƙuri dai, naji tsayuwar Babur a waje, ina ga Ila ne ya dawo, maza jeka ku samo akori kura a kai shi Asibiti"
Haka akayi, Saleh yaje suka hau babur suka tafi nemo akori kura.
Sosai Fahad ya fara missing ɗin Ramlah, dan ba ƙaramin hutawa yake da ita ba, itama a ɓangarenta tana missing ɗinsa, amma tana so ta tabattar da idan dagaske yana sonta, kamar yadda Amal ta goranta mata.
Fahad ya ɗau waya ya kira Ramlah, tana ganin kiransa babu ko jan aji ta ɗauka da rawar jiki
"Hello Baby, shine kika watsar dani ko?"
"ba watsar da kai nayi ba, kaine ka watsar dani ka kasa Yimin abunda na tambayeka"
"Ramlah ki gane, baƙi nayi ba fa, kin san halin Daddy, ko zancen baya so na ɗakko masa, yaƙi saurarata sam gashi bani da lafiya se tunaninki nake, kuma nasan damuwa ce tamin yawa"
"dan Allah dagaske baka da lafiya? Ai ban sani ba, ohhh Sorry please i understand you, nasan kana son za kayi iya ƙoƙarin ka, bakomai hakanma nagode sosai my love"
Yayi ajiyar zuciya yace "Never mind baby, yanzu ya za'ayi ne? Inzo mu ɗan fitane yau ɗin?"
"Ni gaskiya a'a"
Ya ƙara marairaicewa yace "please na, ko so kike ace kizo ga gawata?"
"No bazata kaimu ga haka ba, kazo anjima mu fita, kasan bana son dsmuwarka my one"
"wow that's my only Ramlah, na ɗauka nikaɗai nake sonki na damu dake ai, shikenan dan Allah ki ƙure a daka, kiyi kwalliyar nan wadda ke narkamin zuciya"
"shikenan karka damu, sekazo"
Sukayi Sallama Fahad yace "akanme zanso a sako wani Anwar, yazo ya hanani rawar gaban hantsi, ai gara ayi ta tsare shi a can kowa ma ya huta.
Wasa2 labari ya karaɗe gari, an nemi Daula an rasa, abu kamar wasa kusan sati biyu amma babu ko wanda yaji ɗuriyarsa, Alhaji Munir ne da Alhaji Haruna zaune a office, sunyi jugum jugum.
Alhaji Munir yace "Nifa gaba ɗaya abubuwan nan suna nema su kwaɓe, wai kamar almara har yanzu babu ɗuriyar Daula, babu ta wannan shegiyar 'yar tasa me baƙin taurin kai kamar ubanta, kuma gashi an ɗaga taron kasuwanci komai ya watse, nifa gaba ɗaya na fara karaya"
Alhaji Haruna yace "wace irin karaya kuma? Ai ba gudu ba ja da baya a wannan harkar, mun ɓata shekaru da dama akan wannan sabgar, kawai kuma semu sare yanzu, a'a baze yuwu ba, ni yanzu na fara tunanin anya ba wanine yake mana maƙarƙashiya ba?"
"Hmm bari kawai, ni kaina nayi tunanin hakan, an tuhumi doctor Sufyan har yanzu yace be san komai akan ɓatan Daula ba, ga ɗan gidan Hajiya Halima shima da yake kula da Daula, an tsare shi amma yace besan komai ba, wannan wane irin lamarine haka?"
Alhaji Haruna yace " Wani abun haushin ma, Halima se shiga take tana fita a sakar mata ɗanta, tana neman ta tona mana Asiri "
Alhaji Munir yace " Ai duk wata sabga daza'a saka mata a ciki, to tabbas za'a sha takaici, tun farko nace kar a saka matar nan amma aka ƙi bin shawarata, gashi nan komai se kwaɓewa yake"
"Haba Munir, kai badan da temakonta ba ai da wata nasarar bamu sameta ba, ta bamu gudunmuwa sosai, sedai yanzu tana neman ta ɓata rawarta da tsalle"
Alhaji Munir yace "Kai ba wannan bama, kasan se siyar da manyan motocin Daula, tana ta holansuba ɓoye tana siyarwa, da wasu ƙananan kadarorinsa a ɓoye"
Zaro ido Alhaji Haruna yayi yace "bangane ba, kai waye ya gaya maka?"
"Al'amarin duniya baya ɓuya fa, nima labari naji kuma kana ganin mun fita wayo ne, kar take kallonmu matar nan mugun wayo ne da ita fa, tsohuwar 'yar duniya ce"
Shiru Alhaji Haruna yayi yace "Amma wannan ta cika muguwa, rabu da ita in tasan wata ai bata san wata ba, zamuyi magana da Musa, su tattauna da Bukar, muga yadda zamuyi maganinta"
Se wajen la' asar sannan Saleh suka zo da Mota, sedai akori kuran ta ɗanfi wadda aka kawo su ƙauyen a ciki, da ƙyar Yusuf ya miƙe Saleh ya riƙe shi, yana takawa a hankali.
Widad ta zuro Hijjabi tace binsu zata yi, Aikuwa Seleh yace "A'a base kinje ba, nida Ila da Megari za muje mu kai shi"
Ai nan da nan tasha gabansu ta tsaya ta kalli Seleh tace "wai kai a tunaninka har nayi yaddar da zaka ɗauke shi ka tafi da shi, bayan ban san inda zaka kai shi ba, baze yuwu ba duk inda za'aje sedai aje dani"
Saleh yace "look, idan ina da nufin cutar daku, to da yanzu ba wannan zancen ake ba, ni bani da niyyar cutar ku, Asibiti zamu kai shi"
Megari yace "ki kwantar da hankalinki, Insha Allah babu abunda ze sameshi"
Kunyar Megari da Gwaggo ne yasa Widad fasa binsu, ta kalli Yusuf tace "Allah ya baka lafiya Yoseef, Allah ya kula da kai kamar yadda kake kula dani"
Ɗagowa Yusuf yayi ya kalle ta, ya sakar mata murmushi suka yi waje.
Wajen ƙarfe Biyar na yamma, Anwar yazo gidansu Ramlah, ya kirata a waya ta fifo, har tazo falo suka haɗu da Amal, Amal ta kalli Ramlah tace "se ina?"
"zan fita ne" Ramlah ta bata amsa.
Amal ta jinjina kai tace "A dai dinga kula Ramlah, a dinga abunda ƙuda zebi, wannan gabtalin da kike ba yau ba gobe, ze ɓata miki suna ne"
"Ke dalla sauraramin, bana son shisshigi na gaya miki, ina ruwanki dsni ne? Kinfa fara isata na gaya miki"
Ta sa kai ta fice daga falon cike ɓacin rai.
Kai tsaye taje ta shige motar Fahad suka fita, Nura yace "Allah wadaran wannan shegiyar Ramlah me kama da balbela"
Isa yace "bari, iskancin da take mana a gidan nan ko Gimbiyar Daula ba tayi shiba, kullum suna titi ita da wannan me kai kamar tumatir ɗin"
Murtalah yace "Ai har gara ma Amal da Anwar, Amma da matar gidan nan da Ramlah Allah ya tsine musu Albarka"
Isa yace "Ameen ya Allah, kalli duk manyan motocin dake gidan nan tabi ta siyar, kamar dasu tazo se facaka suke da kuɗi, Kai ta wani fannin yanzu bana ganin laifin 'yar masu gida da take musu rashin mutunci"
Murtalah yace "dama Hausawa sunce,' kada Allah ya kawo ranar yabo' duk rashin mutuncin da take Yusuf se yayi ta kare ta, se yanzu nake ganin gaskiyar zancensa da yace bata yiwa mutum wulaƙanci seya yi mata laifi"
Nura yace "Mhmm Ai kawai Allah yasaka mana, amma gidan nan ana abubuwa sedai fatan Allah ya kyauta"
Duk inda Hajiya Sarah tasan zata buga ta buga, amma anƙi sakin Anwar, gaba ɗaya ta rasa inda zata tsoma ranta, Anbi an toshe duk wata hanya da zata saka a samu belin Anwar.
Yanzu ma haka ta dawo fakan fakan kamar korarriya, a mugun guje ta shigo da mota gidan.
Tana shiga ta fara kiran "Ramlah! Ramlah! Ke Amal kuna inane?"
Amal ta fito tace "Mummy Ramlah fa bata nan"
"gidan ubanwa taje?"
Amal tace "sun fita ita da Fahad"
"zanci ubanta ita da Fahad ɗin kuwa, ai tunda ubansa ya watsa min ƙasa a ido, to tabbas zan masa rashin mutunci, zan nuna masa wacece Halima idan ya manta"
Amal tace "Mummy ɗan uwan naki?"
"Eh shi ɗin, tunda bani da kima a idon sa, nima zan nuna masa bashi da ita a nawa idon"
Amal tace "Mummy a bi dai komai a hankali, kar azo ayi aika aika"
Hajiya Halima tace "dalla rabu dani, ze gane ni ya taɓa, ai ɗa befi ɗa ba, yasani yaron nan besan inda aka kaai mutumin nan ba, amma se cemin yake wai in ƙyale doka tayi aikinta, na zagi dokar shi doka nawa yayi fatali da a rayuwar sa, zega tsiya"
Tai part ɗinta tana cigaba da banbami, kamar wadda ke shirin Zarewa.
Saleh da Yusuf da ɗan megari suka tafi kai Yusuf Asibiti, aka bar Widad da mutan gida tana ta faman yi musu kuka.
Gwaggo da