Showing 15001 words to 18000 words out of 135096 words

Chapter 6 - Akidata Book 1 Hausa Novel Complete

01 Jan 2025

746

Aure shine ya dace dake, domin shine ze gusar miki da wannan larurar ki zama kaman sauran mutane"

"na taɓa ce maka ina son Aure ne? Ko kuma akwai shi a cikin tsarin Rayuwa ta?"

"look daughter, Aure shi ze gusar miki da dukkanin wannan halin da kike ciki, babu yadda za'ayi lafiyayyen mutum ya rayu ba tare da mutane a cikin Rayuwar sa ba, shi yasa muka yanke shawarar Aurar dake"

"ka dai yanke shawara sannan ka cusawa Daddy na ra'ayin hakan, ace har Daddy yamin laifi sannan ya fita harka ta dan naƙi yadda da batun Auren nan, duk kai ka jamin, sannan nida ban yadda da soyayya ba balle inyi ta har in samu mijin Aure, wazaku aura min?"

Gyara Zama Bulama yayi yace
"Fuhad mana first born ɗina, kun dace sosai, ze soki tsakani da Allah ya zauna dake, tunda ke 'yar uwassa ce"

Shiru tayi ta kalli Bulama sannan tace "what the fucking shit are you talking about? meye wani ze soni tsakani da Allah? Let me tell you something, i don't believe in Love talk less of true love, Love is just an imagination full of bull shits and stupidity, so ke sa ayi aure ko? To ban yadda yayi existing ba, dan haka ka gaggauta warware wannan maganar, dan ko aure zanyi bazan auri namiji bahaushe ba, you people that are not romantic at all, babu abunda kuka iya banda iko da ɗaukar matayen ku tamkar bayinku, baku damu da halin da zasu shiga ba idan har taku buƙatar zata biya, baku iya komai ba se masifa da hantara, don't you see how women are complaining about you? How Hausa women's are suffering because of your poor marital life? Women's are always complaining about marriage issues, this is type of life you want me to do? Do you think I can live with someone that will be shouting at me?"

Shiru Bulama yayi yana kallon ta, Ta gyara zama ta kalli cikin idon Bulama tace
" idan baso kuke ku ƙara tunzura haukan nawa ba kaman yadda kuke iƙrari ba, ya kamata ku ƙyaleni da maganar nan"

Numfasawa Bulama yayi yace "Amma kin san mahaifinki ma bahaushe ne, kike wannan maganganun akan mazan hausawa"

"da nace ban dashi a ciki ne? Shima badan yayi rayuwar Turai ba he will have the same negative habits on his wife, it seems it is in your genes, Alhaji Bulama daga yarin tata sanina da kai mata nawa ka aura bakwa tare yanzu? Go back to your senses Sir, Am not ready to ruin mad, i don't have interest of getting marriage, i don't know maybe later, but I can't married a man from hausa people, they don't value their wives "

Ba Bulama ba, Yusuf kansa yaji haushin cin mutuncin da Widad tayi wa ƙabilar Hausawa, duk lalacewar Al'umma akwai mutanen kirki ai, Amma ba shida ta cewa, tunda shi ɗan karere ne.

Ta miƙe tsaye tayi gaba abun ta, Yusuf ya rufa mata Baya, yauma har suka je gida ba wanda ya kula wani, sedai da suka koma gidan, a mota ta bar jakarta da wayarta, dole Yusuf ya ɗauka ya bita da su ba dan yana so ba, dan sam baya son shiga cikin gidan, ba ƙaramin tsarguwa yake da irin kallon da mutan gidan ke masa yake ba.

Yanzu kam ba 'a hankali take tafiya ba cikin gaggawa take tafiya, kaman tana son tayi wani abune, ta falon da zata bi ta wuce ta tarar da Mahaifinta a zaune da shi da matarsa, ko kallon su batayi ba tasa kai zata wuce.

"Widad" Mahaifinta ya kira sunan ta ba tare da juyo ba ta tsaya cak, be damu ba ya ɗora da cewa
"Munyi waya da Bulama ya gayamin abunda kika je kika ce masa, ki sani wannan karon dole kibi abunda nake so, bani zan biki ba, am doing all this for your benefit, in the next two Months insha Allah Fahad zezo ƙasar nan, ina son ayi Auren ku kafin ya koma"
Cigaba tayi da tafiyar ta ba tare da cewa Mahaifinta komai ba. Yusuf dake tsaye yana jinsu ya ƙarasa ya gaida mahaifin Widad da matarsa Hajiya Halima.
Ya amsa masa cikin, yayin da Hajiya Halima ta Amsa masa a ciki.

Yusuf ya miƙa wa Mahaifin Widad jakar ta da keys ɗin motar ta, yayi musu Sallama ya fice.

"Yaya Yusuf" yaji an kira sunan sa, tsayawa yayi ya waigo, Amal ce take tahowa da sauri hada ɗan haɗawa da gudu.

"Sannu ashe kun dawo?"
"Eh mun dawo, akwai wani abu ne?"

Ɗan sosa kai tayi tace "dan Allah in babu damuwa so nake ka raka ni Shopping"
"Shopping kuma? Niɗin?"
"Eh amma idan ban takura maka ba"
"ina batun takura ni da nake muku aiki, idan kin shirya kimin magana"
Murmushi tayi tace "nagode sosai Yaya Yusuf"
Shima murmushi ya mayar mata yai gaba abun sa.

(WASA FARIN GIRKI)

Share please 🙏 🙏 🙏

Comment nake so ba sticker ba ko kuma thanks ba, inda suka fi Comment su zasu dinga fara samun posting
Domin gyara, sharhi, kokuma ƙorafi a tuntube ni akan wannan lambar
07063065680
Watpad Ayshercool7724

_*AƘIDA TA*_

*Story and written by*

_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_

The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *

Haƙƙin Mallaka ⚠ : Littafin nan mallaki nane, tun daga sunan labarin zuwa abunda ya ƙunsa, ban yadda wani ko wata ya sauyamin ko yin Amfani da wani ɓangare na labarin ba ba tare da izinina ba, Nagode

ELEGANT ONLINE WRITER'S

                            PART1
                                  Page 5

Yusuf ya fita yaje yai alwala yai salla saboda lokacin salla yayi.

Widad kam tana zuwa ɗakin ta ta jefar da Jakarta da wayar ta akan gado ta fara safa da marwa a ɗakin ta

"Bulama ina ganin girman ka, ina maka kallon uba amma kana ƙoƙarin ƙetare gona da iri, kana ƙoƙarin tsallake iyakokinka, a tunanin ka yin Aure ze sa in canza ra'ayina? Daddy kunyi kuskure daga kai har Bulama, kuma bazan taɓa bari wannan kuskuren naku yayi tasiri a kaina ba, dole inyi wani abu" haka ta cigaba da surutai ita kaɗai.

Hajiya Halima ta kalli maigidan ta tace "Nikam wai Alhaji dagaske Widad zakayi wa Aure ko kuma yaya? Na kasa gane kan lamarin"

Ɗan shiru yayi sannan yace "Eh hakane, Bulama ya bani shawarar akan cewa muyi mata Aure hakan ne kawai zesa ta canza wannan halin nata, Amma yarinyar nan kin san halin ta da kafiya da taurin kai, ta tirje tace sam bata san zancen ba, Amma a wannan karon bazan canza ra'ayi ba, ina son inga ta dawo da walwalarta, wannan karon dole tayi biyayya ga umarni na"

"Amma Alhaji baka ganin yin hakan tamkar ze ƙara tunzura rashin lafiyar ta ne, zaka ƙara sawa rashin lafiyar ta ya tsanan ta, ko ka manta sharuɗan da likitoci suka gindaya ne akanta?"

Alhaji Nasir Ya numfasa sannan yace

"Shima zaman ta a hakan bakomai ze ƙara mata ba face cigaba da dawwama a cikin damuwa da rashin walwala, akwai buƙatar ko bayan raina Widad ya zama na tana da kafaɗar da zata tada kai, ya zamana tana da wanda ze kula da rayuwar ta"

"Amma Alhaji wa zaku bawa Auren ta? ina fatan wanda zaku bawa yasan yanayin larurar ta? Tunda kaga ba shiga mutane take ba balle a ce tana da wanda take so, kar a bawa wanda besan ya take ba abu yazo ya ɓaci"

Alhaji Nasir yace "Ai ba wani bane za'a aura matan, fahad ɗin Bulama ne, itace dai batayi wayon saninshi sosai ba, rabon da su haɗu tun tana yarinya ƙarama, Amma shi ya santa kuma nasan baze bamu kunya ba Insha Allah, tunda itama tamkar ƙanwa take a gurin sa"

Jinjina kai kawai tayi ba tare da ta kuma cewa komai ba.

Wajejen la'asar Amal ta shiryo cikin wata irin doguwar riga wadda ta kama jikin ta matuƙa, se zuba ƙamshin turare take wanda turaren har hawa ka yake yi saboda ƙarfin sa ta hau kan wani takalmi me uban tsini, duwatsun jikin rigarta se ƙyalli suke suna rawa.

Cikin iyayi ta ƙarasa inda Yusuf yake zaune da su Nura da sauran ma'aikatan gidan tace "Yaya Yusuf mu tafi ko na shirya"
Ba musu Yusuf ya miƙe yayi wa su Isa sallama.

Ya karɓi mukullin Motar Amal, suka shiga mota suka fice.

Yusuf na barin gurin Murtala me bawa shukoki ruwa yace
"wai kunga abunda na gani ko kuwa?"

Nura yace "mun gani, kai kaga wata irin kwarkwasa da take masa? , anya yarinyar nan Amal ba san shi take ba? Kaga wani iyayi da take yi tana fari da idi"

Murtala yace "Amma kuwa da ta faɗo, duk zuƙa zuƙan Samarin dake zuwa gurin ta? duk iya yin da wulaƙancin nata ta ƙare a direba, wallahi da tayi faɗuwar baƙar tasa"

Isa yace "to ai gara Amal ɗin akan yayar ta Ramla, kun san agola musamman in aka samu guri akwai iskanci, yadda suke hura hanci suna Wulaƙanta mutane kai kace gidan ubansu ne, Amma fa duk da haka gara nasu lafiya ne akan 'yar masu gida wai wa yaga Azaba, idan bata ga dama ba fuskarta idan ka kalla seka yi fitsari a wando, saboda sam bata da rangwame, Azababbiyar Yarinya idonta fiƙi fiƙi kamar me maye"

Nura yace "wallahi ko san haɗa hanya da yarinyar nan bana yi, nagode Allah da yasa ba ita nake tuƙawa ba baban ta nake tuƙawa, ni nayi mamaki ma yadda Yusuf ɗin nan har yanzu basu samu saɓani taci mutuncin sa ba, dan naga wani jin kan sa yake shima, musamman idan yana jan manyan motocin nan se kace na gadon ubansa, kamar har mantawa yake direba ne shi"

Isa ya gyara zama ya waiga sannan ya ƙara ƙasa da muryar sa yace

"ku nifa ban gama yadda da Yusuf ɗin nan ba, kuna ganin sa wani haɗaɗɗe da shi, kullum tsaf tsaf da shi, babu alamar wahala a tare da shi, ga jan aji duk yafi mu kyan gani sannan ace ya ƙare a direba anya babu lauje cikin naɗi a wannan harkar kuwa?"

Murtalah yace "Nima nayi wannan tunanin, amma ya zamu san gaskiyar lamarin? Dan ya fara bani haushi wallahi, yadda megidan nan ya fara wani girmama shi wai yana da sunan yayan sa, har wani Yaya na yake ce masa shi kuma yana washe baki yana sunkuyar da kai, damabidan mutum yavfiye sunkuyar da kai munafuki ne"

Isa yace "ku ƙyale shi zan bugi cikin sani inji ko zamu samu wani bayanin muji, ai duniya seda labari, Amma ina tunanin ta yadda za'ayi kamar wannan da beyi kama da wanda yake cikin wahala ba yazo yana aikin direba"

Yusuf ya ƙudurcewa ransa ze ɗan dinga sakarwa Amal, domin samun sanin wasu abubuwa da suka shige masa duhu game da yanayin tsarin Rayuwar mutanen gidan. Suna tafiya a hanya Amal tace

"Yusuf dan Allah ka dinga haƙuri da abunda Widad take maka, sam abunda tayi maka ɗazu banji daɗi ba wallahi haka take bata san darajar ɗan Adam ba mussman talaka, bata da mutunci, mu kanmu haƙuri kawai muke da ita sam bama jin daɗin zama da ita, shiyasa babu wanda yayi farinciki da dawowarta"

Yusuf da sauri yace "A'a uwa ɗakina ce fa ranki ya daɗe, ya zaki ce bata da mutunci a gabana? ai bazan ji daɗi ba gaskiya banji daɗin yadda kika aibata ta ba"

Kallon Yusuf tayi galala cike da mamaki tace "kana nufin baka ji haushin abunda tayi maka bane? Ai ba ƙarya nayi mata ba, da tana da mutunci da bata muzanta maka ba, harta jefe ka da key a fuska ba"

Yusuf yayi murmushi yace "yana da kyau mu dinga girmama doka kafin muyi ƙorafin anci zarafin mu, ko ba'ayi mana adalci ba, da hannu na na saka hannu akan dokokin ta kafin in fara mata aiki, na saka hannu na amince da zanbi sharuɗan data gindaya min, dan haka tunda ni na saɓa abunda na sakawa hannu, komai tayi min be kamata inji haushi ba, ko kuma ince bata da kirki ba, idan nayi haka banyi wa kaina adalci ba"

Amal tayi ajiyar zuciya tace "indai wannan ce kai da kanka zaka dawo daga rakiyar ta saboda wulaƙancin ta, dan wataran seta maka abunda zesa ka tsaneta tamkar mutuwar ka, tun bamu kai haka ba mahaifiyar mu ta auri mahaifin ta muke zaune tare, Amma bamu da daraja ko ƙima a idon ta, kai bamu ba har mahaifiyar mu bata ɗagawa ƙafa, Alhaji Bulama ne ya bada shawarar a bar ƙasar nan da ita, shine ma muka samu muka huta na wasu shekaru kafin ta dawo, se a dinga fakewa da bata da lafiya, tana taka mutane tana nuna isa da Izza"

Yusuf yace "bata da lafiya kuma? Kamar ya bata da lafiya, Meke damun ta?"

Ɗan taɓe baki Amal tayi tace "wai bata da lafiyar ƙwaƙwalwa, ko da yake me lafiyar ƙwaƙwalwa baze abunda take ba, wannan dukiyar ta mahaifin ta, da ita take taƙama da ita take wulaƙanta mutane, ta yaga duk wanda yayi mata abunda yake saɓanin raa'yin ta, aikin banza, dukiyar da'ake farautar ranta akanta, Amma take da damar Wulaƙanta mutane saboda ita"

Da sauri Yusuf yace "kamar ya farautar rai? Ranwa ake farauta, saboda dukiya?"

"Ran Widad ɗin mana, yana ɗaya daga cikin dalilin da yasa ta bar ƙasar nan fa, bayan larurar Ƙwaƙwalwa da take dashi ana farautar ranta ne, tunda maman ta ta rasu take fama da larurar ƙwaƙwalwa, kuma a kazo ana nema a kashe ta, abundai gashi nan, Amma kodan wulaƙanta mutane da take dole wani yai ƙudurin kashe ta ya huce takaicinsa, bayan wulaƙancin da take wa mutane, har ɗaure mutane take sa ayi"

Jinjina kai Yusuf yayi yana kuma nazarin maganganun Amal, baya so ya cika ta da tambayoyi, karta fuskanci wani abu dan haka yayi shiru yana ɗan satar kallon Amal yana tunani a ransa.

Yusuf ya kai Amal wani katafaren mall kaman yadda ta buƙata ta dinga ɗibar kaya, sannan tace Yusuf ya ɗauki abunda ya keso.
"A'a nagode amma ni bana buƙatar komai"
Amal tace "haba Yusuf dan Allah ka ɗauka, karka ji komai"
Fafur Yusuf yaƙi yadda ya ɗau komai se haƙura tayi.

Bayan sun dawo gida tace dan Allah ya taya ta ɗaukar kayan da ta siyo, babu musu ya ɗau kayan yabi bayan ta kamar yadda suke da Widad, Sedai tun a babban falon ƙasa suka ci karo da hakimar ƙafar ta ɗaya kan ɗaya tana shan tea, gefen ta kuma tana bawa magenta madara, bata kula su ba su kayi gaba za su wuce, muryar ta suka jiyo tace

"Stop there" ta faɗa kai tsaye cikin bada umarni, gaba ɗaya suka tsaya suna jiran me za tace.

Se da ta ja wasu seconds sannan tace

"Amal yaushe muka fara sharing ɗin abu nida ke ne ban sani ba? Ya akayi matsayinki har ya kai kiyi amfani da abina ba tare da kin nemi izini na ba?" tai maganar tare da miƙewa tsaye, tavtako ta zo har inda suke tsaye ta kalli Amal, ta tsaida dubanta kan Amal, Amma tace wa Yusu

"waye ya ɗauke ka aiki a cikin gidan nan?"

"kece ranki ya daɗe" ya faɗa cikin girmamawa

"Wa kayi wa aiki yanzu?" tai maganar me cike da bayyanar da tsantsar Izzar ta

" 'yar uwarki ranki ya daɗe" ya bata amsa

Ta ɗan lumshe ido sannan ta buɗe tace "Na taɓa gaya maka ina da ɗan uwan ko' yar uwa ne?"

"A'a"

"lokacin dana ɗauke ka aiki na gaya maka nida wani zakayiwa aiki?"

"A'a" ya sake bata amsa

Ta maida idon ta kan Yusuf cikin ɗaga sauti tace

"Ka karyamin doka karo na biyu da wani suna ya kamata in kira kane? Bagidajen ina ne kai? Ko kuma ince daga wani jejin kake? a haka you look civilized amma kwata2 shashasha ne kai, hala ka manta akan death contract kayi signing? Inaga ka manta ne, ko kuma ka ɗauka wasa ne shiyasa kake wasa da rayuwar ka"

Ya girgiza mata kai alamar A'a

Hayaniyar da Hajiya Halima take ji sama sama ne ya sa ta fito ita da ramlah suka tsaya suka yi cirko cirko a falon Widad tana ta zuba tsiyata kunta san ranta.

Widad tace "Yanzu ina maka hukunci se ka kirani azzaluma ko? Saboda haka ɗabi'ar ku ta matsiyatan mutane take, ku kullum akan daidai kuke masu kuɗi kuma Azzalumi ko?, dukda bana maimaita magana yau zaka sani na maimaita, Ni Widad ban yadda da kowa ba, duk yadda muke da mutum karyamin dokoki na daidai suke da yunƙurin cin amana ta, kuma penalty ɗin wanda yaci amana ta, bana jin tantirin talaka wanda bashi da komai kamar ka ze iya ɗauka "

Amal tace " haba Widad be kama......

Ɗaga mata hannu Widad tayi ba tare da ta kalli Amal ba tace "har yanzu 'yar alfarma ce ke a cikin gidan nan, matsayinki be kai na 'yar masu gida ba, karki ƙara gangancin ina magana ki katseni ko kisamin baki, idan ba haka ba kin san sauran, kai kuma daga yau nikaɗai kake wa aiki a cikin gidan nan, ban yadda wani ya saka aiki kayi ba, duk wanda yace kai wani abu kace Widad kake wa aiki ba wani ba, sannan kayi a rabin salary ɗinka shine hukuncin karya min doka da kayi har sau biyu dismiss from here"

Yusuf ya risina ya ɗanyi murmushi yace "godiya nake uwaɗakina, Allah ya ƙara girma Insha Allah zanyi ƙoƙari in kiyaye dokokin ki, bazan ƙara karya miki doka ba, Allah ya huci zuciyar ki"

Gaba ɗaya suka bi Yusuf da kallo wato shi duk wannan cin zarafin da aka yi masa godiya yayi, lallai wani talakan Jaki ne, besan ciwon kansa ba, Ramlah ta faɗa a ranta.

Widad ta kallesu ɗaya bayan ɗaya tace "bana buƙatar kowa a falon nan, madam zaki iya jan zugarki ku ɓace min daga nan"

Saboda tsabar baƙinciki da takaici Amal watsi tayi da kayan shopping ɗin da tayi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login