Showing 18001 words to 21000 words out of 135096 words
a falon, tai cikin part ɗinsu da gudu tana kuka, abun yayi yawa taji zafin cin mutuncin da akayiwa Yusuf ga tsabar wulaƙanci da suke fuskanta a gidan nan se kace Almajirai, kokuma wasu bayi.
Ramlah ta kalli mahaifiyar su tace
"Mummy am tired wallahi enough is enough are we slaves? see how this little baby is shouting at both of us including you, Mummy you have to do something"
Kafin Mummy tayi magana Amal ta shigo tana kuka.
Mummy tace "Amal meya saki kuka?"
"gaskiya ni Mummy zan tattara kaya na in bar gidan nan na gaji, wannan wane irin cin zarafi ne?"
Mummy tace "duk nasan da haka amma kuyi haƙuri ku ƙara wataran se labari da munsamu abunda muke so shikenan fa an wuce gurin"
Amal tace "dan Allah Mummy yaushe wataran ɗin nan zata zo, shekara nawa muna zama kaman bayi? Wallahi nagaji kalli cin mutuncin da tayi wa wannan bawan Allah dan kawai ya kaini unguwa"
A fusace Ramlah tace "dallah rufewa mutane baki, dan taci masa mutunci seme ina ruwan wani? Shi ta fara yiwa cin mutunci? Dama naga yadda kike wani zaƙewa a kansa tun wuri ki nutsu dan ni natsane shi wallahi sam ban yadda da shi ba"
Amal tace "Malama ba ruwan ki da abunda nake yi seki ta tsanar tasa ai, seki kashe shi tunda kin tsane shi"
Mummy tace "kunga dan Allah ya isa haka kar kuyi min faɗa, ni kaina ban yadda da wannan Yusuf ɗin ba, narasa yadda aka yi megidan nan ya wani ɗaukake shi haka, ina son sanin daga ina yake"
Haɗe rai Amal tayi ta zumɓura baki
Mummy tace "ku kuke tada hankalinku, Ramlah zancen da kika yi min ranan na tambayi babanta ya tabbatar min da cewa Aurar da ita zeyi"
Da yake Amal bata san zancen ba da sauri ta waigo tace "Aure kuma? A hakan za ai mata Aure? Waze kwashi wannan Jarabar"
Ramlah tace "Mummy dama na gaya miki, Amma wane me tsautsayin za'a liƙawa wannan Mahaukaciyar? Nasan dai bata da saurayi to waze ma kulata taci masa zarafi"
Mummy tace "ba wani bane Fahad ɗin Alhaji Bulama ne"
Asahar Ramla ta saki tace "Wane Fahad ɗin?"
Murmushi Amal tayi tace "Bulama nawa muke da shi? Fahad dai da kika sani, Fahad naki shine me tsautsayin"
Ramlah tace "Taɓɗijan wallahi da sake, baze yuwu ba akan me? Ita Hajiyar sa tana me za'a aura masa wannan tantiriyar ga hauka gashi maybe ta gama watsewa da turawa, shekararta nawa a turai, Allah kaɗai yasan me take acan baze yuwu ba"
Ta miƙe ta bar ɗakin tana masifa.
Yusuf be bar gidan ba ranar se bayan sallar isha'i.
Koda yaje gida ya tarar Umman sa ba taci Abincin dare ba shi take jira, seda sukaci Abinci suka yi hira sannan ya koma ɗakin sa.
Ya ɗakko laptop ɗin sa ya shigar da duk abunda ya faru da date da komai, dukkanin hirar da suka yi da Amla seda ya rubuta sannan ya kwanta.
Tun daga ranar Yusuf yake taka tsantsan gurin bin dokokin Widad, Sannan yana ta ƙara lura da yanayin mutanen gidan da ɗabi'ar kowa daga cikin su.
Widad ta aika Ramla ta kira mata Yusuf.
Ramlah tana zuwa inda suke zama ta kalle shi a wulaƙance tace
"kai wa kake kazo inji waccan yarinyar"
Yauma Yusuf ya shirya tsaf ze kai Widad Store za tayi siyayya bayan fitar su, Hajiya Halima ta aika aka kira mata Isa mai gadi, yaje ya same ta a ya durƙusa ya gaishe ta, ta amsa masa a wulaƙance sannan tace
"kaine ka kawo wa Widad direba ko?"
"Eh nine Ranki ya daɗe"
"Good, ina son sanin daga ina yake?"
Isa ya risina sosai sannan yace "Wallahi ranki ya daɗe ban san daga inda yake zuwa ba, nima wani abokina ne Sani ya kawomin shi yace ɗan uwan sane amma ban daga ina yake ba"
"ka buɗe kunnen ka da kyau ka saurareni"
Isa yace "to Hajiya"
"Ina so duk yadda za'ayi in san daga ina yake? Daga ina yake zuwa gidan nan, sannan ina so ka ƙara samun ido akan sa sosai ina tunanin akwai wani ɓoyayyen abu a tare da shi"
"An gama ranki ya daɗe insha Allah zanyi yadda kike so"
"sannan wannan maganar ina so ta tsaya daga ni se kaine, bana son wani ya san munyi ta"
"babu me ji ranki ya daɗe"
"tashi ka tafi" Isa ya tashi fita.
Yusuf kam wani katafaren shago ya kai Widad, ta siyi kayan da take buƙata, hatta ruwan roba da zata sha seda ta siya abun ta.
Banda kayan ciye2 da sauran kayan ƙyale2
Seda sukaje gurin biyan kuɗi ta kalli Yusuf tace "jeka mota ka ɗakko jaka ta"
Ba musu yaje ya ɗakko 'yar ƙaramar jakar ta ya kawo mata"
"buɗe ka ɗakko ATM card ɗina"
Ya ɗakko ya riƙe aka lissafa kuɗi, kuɗi ne masu yawan gaske, ko a jikin ta tace
"basu ATM ɗin" ya miƙa musu suka saka a POS suka miƙo masa yasa ka password ya sa hannu ya karɓa ya miƙo mata domin ta saka lambobin da zasu bada damar cirar kuɗin, a hankali tai ƙasa da muryar ta tace
"7724" Yusuf ya gane me take nufi haka ya danna lambobin ya miƙa musu.
Suka ciri kuɗin su yana mamakin me yasa ta gaya masa password ɗin cirar kuɗin ta.
Sun fito harabar Store ɗin zasu tafi suka wuce ta gefen wani mutum dake ƙoƙarin rufe motar sa yabi Widad da kallo tare da faɗin subhanallah.
Da sauri yabi bayan su Widad, Yusuf yayi gaba yana zuba kaya a mota mutumin ya sha gaban Widad yace
"Ahh excuse me Madam you look so hot"
Zare glashin fuskarta tayi tai masa kallon sama da ƙasa ta mayar da glass ɗin ta, tai gaba abunta.
Sake binta mutumin yayi ya sha gaban ta zeyi magana Widad tace "wai me kake nema ne?"
Yusuf kam ganin ta tsaya ya sashi komawa inda take tsayen dan ganin meke faruwa.
Mutumin yace "Wow ashe bahaushiya ce? Gaskiya beb bazan ɓoye miki ba kin tafi da imanina, kin min ina sonki, ki bani contact ɗinki mana se muyi magana, you look sexy" yai maganar yana wani kashe ido irin na 'yan bariki tare da miƙowa Widad wayar sa
Karɓar rantsatsiyar wayar tayi kaman gaske, ta sake ta a ƙasa ta fashe sannan tace "waya gaya maka samun lamabr mace kamar ni a gurin ƙasƙantattun mutane marasa amfani irinka abu ne me sauƙi, dalla matsa a gabana ko in tsinka maka mari sakarai kawai"
Waro ido mutumin yayi "ni zaki tsinkawa mari? Kin san waye ni kuwa? In baki wayata ki fasa min"
"Waye kai banda banza wofi, matsiyaci mara amfani? Kauce a gaban kafin inyi maganin ka"
Kan Widad mutumin yayo yana kumfar baki "Wallahi sena nuna miki koni waye a garin nan, 'yar uban waye ke da zaki min haka? Sena ci zarafin ki na wulaƙanta ki"
Tuni Attention ɗin mutane ya fara yowa kansu kaman ze daki Widad, Yusuf ya shiga tsakanin Widad da mutumin ya kalli mutumin yace
"kana ta mana kumfar bakin ba' a san waye kai ba, ita kasan wacece? Ina ruwan ka da ita da zaka biyo ta kafaɗi maganar banza akan ta, ka kiyaye harshen ka kafin a nuna maka ƙarfin ikon data ke dashi"
"Kaikuma waye kai waye ya sakoka a cikin wannan maganar?" mutumin yasa hannu a aljihu ya miƙowa Yusuf id card ɗinsa, kafin Yusuf ya karɓa Widad tasa hannu ta karɓe ta duba id card ɗin nasa sannan tace
"Ashema matsiyaci ne taƙamarka kaki ko? Zan iya sawa a keta kakin naka a gaban mutane a wulaƙanta ka, a tozarta min kai, sannan in ɗaure ka, kuɗi sunfi wannan kakin banzar da kake tin ƙaho dashi, Widad Nasir Daula inada Arzikin da zan wulaƙanta ka ka ƙare a gidan yari sakarai kawai "
tayi jifa da ID card ɗin nasa ta tofa miyau akai
Ai Sunan ta data faɗa yasa mutumin nan wani mummunan zare ido tare da sauke numfashi yana kuma maimaita sunan nata.
Widad ta wuce mota Yusuf ya bita suka tafi, suna tafe tana ƙwafa tareda yin tsaki jefi2 kallon ta kawai Yusuf yake.
Suka isa gida ta buɗe murfin motar ta fice abunta, Yusuf ya ɗebo kayan ya bita dasu, matar gidan tana falo tana kallo, Yusuf ya shigo yabi bayan Widad har ɗakinta ya ajiye mata kayan, ze juya ya ɗebo sauran tace "ɗan tsaya" Yusuf yaja ya tsaya tazo ta duba kayan, ta ɗakko wata Jaka da turaruka a ciki ta ajewa Yusuf, cike da iko da kashedi tace
"daga yau karka ƙara saka wannan banzan turaren da kake sawa in zaka zo inda nake, ga wannan turarukan kar in kuma jin kasa wannan turaren dan yana samin tashin zuciya ina fatan ka gane?" jinjina mata kai yayi alamar Eh.
Ya ɗau ledar turaruka ya fita ya kwaso mata sauran kayan ya kawo mata, yana zuwa ya tarar ta shiga wanka, dan haka ya haɗa da ledar turarukan da ta bashi, ya ajiye mata akan gadonta yai ficewarsa.
Bayan Yusuf yayi sallar Azahar ya nemi guri ya zauna a inda suka saba zama da sauran ma'aikatan gidan, Isa mai gadi yace
"Yusuf manyan ƙasa, gaskiya ka ciri tuta a gidan nan, ina jinjina maka"
Yusuf yace "Mena yi na cancanci jinjina haka"?
"Ahh irin yadda kake jure cin mutuncin wannan yarinyar mana, naga da alama kaman kai bata yi maka wulaƙsncin, amma dukda haka kana haƙuri wallahi yarinya se kace sheɗaniya, zuciyar ta babu Imani se miyagun Aƙidun turawa to aibtama ci uwar turawa wannan"
Yusuf yace "kaga dakata Isa, kana gidan mahaifinta kana cin Arzikin su sannan kuma ka dinga zagin ta? Aiba'a haka a rayuwa, ni duk wannan abubuwan da kuke faɗa akan ta ni bana gani, danni ba ta yi min ba"
Isa yace "ni na rasa me yasa kullum kake ƙoƙarin kare ta, da anyi magana ka hau kare ta, ina tausayawa ranar da zata maka mugun halin nata, naga yadda zaka yi ai"
"kaga Isa abar wannan maganar dan Allah"
Isa yace "shikenan tunda haka kace, nikam nace ina Sani kuwa? kwana biyu baya zuwa gidan nan ko a waya bana samun sa, nasan kai kuna haɗuwa tunda unguwar ku ɗaya"
Yusuf yace "waye ya gaya maka unguwar mu ɗaya?"
"Ai gani nayi ɗan uwanka ne shiya kawo ka gidan nan, dan haka nayi zaton unguwar ku ɗaya"
Yusuf ya murmusa yace "A'a ba unguwar mu ɗaya ba"
"to kai a wace unguwa kake? Ko ince inane ƙauyen ku? Dukda baka yi kama da 'yan karkara ba, ni mamaki ma nake yadda matashi kamar kai yake aikin direba"
Yusuf yayi murmushi yace "Isa kenan, dama su' yan ƙauyen wata kamace dadu ta daban ne? meyasa ka damu da sanin unguwar da nake?, indai Sani ne zan nemo maka shi dukda ba unguwar mu ɗaya ba, zan kawo maka shi har nan yazo"
Yusuf ya basar da zancen yaƙi gayawa Isa unguwar da yake.
Duk wasu hikimomi Isa yabi, Amma Yusuf ya nuna masa ƙwarewa irin ta jami'in sirri ya basar da zancen ya shiga wani.
Daga ƙarshe ma ya miƙe ya bar gurin, Isa yace "wannan anyi Jarababbe me taurin kan masifa, ƙiri Ƙiri yaƙi gayamin, amma zaka ga tsiya, in kasan wata baka san wata ba, zan biyo maka ta inda koka ƙi Allah seka faɗa"
Share please 🙏🙏🙏
Masoya masu Comment ina godiya, Allah ya bar ƙauna 😍 😍 😍 ku sani yanzu aka fara wasan, amma gaskiya idan ba'a Comment yadda nake so zan ɗau matakin da ya dace, dan Allah idan kin karanta idan kin san Tanks kawai zakice koki turamin sticker ki riƙe abun ki please 🙏🙏🙏
Domin sharhi, gyara ko shawara ƙofata a buɗe take, feel free to contact me, sedai in ban buɗe saƙon da wuri ba ayimin afuwa, ina godiya 😍
Ayshercool
07063065680
_*AƘIDATA*_
PERFECT WRITERS ASSOCIATION
(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)
https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
P. W. A
*Story and written by*
_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_
The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *
I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum
Haƙƙin Mallaka ⚠ : Littafin nan mallaki nane, tun daga sunan labarin zuwa abunda ya ƙunsa, ban yadda wani ko wata ya sauyamin ko yin Amfani da wani ɓangare na labarin ba ba tare da izinina ba, Nagode
https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends
ELEGANT ONLINE WRITER'S
PART1
Page 6
Widad kam koda ta fito daga banɗaki, da jakar turarukan nan data bawa Yusuf ta fara yin arba akan gadon ta, ta ƙarasa a hankali ta duba, sune dai turarukan da ta bashi,
"lallai wannan ɗan rainin hankali ne, ni zan bashi abu yazo ya ajiye min?"
Fita tayi falo ba kowa dan haka ta wuce part ɗinsu Amal, tana zuwa ta tarar da su a kitchen suna ta girki suna hirarsu, Wai Ramlah zata yi baƙi, se hada hada suke da kaji da sauran kayan masarufi.
Basu san da zuwan Widad ba se muryarta da suka ji cikin isa tace
"Ramlah kije gate ki kiramin driver na yanzu"
Cike da ɓacin rai, ba tare da Ramlah ta kalleta ba tace "to"
Haka Ramlah ta fita tana ƙunƙuni ta nufi bakin gate.
Tana zuwa ta tarar Yusuf ya siyo Abinci ze fara ci, Ramlah tazo kansa ta tsaya ta ƙare masa kallon up and down a wulaƙance, ta kalli gurasar gaban sa ta masu balango da nama ta kuma kallon sa ta taɓe baki ta ɗanyi tsaji taxe
"kai kazo inji waccan yarinyar"
Banza Yusuf yayi mata ya cigaba da ƙoƙarin cin Abincin sa.
"Wai baka ji ne?" ta masa magana cikin tsawa.
Nura direban Alhaji yace "Yusuf da kaifa take magana"
Yusuf ya ɗago ya kalli Nura yace "yawwa Sunana ka ambata, meze hana ta kirani da Sunana dan me zata cemin kai, kuma ni ban san wata yarinya a gidan nan ba"
Mamakine ya kama Ramlah, dama yana magana haka da wulaƙanci amma yake iya tsayawa Widad taci zarafin sa? Ba mamaki saboda kwaɗayin abun duniya kar a kore shi shiyasa yake shnaye wulaƙancin Widad, amma har ita wannan talakan ze buɗe baki ya gayawa magana a fusace tace
"kai saurara bazan kira sunan naka ba, uban waye kai da zaka dinga tambayar ban san sunan ka bane? Kai a wa? Ka kiyaye ni wallahi bana son shirme idan kace zakamin rashin mutunci zaka ga abunda ze biyo baya, sannan idan kaga dama kaje, in baka ga dama ba karka je ka san sauran"
Yusuf yayi kaman ba da shi take ba ya ci gaba da antaya gurasar sa. Ran Ramlah ne yai mugun ɓaci da ganin wannan rainin hankalin na Yusuf, ƙwafa tayi ta koma cikin gida.
Nura yace "Yusuf dan me zakayiwa Ramlah haka? So kake kaja wa kanka a kore ka?"
Yusuf yace "Nura kenan, to a korenin mana seme?" ya ci gaba da cin gurasar sa seda ya gama cin Abincin sa, Sannan ya miƙe ba tare da ya kuma cewa komai ba ya nufi cikin gidan.
Yana zuwa ya tarar da hakimar ta ɗora kafarta akan centre table tana jiran isowar sa.
Yusuf ya ƙaraso cikin girmamawa yace "gani ranki ya daɗe"
Widad tace "se yanzu ka ga damar zuwa? Na tura a kira ka kace bazaka zo ba seka gama abunda kake?"
Da confidence ɗin sa yace "bance ba zanzo ba ina cin Abinci ne lokacin"
"ba tun ɗazu aka kaiwa ma'aikatan gidan nan Abinci ba?"
"Aini ban sani ba munfita tare da ke, kuma ni ba'a taɓa Abinci ba"
Tsuke Fuska Sosai Widad tayi tace "Ramlah kiramin larai" Ramlah ta juya ta tafi kiran larai, Widad ta kalli Yusuf a wulaƙance tace
"me kake nufi da in baka abu ka ajiyemin kayi tafiyar ka? Me kake nufi da hakan? Harni zan baka abu saboda wulaƙanci da girman kai irin na talaka harni zaka gwadamin halin naku na talakawa na girman kan banza akan abunda baku dashi"
Yusuf ya ɗanyi murmushi yace "ba girman kai bane Madam, bakomai ne yasa na ajiye ba face abunda kika bani yafi ƙarfin talaka kaman ni in saka, duk wanda yaji ƙamshin wannan rantsatsun turarukan to tabbas zan zama abun tuhuma ga al'umma, kiyi hakuri wannan turaren seke"
Wani irin murmushi Widad tayi wanda ita kaɗai tasan ma'anar sa, sannan ta tsuke fuska tace
"Amma fa ka iya rainin wayo sosai, shikenan amma idan na kuma jin tashin wannan banzan turaren a jikin ka kasan sauran"
"Insha Allah bazan sake saka turaren da shugaba ba taso ba"
Ramlah ce ta dawo tareda 'yar aiki larai na biye da ita, jikin larai se tsuma yake tazo gaban Widad ta durƙusa.
"Larai Me yasa ake hana direba na Abinci?"
Larai ta kalli Ramlah a ɗan dirirce sannan ta dawo da kallon ta kan Widad za tayi magana, Widad tace "Idan kikamin ƙarya sena hukunta ki"
"Wallahi ranki ya daɗe Hajiya ce tace kar a sake a bashi Abinci, ba a cikin ma'aikatan gidan nan yake ba"
Widad tace "hmmm tunda ita ta siyo ta kawo ko? Ke Ramlah kije ki gayawa mahaifiyarku, ko kare na ajiye a gidan nan ya zama dole a bashi duk abunda yake buƙata tunda lokacin da'ake tara dukiyar gidan nan bada gumin ta aka tara ba, sannan....
Yusuf katseta ta hanyar cewa "Amma uwa ɗakina ina ganin idan kika yi haka baki kyau ta ba, ki bari...
"Shut up....., do you think am doing it because of you?, let me tell you something, ba nace a baka Abinci a gidan nan dan komai ba sedan kauce wa hatsarin dake tattare da hakan, karka manta YOU SIGN ON YOUR DEATH CONTRACT ya rage naka kula da rayuwar ka"
Ta miƙe ta nufi part ɗinta cikin takunta na isa.
Jiki a sanyaye Yusuf ya fice yana mamakin waime take nufi da wannan death contract ɗin ne?
**********************
Manyan Mutane maza su uku, zaune a