Showing 132001 words to 135000 words out of 135096 words

Chapter 45 - Akidata Book 1 Hausa Novel Complete

01 Jan 2025

759

ware"

Widad tace "Toke ya kika gani? A garin nan banda Allah se shi na sani, idan lafiyarsa ta taɓu akwai damuwa sosai"

Gwaggo tace "ƙyaleta Amarya, zolayarki take"

Widad tace "Mama, dan Allah abun nan na ɗakinki sunmin kyau sosai"

Gwaggo tace  "me fa?"

Widad tace "kwanukan nan da kika shirya a ɗakinki, sunyi kyau sosai fa"

Gwaggo tayi murmushi tace "Widad kenan, kayan Su Samira da fanteka kenan, mu dasu mukeyin adon ɗaki"

Widad tace "Masha Allah, gaskiya sunmin kyau sosai Mama"

Can ta hango bulugari, a gefen Gwaggo zata kaɗa miya.

Widad tace "ya sunan wannan Mama? Wanda kike juya miya dashi"

Gwaggo tace "Bulugari kenan, dashi muke kaɗa miya"

"Mama wannan tunkunyar naganta baƙa sosai"

Gwaggo tayi murmushi tace "wannan itace Talle Amarya, tukunya ce ta ƙasa, muna girki a cikinta, miya tafi zaƙi da daɗi Sosai"

Widad tayi murmushi tace "taɓ Mama duk ban san wannan abubuwan ba, ban taɓa ganinsu ba"

Gwaggo tace "hakane dama, tunda ba kuyi rayuwar karkara ba ba lallai ki sansu ba, bari inje ɗaki in ɗakko abun kaɗi"

Gwaggo ta tashi ta tafi, tana tafiya
Hanne  tayi tsaki tace "Aikin banza mutum ya zauna yaita ƙarya, mtseww aikin banza dana wofi, wai bata san bulugari da fanteka ba"

Widad ko waigawa ba tayi ba, tai shiru abunta, Hari tace "wato Wudas kinfi jin tsoron Hanne, ta gayamiki duk abunda data ga dama, kiyi ƙus amma da nice da tuni kim hayayyaƙomin"

Wani irin kallo Widad tayi wa Hari, nan take cikin Hari ya kaɗa, ganin wani irin kallo da Widad tayi mata, se taga kamar ta canza gaba ɗaya daga kamaninta, ba shiri Hari taja bakinta ta tsuke.

Saleh ya kalli Yusuf yace "Sannu Yusuf, gaskiya kana fama, yanzu haka kuke zaune? Tana maka wannan gadarar da jin kan, bayan taimakonta kake"

Yusuf yayi murmushi yace "lafiya ƙalau muke zaune da ita, duk wannan abubuwan bata Yimin, ƙalau muke zaune Alhamdilillah"

Saleh yace "kaga nifa bana son wannan kawaicin naka, kalli yadda take wani bintsire bintsire, tana cin magani, na zata tuni ta dena wannan halin nata?"

Yusuf yace "Kai da ita ta baka amsar wannan tambayar, Amma nan ma shigo ka tarar tana bani Abinci ai"

Saleh yace "kuma fa hakane, lallai kai ɗan baiwa ne kuma na musamman Yusuf, wannan yarinyar me Azabar taurin kai, amma take kula da kai haka, ta yadda ka shiga jikimta gaskiya abun da mamaki, kayi namijin ƙoƙari fa"

Yusuf yayi murmushi yace  "Haka lamarin ubangiji yake, yanzu ya jikin mahaifinta?"

Saleh yayi shiru da alama jikinsa yayi sanyi yace  "labari mara daɗi Yusuf, yanzu ma badan ka tambaya ba bazan gaya maka ba"

A rikice  Yusuf yace "Subhanallah, meyafaru kuma?"

Saleh ya gyara zama ya waiga yaji babu motsin kowa sannan ya waigo ya kalli Yusuf yace "An sace Daula akan gadon Asibiti"

Dafe ƙirji Yusuf yayi yace "Innalillahi wa inna ialaihi raji'un, kamar yaya?"

Saleh yace "kaima dai ka tambaya, abun kamar almara, Kasan tunda yake rashin lafiya Anwar ne kawai yake sintirin jinyarsa, matarsa da sauran yaran ba ruwansu dashi, daga ya ɗan fito daga ɗakin, ya koma aka nemi Daula aka rasa, yanzu haka an kama Anwar da me Asibitin ana tuhumarsu, yau sati uku kenan sun tsare "

Dafe kai Yusuf yayi ya shiga murza goshi, wannan wane irin bala'i ne? Duk yadda yake zaton lamarin ya wuce tunaninsa, wane irin tashin hankali ne haka?

Saleh yace " ka kwantar da hankslinka fa, ban gaya maka dan ka ɗaga hankalinka ba, sedai ka tayata da Addu'a, sannan karka bari ta sani"

Yusuf yace "kuma ana bincike akan lamarin, ba'a gano inda yake ba?"

Saleh yace "kai dai ayi sha'ani, har yanzu babu Labari"

"Amma naji kamar kace kasan suwaye ke wannan abubuwan"

Saleh yayi murmushi yace "kaifa jami'in tsarone, kuma kai aka bawa wannan aikin na binciken, zuwa yanzu ai nasan ka samu haske akan binciken da kayi"

Yusuf yace "kamar yaya kenan?"

"Kana nufin baka gane me nake nufi ba? Ai shikenan mu bar zancen, kar tazo ta same mu muna maganar"

Yusuf yace "Ya Ummana kuwa Saleh?"

"tana nan lafiya, Suleiman yana kula maka da ita"

"Amma Saleh, Akwai wani abokin aikina Abbas, babban Abokina nane, yana Ibadan akan aiki, ko Suleiman yayi maka maganrsa, nasan idan yasan ina nan Abbas ze shiga damuwa ina da tabbacim se yazo nan"

Ƙura masa ido Saleh yayi, ya ɗanyi shiru sannan yace "gaskiya ba muyi maganar wani da shi ba, kai dai kunci gaba da haƙuri, komai ze wuce kamar ba'ayi ba Insha Allah"

Yusuf yace "Allah yasa"

Saleh yace  "bari in ɗan fita waje, in zaga gari"

Yusuf yace "bari in bika bana son zaman gidan ne, gara in fita in ɗan tattaka"

Saleh yace "kar kasa matarka tamin tijara fa"

Yusuf yai murmushi yace "bakomai"

Suka fito shida Yusuf, Can Saleh ya hango Widad a kusa da Gwaggo suna hira, Widad ta maida hankalinta sosai akan Abunda Gwaggon take yi.

Saleh yace "iko se Allah, da a mafarki aka haskomin wannan abun ze faru, zance sharrin mafarki ne"

Widad ta ɗaga ido ta hango Yusuf, ya fito da alama fita za suyi, Widad tace "ya dai, naga ka fito, ina zaka haka?"

"You leave alone in the room, am so boring, Saleh is going out, so i feel like to follow him"

Widad tace "gaskiya ban yadda ba, ka koma ka huta in kuma ka faɗi fa?".

"Bazan faɗi ba insha Allah, ina son in ga gari ne kawai"

Widad tace "Shikenan, kar kayi nisa dai"

"As you wish your majesty"

Saleh jinjina kai kawai yayi, yayin da Yusuf yake jin wani irin matsanancin tausayinta, ko ya zataji idan taji labarin mahaifinta ya ɓata shima?.

Haka yabi Saleh suka fice.



A harabar gidan su Nurat kuwa, Nurat ce zaune a ɗaya daga fararen kujerun dake harabar gidan, ita da Barrister Khalil cousin ɗinta, teburin gabansu ɗauke da lemu ka da kuma kofunan glass.

Barrister Khalil yace "kince kina son ganina, gashi nazo amma kin kasa cemin komai"

"Brother, aini sam ban san ta ina zan fara maka bama, na rasa me ya kamata ince maka"

"Ki nutsu, ki gayamin komai a hankali, an fahimceki Insha Allah"

Ta ɗanyi ajiyar zuciya sannan tace  "brother, game da maganar da mukayi da kaine na belin Anwar" Se kuma tayi shiru.

Khalil yace "Mhmm ina jinki, gayamin ke nake sauraro"

"Barrister, kai ɗan uwana ne, kona ɓoyewa kowa wani abun, kai bazan ɓoye maka ba, amma ina son maganar ta tsaya iya nida kai, ko Kasan akwai hannun mahaifina a cikin abubuwan da suke faruwa da Alhaji Daula?"

A hankali Khalil ya zare glashin fuskarsa, ya kalle ta yace  " kamar yaya? Ban gane me kike nufi ba"

'Nasan abun ze baka mamaki, amma kasan Alhaji Daula me silar ɓacin siyasar Mahaifina? "

"Eh na sani, nasan da wannan"

"Mahaifina yayi alwashin ko ze mutu se ya rama abunda Alhaji Daula yayi masa, ya haɗa kai da wasu manyan abokan kasuwancin Alhaji Daula, suna ƙoƙarin ganin bayansa, zancen da nake maka, da saninsa aka sace 'yar gidan Daula da direbanta"

Hankici ya ɗakko a aljihunsa ya share gumin fuskarsa yace "wani tabbaci kike dashi, akan wannan maganar da kike yi"

"Brother, nikaɗai ce sheda, se Mummy amma kasan halin Mummy da tsoro, ba zata taɓa bamu goyon baya ba, yanzun kaima ma gaya maka ne, saboda yadda abun ke cin zuciyata, na rasa wa zan gayawa inji daɗi a raina"

Khalil yayi shiru sannan yace "am sorry to say, Nurat mahaifinki gaba ɗayansa zuciyarsa babu Allah a cikinta, yanzu muddin ya gano mum sam me yake yi to tabbas ze ɗau mataki a kanmj, nasan shi ba tun yanzu ba"

"Nasani brother, nikaina tunda naje na duba Daula a Asibiti ya samun takunkumi, ya hanani fita, rannan dana fita baka ga yadda ya shaƙeni ba kamar ze kasheni"

Khalil ya jinjina kai yace "yanzu Addu'a zamu ci gaba dayi, mahaifinki yana da goyon bayan manya sosai, dan haka babu wanda ze tsaya ya ɗau mataki, sedai muyi ta addu'a"

Nurat tace "hakane Brother, but am so much disturbed wallahi"

"Kakri damu, ki kwantar da hankalinki, Dukda haka zan duba inga me zan iyayi akai"

"Shikenan nagode sosai brother, Allah ya ƙara ɗaukaka"

"Ameen ya Allah karki damu kinji, ki  kwantar da hankalinki, komai zezo da sauƙi"

Haka sukka cigaba da tattaunawa.





"Alhaji Musa wai yanzu duk kuna kallo haka ɗana ze cigaba da zama a prison? Ba zakuyi komai akai ba? Na gaji da yawon da kukemin da hankali fa"

Alhaji Musa yace "Ni yanzu me kike son inyine? Nifa bani na sa aka kama ɗanki ba, me kike so inyi?"

"Idan ba ku kuka sa aka kamashi ba, amma kuna da ƙarfin da zaku sa a sakarmin shi aiko? Wane irin abune haka, se zarya nake a tsakanin ku, amma kowa da kalar rainin hankalin daze mun"

"Kinga saurara, ni babu abunda zan iyayi akan wannan al'amarin, wannan babban case ne da yake buƙatar bincike, idan bashi da laifi zasu sake shi fa"

Hajiya Halima tace "Shikenan nagode sosai da abunda kukayi min, wato na gama yi muku amfani, zaku watsamin ƙasa a ido, zaku ga abunda zanyi"

Ta juya fuuu tayi waje kamar zata tashi sama, tana tafe tana banbami, ofishin Bulama ta tafi, ta tarar yana shirin fita, ya kalle ta yace "Halima lafiya kuwa?"

"karka ƙara tambaya ta ko lafiya, lafiyar kenan kana nan hankalinka kwance, ni kuma nawa a tashe ko baccin kirki bana samu, na zama kamar mahaukaciya, ɗana yana can a tsare, kun nunamin halin ko in kula, kun nuna baku damu da halin da nake ciki ba"

Bulama yace "Nikam Halima kina bani mamaki, ɗanki fa ɗana ne, nima nawa hankalin ba'a kwance yake ba, muna iya ƙoƙarin mu, amma abunda ake gayamana shine, ana zargin da sa hannun Anwar a wannan abu daya faru, kuma duniya ta kasa kunne taji wani mataki za'a ɗauka, me kike tsammani idan aka ji da sa hannuna aka saki Anwar? "

" Kaga sauraramin dan Allah, bana son maganar banza data wofi, na sani ka sani Anwar baze iya aikata laifin da ake tuhumarsa ba"

"A'a karki  shedeshi, ba'a shedar ɗa a zamanin nan"

"Bulama, na gama magana da kai, zanje inyi abunda ya dace kawai"

Bulama yace "abunda ya dace kamar yaya?"

"Ka zuba ido zaka gani, bar ganin kai ɗan uwanane zan iya yin komai akan ɗana, na gaya maka"

Bulama yace "hmm kibi a sannu dai, kin san ido ya fara dawowa kanki yadda kike wadaƙa da wasu daga cikin kadarorin mijinki? Mutane sun san me kike aikatawa, ki sani tsalle ɗaya ke kai mutum rijiya, amma se yayi dubu be fito ba"

Tsaki tayi, ta ɗau mukullin motarta tace "wannan kuma kai ta shafa bani ba, nasan abunda nakeyi"

Tai waje abunta, tana fita Bulama ya ɗau waya, ya danna yasa a kunnensa yayi shiru, can kuma yace "Yawwa kana jina da kyau, ina son ku ƙara tsananta tsaro da sa ido akan yaron nan Anwar, under no circumstances zaku bada belinsa, ku matsa se ya faɗi inda Daula yake, dan uwarsa ba abunda ba zata iya ba"

Daga cam ɓangaren yace "Ok sir an gama Insha Allah"



Bayan barin Hajiya Halima Office ɗin Alhaji Musa, su Alhaji Haruna suka dira, dukda haushinsu da Musa yake ji, amma ya maze ya sakar musu fuska yace "kun san yanzun nan wannan mahaukaciyar ta bar gurin nan"

Alhaji Haruna yace "wa kenan?"

"Hajiya Halima mana, tazo nan tana ta banbami, wai munƙi saka baki a sakar mata ɗa"

Alhaji Munir yace "ƙyale wannan mahaukaciyar, ni wata shawara nazo mana da ita"

Suka tattara masa hankalinsu, suna saurarensa  "Abunda nake gani shine, mu samu lauyoyin Daula, mu siye su, su saka hannu su fitar mana da wasu daga kadororinsa, a sasu a kasuwa a karya su, sannan ayi takaddun ƙarya, muce muna binsa zunzurtun bashi"

Alhaji Haruna yace "kayi magana mekyau, sedai abunda ka manta shine, lawayoyinsa basu san kan dukiyarsa kamar yadda wannan koɗaɗiyar 'yar ta sani ba, ta san komai tasan inda komai yake"

Alhaji Munir yace "to tunda yanzu ba ita babu ubanta aise muyi yadda zamuyi mu kwashi rabonmu, ko so kuke se wannan mahaukaciyar matar tasa ta ƙarar da komai ita da' ya'yanta? A ɓoye fa se saida kadarorinsa sukeyi, haka zamu zauna mu zuba ido."

Alhaji Musa ya nisa yace "duk naji ta bakin ku, kuma kowa yazo da magana me kyau, zamu jarraba lawyoyin suma, danni yanzu kuɗin tsayawa takara nake nema"

Kallonsa sukayi gaba ɗaya sukace "kamar ya tsayawa takara?"

"kamar yadda na gaya muku, bazan zauna bani ga tsuntsu bani da tarko ba"

Alhaji Haruna yace "hala ka manta da baƙin fentin da kake da shi, a dalilin Daula?"

"ina fa na manta, sedai a ƙasar nan indai kana da kuɗi ba abunda baze yuwu ba"

"Amma baka ganin hakan, ya saɓa da Yarjejeniyar mu, idan kayi haka kamar ka zame daga cikinmu ne, kuma me zaka cewa Bukar?"

"Bukar ubanane, ko haifata yayi? Ba gudu ba ja da baya, ina tare da ku amma tabbas zanyi takara"




Gaba ɗaya Yusuf ya fara jin kunyar mutanen da yake ja salla, musamman idan ya tuna abunda Widad tayi a gaban su, tunda su hakan kamar baƙon al'amarine a gare su, haka nan ya ɗan dinga basarwa, sukayi sallar magariba da isha'i suna ta sake duba shi.

Widad jin shiru Yusuf be shigo ba, yasa ta fito tsakar gida ta samu wani ɗan gidan Hansai tace masa  "kaga ɗan jeka waje ka cewa Yoseef in jini nace, baze dawo ba se sauron ya sake cizonsa yazo ya kwantamin?"

Gwaggo dake alwala tace "A'a kul kaje ka faɗi haka, kace tace  'dan Allah ya shigo gida, kar sauro ya kuma cizonsa'"

Widad tace "to ai kusan abunda na faɗa kika maimaita"

Gwaggo tace "A'a ke naki umarni da kashedi kika yi, aishi miji abun lallaɓawane da tattalawa, ki kalli yadda kika damu da bashi da lafiya, ki dinga masa magana da girmamawa kinji Amarya, yana da kirki mijinki, kema ki dinga tausasa harshen ki a kansa"

Widad tace "To Hajiya Mama"

Gwaggo tace "ni  a Hajiya, to me rai baya fidda rai da rahama, amma abun da wuya"

"Insha Allah indai da rai da rabo, zaki je saudi Arabia in dai Allah be ɗau rayuwar wani daga cikin mu ba, idan muka koma gida lafiya zaki je ƙasa me tsarki"

Tsaki Hanne tayi tace "san a sani, ji wata ƙarya kuma da son nuna iyawa, karma kisa rai ana gayamiki gaibu"

"Ke! Ki kiyayeni, dake muke taɗin, ina ruwan ki Hanne ki kiyayeni fa"

Widad ta juya kawai ta koma ɗaki, ta ɗakko ƙaramar fitilarsu ta kunna, batirin ma ya fara sanyi.

Ta zauna tayi shiru tana tunani, sallamar Yusuf ce tasa ta ɗago ta amsa masa, yaje kusa da ita ya zauna, daya kalleta se tausayinta ya kama shi yace "gani naji ance kina nemana"

"shine tun la'asar kaƙi dawowa, se sauro ya kuma cizonka ko?"

"Ai na warke, Alhamdilillah"
"dan ka warke shine se kaje, ka kuma kwaso wani zazzaɓin, kazo ka ɗagamin hankali"

"Insha Allah na warware ai, ance jinina ma yayi ƙasa, dole in dinga cin ganyayyaki"

"Sannu kaji jiki ai"

"Gaskiya muje ki dawomin da jinina dana baki"

"wai jininsa, jinin naka ma duk malaria ya ƙara samun zazzaɓi, zan biya ka jinin ka harda riba ma"

Dariya Yusuf yayi yace "ni iya nawa nake so, bana son naki danni bana son jinin me taurin kai"

"kai kai, nice me taurin kai? Zaka ga taurin kai'

Kwanciya yayi a kafaɗarta yace " dan Allah a sake rungumeni mana, i need your body warm "

Ture shi tayi tace 'kaje kaji ɗumin bargo mana"

Cikin kwantar da kai yace "A' a ni gaskiya naki nake so, ai naga yau ke kika rungumeni, idan muka koma gida sena gayawa Ummana, nima ince kina rungumeni"

Widad tace "ai kai ka fara bani ba, ka koyamin abunda ban iya ba"

Dariya Yusuf yayi yace "nayi mamakin yadda kika damu da rashin lafiya ta My queen"

"A cikin AƘIDATA babu butulci, bana manta alkhairi, bazan taɓa manta wahalar daka sha saboda rayuwa ta ba, idan na nuna halin ko in kula ga kafiyarka to tabbas banwa kaina adalci ba, dukda ana faɗin bani da kirki, banj da mutunci amma bana manta alkhairi"

Yusuf yace "waye yace miki baki da kirki, kina da kirki uwaɗakina"

"Hmm yoseef kenan, ka dena kareni danka burgeni, amma nasan bani da kirki kamar yadda da yawa mutane ke faɗa"

"ba kareki nake dan na burgeki ba, ina faɗa miki gaskiya ne kawai, amma kince bakya manta alkhairi, amma meyasa bakwa jituwa da Saleh, dukda irin taimakonmi da yayi?"

"saboda bana yafiya ga mutane ma'abota fuska biyu, da fari mahaifina ya yarda da shi da ɗam uwansa, amma ya koma ɓangaren maƙiyanmu, yanzu ya kuma dawowa ɓangaren mu, wani tabbaci muke dashi na muma baze sake juya mana baya ba? Duk yardar da nayiwa mutum, duk girman Alkhairin da yayumin, muddin yaci amanata koya min ƙarya to tabbas ze shafe dukkan alkhairansa a idona, bana yafewa mayaudari da maƙaryaci ko me fuska biyu, wannan itace AƘIDATA!!!




TOFA! Alhamdilillah nan na kawo ƙarshen kashi na ɗaya a littafin AƘIDATA,

Ɗanɗano daga Littafi na biyu



(idanunta sunyi jawur, kamar wadda aka zubawa barkono saboda kuka, ta sunkuyaf da kanta ta shafi ciknta, cikin zubda hawaye tace "wace amsa zan bawa abunda yake cikina, idan har ya girma ya samu labarin mahaifiyarsa taje kotu ta bada sheda akan mahaifinsa an kai shi prison, kaicona haɗuwa ta da Yusuf ta zame masa babbar ƙaddara a rayuwarsa, ya sadaukar da rayuwarsa don in ganta tawa, amma maƙiyana sun na ƙoƙarin cin galaba akanmu, abun da basu sani ba shine...............)

Karku bari a baku labari, saƙar labarin mukayi a na farko, tufaka da warwarar gami da cakwakiyar suna littafi na biyu dana uku, anan gwaramar take


SHINE MEYE LABARIN YUSUF?
MEYE LABARIN WIDAD?
WAYE MAMALLAKIN ABUNDA AKE NEMA A HANNUN WIDAD?
MEYE ABUNDA AKE NEMAN?
WAYE YA SACE DAULA?
SHIN ZASU BARO ƘAUYEN NAN?
ZASU KOMA GIDA DA WANNAN AUREN?
YA ZATA KAYA TSAKANIN WANNAN MANYAN ALHAZAI?
YA WIDAD ZATA YI

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login