Showing 60001 words to 63000 words out of 135096 words

Chapter 21 - Akidata Book 1 Hausa Novel Complete

01 Jan 2025

760

case ɗinsa a hannun sa.

Yusuf ya ƙarasa da sauri yana gaida Alhaji Nasir tareda karɓar brief case ɗin hannun sa.
Alhaji Nasir yace "Yayana na kaina, fatan na sameku lafiya ya amana ta?"

Yusuf yay murmushi yace "Alhamdilillah"

Ya kalli Widad yace "my Lovely har yanzu kina fushi da Dad ko?" yai maganar yana rungume Widad, kamar anmata dole tace "Welcome Daddy"

Alhaji Nasir ya ɗan shafa bayan ta yace"thank you sweetheart" suka ɗunguma zuwa mota gaba ɗaya, suna tafiya Alhaji Nasir da Yusuf ne kawai ke hira, Amma Widad tunanin ta ta yaya zata hukunta Yusuf.

Har Yusuf ya gama aikin sa na ranar ya tafi Widad bata samu mafita ba.

***********************************

"Jama'a bafa a bori da sanyin jiki, wannan ce damar da yakamata muyi amfani da ita, tunda Allah yasa yarinyar nan tana ƙasar nan musan abunda za muyi" cewar Alhaji Munir

Alhaji Musa yace "Ni idan an samu abun nan falillahil hamd, amma babban burina be wuce in Wulaƙanta Alhaji Nasir a idon duniya shida ahalinsa ba kamar yadda ya Wulaƙanta ni ya ɓata min suna"

Alhaji Haruna yace "gaba ɗayanmu buƙatar mu ɗaya ce, kuma kunsan Alhaji Bukar shike bamu umarnin abunda zamuyi, karmu yadda muyi abunda ze waegaza shirin mu, yanzu yarinyar taje gidan yari tayi wa Hashim barazana akan indai da hannun sa akan wannan lamari daya samu Bala to tabbas zata ɗau mataki akansa "

Alhaji Musa yace " Umarnin Alhaji Bukar kawai nake jira, amma akwai yuwuwar shima a kauda shi, dan komai ze iya faruwa barinsa a doron ƙasa"

Alhaji Haruna ya zame akan kujera yana shafa tumbinsa yace
"Ni dai kam da zan samu yarinyar nan, So nake gaskiya, dan akwai ta da ƙira daidai gwargwado".

Tsaki Alhaji Munir yayi yace "kai ka fiye shirme, ana ta kai wake ta kaya, in in hutawa kake so, ka fita ƙasashen waje ga mata nan farare yadda kake so, amma yanzu ka bari idan muka karɓi abunda muke so, muka aika Nasir Daula kiyama, se kayi yadda kaso"

Wata uwar dariya suka saki hadda shewa.

**********************************

"Bulama tafiya tayi Alhamdilillah, na samu approval na fara business ɗina da China"

"Masha Allah, naji daɗin hakan, Allah yayi jagora"

Baban Widad yace "Ameen ya Allah, sedai ko kun samu saɓani da 'yar taka ne? Tunda na dawo naga bata walwala ko akwai matsala ne?"

Alhaji Bulama yai murmushi yace "hmm Widad' yata ta kaina, tabbas munyi faɗa, kasan tunda nace ayi mata Aure take jin haushi na, tazo ta sameni akan wai sena mata Visa ta koma naƙi, shine take fushi"

Alhaji Nasir ya girgiza kai yace "Nima wancan satin ta kirani tana kuka, akan lallai sena kiraka nasa an mata visa ta koma, ni kuma gaskiya bazan bari ta koma ba, idanma zatavkoma se bayan Auren ta da Fahad sa tafi tare"

"hakane, daga lokacin da ta fara tara iyali dole ta dena wannan halayen nata, sannan mamanta ta kawomin ƙararta akan yadda suke da direban nan, na kirata nayi mata faɗa, nanma ta sake yin fushi dani"

Alhaji Nasir yai murmushi yace "ina tunanin akwai wani ɓoyayyen al'amari a tattare da yaron nan, ba ƙaramin daɗi naji ba ganin shine mutum na farko bayan nida kai da Widad take sakewa dashi"

"Amma karfa muyi sake yazo suyi shaƙuwar da zamu yi da nasani"

"Insha Allah ba zamuyi ba, dan yaron yana da tarbiyya sosai"

"Amma idan soyayya ta shiga tsakanin su fa?"

Alhaji Nasir yace " Yarinyar da bata yadda da soyayya ba, ta ina zasu fara soyayya? Gaba ɗaya Widad ɗina a birkice take bata da alƙibla"

Bulama yace "Kasan bata da alƙibla ai kuwa ba abun mamaki bane ta fara soyayya da direban ta, tunda shi so baya sallama".

"to nidai duk abunda ze saka ta farinciki shi nake so, idan ta kawo shi tace tana so bakomai se in Aura nata shi"

Bulama yace "Allah ya kiyaye mu aura mata direba haba Daula"

"to masu 'ya, ai seka biye mata kuyi tayi"

Sukayi dariya suka shiga hirara duniya.

***********************************
Sintiri take a ɗakin ta, tana son gazgata abunda take ji a zuciyar ta game da Abokin ta. Dagaske na kamu da Son wanda yake daga ɓangaren maƙiyin mahaifi na, amma ban san alaƙarshi da Widad ba, amma tunda na gansu tare suna da alaƙa.
Shiru tayi tana tuna yadda ya zauna a kusa da ita yana mata magana, cikin rarrashi danta saki jiki dashi.

Kamar light da yake kiran ta dashi yafi komai yi mata daɗi, Amma dagaske yana da Aure? Ta tambayi kanta, anya za'a yarda a auramin me mata? Gashi kuma ɗan uwan Widad.

Dafe kai tayi tace "Subhanallah"

"ke lafiya kuwa? Sintirin me kike tayi haka kamar kinwa sarki ƙarya?"

Juyawa tayi ta kalli inda Maman ta ke tsaye tace "bakomai fa"

"bakomai, a hakan? Gaba ɗaya alamu sun nuna baki da gaskiya sam"

Ta ɗan tura baki tace "wallahi ina da gaskiya"

"shikenan, idan tayi wari maji"

Nurat ta koma kan gadonta ta zauna ta ɗakko wayarta ta shiga kiran layin Yusuf amma shiru baya shiga, tayi2 harta gaji ta ajiye, tana mamakin ya akayi hakan ta faru?

Shikuwa Yusuf tun ranar data kira shi agaban Widad, yana komawa gida ya cire layin ya ajiye gaba ɗaya.

**********************************

Oga Suleiman ne zaune akan kujera yana gwadawa Sakina wasu ayyuka a computer, sun maida hankali sosai kan aikin.

Abbas ne yayi sallama, suka ɗago gaba ɗaya suka dube shi tare da amsa sallamarsa, Sakina ta gaida Abbas, yayin da Abbas ya ƙamewa Suleman cikin girmamawa.

Suleiman ya bashi damar zama, sannan ya miƙa masa hannu suka gaisa, Suleiman yace "Abbas kwana biyu banga Yusuf ba fa, ya kamata ace yazo ya gabatar min da sakamakon binciken da yayi"

Abbas yace "ranka ya daɗe, nima kaina na kasa gane inda yasa gaba, gaba ɗaya kamar ba aikin yake ba, yaje ya shantake se abun Arziki yake samu a gidan, alherin da suke masa yasa gaba ɗaya hankalin sa baya kan aikin, da dai da hali a canza shi da wani kawai"

Suleiman yace "Amma kaika cemin ze iya aikin, da kai nace zan bawa ka nunamin ya fika haƙuri da juriya"

"Ai Oga sam ban san haka ze faru ba, ban taɓa sanin Yusuf yana da son abun duniya ba seda ya karɓi aikin nan, ba abunda yake se neman gindin zama a gidan da yake"

Sakina kam sakin baki tayi tana sauraren yadda Abbas ke ɓata Yusuf a gurin ogansu, wanda hakan ze iya jawowa Yusuf babbar matsala a gurin aikin nasu, Yusuf ya yadda da Abbas sosai, dan yana masa kallon ɗan uwa bama abokin aiki ba.

Oga Suleiman yace "shikenan, zan duba idan da dama zan kira shi a waya ma, inaga karɓar aikin zanyi daga hannun sa in bawa wani"

***********************************

Gidan shiru babu kowa, Yusuf yana inda ya saba zama idan yaje gidan su Widad, Murtalah ne yazo inda Yusuf yake yace "Malam Yusuf kana nan kana hutawa ashe?"

"wallahi kuwa Murtala ya aikin?"

"Alhamdilillah, ai kana fama Yusuf, kullum se kazo ko zakayi aiki ko ba zaka yi ba"

Yusuf yayi murmushi yace "to ya za'ayi tunda na yadda zanyi aikin, ai dole in cika ƙa'idar aikin"

Murtalah yace "hakane" suna cikin hirar Amal ta fito, ta ƙaraso inda Yusuf ke zaune, ranta a ɓace tace "kazo ana son ganin ka"

Ba musu ya miƙe yabi bayan ta, suna shiga babban falo har Yusuf zeyi hanyar ɓangaren Widad, dan yasan be wuce ace ita take kiransa ba, tunda Alhaji Nasir baya nan.

Amal tace "A'a,  ba a nan ake neman ka ba"
Ta nuna masa hanyar ɗaya part ɗin dabe taɓa taka gurin ba, seda ya ɗanyi jimmm ya kalle ta sannan yace "shikenan muje"

Suka rankaya ɓangaren data nuna masa, tana tafe yana binta a baya
Wata ƙofa ta buɗe suka shiga, matsakaicin bedroom ne, me ɗauke da kayan more rayuwa sedai be kai haɗuwar na gimbiyar gidan ba.

Amal ta juyo ta kalle shi tace "Yusuf Meka ke nufi dani ne?"

Cike da rashin fahimta yace "kamar yaya? Kince ana kirana kuma kin kawo ni nan"

"Yusuf nina nake nemanka ba wani ba, na gaya maka abunda ke raina amma ka maidani kamar wata banza, Haba Yusuf me yasa baka da tausayi ne? Soyayyar ka nata wahalar dani amma hankalin ka yana kan waccan banzar mahaukaciyar, har dama ka samu a kanta wanda zaka rama irin wulaƙancin da take maka, ATM ɗinta kwanansa nawa a gurin ka? kamata yayi kayi amfani da wannan damar ka azurta kanka, tausayin mara tausayi asara, asara ne gagaruma ko dai dan Widad tana da kuɗi shiyasa kake Wulaƙanta ni?"

Yusuf be taɓa jin son Amal a ransa ba, ta yaya suna muzanta wadda suke cin Arzikin gidan su, ina gashi da yake bare? Kuma suna ta jadadda masa yayi wannan gagarumar sata haka?

"Amal ki fuskance ni, niba na Wulaƙanta mutane, sannan bani na tara musu dukiya ba, ta yaya zan musu wannan mummunan aiki? Ni ba Ɓarawo bane, dukiyar Widad bata gabana mutunci da girmamawa ya fiye min wata dukiya komai yawan ta, indai ban rasa ci da sha ba Alhamdilillah a yadda Allah ya ajiye ni, Widad batamin laifin komai ba, babu wani abu da tayi min wanda zesa in cutar da ita ko mahaifinta, tsakanina da su in musu aiki ne su biyani bisa ga yarjejeniyar da na sakawa hannu, Amma Amal tsakani na dake babu batun Soyayya duba da banbanci da kuma tazarar dake tsakanin mu, ke 'yar masu kuɗi ce, ni kuma talaka ne matsiyaci kamar yadda mutan gidan ku suke faɗa"

"Yanzu kana nufin ba zaka karɓi Soyayya ta ba Yusuf, ka zaɓi cigaba da wahalar da zuciya ta, mace me kima kamata ince ina sonka amma ka watsamin ƙasa a ido? To wallahi baka isa ba, zaɓi biyu ke gareka kodai ka karɓi Soyayya ta, ko kuma in shirya maka gadar zaren da idan ta rufta da kai har Abada ba zaka sake wani Amfani ba"

'Kiyi duk abunda ki kiga dama, tabbas da soyayyar gaskiya kike min da baki faɗi haka ba, tabbas na taɓa Soyayya nasan zafin ta, Amma ba' a dole a soyayya "

Yana gama maganar ya juya ya fice daga ɗakin, biyo bayan sa tayi tana ƙwala masa kira, Amma yaƙi tsayawa yana buɗe ƙofar part ɗin ze fita yayi tozali da gimbiya 'yar masu gida, Widad ce a tsaye a bakin ƙofar dake facing ɗin wadda ya fito, se muzurai take idanunta sunyi Ja, tana masa wani irin kallo me wuyar fassara.

Me kuke tunanin ze faru?

(Masha Allah, am speechless wlh, Addu'arku tayi tasiri a gareni ina miƙa muku godiya, masu tambayar jikin Daddy Alhamdilillah ya warke ras💃💃💃  almost done with the exams only some part remains, saura fatan Nasara, farinciki yasa nace bari inyi surprising ɗinku da posting, ina jiran jin comments me fasa waya, idan anyi Comment yadda nake so gobema akwai posting insha Allah 😍😍😍 ina godiya masoya)

Domin sharhi, gyara, ko shawara feel free to contact me
Ayshercool
07063065680                    _*AƘIDATA*_

PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

P. W. A

*Story and written by*

_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_

The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *

I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum

                          PART1
                                Page 15

ELEGANT ONLINE WRITER'S

Turus Yusuf yayi ya rasa me yakamata yayi? Me zeyi wanda zesa Widad ta yadda da shi, Amal ma da ta ƙaraso domin cimma Yusuf, tana ganin Widad itama tayi Turus ta shiga rarraba ido kamar an sacewa karya 'ya' ya.

Widad tayi wa Yusuf alama da hannu ya biyo ta, ji yake kamar ƙasa ta tsage ya shige, haka ya bi bayan Widad zuwa part ɗin ta, gaba ɗaya ya saddaƙar yana jiran jin ruwan masifa daga bakin Widad.

Ta kalle shi tace "nayi list na abubuwa da nake buƙata ne, za kaje ka siyomin, ka lura da duka abunda na rubuta bana buƙatar product ɗin basu nace ba"

Jiki ba ƙwari ya jinjina mata kai, ta ɗakko paper ta miƙa masa tare da ATM card, a sanyaye yasa hannu ya ksrɓa, amma harya juya  zefita beji tace masa komai akan ganinsa ya fito daga sashin su Amal ba.

Har ze fita ya tsaya ya juyo ko zata yi magana, amma yaga tana danna wayarta, tana ɗaga ido suka yi ido huɗu dashi ta kalle shi tace

"Lafiya? Ka tafi mana"

Ya kalle ta yace "bakomai"

Ya juya ya fita yana sake waiwayen Widad ko zata yi magana.

Fahad ne keta shirya kayansa a trolley, Anwar ya kalleshi yace "Fahad ji nake kamar in bika mu koma Nigeria tare, amma ba yadda zanyi, munzo tare ka rigani kammaluwa"

Fahad yace "Ai kai ba komawa Nigeria ce ta dame ka ba, zuwa kaga wannan yarinyar ne ya dame ka"

"ƙwarai kuwa faɗi ka ƙara Fahad, ni kaɗai nasan abunda nake ji game da ita, nima ina nan dawowa ai Insha Allah, inga farincikin zuciya ta"

"Allah yayi maka magani, dan kaibnaga abun naka ka afka da yawa"
  "kadai bari kawai, dan Allah Fahad kayi ƙoƙari ka samo min lambar ta idan kaje Nigeria"
Yatsuna fuska Fahad yayi yace  "gaskiya ban maka Alƙawari ba, dan tamin rashin mutunci marinta zanyi"
Anwar yayi dariya yace 
"da kuwa ka ƙare rayuwar ka a prison"
"kaini ka isheni da zancen yarinyar nan haba"

Ƙarshe Fahad ya fice ya barwa Anwar ɗakin, dan ba ƙaramin haushi yake bashi ba idan yana zancen Widad.

***********************************

"Ana ƙoƙarin a hallaka min ɗan uwana, sannan kuna min barazana da rayuwa ta, gefe guda ga yarinyar nan itama ta sakoni gaba, anya Alhaji Haruna kunmin adalci kenan?"

Alhaji Haruna yace  "Adalci ɗaya za muyi maka Sale, kayi aiki nan na ƙarshe da muke so, in ba haka ba da kai da ɗanuwanka haka zaku ƙare kuyi biyu babu, tabbas muka samu abunda muke so zamu fidda ɗan uwanka, sannan baku ba na kusa da kuma seya azurta"

Saleh ya fesar da iska yace  "kamar yaya? Yanzu dai ta tabbata kune kuja bawa ɗan uwana abunda yasa rashin lafiya ta kama shi, don ku kasheshi karya tona muku asiri"

Alhaji Haruna yayi murmushi yace  "zata iya kasan mune, kuma zata iya kasancewa bamu bane ba, ka sani ko ɗan uwanka ya tona mana Asiri bashi da wata cikakkiyar hujja a kanmu, kuma muna da ƙarfin da zamu siye Alƙalai da lawyoyi, shari'ar ta tafi a banza, shi kuma a cigaba da tsaron sa, abu ɗaya ya rage maka, shine ka haɗa kai damu mu gudanar da wannan aikin tare "

Maimakon Saleh yayi magana, sema tsaki da yayi yai waje yana wani irin huci kamar kumurci.

***********************************
Kafin Yusuf yaje aiken da Widad tayi masa seya wuce gida ya ɗakko system ɗinsa ya wuce office.

Yana shigowa harabar station ɗin ya tsaya yana gaisawa da mutane, Sakinace ta hango shi, ta yunƙuro ta fito da sauri ta tare shi, ta kalle shi tace
"Sannu da zuwa yau ka leƙo mu kenan?"

"Yawwa sannu" kawai yasa kai ya wuce, ya nufi office ɗin Abbas, gaba ɗaya dirircewa tayi ta shiga tunanin ya zata yi ta fahimtar ds Yusuf, irin illar Kasancewar sa da Abbas.

Yusuf yana zuwa ya miƙawa Abbas hannu suka gaisa, Abbas yace "mutumina gidan daula sun ɓoye mana kai gaba ɗaya fa"

Yusuf yace  "bari kawai Abbas, kullum a cikin zullumi nake, the more nake binciken the more nake sake gano Wata sarƙaƙiyar, in taƙaice maka ma an fara bina wallahi"

"Kamar ya an fara binka?"

"Wai wani abu ake so in karɓo a hannun Widad, gashi yau na shiga wata cakwakiya a gidan nan, ina ta jira ta sauken kwandon bala'i amma taƙi kulani, ƙarewa ma aikena tayi, shine nace tunda na samu chance bari inzo inga oga Suleiman"

Abbas yace  "ka gan shi kayi masa me?"

"In fara presenting abunda bincike na ya nuna min mana, akwai buƙatar tsananta bincike a wasu guraren, amma kaga ai yakamata in gaya masa"

Abbas yace  "garajen Meka ke hakane Yusuf? Ka bari ka kammala binciken nan, idan ka kammala base ka kawo masa ba, Yallaɓan mafa baya nan ana nemansa a headquarter za suyi meeting, kasan koka bashi cewa zeyi kabi komai a hankali"

"So kake inzo inyi laifi kenan? Ni nafi ganewa in fara presenting ɗin aikin"

Abbas yace  "A'a karka damu, kabi komai a hankali"

Yusuf yace "shikenan bari in tashi in tafi, dama nan aikena aka yi"

Abbas yace  "Amma Yusuf akwai cigaba a cikin binciken kuwa?"

Yusuf yace  "Sosai makuwa, an samu ci gaba, the more nake binciken the more nake sake cin karo da wasu matsalolin, Amma idan bincikena ya tabbatar da abunda nake zargi, mutane da yawa a ƙasar nan za suji kunya"

Abbas yace  "wai tukuna ma inga abunda kayi kake son ka nuna masan, suwaye za suji kunyar?"

Yusuf yace  "kabari sena kuma dawowa se mu cigaba da zancen yanzu ina sauri tunda baya nan tafiya zanyi"

Yusuf yaja System ɗinshi yai waje, bayansa Abbas yabi da kallo yana ƙwafa, 'Sena sa an Ƙwace aikin daga hannun ka tukuna za kayi bayani'

Sakina tana so ta yiwa Yusuf magana, amma sam yaƙi bata fuska, tana ji tana gani ya fice daga gurin, tunani ta shiga yi, yadda Yusuf ya yadda da Abbas babu lallai kota gaya masa ya yadda da abunda tace.

Yusuf yaje yayiwa Widad siyayyar data aike shi, ya wuce gida ya gama abunda yake yi sannan ya koma gidan su Widad.

Har yanzu gabansa faɗuwa yake, ya ɗau kayan ya shiga ya kai mata, sedai da yaje bata part ɗin nata se maganta akan gado.

Ya ajiye mata kayayyakin, ya ɗaga ƙasan pillow ɗinta ya sa mata ATM Card ɗinta ya fito.

A falo ya ci karo da maman su Amal, ta masa wani irin mugun kallo tace  "kai daga yau, bana son sake ganin ka shigomin falo ba tare da ka nemi izini ba, na gaji da wannan sintirin da kakemin, baligi kana ratsawa kana wuce ɗakin ta, baze yuwu ba"

"kiyi haƙuri Hajiya, nima ba da san raina ba, sedai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login