Showing 105001 words to 108000 words out of 135096 words

Chapter 36 - Akidata Book 1 Hausa Novel Complete

01 Jan 2025

776

ita ya ɗaga .

"ban samu halartar zaman da kuke a daren yauba, hakanma duk yana cikin shirina ne, yakamata ku maida hankali gurin gane cewar wani yana muku zagon ƙasa, akwai na jikinku wanda yasan siriinku shine yake ta dagula muku lissafi, ku maida hankali gurin gano waye, sannan kusam duk yadda zakuyi ku kama wanda sukayi garkuwa da 'yar gidan Daula ku kashe su, in bahaka ba akwai gagarumar matsala, sannan ko a mace ko a raye ku tabattar an kama yaran nan an kashesu"  yana gama maganar ya kashe wayarsa.

Nan fa suka sake shiga wani ruɗanin, tabbas inba wanda yake cikinsu ba babu ta yadda za' ayi Su Widad su iya tsira daga inda aka ɓoyesu.

Alhaji Haruna yace "to kun daiji abunda Alhaji Bukar yace, yanzu abunda za'ayi shine, kusa a binciko mana wanda aka bawa bincike hukumar jam'ian tsaro, ayi karɓo mana sakamakon binciken, hakan ze ƙara haska mana wani abun"

Alhaji Munir yace "wannan kuma aikin Saleh ne, shi'aka ɗorawa wannan ragamar"

Alhaji Musa yace "Na kira shi sam labarsa bata shiga, inaga zan tura ɗan aike a kiramin shi da safe"

Haka suka gama tattaunawa suka tashi ba tare da cimma wata ƙwaƙwarar matsaya ba.

Da safe Hajiya Halima nata safa da marwa, layin Ramlah sam baya shiga, ƙarfe goma na safe sega Ramlah ta dawo, Hajiya Halima tace  "daga ina kike?"

Kafin tayi magana Fahad ya shigo, Yace  'Mummy barka da safiya, mun miki laifi ko? Wallahi bayan mun dawo daga cinema ne naga kwana biyu ba taje gidanmu ba, kawai muka zarce can, daga nan kuma mumsy tace seta kwana tunda bata zumunci "

Hajiya Halima tace " Aida ta kira ta gayamin, hankalina ya tashi ince kaddai kuma an sace mana ku"

Ramlah tace "haba Mummy wani irin sacewa kuma, ai an san wanda ake sata, ina tare da Fahad waye yavisa ya saceni"

Sukayi dariya gaba ɗaya, Fahad ya kashe mata ido, sukayi Sallama ya tafi.

Ramlah na zuwa ɗakinta ta jefar da jakarta ta kife akan gado ta cigaba da bacci, saboda har yanzu ƙwayar da ta sha bata saketa ba, kuma ga rashin sabo dama, dan bata taɓa shan kayan maye ba.

Yusuf bayan ya dawo daga sallar Asuba, har ya kwanta ya tashi, ya duba shimfiɗar Widad yaga bata nan, zumbur ya miƙe zaune a gigice yana waige waige, miƙewa yayi ya fito tsakar gidan bakowa, saboda yanayin garin da sanyi kuma gari be gama waye ba, leƙe leƙe ya shiga yi yana nemanta, can ya hangota daga wani ɗan lungu tana tsaye tana leƙa wata taga se murmushi take, hannunta riƙe da brush da toothpaste, kan nan ko ɗan kwali babu, gashinta ko taza babu ta naɗeshi da ribbon ya kwanta a bayanta.

A hankali ya ƙarasa inda take cike da son sanin me takewa wannan murmushi haka?

Jin mutum tayi a tsaye a bayanta, ta juyo a ɗan razane, Yusuf ta gani a tsaye a daf da ita.

"meye haka?"

Yusuf yace "gani nayi kina tsaye kina murmushi, shiyasa nace bari inga abunda ya saki nishaɗi haka? Sannan gari akwai sanyi fa, kalli kanki babu ɗan kwali kar mura ta kamaki, sannan kayan jikinki  maza na shiga na fita a gidan nan, kar gari yayi haske suzo su sameki a haka, su kansu matan gidan zasu ga hakan wani iri saboda ya saɓawa Al'adunsu"

"Wai kai meyasa ka fiye shishshigi da takura ne?"

"ba shishshigi da takura bane, kinga yanzu kina da Aure fa"

"kaga wannan Auren fa dashi da babu duk ɗaya, karka ƙara sawa ranka wani Aure mukayi"

Yusuf ya ɗanyi murmushi, cike da basar da zancen  yace   "kin tsorata nifa, harna kwanta na duba ban ganki ba, shiru shiru kuma naga baki shigo ɗaki ba"

"hmm kayi zaton zan gudune? In gudu inje ina? Ko kana zaton zan gudu da wannan Auren naka a kaina? Idan kaga na gudu ko na bar ƙauyen nan to tabbas ka sakeni ne"

Yusuf yace "idan kuma ban sake kin bafa?"

Juyowa tayi ta saka idonta a nasa tace "me kace?"

Girgiza mata kai yayi alamar bakomai, ta harareshi tace  "ban guri in wuce"

Seda ta tafi ya Leƙa me take kallo, ɗakin zomaye ne, an kunna musu aci balbal an rataye ta, se guje guje suke suna haƙa ƙasa, da wasanninsu shine abunda yasa ta nishaɗi ta tsaya take kallonsu.

Yusuf ya koma ya kwanta bacci ya ɗauke shi, ita kuwa Widad data gama brush ɗin komawa tayi ta cigaba da kallon zomaye, seda ta gaji sannan ta koma ɗaki.

Yusuf yayi juyi ya buɗe idonsa a hankali, ya sauke su akan Widad, ta gyara shimfiɗarta sa kanta, ta sauke Akwatunanta tana ta gyara kayan ciki, ta ware masu datti ta tattare Akwatunan ta canza musu guri, duk Yusuf yana kallonta, Widas sam bata son ƙazanta, tana da matuƙar son tsafta a rayuwarta.

Yusuf ya tashi ya kwashe kayan shimfiɗarasa ya ninke, bata kula shi ba sabgoginta kawai take, Yusuf yayi mamakin danganar da Widad tayi, dukda har yanzu bata saba da abubuwa da yawa ba.

"wai babu inda za'a samu inji wanki ne? Ina son a wanke min wannan kayan ne"

Yusuf yace "Ai baki da wani injin wankin daya wuceni, in kin haɗa se in ɗiba inje in wanko su"

Widad tace "kaine zaka wankemin kayan?"

Yusuf yace  "eh mana, ko kinga alamar injin wanki a garin nan, tunda muka zo kin taɓa ganin wuta?"

"to gasu nan na haɗa, kaje kace a bani ruwan wanka"

Yusuf ya girgiza kai yace "to"

Ya miƙe ya ɗau bokiti ya fita, Widad ta buɗe Akwatinta ta ɗakko towel ta ɗaura, ta saka hijjabi ta biyo bayansa yadda ana haɗa ruwan se ta shiga tayi wanka.

Mutan gidan sunata hada Hadar yadda za'a haɗa karin kumallo, ga dukkan alamu yau mutuniyar Widas ce da girki, wato Harira.

Yusuf ya durƙusa ya gaishesu, cikin jin nauyi kafin yayi magana Gwaggo tace  "Yusufa na ganka da bokiti, ruwan wankan za'a zuba mata?"

Yusuf yace  "eh Mama"

Tace  "kawo in zuba maka anan, ya jikin nata kuwa"

Yusuf yace "jiki Alhamdilillah"

Tace  "Madalla, nikam ya sunan nata ne? Bamu san sunanta ba"

Yusuf yayi murmushi yace "Sunanta Widad"

Hari dake gaban murhu ta juyo da sauri tace 

"Bala'i, wannan wane irin sunane? Hudas ko wudas sekace kayan citta da masoro wane irin sunane wannan"

Tsakin Widad ne yasa Yusuf juyawa, yadda ta tamke fuskane ya tabattar maaa sa taji abunda Hari tace, Yusuf kamar yayi dariya Amma ya basar kar suyi faɗa a gaban mutane.

Gwaggo tace "kaga 'yar halak, ana zancenta se gata, sedai ni wannan sunan nata na Larabawa bazan iya faɗa ba, Amarya ya jikin naki?"

Widad a ranta tace "wai Amarya Taɓɗijan"

Yusuf yace "Ana miki ya jiki?"

"Naji sauƙi"

Galala Hari ta bita da kallo tace "Ashe bahaushiya ce, wallahi ganinta nake kamar bata jin hausa, yo aini harna fara tunanin ko kurma ce, ashe tana magana sannu Amarya wudas, ashe kina magana Allah sarki, ya jiki?"

Sake yamutsa fuska Widad tayi, 'ita dai wannan matar bata gajiya da magana, kodai bata san yadda haƙoranta suke bane take buɗesu tana surutu haka, bar wani kore kore ne a jikinsu, ga maganar tsiya da take dashi"

Widad bata kulata ba, aka haɗa mata ruwanta, Yusuf ya kaimata inda take wanka.

Aka haɗa Yusuf da yaro ya rakashi rafin da matasan garin suke haɗuwa suyi wanki.

Amlace ta shiga ɗakin Ramlah, ta dinga bubbuga mata filo, da ƙyar Ramlah ta tashi a fusace tace  "Meye haka Amal?"

Amal tace  "Anya lafiyar ki kuwa? Ƙarfe biyi fa, amma har yanzu bacci kike, yakamata ki tashi haka ai"

Miƙewa tayi zaune tana miƙa tare da duba agogo, dagaske biyu na rana, haka ta miƙe ta tafi banɗaki tayi wanka sannan ta ɗanji ƙarfin jikinta.

Koda Saleh ya dawo kano, be biya ko'ima ba Asibiti ya fara zuwa duba jikin Alhaji Nasir, amma yanayin jikin nasa se godiyar Allah, Nurses suka gaya masa Anwar yaje masallaci.

Saleh ya zauna a kusa da Alhaji Nasir, wanda idanunsa ke lumshe yake numfashi da temakon Na'urar dakw bashi iskar Oxygen, ya riƙo hannunsa da suka yi sanyi ƙalau, cike da tausayawa ya kai bakinsa daidai kunnensa  yace
"Allah ya baka lafiya Yallaɓai, 'ya' yanka sun kuɓuta daga hannun miyagun nan, yanzu haka suna wasu ƙauye na basu mafaka, saboda tseratar da Rayuwarsu, Yusuf yayi ƙoƙari matuƙa ya kula da Amanarka, yana kula da gimbiyarka sosai, Amma munyi maka wani laifi da ban san ya zaka ɗauki abunba, Na wuce gaba Yusuf ya Auri 'yarka, dan kasan bata yadda da kowa seshi, kuma baze yuwu ya cigaba da kula da ita ba, tunda ba muharramarsa bace"

Dukda Alhaji Nasir ba iya magana zeba, da alama yana jin abunda Saleh yake faɗa, ƙara riƙe hannun Saleh yayi gam sannan yayi masa murmushi.

Saleh yace "Amma karka kuskura ka gayawa kowa, kayi shiru da bakinka"

Anwar ne ya shigo bakinsa ɗauke da Sallama, yana ganin Saleh yayi murmushi yace "Saleh sannu da zuwa, naje Sallane"

Saleh yace  "bakomai Anwar, ya me jiki?"

Shiru Anwar yayi, ƙwalla na taruwa a idonsa yace 

"Saleh na rasa wane irin abokai Allah ya bawa bawan Allah nan, sam hankalinsu baya kansa, amma lokacin da yake da lafiya sune kan gaba gurin nuna masa ƙauna, Amma dubi yanzu, look at how he's suffering alone, ba wanda ya bani mamaki kamar mahaifiyata"

Anwar ya ƙarasa maganar, jijiyoyin kansa na tashi idonsa yayi ja, Alhaji Nasir ne yayiwa Anwar Alamar yaje da hannunsa.

Anwar  ya ƙarasa gaban gadon Alhaji Nasir ya zauna.

Alhaji Nasir ya kamo hannun Anwar, sannan ya miƙa hannunsa ɗaya yana shafa kan Anwar tareda yi masa murmushi a hankali yace  "Nagode, Nagode"

Kawai Anwar ya rungume Daula ya fashe da kuka, shima Daula hawayene suka fara bin gefen idonsa, da ba ƙaramin mamaki ya shiga ba, ganin yadda gaba ɗaya mutanensa da suke tare dashi suka watse suka barshi, ciki harda matarsa da take morarsa.

Yusuf yaje ya tarar da matasa da magidanta a gurin wankin nan, wasu na wanki wasu na wanka a ruwan, in an koro dabbobi suma suzo su sha ruwan, amma a haka yaga wasu na ɗiba na tafiya dashi abun ya bashi mamaki, dama a gurin salla megari ya gabatar dashi, dan haka wasu daga cikinsu sun sanshi.
Duk rashin son mutane irin na Yusuf ya ɗan sake dasu, suka dinga hira suma bashi labari akan yanayin garin nasu.
Abun ya dinga bawa Yusuf mamaki, suna rayuwa cike da son juna mutanen ƙauyen, sedai abun mamaki ɗan majaillisar dake wakiltar yankin kakannisa 'yan garinne, amma abun mamaki sukace lokacin da yake campaign har falafalan wuta aka samu su, ya gina musu borehole guda ɗaya can wajen gidan kakaninsa shima se anyi tafiya me nisan gaske borehole ɗin yake, yace idan suka zaɓe shi yaci ze janyo musu wutar lantarki, tundaga wannan campaign da yazo tsawon shekara uku basu sake ganinsa ba, ko gidan kakannin nasa baya zuwa ziyara gaba ɗaya ya koma Abuja.
Haka Yusuf suka cigaba da hira shikuma yana wankinsa, seda ya gama suka bushe ya ninko kayan tsaf, sannan suka taho sa wani maƙocin gidan megari zuwa gida.

Yana zuwa gida ya tarar da Widad a ƙofar ɗakinsu a zaune, zaman dirshen a ƙasa fuskarta tayi jawur saboda kuka, Yusuf ya razana ko ciwonta ne ya tashi.
Gwaggo na ganinsa tace "yawwa Yusufa, wallahi muna tsakar gida muna aiki muka jiyo ihunta, ta fito da gudu mukaje kanta, juyin duniya taƙi magana tayi zamanta a nan gurin, munce ta bar ranar ta shiga ko ɗakina ta zauna taƙi.

Yusuf ya ƙarasa inda take ya ajiye bokitin hannunsa me ɗauke da ninkakkun kayansu  yace "lafiya kuwa? Meyasameki haka?"

Cikin harshen turanci tace masa, "wasu ƙwarine suka yi ta cizona, sekuma naga spider manya guda biyu a ɗakin, dana fito nan ma ƙwarin suka cigaba da cizona"

Girgiza kai yayi yace "shikenan tunda na dawo tashi mu shiga ɗaki, kalli a yadda kike kin zauna a tsakar gida kowa yana kallonki a haka, kuma kinga kin tayarwa da mutanen gidan hankali"

"wallahi bazan shiga ba se an cire wannan spider ni bana sonshi, bana son ganinsa it's irritating me, looks at my body"

Se yanzu ya lura da yadda kafofin gashinta suka buɗe, jikinta yayi wani irin burɗin_ burɗin, fuskarta ma tayi ja saboda cizon sauro.

Hari tace "Allah dai yasa ba wani abun mukayi mata ba, dan naga alamar makirace, tun ɗazu muke fama taƙi magana, Amma tana ganin mijinta ta fara magana hadda karairaya"

Widad ta ɗaga kai ta ƙurawa Hari ido, yayin da gwaggo taji haushin abunda Harin tayi.

Yusuf kam ba ƙaramin dariya Hari ke bashi ba idan ta kunna Widad, yasan Widad tana mata kawaici ne kafin ta ɗan sake.

Yace "ba wani abun kukayi mata ba, wai wani abune ya cijeta amma, bakomai yanzu zan shiga in duba"

Yusuf ya shiga ya duba bega gizo2 ba, sedai cinnaku dake yawo a ɗakin, da alama su suka cijeta.
Yasa tsintsiya ya shashsharesu tsaf, sannan yace ta dawo ɗakin.

Yusuf "Yace meye ya cijekin?"

Guri ta zauna ta janye rigar jikinta, ta nuna masa cinyarta, fara tas fiye da fuskarta, sedai tayi ja saboda cizon cinnaka, banda wanda ya gasa mata a hannu.

Yusuf yace  "Sannu bari in tambayi gwaggo inda zaitun ta bani ki shafa"
Zumɓura baki tayi tace  "ni banyi wanka ba"

Haka ya karɓo ruwa tayi wanka, sannan ta dawo ɗakin, ya bata guri ta sa kaya, ya ɗakko zaitun ta zauna ya shafa mata a na hannun, ya fara shafa mata a ƙafarta ne a hankali, haka kurum taji jikinta wani iri, kawai seji yayi ta doke hannunsa tace
"meye haka?"

"Me kuma nayi miki?"

"ban sani ba" ta bashi amsa tare da miƙewa, ɗan sunkuyar da kai yayi yana murmushi.

Daga Asibitin gurin Alhaji Musa Saleh ya wuce, yaje ya sames hi a office ɗinsa.
Saleh yace  "Ranka ya daɗe kwana biyu bani da lafiya, ko ƙofar ɗaki bana iya fitowa, shiyasa kwana biyu bana zuwa"

Alhaji Haruna yace "Akwai damuwa fa, ko Kasan me Adda ya cemin yarinyar nan sun gudu"

A razane Saleh yace "wace irin maganar banzace wannan? Kamarya sun gudu?"

"Nima dai abunda na gani kenan, gaba ɗaya sun mayar mana da aiki baya, yanzu Bukar yace ko a raye ko'a mace anemosu a kashesu kar Asirinmu ya tonu, sannan kaje ka bincika mana wa'aka bawa aikin binciken nan a cikin jam'ian tsaro?"

Saleh yace "Amma fa wani hanzari ba gudu ba, ina kyautata zaton me Adda yana sane ya sake su, wataƙila tace zata bashi kuɗine koma ta ninka masa abunda kuka bashi, shine ya sake su, in bahaka ba ta yaya zasu iya tserewa? Kokuma a cikinku ne wani ya zagaya ya haɗa baki dashi, idan an karɓo abun a gaya masa shikaɗai ba"

Shiru Alhaji Haruna yayi yace "Biri yayi kama da mutum, kuma fa Saleh kayi magana, tabbas dan nasan zata iya, kuma babu Abunda me Adda baze iya akan kuɗi ba"

Jinjina mara adadi ga ɗumbin masoya littafin AƘIDATA, niba abunda zance muku se godiya Allah ya bar ƙauna, ga dogon page nan, nima inga dogon sharhi, ga link ɗin telegram nan a ƙasa

https://t.me/joinchat/SYIfEaoQo_JlNDM0

Share, share and share please 🙏 🙏 🙏
Domin gyara sharhi, ko shawara
Ayshercool
07063065680

                       _*AƘIDATA*_
       

PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

*Story and written by*

_*AISHA HUMAIRA _
(Daddy's girl)*_

The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *

I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum

Haƙƙin Mallaka ⚠ : Littafin nan mallaki nane, tun daga sunan labarin zuwa abunda ya ƙunsa, ban yadda wani ko wata ya sauyamin ko yin Amfani da wani ɓangare na labarin ba ba tare da izinina ba, Nagode

https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends

NOT EDITED

ELEGANT ONLINE WRITER'S

                         PART1
                                Page 34_35



Saleh ya cigaba da ziga Alhaji Haruna, akan lallai yayi bincike, dan zata iya yuwuwa abokan harƙallaesa ne wani yasa a karɓo masa abun hannun Widad, shiyasa me Adda yace masa sun gudu.

Alhaji Haruna yace "Nagode sosai Saleh, Insha Allah zanyi tunani akai"

Saleh yace "bakomai yallaɓai, bari in ɗanje gida in huta, kasan bana jin daɗin jikin nan nawa"

Alhaji Haruna yace  "shikenan Allah ya sawwake"

Saleh ya tashi ya tafi

Sakina ce fuskarta ɗauke sa damuwa ta shiga ofishin Suleiman, Suleiman yace "Sakina lafiya kuwa?"

Sakina tace "Yallaɓai akwai damuwa, yau sati biyu sa sace Yusuf amma har yanzu babu wani kyakkyawan rahoto, da yake nuna ana bincike akan lamarin nan, anya anyi adalci kuwa duba da yadda Yusuf yake bada gudunmuwa akan harkar tsaro, amma ace shi wannan iftila'in ya faɗa masa amma babu wani yunƙuri da'ake gurin ceto shi, idan ya rasa ransa fa? "  ta ƙarasa maganar kamar zata yi kuka.

Suleiman yace "look Sakina, kiyi wani tunani kodan Albarkacin 'yar babban attajirin da' aka sace su tare, yaci ace an maida hankali akan nemansu, amma har yanzu shiru, shikansa Daulan yana gadon Asibiti a kwance, na kai ƙorafi akan abari muma mu gudanar da namu binciken, amma daga sama aka bani umarnin cewar ba'a samu ba, ana gudanar da bincike akan al'amarin, babu wani abu da zamu iya banda muyi musu Addu'a "

Sakina tace " shikenan Yallaɓai, ubangiji Allah ya kuɓutar dasu lafiya, bari in koma kan aikina"

"Shikenan Sakina, Allah ya taimaka"

Sakina na tafiya, telephone ɗin gaban Suleiman ta fara ringing, ya sa hannu ya ɗaga, jin muryar wanda ya kira shin yasa shi miƙewa tsaye cikin girmamawa yana amsa wayar.

"A cikin ma'aikatanka wa'aka saka akan binciken masu bibiyar Alhaji Nasir Daula?"

Suleiman yace  "Yallaɓai Yusuf ne, wanda aka ƙarawa matsayi kwanan nan"

"A gaggauta kammala binciken nan, a miƙo bayanan binciken nan headquarter"

Suleiman yace "Ok Sir"

Yusuf ya kalli Widad da tayi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login