Showing 87001 words to 90000 words out of 135096 words

Chapter 30 - Akidata Book 1 Hausa Novel Complete

01 Jan 2025

770

mutum a ƙasar nan, Insha Allah zasu kuɓuta"

Daula yace "ai ba wai kuɓutar tasu ba, yadda zasu tsira da rayuwar su bayan sun kuɓutan shi nake tunani"

Saleh yace "karka damu da wannan Yallaɓai, yanzu Addu'ar mu suke buƙata insha insha Allah zasu kuɓuta"

Bulama ne da matarsa suka shigo ɗakin shida Anwar da su Ramadan, Bulama yace "sannu ya jikin naka?"

"Alhamdilillah"

"Ubangiji Allah ya ƙara afuwa"

"Ameen" na suka shiga yi masa sannu, Anwar ya ƙarasa kusa dashi yace "Sannu Daddy Allah ya baka lafiya"

Kasa Amsawa yayi sema share ƙwalla da yayi yace "Anwar an sacemin Widad, an sace autar daula, ga yaron dabe ji ba be gani ba shima ta ritsa dashi"

Cikin damuwa Anwar yace "ka kwantar da hankalinka Daddy, Insha Allah zasu kuɓuta, za'a gansu, babansu Fahad yace min an kai report"

Alhaji Nasir yace "Allah yasa su kuɓuta gaba ɗaya yasa karsu cutarmin da su"

Alhaji Bulama yace "ka jika da wani zance, muji da 'yarmu da' aka sace kana wani kar'a cutar dasu"

Alhaji Daula yace "haba Bulama, ai gara su riƙe Widad su saki Yusuf, yana zamansa a dalilina da 'yata ya shiga hatsari, in gaya maka gaskiya tsakanin Widad da Yusuf ba wanda bana so, Allah ya samin ƙaunar yaron a zuciya ta, bazan so ya rasa ransa ba shima, Allah ya bayyana min su duka ba wanda bana so"

Kuka sosai Alhaji Nasir yake kamar ƙaramin yaro, Anwar ne ya rungume shi a jikinsa, yana faɗin "yi haƙuri Daddy, duk zasu kuɓuta cikin ƙoshin lafiya, kar lafiyar ka ta taɓu, kaima muna buƙatarka"

Hajiya Sarah tace "dole Baban Widad yayi kuka kuma gaskiya ya faɗa, yaron nan shima abun tausayi ne, beji ba be gani ba tsautsayi ya ritsa dashi abun da tausayi"

Alhaji Bulama yace "dama ku mata wani lokacin ba hankali kuka cika ba, dama Allah yayi haka zata faru dashi, amma mudai mu samu 'yarmu ta kuɓuta"

Hajiya Sarah tace "shi Yusuf ɗin ba uwace ta haife shi ba? Ya zataji idan ta samu labarin ɓatan ɗanta?"

Ramadan ne yai saurin cewa "Mummy kiyi haƙuri kiyi shiru, duk zasu bayyana insha Allah, Allah sarki Yusuf ɗin nan yana da kirki wallahi ga haƙuri da yawan murmushi"

Likita ne ya shigo ze duba Alhaji Nasir, dan haka duk aka basu umarnin su fita daga ɗakin domin a duba shi.

Anwar ya maida su Alhaji Nasir gida, ya shiga part ɗin Fahad, sedai ya tarar da shi da mace suna shan shisha, Anwar ya girgiza kai dan ya saba ganin Anwar a wannan halin, mussman da suna ƙasar waje, Anwar yace "Fahad baka san meya faru da Widad bane da direbanta, ina ta kiranka baka ɗaga ba?"

Fahad ya fesar da hayaƙi yace "Nasani mana"

"Amma ko Daddyn namu ai yakamata kaje ka duba"

Fahad ya kalle shi yace "Daddynku ku suwa? Baza'a dubo shi ɗin ba, ni burina duk inda ta shiga a nemo min mata ta, dan nasan wannan tsinannen direban ne ya gudu da ita, kuma sena nuna masa iyakarsa"

Karuwar dake tare da Fahad tace "Baby wai maganar wa kuke yi ne?"

Fahad yace "ba ruwan ki uwar shishshigi, jeki shirya inzo in maida ke gida"

Anwar yace "Fahad se yanzu na sake tabattar da Widad a kan gaskiya take na ƙin yadda da mutane, yanzu Fahad kasan nida kai iyayenmu basu da ƙarfin kaimu ƙasashen waje, amma ya ɗauke mu kamar yaransa, ya kaimu ƙasar waje mukayi karatu, dukkaninmu ba wanda be mallakawa motar hawa ba da gidan kansa, muba komai ba silarsa muka zama wani abu, kalli yadda muke fantamawa a cikin rigar arzikinsa, albarkacin sunansa duk inda muka shiga a faɗin ƙasar nan muna da Alfarma, yau shine Iftila'i ze faɗa masa amma ka nuna halin ko in kula, Anya Fahad kana gayawa kanka gaskiya kuwa "

Fahad yace " A'a sedai idan yanzu zaka fara gayamin gaskiyar "

Yai maganar tareda miƙewa ya shige bedroom ɗinsa, jiki a saɓule Anwar ya baro gidan Bulama ya koma Asibiti, ya bawa Alhaji Nasir Abinci ya canza masa kaya, sedai yaita mamakin rashin ganin mahaifiyarsa taje Asibitin gurin mijinta.

Gida ya koma yana tunanin butulci irin na Fahad, a falo ya tarar da Hajiya Halima tana cin Abinci suna kallon zee world, sedai kamar Amal ce a cikin damuwa.

Anwar yayi sallama suka amsa gaba ɗaya, Anwar yace "Mummy meyasa ba kije Asibiti ba?"

"bana jin daɗine, bana son inje inga abunda ze sake ɗagamin hankali"

"Amma Mummy ai jikin nasa da sauƙi, kuma yakamata ace ko su Ramla sunje duba shi"

A fusace tace "Ubansu ne da lallai se sunje duba shi, fita ka bani guri dalla"

Buɗe baki yayi yana kallon mahaifiyarsa yana ƙoƙarin tabattar da anya daga bakinta wannan maganar ke fitowa?



Duhu ya fara yi, sauro ya shiga ambaliya a gurin nan, Yusuf ya zauna se akin yi mata fifita yake da wani gutsararren kwali, A hankali Yusuf yace "Kidena musu taurin kai kinji, sannan idan an baki Abincin ki karɓa kici, baze yuwu ki zauna da yunwa ba"

"ba zanci ba" ta bashi amsa

"kin fi son su cigaba da azabtar dake?"

Shiru tayi masa ba tace komai ba, can ya kuma cewa

"dan Allah ki basu abunda suke nema, dan su ƙyale ki ko a yanzu kin galabaita"

"wallahi ko zasu kasheni bazan basu ba, shiyasa nace tun farko su sake ka ni su barni anan"

"tayaya zasu sakeni in tafi, alhalin kina gurinsu sedai kome ze faru ya faru muna tare"

Ajiyar zuciya ta shiga saukewa, tana jin yadda sauro ke shagali akanta, abunda bata saba ba, bata son yin kuka dan yanzu Yusuf ze ɗaga hankalinsa

Cikinsu babu wanda ya rintsa, har gari ya waye, taimama sukayi sukayi sallar Asuba.

Fuskar Widad duk ta kumbura saboda sanyi da cizon sauro, kuma har a lokacin jikinta babu ƙwari.

Yusuf yana zaune, yayin da Widad ke kwance akan tabarmar, buɗe ƙofar ɗakin akayi suka sake shigowa su huɗu.

Suka kalli inda Widad ke kwance, ɗayan ya buga mata tsawa yace

"tashi ko in taka ƙafarki in karya banza"

Gyara kwanciya tayi ta juya musu baya, alamar bata da niyyar tashin, yau Yusuf ya ƙara tabbatar da azababben taurin kai da Widad ke dashi.

Da sauri Yusuf yazo inda take ya ɗaga ta zaune yace "ya haka ne, so kike yauma su dake ki"

Wani banzan kallo tayiwa shugabn nasu ta ɗaunke kai tana hura hanci.

Ɗayan yace "shegiya se kyau kamar ita tayi kanta, amma zuciyar ta kamar dutse shegiya me kama da sadakar yalla"

Babban su yace "zamuyi maganinta kafin tabar gurin nan, da ganin idonta yunwa take ji, amma saboda taurin kai taƙi cin Abinci, ku ɗakko Abinci ku bata idan taga dama taci"

Shinkafa da wake ce irin garau garau ɗin nan takan 'yan talla, tayi sanyi ƙalau ga ba mai sosai, suka dire mata a gabanta, yunƙurawa tayi zata sake fatali da Abincin Yusuf ya riƙe ta yace "dan Allah ki daure kici, kinga tun shekaranjiya rabonki da Abinci"

Ta kalli idon Yusuf tace "bazan ci ba"

Ɗayan yace "kai dalla ka ƙyaleta mana, kar taci ubanwa tayiwa, Oga ka fara aiki kawai"

Rarrashin duniya Widad tayi mursisi taƙi cin Abinci.

Babban cikinsu ya ɗakko wayarsa zeyi kira.



"Nurat ki kaiwa Daddynki tea ɗin nan da baƙinsa, kafin yazo ya ishemu da faɗa"

Nurat ta miƙe ta ɗauki kayan tea ta nufi part ɗin mahaifinta.

Alhaji Munir ya shafa ƙaton cikinsa yace "nifa bakina yaƙi rufuwa ma, nasan dole abun nan yazo hannunmu a yau base gobe ba, nace a tura masa saƙo, kodai ya bayar ko mu cigaba da tsare ta"

Alhaji Musa yace "ba kai kaɗai ba ni kaina ina cikin murna, sun kwana a hannu, Daula yana gadon Asibiti yana ta sharɓar hawaye, mutum se taurin kan tsiya kamar arnen dutse"

Suka kwashe da dariya, Alhaji Haruna yace "dalla ƙyaleshi, gefe guda baze samu Halartar taron shekara na kasuwanci ba, da haka zamu sanar da cewa an samu gagarumar Asara kasuwancin da muke yi, zamu bada fake Account statement, zamu kwashi rabonmu kafin wancan yazo hannunmu, ai daula ya gama yawo wai shi me gaskiya"

Suka sake kwashewa da dariya, wayar Alhaji Haruna ce ta fara ringing, ya ɗaga ya sa musu a hands free, Alhaji Haruna yace "Ya me ake ciki ne?"

"Yallaɓai tunda nake aikin nan, ko a maza ban taɓa ganin mutum me baƙin taurin kai kamar yarinyar nan ba, kwana biyu kenan taƙi cin Abinci, ruwa kawai take sha, gashi kamar bata da lafiya kullum tana kwance ko magana seta ga dama take yi"

Alhaji Munir yayi tsaki yace "dalla ku rabu da ita, ku karɓo mana abunda muke buƙata, sannan ku turawa ubanta saƙo shima koya bamu ko kuma ku kashe ta"

Daga wayar akace "An gama Oga, yadda kukace"

Nurat da taje kai musu shayi jikinta ya shiga ɓari, dan tsaf taji hirar da mahaifinta suke yi, cikin sanɗa taje ta ajiye farantin kayan shayin, ta ruga da gudu ɗakinta ta saka hijjabi ta ɗau wayarta ta fice daga gidan.



Babban cikin mutanen wanda suke cewa me Adda ne ya ɗakko wata kujera ya zauna a gaban Widad ya kalle ta cikin tsawa yace

"ke kalleni nan, ina takaddun nan suke? Ki gayamin cikin ruwan sanyi ko kuma in kasheki in koma in kashe wancan daƙiƙin uban naki"

Sunkuyar da ka tayi tai shiru, Yusuf yace "Yana miki magana ki gaya masa, su ƙyaleki ki huta"

Kallon Yusuf tayi da jajayen idonta sannan tace "takaddun da suke nema, akwai masu shi nayiwa Daddy Alƙawarin miƙasu ga masu shi, kuma na bawa masu shi suna can suna yawon su a gari, me suke so kuma ince musu"

"ƙarya kike, duk binciken da'akayi sun tabattar da suna wajen ki dan haka ki gayamana inda suke"

A harzuƙe tace "bazan faɗa ba, nace bazan faɗa ba kayi abunda zaka yi!"

Kan bindiga ɗaya yasa ya buga mata a baki, take jini ya shiga zuba daga bakinta Yusuf ya gigice ze tashi, suka ɗora masa bindiga aka "kana motsawa zamu fasa kanka da harsashi"

Widad ta tattaro dukkan yawun bakinta, me ɗauke da jini ta tofawa shugabannin nasu tace "wallahi ko me zaki sedai kayi, bazan bayar ba ka koma ka gayawa Azsaluman da suka saku aiki cewar bazan bayar ba, kuma matsorata ne tunda suka gaza fitowa gaba da gaba su karɓi abunda suke so, kuma ko sun kasheni na kafa musu tarkon da ko bayan raina se Asirinsu ya tonu, saboda na sansu kuma na tattara duk wata hujja da yakamata a kansu san......

Bata ƙarasa ba ta kuma jin wani marin a fuskarta, a duk lokacin da suka daki Widad Yusuf ji yake kamar ƙirjinsa ya tsage dan baƙin ciki, sedai ba yadda ya iya muddin yayi wani yunƙuri dabe gamshesu ba zasu mata illa, dan ba imani ne dasu ba, ga Widad bakinta yaƙi mutuwa.



Nurat bata tsaya ko ina ba se gidan su Widad, a waje ta tarar da Anwar ya fito da mota ze fita, Anwar ne ya ganta dan sam bata lura dashi ba yace "Nurat"

Ɗaga kai tai ta kalle shi sannan tace "Yaya Anwar ashe ka dawo, babu Labari"

Anwar yace "Na dawo, ina zaki haka naga kamar bakya hayyacinki"

Nurat tace "gurin Widad nazo"

Anwar yace "baki san na sace ta ba ita da direbanta?"

Hannu ta ɗora a ka, ta durƙusa a gurin ta fashe da kuka, Anwar ya fito daga motar yace "Nurat lafiya kuwa?"

Nurat tace "lafiya ƙalau, dan Allah kasan wani ɗan uwanta wanda suke yawo tare?"

Anwar yace "Ai Widad bata da ɗan uwa"

Nurat tacs "Nasani, wannan zaka ga tare suke yawo, ban san sunashi ba ya cemin ɗan uwanta me shi, wani dogo kamar bafulatani, me yawan murmushi"

Anwar yace "ko Yusuf kike nufi?"

Nurat tace "ban san sunansa ba"

Anwar yace "indai Yusuf ne tare suke yawo kam, kuma tare aka sace su"

Zare ido waje tayi tace "tare aka sace su, na shiga uku ni Nurat, meyasa aka sace su?"

Anwar yace "shine abunda bamu sani ba, amma 'yan sanda na nan na bincike yanzu haka zanje Asibiti gurin daddynta ne, daga nan mu koma station"

Nurat tace "zan iya binka in duba shi?"

Anwar yace "meze hana? Muje"

Suka shiga motar suka tafi.



Me Adda ya jinjinawa wannan baƙi taurin kai na Widad, yasa bakin bindiga ya daki kanta dashi ta kurma wani uban ihu tace "wallahi ba zan faɗa ba, sedai kayi min duk abunda zakamin"

Ya kuma ɗaga bakin bindiga ze da keta, Yusuf ya miƙe ya riƙe shi gam yace 'Anya akwai imaniba zuciyar ka, kalli yadda take kururuwa amma ba zaka ƙyaleta ba"

Me adda yasa hannu ya hankaɗa Yusuf amma Yusuf ko gezau beba, ya kalli Yusuf ya kuma ƙoƙarin hankaɗeshi amma Yusuf ko gezau balle ya kai ƙasa dukda ya kwana biyu ba Abinci amma hakan besa ya faɗi ba.

Haɗuwa sukayi su huɗu suka kama dukan Yusuf, da manyan sanduna, suka masa jina jina sannan suka ɗaureshi, tun suna dukansa Widad na ihu harta suma a gurin.



Koda Anwar yaje a Asibiti seya tarar da mahaifiyarsa da su Ramlah a gurin, tayi masa ƙaryar wai da'aka gayamata abunda ya faru suma tayi seda aka kaita Asibiti shiyasa bata zoba, shi kuma Daddy ya yarda da abunda ta faɗa.

Anwar tun yana mamakin abubuwan da suke faruwa harya dena.

Nurat ta ƙarasa gaban Gadon Alhaji Nasir tace "Sannu Daddy ya jiki".

Ta faɗa tana sheshesheƙar kuka.

Alhaji Nasir yace "da sauƙi Nurat, ashe kin samu labarin ɓatan ƙawar ki?"

Ta jinjina masa kai alamar eh, yace "to ki cigaba da Addu'a Allah ya bayyana ta, sannan ki koma gida kar babanki yayi miki faɗa kinzo nan"

Ya kalli Anwar yace "ɗan beauty mayar min da ita gida kaji"

Yai maganar cikin ƙarfin hali cike da zolayar Anwar.
Anwar yayi murmushi, tare da wayancewa ya goge ƙwallar dake idonsa, kallo ɗaya zaka yiwa Alhaji Nasir kasan yana matuƙar jin jiki.

Tunawa yayi da abunda Widad ta gaya masa daren da abun ze faru, take yaji wasu hawayen na bin idonsa, duniya Kenan Abun tsoro.

Saleh ya kasa zama, ya kasa tsaye abun duniya ya dames hi, tabbas Alhaji Nasir mutumin kirki ne ya masa alkhairi daban daban a rayuwar sa, ga Yusuf dabe ji ba be gani ba shima an ritsa dashi, anya hakki ze barshi kuwa, wannan tunanin ne ya cika masa zuciya ko Abinci ya kasa ci.


Widad ta buɗe ido a hankali ta kalli inda Yusuf ke kwance, duk jikinsa jini, se sauke ajiyar zuciya yake, gashi an ɗaure shi tamau da sarƙa.

Ko tashi bata iyayi saboda dukan da take sha, jikin ta ko ina rauni ne, ta janyo jikinta a hankali tazo inda Yusuf ke kwance kawai ta faɗa kansa tana kuka.

"Yoseef dan Allah ka tashi, dan Allah kayi magana idan kana jina"

A hankali can ƙasan maƙoshinsa ido a lumshe yace "Insha Allah zamu kuɓuta, ki dena kuka, ina mana Addu'a nasan Daddynki ma yana yi, Ummana ma tana yi mana"

Haka ta cigaba da ƙoƙari ko zata iya kwance Yusuf, amma abu yaci tira.

"Ranka ya daɗe yarinyar nan fa baza tayi magana ba, mun daka mun daka amma kamar jinjirar jaka saboda taurin kai, mun mata jina jina amma taƙi faɗa se rashin kunya take yi, gashi kwana huɗun nan Ruwa kawai suke sha, ita muna bata Abinci amma taƙi ci duk ta galabaita "

Alhaji Haruna yace " A tauna tsakuwa, dan aya taji tsoro kuyi mata azaba wadda zataji a jikinta"

Me adda yace "An gama ranka ya daɗe"

Ya buɗe ƙofar ɗakin dasu Widad ke ciki, tana zaune a gaban Yusuf ta zuba masa ido idonta yayi jawur saboda yunwa da wahala, gashin kanta duk ƙasa da abun ciyay, saboda birgimar da take a gurin, ya sauka a kafaɗarta ya baje kamar mara hankali.

Suka ƙaraso suka kwance Yusuf, da shima yake a mugun galabaice, suna kwance shi Widad ta kama ƙasan rigarsa tana goge masa jinin jikinsa, me Adda ya fizgota ya zaunar da ita tana fuskantar sa yace "ke dan uwarki wannan shine karo na ƙarshe da zan tambayeki, dan mun gaji da wannan sintirn a wannan surƙumin dajin, ina takaddun nan suke?"

Cikin tsawa tace "ban sani ba! Kuma karka sake zagin uwata dan uwa bata fi uwa ba"

Yadda gashin kanta baƙi kamar na Larabawa ya baje, gaba ɗaya seta burgeshi danƙo gashin kanta yayi ya miƙar da ita tsaye, tsanani zafi yasa ta fasa ihu, Yusuf ya yunƙura ze miƙe suka sake buga masa sanda a ƙafa ya faɗi ƙasa.

Ya kai bakinsa na Widad da niyyar ya haɗe bakinsu, tayi masa gware da kanta, dukda yaji zafi hakan besa ya cikata ba, ya kuma danƙar gashin kanta ze haɗe bakinsu, ta tattaro ƙarfinta ta daki mararsa da ƙafarta, a gigice yayi jifa da ita, ya ɗakko ƙaramar pistol ya harbe ta a hannu, tare sukayi ƙara da Yusuf ta zube a gurin jini na zuba a dantsenta.

Me adda miƙewa tsaye ma kasawa yayi saboda bala'in azabar da yake ji, 'yan uwansa suka ɗauke shi, suka sake kulle su Widad.

Yusuf ya ƙarasa kan Widad ya ɗagota, a gigice yake magana "Widad sannu, kina ganina?"

Ta jinjina masa kai dukda idonta na ƙoƙarin lumshewa, jikinta se rawa yaje gumi na tsatstsafo mata ta ko' ina.

Yusuf ya ɗau ɗan siririn mayafint da tazo dashi ya ɗaure mata damtsen, ya rungomata jikinsa yana jijjigata yace

"Dan Allah karki tafi ki barni, zamu bar gurin nan insha Allah, zan maida ke gurin Daddy, dan Allah Widad karki tafi ki bar Yusuf"

Sosai hawaye ke zuba daga idon Yusuf, magana takeson tayi amma ta kasa, se rawa da bakinta yake yi kawai, ta ɗaga hannu da nufin ta kaishi fuskar Yusuf amma abu ya gagara hannun ya sauka tun tana ganin Yusuf dishi dishi harta dena ganinsa wuyanta ya langaɓe.

Rungume ta yayi a jikinsa yana ambaton Allah, yana sheshesheƙar kuma, yayin da mayafin da ya ɗaure mata hannu dashi ya jiƙe sharkaf da jini.



In an karanta ayi share please, masu neman recent pages dan Allah ku dinga dubawa a watpad, @ Ayshercool7724.


Domin gyara, sharhi ko shawara
Ayshercool
07063065680

                    _*AƘIDATA*_
       

PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

*Story and written by*

_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_

The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *

I dedicated this book to

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login