Showing 276001 words to 279000 words out of 382522 words

Chapter 93 - Raina Kama 1 And 2 Hausa Novel Complete

03 Jan 2025

4957

sauk'i da zamubi, inhar muka bari harya bud'e da kansa lallai zai lalata komaine, Dan wannan shine shirinsu”. Sir Isa ne mai maganar.
Galadima ya danna abin kunnensa yana fad'in “Vijay mubashi dama kawai, a lokacin daya shiga kaikuma ka tabbatar da ka zuk'e dukkan nasa shirin, ga wata akwatinan dayake yawo da ita a bayan handle d'in Computer d'insa, karka ta6ata Dan makircine ya shirya a cikinta, munayin kuskuren ta6awa labari zaisha Banban. Alex yay gaggawar had'amin sabbin Securitys muga kozasu ja hankalinsa can, ga hoton yaranan zan d'ora masa, dasu zaiyi amfani, dan dolene mu kauda masa hankali, yasan mi yakeyi sosai”.
“Ok! Ok! muje zuwa kawai” vijey ya amsa a hanzarce.
Da sauri Galadima ya maida kallonsa ga Sauban yana fad'in “dakaje duk ka d'auki su Amaturrahman ne?”.
“Eh yaya dukna d'aukesu”.
“A lokaci d'aya ko daban-daban?”.
Na d'aukesu lokaci d'aya, nakuma d'auki kowa shi kad'ai”.
“Alhmdllh taso nan”.
Tashi Sauban yayi ya matsa inda Galadima yake, wani glass Galadima ya tura masa, yace, “'Dora duka hannayenka anan mugani”.
'Dorawa Sauban yayi, bayan ya ta6a wani farin Abu da Baffi ya bashi, shatin hannun yaran suka bayyana, dayake yayi musu wasa sosai, amma kuma hakan bazai gamsarba.
Daga can Alex yace bazaiyiba, dole akawo yaran. Shima Galadima ya tabbatar bazaiyinba, sai hankalinsa ya kuma tashi, yaran sunyi k'ank'atar daza'a fito dasu daga gida.
Muftahu yace, “Ranka ya dad'e bara kawai naje Na kawosu inaga zaifi sauk'i”.
Baffi yace, “hakan shine kawai dai-dai sai dai bakai yakamata kajeba, a kira mahaifiyarsu tabama Wanda zai iya 6adda bamanni wajen kawosu, kuringa tunawa sumafa idonsu nakan kowane motsinmu a yanzu, shiyyasa tun a jiya naima Sameer hannunka mai sanda akan hakan”.
Galadima daya zubama Computers d'in ido kawai yana kallon 6arnar da ake shirin masa. Ya mik'e tsaye yana fad'in “Muftahu ka kira mai taxi d'innan yaje inda yata6a ajiyeta za'a kawo masa yaran”. fitowa yay daga d'akin yana k'ok'arin neman number Munaya ya kira.
Bugu biyu Munubiya da wayar ke hannunta ta d'aga, tana mannama Munaya wayar a kunne, bai amsa sallamarta ba yace, “Yanzunnan ki bama Innaro da laraba su Abdurraheem, sufito bakin layinku akwai mai taxi zai d'akkosu”.
Cike da mamaki Munaya tace, “yalla6ai ban ganeba?”.
A tsawace yace, “basai kinganeba, Dalla malama kibasu karki 6atamim lokaci”.
Sosai Munaya ta tsorata da tsawar tasa, kad'an yarage wayar ta su6uce mata ta daiyi azamar rik'ota, batada za6in daya wuce bin Umarninsa, dukda hankalinta bai kwantaba da hakan. Yanda yace ayi haka tayi, innaro da laraba Na fitowa suka samu mai taxi yana jiransu.
Cikin mintuna k'alilan suka iso, Muftahu da Sauban sukazo suka kar6i yaran, akabar su innaro a mota zasu jira.
Akan wani Abu akad'an d'orasu, da hotonsu ya fota a Computer d'in sai'a ciresu, sud'uka duk aka d'ad'd'orasu, sannan su Muftahu suka maidasu wajensu innaro aka koma dasu. Sudai duk mamaki ya cikasu akan miya faru? Basuda mai basu amsar wannan lamari.

Bayan su Galadima sun turama su Alex hotunan yaran sai duk suka koma gefe suka zubama Computers d'in ido, sauran lamari sunbarma ubangiji. Suna kallo wancen ya shige inda yakeso, bayan sun bashi dukkan dama, tashin hankalin Galadima shine, mutumin lalata komansa yakesonyi bawai d'auka ba, idan da ace d'aukace hakan mai sauk'ine, k'iris yarage wancan ya cinmusu, Galadima ya lumshe idonsa zuciyarsa Na k'una yana ambaton sunayen ALLAH, abinda ya d'auki tsawon shekaru yana tanadinsu ga wani banza zai gogesu cikin seconds, hakan ya tabbatar masa da Harun ne yabada wani yanki Na sirrinsa, saboda yasan abubuwa da yawa akan aiyukansa, sauban ma k'asa yay dakai yana hawaye, shikenan dukkan hujjojinsu da suke ganin zaisa su samu a hukunta masu laifi suntafi, baffi da sir Isa da Muftahu ma duk jikinsu yayi sanyi, kowa sai zuciyarsa Ce ke bugawa......
Sauban yace, “Yaa Sam!”.
Galadima ya tashi zaune sosai yana bud'e ido da kallon Sauban, batareda ya amsaba.
Sauban yace, “yaa Sam mizai hana mu gwada dabaran kashe Computers d'insu, kaga seconds 30 kawai yarage ya cimma burinsa”.
Ajiyar zuciya Galadima ya sauke, murya a sark'e yace, “Sauban abinda ya rage mana yayi kad'an wajen yin hakan, kuma zamu iya kuskuren da komai zai goge d'in da kanmu, kubarsa kawai yayi yanda yakeso......”
Katseshi baffi yay da sauri, “Sameer mu gwad'a d'in kawai, maybe a samu dacewa”.
Badan Galadima yayi tunanin samun nasaraba yatashi zaune jiki a sanyaye yana dannawa, Sauban yakuma fad'in “yaya Please kayi da yak'ini, saura 20 seconds fa”.
Tamkar Sauban yayima Galadima allura ne, yafara komai cikin hanzari, yayinda sir Isa ke taimaka masa.
Muftahu da Baffi dai y'an kallone, Dan basusan komai dangane da wannan harkarba.
Saura second 1 ya rage Galadima yasamu damar kashe Computers d'insu dana wad'ancan.
Suda ke murnar samun nasara duk sai sukayi tsit, su Galadima kuma Sauban ya sanya ihu.
Hararsa Galadima yayi, yayinda su Baffi sukai dariya.
Dukda suna addu'ar samun nasara hankalinsu bai kwantaba, Dan sai an kunna Computers d'in zuwa wanu lokaci, idan an tabbatar da samun nasara sannan.


***************

Hankalim Munaya bai kwantaba saida taga su innaro sun dawo k'alau, babu kunya taita d'aukar yaran tana jujjuyawa wai kozataga wani abinda aka musu, saidai kuma bataga komaiba.


***************************


Baffi ya kalli Galadima dayay shiru ido a lumshe, yace, “Sameer dolenefa komai yazo k'arshe yau, kabi ta hanyar da katsara domin zuwansu hannu gaba d'aya, daga baya saimu cigaba da Neman camera, dan Na tabbata bazasu hak'ura ba, shiyyasa tun a jiya Na sanarmaka”.
Galadima ya jinjina kansa batare da ya bud'e idoba yace insha ALLAH komai yazo k'arshe Baffi, safiyar gobe zaku tashi dajin yanda ta kasance, Nuren yana hanyar dawowa. Zamu tafi matakin k'arshe yau”.

Atare suka had'a baki wajen addu'ar ALLAH ya bada nasara.
Galadima ya amsa akan la66a da amin...............✍🏻




Lallai gobe da kallon kenan. Galadima manmu ka cika musu aiki kawai🤸🏻‍♀🤸🏻‍♀🤸🏻‍♀🤸🏻‍♀.







*_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭🙏🏼
*_Typing📲_*



*_💡HASKE WRITERS ASSO...._*


*_♦RAINA KAMA...!!♦_*
_(Kaga gayya)_


*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*
_________________________

_Masoyan RAINA KAMA... Alkairin ALLAH yakai gareku aduk inda kuke❤❤❤❤, bilyn Abdull nayinku fiye da yanda kukeyinta._

*TASKAR LITTATAFAN HAUSA*😘👌🏻
*ZAUREN HASKE*😘
*KUNDIN HASKE*😘
*RAINA KAMA FANS CLUB* GROUP 1,2,3,4,5 duka Na gaisheku, Wanda Na bud'e da Wanda masoya suka bud'e, inayinku over wlhy, I love you irin Trillion's d'inan fa🤸🏻‍♀😘.
*ZUREN BIEBIE ISA*😘👌🏻
*NICE N COOL NOVELS*😘
*PHARTY NOVELS*😘
*HUGUMA CONVERSETION*😘
*RANO NOVELS* 😘
*MANSHAT NOVELS*😘
*XUMUNTA NOVELS*😘

_Aradun ALLAH kunada matuk'ar yawa, gashi bana kusa balle naita jeroku babu gajiyawa, ina missing naku gaba d'aya, irin babu dad'i d'innan😔😂._
I love you all irin manya-manya d'innan😘😘😘😘😘😘😘🤸🏻‍♀👌🏻
__________________________

*_BOOK 3_* 👉🏻1⃣4⃣


.................Duk da dai sumbar komai a halin k'ila wa k'ala haka kowa yafito jiki a sanyaye, Baffi da Sir Isa suka wuce, Galadima ma kallon Sauban yayi daya zuba uban tagumi, yad'an murmusa yana fad'in “Haba autan Momma, miye kuma Na damuwar haka? katashi kuwuce kawai kar yamma tayi”.
Shagwa6e fuska Sauban yayi yana kallon yayansa, yace, “please Yaa Sam kabarni sai gobe saina wuce insha ALLAH”.
Galadima yay shiru alamar tunani, saikuma ya girgiza kansa, “uhm-uhm Sauban ka wuce yau, Dan gobennan akwai riski”.
Kamar Sauban ya tambaya dai amma yay shiru, yasan halinsa mawuyacine ya sanar masa. Dan haka saiya amsa da to kawai. Badan yasoba yaymusu sallama shima driver dazai kaisa yad'aukesa suka tafi.
Ajiyar zuciya Galadima ya sauke, zuciyarsa Na k'una da tsantsar damuwa.
tausayinsa ya kama Muftahu dake zaune shima yayi shiru damuwa da tausayin d'an uwan nasa fal ransa.


★★★★★★

Gaba d'aya zuciyar Munaya takasa sukuni gameda yanda taji muryar Galadima, tunda kuma aka maido yaran saita kasa zaune ta kasa tsaye, Munubiya dai da innarsu duk suna hankalce da ita, kamar Munu zata shareta saidai tamata magana.
“Nikam aganina da wannan zagaye-zagayen da kiketayi Sweetheart ai gara ki kirashi kisan damuwarsa, koma ladan kwantar masa da hankali k'yasamu”.
Munaya dake kwance akan gado ta kifa meenal saman cikinta datai barci ta kalli Munubiya, amma sai munu ta basar tamkarma ba ita tayi maganarba. Ajiyar zuciya Munaya ta sauke, yayinda Munubiya ta tashi tamayi ficewarta daga d'akin duka, harta fice Munaya nabinta da kallo, saida tabar ganinta sannan ta janye idonta a k'ofar tana cigaba da shafa bayan meenal.
Shawarar Zuciyarta dake cigaba da k'arfafa mata shawarar y'ar uwarta ta addabeta da k'awato mata Galadima a damuwa, da alk'awarin dataima Mahaifiyarsa. Kasa daurewa tayi saboda tausayin ahalinsa dashi kansa daya kamata, ta jawo wayar tana lalubo number sa, dukda k'irjinta Na dukan gama-goma Na tsoron tsawar daya mata d'azu da yanda suka rabu jiya. Haka dai ta dake tayi dialing number sa.

Galadima suna zaune cikin halin shiru da Neman mafita a zukata shida Muftahu kira ya shigo wayarsa, sharewa yay tamkarma bai jiba, ganin zata tsinke muftahu ya taso yay picking da sauri ganin *My Mata* yasan dai Munaya Ce, a kunne ya saka masa, Galadima ya bud'e jajayen idonsa ya kallesa, Muftahu yamasa alamar please da fuska.
Baice komaiba ya kar6a wayar yana maida idanunsa ya lumshe, Muftahu kuma ya fice abinsa.
Munaya tayi shiru takasa magana, kamar yanda shima yak'i cewa k'ala, sai sautin ajiyar zuciyarsa take jiyowa kad'an-kad'an, daurewa tayi tace, “Assalamu alaika”.
Dukda yasan itace saida yaji sanyi a ransa, Dan ita kad'aice kemasa haka a waya ya jure, saida ya d'auki wasu seconds kafin ya amsa sallamar.
Yanda ya amsa sallamar kawai ta tabbatar akwai matsala, Cikin aro jarumta tace, “Ranka ya dad'e barci kakeyi?”.
Yad'an murmusa, a zuciyarsa yace yarinyarnan a kwai wayo, “Uhm-uhm”. ‘yafad'a a sanyaye’.
Ganin tafara samun dama saita kuma saita muryarta tace, “'Dan gatan Abie, to mikakeyi ne haka? naji muryar taka can k'asa”.
Zamewa Galadima yayi ya kwanta cikin kujerar, yanzunma tamkar bazai amsaba, saida ya gama basarwarsa sannan yace, “k mikikeyi?”.
Munaya tayi murmushi mai sauti har yana jiyowa, ta shafa kan Meenal tana fad'in “kwance kawai nake ina tunanin rayuwa da abinda ta k'unsa, harma da Wanda ke gudana a cikinta”.
Yace, “Humm kamar mikenan?”.
“Kanason ji?”.
Ya kuma cewa “Uhm”.

“humm yalla6ai nakula duk yanda bawa yakai da samun komai Na rayuwa saikaga wata damuwa ko tawaya mai kutse acikin al'amuransa, bana manta maganar nan taka da kata6a fad'amin wani lokacin murmushin da jama'a kanyi iyakarsa fuskane, amma zuciyarsu sune kad'ai sukasan sirinta, lallai wannan gaskiyane, amma kasan mike birgeni da k'aramin k'warin gwiwa a rayuwata koda ace Na tsinci kaina a fagen sanyin jiki?”.
Galadima yace, “uhm-uhm”.
Munaya ta sauke wata sassanyar ajiyar zuciya da Galadima yajita har cikin ransa, yayinda wani Abu ya tsarga masa ta cikin kai har zuwa yatsan k'afa, ya gyara kwanciyarsa yana jiran jin mizatace.
“Komai girman fad'uwa inhar da yak'inin HAK'URI dana k'arfin ZUCIYA to lallai akwai tagomashin sirrin samun NASARA, hak'uri da juriya basa ta6a zama fad'uwa, inhar kaga bawa yayi hak'uri babu kuma NASARA a ciki to lallai hak'un nasa kad'anne, sometimes gaggawa aikin shaid'anne, saikuma ansha wahala ake shan dad'i, abinda kawai muke kasa fahimta shine riba akan sameta ne a muhalli biyu, walau a duniya kokuwa a lahira, duk wadda bawa ya samu sunanta nasara, amma kowa yafi fata da samun ta duniya, saidai ta lahira ita yakamata mufi d'oki da addu'ar samu, meybe tazame mana tsani Na zuwa inda bamuyi zatoba, hikimar Ubangijice yabaka nasarar anan kokuma a can, Dan babu yanda za'ayi a zalunceka mai kowa da komai sarkin Rahma da jink'ai ya bari, bai yarda da zalunciba, yakuma haramtashi agaremu mu bayinsa”.
Wasu k'ananun hawaye suka gangara ta gefen idon Galadima, fuskarsa d'auke da murmushi, yayinda kalaman munaya ke tasiri adukan magudanar jininsa da zuciya, wata nutsuwa ta musamman daya rasa tashiga ratsashi da bashi k'arfin gwiwa, a hankali yace, “ke y'ar baiwace matar Contract”.
Dukda maganar k'arshe ta sosa zuciyarta saita murmusa, cikin kuma kwantar da murya tace, “Ni a suwa Mijin contract ”.
Ya d'an dara batare daya shiryaba. Yace, “one-one kenan?”.
Munaya tayi dariya tana fad'in “nidai bada manufa na fad'aba”.
“Fad'i gaskiya dai yalla6iya tsiwa”.
“Gara mai tsiwa da miskili, koba komai akansan muna waje ai saboda tsiwarmu”.
Galadima ya kuma Murmusawa. Yace, “ki kiyayi randa zan kamaki ALLAH”.
Itama dariyar tayi. Tace, “yalla6ai ka fad'i wani Abu nabaka k'yauta mana”.
Yay d'an jimm tunanin mikenan?, saikuma yayi ajiyar zuciya yace, “mikenan?”.
Cikin wani salo Munaya tace, “R. Ita kawai nakeson ji a harshenka”.
Lallai yarinyarnan taga gadon barcinsa wlhy, yay maganar a zuciya fuskarsa na k'awatuwa da murmushi. yace, “Okay, kibari sai ina gabanki”.
“Tab, Indai ba yanzuba na fasa”.
“uhmyim, miye na karayar hajiyar tsiwa?”.
“Aiba karaya nayiba, lokacin kawai kabari ya wuce, ni karmafa yarannan suma su gadoka”.
“Dai-dai kenan ai y'ammata, kokin manta k'yan d'a ya gaji ubansa”.
“Humm Alfahari kenan, ita uwa an rainata”.
Dariya tabashi, amma ya daure baiyiba. Yace, “keda kike gudunsu mizaisa su gadoki?”.
Munaya ta d'an ta6e baki, cikin juya idanu tamkar tana gabansa tace, “yanzu kana ina?”.
Murmusawa yayi saboda basar da maganar da tayi. Yace, “kinason ganinane?”.
“A'a, son sani kawai nake”.
“Humm, naje tad'i to”.
Shiru munaya tayi, sai kuma ta d'an dara, “Yalla6ai kasan wani Abu kuwa?”.
“Saikin fad'a”.
Cikin danne dariya tace, “irinku kwantai kukeyifa, sai anyima y'ammata tallarku asamo mai taimakonku ta aura, kaima nasan saisu takawa sunmaka haka.....”. Sai yaji kitt, ta yanke wayar.
Wani k'asaitaccen murmushi ya saki yana shafa kumatunsa, ya d'ora wayar saman cikin sa yana fad'in “lallai yarinyarnan kin girma, zaki tabbatar nayi kwantai kuwa”.
Daga canma Munaya dariya taketa k'yalk'yatawa, harta tada Meenal, Mununiya datun d'azun take kallonta ta bayan labule bata saniba tayi murmushin jin dad'i itama tana share hawaye, tanason y'ar uwarta sosai, sannan wayonta da iya mu'amullarta na birgeta, tabbas Munaya tanada tsiwa, amma tanada wayo, inhar zaka takurata bazata ta6a raga makaba, amma tanada tausayi dason ganin farincikin wani koda ita zata rasa nata farincikine, gakuma son girma uwa gyambo, tanason komi zaka mata ka nuna muhimmancinta a gareka, a fili tace, “ALLAH yakawo farinciki mai d'orewa a ratuwarki kema y'ar uwata”.


Amin munu😘☺.


★★★★★★★★

Tunda Muftahu ya shigo yakebin Galadima da kallon mamaki, ganin yasake yanata fara'a tamkar ba shine a matsananciyar damuwa yanzunba, ya zauna zuciyarsa na addu'ar samun mace tagari, dan lallai *MATAN KWARAI RABIN ADDINI ce*.
Galadima ya hararesa yana tashi zaune, “malam lafiya ka k'uramin ido?”.
Dariya Muftahu yayi sosai, yace, “to miye na tsarguwar ranka ya dad'e, wlhy kuna sha'aninku kaida gimbiyarka, yanzu nan harta saukeka daga hawa saman da kayi”.
Filo Galadima ya jefama Muftahu, shikuma ya cafe yana dariya.
Galadima ma murmushin yayi yana danna kiran Sauban. Dan yasan har yanzu yanacan cikin damuwa. Hasashen nasa kuwa yayi dai-dai, Dan har yanzu muryarsa a cinkushe take. Amma jin ta Galadima a sake sai farinciki ya kamashi, cike da zumud'i yace, “yaya an dace ne?”.
Murmushi Galadima yayi mai sauti, yace, “muna fatan hakan autan Momma”.
Alhmdllh Sauban yashiga jerowa, saiya saki jikinsa kuma harda tsokanar Galadima yana dariyar k'eta.
Galadima dai murmushi yakeyi yana girgiza kai, ya yanke wayar zuciyarsa na addu'ar ALLAH ya saka farinciki a zuciyar Munaya fiye da yanda ta sakasu. Massage ya tura mata sannan ya kalli Muftahu


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login