Showing 108001 words to 111000 words out of 382522 words
babu makarinta, itakuma tana sakar da jijiyoyin jikine su daina aiki gaba d'aya, wannan yasaka jikin Sarki Saifudden ya sandare😭.
Wani amintaccen likitanmune yabada shawarar mu maidashi India dansu sunada kwararrun likitoci, kuma zaifi samun kulawa da tsaro a can.
Wannan shine silar dawowarmu wannan k'asa, da cuku-cukun mahaifina Sarki Abdul'fatah, dan komai namu mukam ya k'are, duk abinda Sarki Saifudden kedashi yagama k'arewa a neman Magani.
Tunda muka dawo India kuwa Sarki Saifudden yafara samun kulawa ta musamman, saidaifa maganar ta kud'ine. Wasu sarakuna da yawa sun bamu gudunmawa, wasuma suna akan bamu.
Sanin Zara bata barin dami, gashi kullum cikin buk'atar kud'i muke sai mahaifina yakafa wasu sana'oi da sauran kud'enmu, tanan muke samun kud'in shiga. Karatun Muh'd da Haneefa kuma Mahaifiana ke d'aukar nauyi..
Tundaga primary har jami'a anan Sameer yayi karatunsa.
Kiyayyar Saifudden kuma ga mama Fulani saita dawo jlkan Muh'd gaba d'aya, kokad'an bata k'aunar ganinsa, kullum tsakaninta dashi sai aibantawa da jifansa da kalamai masu had'ari ga yaro.
Tunda Muh'd yafara sanin Kansa, yaga halin da mahaifinsa yake saiya fara canjawa daga mai hakuri zuwa mai zafi.
Ga ciwonsa kuma, duk yabi yayta kuntata zuciyarsa akan ciwon mahaifinsa da burin d'aukar fansa.
Muh'd mai fara'a da barkwanci yakoma mutum marason magana da azabar rashin d'aukar raini, duk da hakurinsa nanan bai dainaba, dan zakata masa Abu ya shareka kamar bai ganiba, sai randa yazo k'arshene zaka gane kurenka a wajensa.
Mahaifina Sarki Abdul'fatah shine yamatsa tun Muh'd na secondary school dole idan akayi Hutu yazo najeria, dan acewarsa tahakane kawai zai fahimci sarautar gidansu.
Muh'd ya karanci Engineering ne, dama tun yana yaro kingansa kullum cikin son had'a Abu yake, shine tsinka wayar fitila tsinka ta redio ya had'a wani abun, tunma ina masa fad'a harna bari kawai. Ashe abincinsa awajen yake. Yanzu haka sunada Company na had'a wayoyi📱 da Computers💻🖥, da sauran kayayyaki dai. Sannan yana wasu business domin dai muke samun kud'ad'en kulawa da mahaifisa da sauran matsalolinmu, dan babu mai kulawa damu a masarautar gagara badau sai Sarki Jalaludden.
Wani zuwa da Muh'd yayi Nigeria shine aka bashi sarautar *Galadima*, galadima Sarautace mai k'arfin gaske, dan sai d'a mafi soyuwa ga Sarki ko k'ani ake bamawa. Kuma akance batada banbanci da sarautar waziri, dan duk abinda waziri zaiyi Galadima ma zai iyayinsa. Akwai ma wasu abubuwan da daga Sarki sai Galadima kan yisu a fada.
Da da farko nace ya mayar musu amma sai mahaifina yace a'a, ai hakan da sukayi dai-daine.
Sharrin kuwa dakika sun masa, har tsautsayi ya jefaki a ciki, sunyine dan hankalinsa ya tashi, har takai zuciyarsa ta buga ya mutu sun huta.
Dan ayanzu ne suke ganin sunfa *kashe macijine basu sare kansaba* Galadima yazamar musu *RAINA KAMA.....*, basuyi tunanin zaikai tsawon rai hakaba, saboda Ciwo mai had'ari dake a tare dashi.
Shikuma Muh'd yafi karkata hankalinsa ga jama'ar wajene sukama mahaifisa haka, koda akwai jama'ar masarautar gagara badau to kalilanne, kuma mama Fulani kawai yake zargi.
Nikuma ba ita kad'ai nake zargiba, amma yakasa fahimtata gaba d'aya har kawo yanzun kuwa. Dagashi har Haneefa sunfi zargin jama'ar waje, don mutananen masarautar suna 6oye musu ainahin fuskarsu ta zalunci, mama Fulani ce kawai tata take a bayyane.
Wannan yasaka tun sharrin da akai muku nasaka amin bincike a kanki, Alhmdllh ban samu wata matsalaba a tarihinki,, daga nan na dukufa addu'a da neman za6in ALLAH.
bamma kai ga furtama kowa matsalata ba sai mahaifina Sarki Abdul'fatah (papi) yace Muh'd saiya aureki.
Nasan ba sonsa kikeba, amma ina rok'on ubangiji da yasa wataran kuso junanku, kinada tarbiyya da wayon da zaki iya canjamin Muh'd, dan banason hallayarsa ta yanzu, nafi son nake ganin walwala atare dashi a ko yaushe, ki taimakeni ki shiga rayuwarsa sosai, dan ke macece, sai kin fishi zama cikin jama'ar masarautarsu, zakuma ki fishi fahimtar halayyarsu, sannan kidinga bashi shawara akan abinda yadace dashi. Inaji a jikina zaki iya canjamin Muh'd, saboda kinada hankali. gudun kar wani yasakama zuciyarki tunani daban yasaka nace yakawoki da wuri, domin kisan yanda zaki rayu a masarautar, kafin kutafi insha ALLAH komai Na zamantakewar masarauta za'a koyar dake kinji”.
Kaina Na gyad'a mata, sannan a sanyaye nace “Momma namiki alk'awarin zai taimakesa akan matsalarnan, kuma zan bama rayuwarsa gudun mawa insha ALLAH, Sai dai Abu d'aya ne ban ganeba”.
“miye baki ganeba d'iyata?”.
“Abokinsa Muftahu, shima a masarautar yake?”.
Murmushi Momma tayi, tace “daga Muftahu har Harun duk 'yan masarautar ne, Muftahu kakanni suka had'a dasu Muhammad, da kakan Muftahu da Sarki Abubakar kakansu Muh'd uwarsu d'aya ubansu d'aya, shikuma Harun d'an waziri ne na yanzu, kuma shima wazirin haifaffen gidanne, saidai inason sanin ko wani Abu kika gani tareda wani acikinsu?”.
Kaina Na girgiza alamar A'a.
Momma ta sauke ajiyar zuciya, “Munaya saikin dage kinji, domin Na had'aki da aiki mai wahalar gaske, mai kuma sark'akiya, musanman akan halayyar Muh'd, dan bai yarda da kowaba dakike ganinsa nan, koyaya Abu ya had'aku sai yayi zargin turoka akayi garesa, kuma zaka Shiga jerin wad'an da yake tuhuma. amma kekad'aice mafi kusanci da Muh'd yanzu, zakifi kowa sanin matsalarsa da wuri, saikuma kin fimu fuskantar tunaninsa, danni kinga jinyar mahaifinsa tasa banwani zauna dasu irin sosai d'innanba, yanzu haka kafin nasan matsalarsa 'Yar uwata Zaitun (mom) tasani ko Haneefa (aunty Mimi), garama Sauban.
Nace “shikenan Momma ki tayamu da addu'a kawai”.
“insha ALLAH muna kan yimuku kullum, ALLAH yayimuku albarka, ya albarkaci aurenku da dukkan rayuwarku da abinda zaku haifa”.
Ban iya amsawa ba, kaina Na k'asa nikam, ko azuciya ma ban amsaba, dan nayi alk'awarin zai taimakesa kamar yanda ta buk'ata. Amma ina gamawa zan nemi sakina, koda nanda shekaru 2 ne kuwa, amma gaskiya Na tausayama Galadima, dan nakula yana cikin tsakkiyar mak'iyane masu fuska biyu. abinda kuma nalura da Momma bata ganeba shine Galadima bawai bai yarda 'yan gidansu nada saka hannu akan ciwon babansa bane, baya dai nunawane kawai, sai dai bansan dalilinsaba.
CCTV camera d'in dana gani a d'akinsace tadawomin a rai, maybe ya sakatane domin sanin masu shiga da fita koda bayanan.
Haka Na kusan yini cikin damuwa da tausayinsa, dan duk saiya bani tausayi wlhy. shiyyasa zaka gansa kullum shiru-shiru, gaskiya 6angaren hak'uri Na yarda yanada hak'uri kam.
***********
Yau saida yamma mukaje muka duba Abie, mun iske Galadima baya asibitin, dama tun da rana yazo gida yay wanka yakuma fita.
Har dare muna a asibitin, saida Galadima yazo muka taho tare, ina gaba ni da shi da khaleel dake barci a cinyata, yayinda sauban da aunty Mimi da Samha ke baya.
Maganar da samha ta fad'amin d'azun a asibiti ta dawomin a rai, Ashe mahaifinsu ya rasu suma shekara 2 kenan, itace d'iyar Aunty Mimi ta farko, sai Hakim da suka rasu tareda babansu, saikuma khaleel auta. Suma a Nigeria da suke zaune, bayan rasuwar mahaifin nasune suka dawo nan india, duk da dangin mahaifinsu sunso kar6arsu papi yahana, babansu tsohon Governor ne shima, mutuwar tasa kuma akwai lauje cikin nad'i shima, dan ya tsananta akan binciken ciwon surukinsa Abie sosai, shiyyasama ake zargin an kasheshine saboda wani Abu daya gani.
Har muka Isa gida bansan hirar dasukeba a baya, dan shima Galadima baya cewa uffan.
Shine ya kar6i khaleel a hannuna, ya sa6ashi a kafad'a muka shiga ciki, har d'akinsa ya kaisa. ni lokacinma harna haye saman..........✍🏼
Barkanku da juma'a.
Zanyi last page gobe idan ALLAH ya kaimu da rai da lafiya⛹🏻♀⛹🏻♀.
Network yanata min iskanci tun jiya shiyyasa kuka jini shiru☹
*_YA ALLAH ka gafartama iyayenmu_*😭🙏🏻
*_Typing📲_*
*_HASKE WRITERS ASSO...💡_*
_(Home of expert and perfect writer's)_
*_♦RAINA KAMA......!!♦_*
_{Kaga gayya}_
*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*
👉🏻3⃣0⃣
..................Da sallama ciki-ciki ya shigo, nayi saurin maida zip d'in rigata sama nafasa cirewa, a sace ya kalleni yawuce bakin gadon ya zaune tareda dafe kansa.
Kallonsa nayi Na kauda idona nima, kusan mintuna 3 kowa da abinda yake tattaunawa da zuciyarsa. d'agowa yayi yakuma kallona, kamar an masa dole yake maganar cikeda k'asaita, “k! Wai bazakima Momma magana ba kikoma d'akinki?”.
Kamar bazanyi maganaba saikuma nayi batare da Na kallesaba, “inaga kaine yakamata kamata maganar ai, dan nima zanfi son haka, duk nabi Na takura zama da Namiji d'aki d'aya”.
Banza yamin bai sake tankawa ba, saima yamik'e yana jan k'aramin tsaki, nikam Na ta6e baki a zuciyata ina fad'in ka iya fad'ar R kafin kamin mazurai.
Baima san ina yiba, yaje wajen wardrobe d'insa ya d'auki kayan barci yanufi bathroom.
Murmushi kawai nayi, danni rayuwar mutuminnan mamaki take bani, ina dad'i kabi ka k'untata kanka irin haka? baka hira da kowa, baka dariya, shifa ko kallo inba labaraiba ban ta6a ganin yanayiba, hakama wak'a banta6a jin yana jiba, koranar dana duba wayarsa karatun Qur'an kawai nagani da Tafseer. nakai dubana gawata 'Yar kanta dakecan gefe a bedroom d'in nasa, mafi yawanci littatafan addini ne awajen, sai English Novels. (To yayi karatun addinine? tunda naji Momma tace anan India ya girma🤔). Wata zuciya tacemin su India basuda musulmai ne?. “hakane kumafa” nafad'a a fili ina mik'ewa.
Ganinaima bara nacire kayana kafin yafito, daya fito saina shiga nima.
Har ga ALLAH banyi tunanin fitowarsa ba yanzun, dan haka hankalina kwance na zuge zip d'in rigar, na cireta gaba d'aya, shima sket d'in nayi k'asa dashi yafad'i k'asa.
Juyowarnan da zanyi da nufin d'aukar towel dana ajiye saman akwatina sai kawai naga mutum tsaye a k'ofar bathroom, hannunsa rik'eda k'aramin towel yayi tsaye yana kallona.
Bansan Na kwalla k'araba wlhy, Na rarumi towel d'in nayi saurin kare jikina, ALLAH ma yaso k'ofar a rufe take, dan dawuya su Aunty Mimi sujini.
K'arata tadawo dashi daga sumar tsayen dayayi, yawani kauda kansa cikeda basarwa yana ta6e baki, saikuma yaja guntun tsaki yaje bakin gadon ya zauna yana cigaba da goge fuskarsa, dan har yayi shirin barcinsa a ciki.
Jinayi tamkar na makesa, d'an rainin hankali yagama kalleni zai wani miskile fuska asfa baiga abin kalloba. hijjabin sallata na janyo Na saka, sannan nawuce bayi ina hararsa.
Ina shiga yamik'e yana wani munafukin murmushi, abin salla ya shinfid'a ya kabbara shafa'i da wutiri.
Nadad'e abayin nak'i fitowa, saida nabar jin motsinsa duka sannan Na fito, dayake nayi shirina a bayin nima, nazata ya kwanta, amma saina iskeshi zaune a kujerar dake gefen kantar littatafan nan ya bud'e laptop yana danne-danne, gefensa kofine yanata turiri, da alama coffee ne aciki.
Yad'an juyamin baya kad'an, dan haka cikin sand'a Na rufe k'ofar, nakuma tako a hankali har zuwa wajen sofa Na kwanta, duk zatona baya ganina, Ashe yana kallon duk abinda nakeyi ta gefen idonsa.
A ransa yace munafunci. cigaba yay da aikinsa hankaki kwance, bai bar wajenba har kusan 1:30pm, maimakon ya kwanta sainaga yashiga bayi ya d'auro alwala.
Nima har time d'in barci yakasa d'aukata, maganar Momma tanata min yawo a zuciyata, tunanin ta inda zan taimaki Galadima kawai nakeyi.
Ina kallonsa ya kabbara salla. saida yay kusan raka'a 6 yanayi yana sallamewa, daganan ya d'auki alku'ani yafara karatu k'asa-k'asa.
Masha ALLAH nafad'a a raina, danjin yanda muryarsa ke fita cikin karatun littafi mai tsarki, gashi yana fidda kowane harafi cikin tsantseni da kwarewa. Tun ina saurarensa har wani barci mai dad'i ya saceni, bansan lokacin daya kammala ba yazo ya kwanta.
Muduka makara mukayi sallar asuba yau, dan haka shima yau a gida yayi.
Bayan ya idar waya ya d'auka naga yayi kira.
Bayan an d'aga daga can sukayi gaisuwa, jin ya tambayi ya Nigeria Na gane da 'yan can yake wayar. yacigaba da fad'in.
“Nuren naga ka turomin hotonsa, shin a inane yake haka?”.
Bansan mi akace masaba daga can, naga dai yayi kwafa, sai yace “ya maganar Minister? dan nagansa wajen d'urin aurena, ban kuma yi zaton zai zoba”.
Canma aka kuma yin wata maganar.
Zamansa yagyara, yakuma jingina da bangon, dayake yana kan abin salla har yanzun. “kayi k'ok'ari Nuren, yanzu abinda nakeso dakai shine, akwai yarinyarsa d'inan datake karatu a nan jami'ar Abuja, inason a sacemin ita k'arshen watannan, yanzu ka saka ana bibiyarmin komai nata, Shikuma Alhaji Balala driver n sa zaku d'aukemin, dan bincikena ya ganomin shekarunsa 30 dawani Abu yana masa aiki, kuma randa su Alhaji balala sukayi zama da Abie shine ya kaisa masarautar mu, inada tabbacin zai San wani Abu koda kad'anne, kuyi aikinku da kulawa Nuren, banason asami matsala kamar wancan time d'in, gobe kashiga birnin gayu plaza kuyi zama Na musamman da Saleem akan maganar CCTV camera data daina aiki randa abinnan ya faru, ni naso Na zauna dashi, amma kaga Momma tamatsa akan dawowata”.
bayan nacan yagama magana.
Yace “ok babu damuwa, zan turo maka number yarinyar, saiku bibiyeta tanan. sai anjima, ka gaidamin Mom d'ina”.
Koda ya ajiye wayar saiya koma gado ya kwanta abinsa, nikam ina zaune sai cud'awa da kwancewa nakeyi, ban fahimci wayar tasaba gaba d'aya, shin wanene kuma NUREN!? shikuma miye alak'arsa da Galadima kuma?.
Tabbas aikina bazai yuwuba saina San wanene NUREN, wane kuma aiki yakema Galadima a sirrence, su waye wad'annan mutanen biyu daya ambata Minister da Alhaji balala? suna cikin wancan case d'in Na Abie ne? kokuwa tasu dabance?.
Kwanciya ta na juya yanda zanji dad'in tunanin da k'yau, saikuma naga ai ba sanin waye Nuren bane matsalata yanzu, kamata yayi nafara sanin shi kansa Galadima d'in da rayuwarsa, na tuna maganar Momma da tece “shi mutumne dabashi da yadda”. Mutum mara yarda kuwa yanada wuyar sha'ani, kad'an na juyo na kallesa, idonsa a rufe yake, amma ban yarda barci yakeba, na janye idona nima na maida lumshe, barcine mai nauyi ya kwasheni, harya fita bamma saniba inata barci, babu kuma Wanda yazo ya tadani.
Sai around 11:30 na tashi, wani masifar ciwo kaina yakemin, haka dai na tak'ark'ara nayi wanka, nagyara d'akin sannan na sako k'asa, gidan shiru tamkar babu kowa, sai television daketa aiki, zama nayi bisa kujera dafe da kaina.
“ranki ya dad'e lafiya dai?”.
Bud'e idona nayi a hankali, sai naga jakadiya ce, namata murmushi tareda yunk'urin tashi zaune, “wlhy kaina ke ciwo jakadiya, halanma ke kad'aice ma a gidan?”.
“subahanalla, sannu ranki ya dad'e, bara na samo miki abinci saikisha magani, eh ni kad'aice ranki ya dad'e su Sauban sun tafi makaranta. Gimbiya Mimi kuma tana asibiti itama, taga kina barcine shiyyasa tahana a tadaki”.
Nace “ALLAH sarki”.
Wucewa tayi zuwa kitchen, babu dad'ewa saigata tadawo da tire, a gabana ta ajiye tana fad'in “gashi ranki ya dad'e, kici saikisha magani kafin Magajin gari yadawo saikuje asibiti”.
Kallonta nayi da mamaki, “jakadiya waye magajin gari kuma?”.
Tayi 'Yar dariya, “ranki ya dad'e ina nufin mai gidanki, ai magajin gari nake cemasa”.
Murmushi nayi ina girgiza kai kawai, na had'a tea nasha, sannan nasha maganin, anan falon na kuma kwantawa, barci yakuma kwasheni.
Jakadiya na zaune tana gadina.
Da sallama ya shigo, jakadiya ta amsa tareda mik'ewa da sauri ta kar6i kayan hannunsa tana masa sannu da zuwa, yad'an saki fuska yana amsawa. d'aya acikin kujerun ya zauna, sai lokacin idonsa ya sauka kaina.....
maganar da jakadiya take masa ce yasakashi janye ido daga kaina ya maida kanta.
“ranka ya dad'e akai kayan samane?”.
“no jakadiya kibari zan hau dasu, ai sunmiki nauyi, ita wannan mike damunta tayi barci anan?”. ‘yay maganar yana maido idonsa kaina’.
“kanta ke ciwo ranka ya dad'e, amma tasha magani ma, shine barcin ya kwashe a wajen”.
Ido yad'an tsuramin, kafin ya cije lips d'insa kad'an.
Jakadiya tajuya zuwa kitchen, babu dad'ewa tadawo da ruwa ta ajiye masa.
Sannu yamata sannan yad'auka yana sha, itakuma tabar wajen.
Kofin da yasha ruwan ya ajiye, ya maida