Showing 285001 words to 288000 words out of 382522 words

Chapter 96 - Raina Kama 1 And 2 Hausa Novel Complete

03 Jan 2025

2977

gida, anbarsa da garadan samarinnan akan sai washe gari, Dan sun tsarama su Zarah duk yanda zasuyi.


Babbar magana, Alhaji Mansur habibu Uba yana shirin kwanciya barci wayarsa tayi tsuwar shigowar sak'o, sharewa yayi, hakan kuma saiya saka matarsa a zargi, tatashi zata d'auki wayar ya hana, saita kuma tsarguwa, a zarginta wata shegiyarce ta turo masa, ganin ta fusata saiya bud'e sak'on.
Babu shiri ya dirgo daga gadon a tsorace yana tambayarta ina nerh-nerh take?.
Da mamaki race, “batace ta sanar maka zataje wajen Rahma ta kwanaba?”.
A rikice yace, “Rahmar ubanwa, maza kiramin ita yanzunnan su Abubakar suje su d'akkota”..
Bata fahimci inda ya dosaba, amma rikicewarsa saiya sakata d'aukar waya ta kira nerh-nerh d'iyarsu, wayar na Shiga amma ank'i d'agawa, cikin tsantsar tashin hankali ta sanar masa, ya daka mata tsawa yana fad'i “ki kira Rahma d'in ko wani d'an gidansu mana!!”.
Maida akalar kiran tayi kan Rahma, itama dai ank'i a d'aga, bataso kiran Hajiya yalwa ba, dan atunaninta kota kwanta, amma dole ta kiratan.
Hajiya yalwa Na zaune kusada mijinta Alhaji Abdul-Naseer Nafi'u kiran ya shigo, tayi mamakin Kiran, Dan hajia Marya bata kiranta a irin wannan time d'in, saitayi tunanin ko takasa hak'urine da rashin nerh-nerh abinka ga auta. Cikin raha tayi picking tana nunama mijinta wayar da baki, yay y'ar dariyarsu ta manya yana kuma kishingid'a da zubama matar tashi idanu.
Tambayar da Hajiya Marya tama hajiya yalwa ce ta rikitata, ta mik'e zumbur tana fad'in “bara Na duba to, Dan wajen 3pm suncemin zasuje zaga gari, amma 7 zasu dawo gida, to wlhy bak'i mukayi suka d'auke hankalina nikuma ban nemi ganinsuba, tunda ina tunanin sundawo suna sashen Rahma”.
Duk kiranda Alhaji Abdul-Naseer kema hajiya yalwa batajishiba, hakan ya sakashi biyota.
Kusan atare suka iso sashen Rahma d'iyarsu, y'an aikinta guda biyu Na zaune a falonta sunata gyangyad'i, kai kace sashen wata mai aurene ba budurwa y'ar 17years ba, Dan itace autarsu suma.
Hajiya yalwa ta dakama masu aikin tsawa tana tambayarsu ina su Rahma?.
A rikice sukace suma dawowarta suke jira tun d'azun (Dan sunsan inhar ta iske sunyi barci zasu yabama aya zak'inta, maybe ma yazama sanadin barin aikinsu).
Alhaji Abdul-Naseer yana k'ok'arin gwada kiran Rahma shima irin sak'on Alhaji Mansur ya shigo masa.
Ai sai suka kuma rikicewa, Ashe sak'o dukya jema sauran abokansu, dan dannan suka Shiga kiran juna kowa yana tabbatarwa d'an uwansa Galadima ya d'auke masa d'a ko y'a.
A wannan Daren suka sanarma police, gidajennan 11 babu Wanda ya rintsa barci, dukda yaran 8 ne a hannun Galadima, biyu basuda sauran yara a gabansu, duk sunyi aure, Galadima kuma yakafa musu nasu tarkon ne daban, biyu kuma a ciki bamasu ta6a haihuwa ba, biyar sun mutu yace bashida matsala da matacce, shi wannan saisunje babbar Court ALLAH zaimusu nasu hisabin. Sauran yaransu irinsu Alh halliru kuma yace nasu mai sauk'ine tunda manyansa suna hannunsa.
Tun a wannan daren manyan police suka Shiga Neman ina Galadima yake, tunda kai tsaye yasaka sunansa a sak'on messages d'in daya turama iyayen yaran.

Galadima yarigada ya tsara komai yanda ya dace, duk wata waya dazata fita a wayarsu saiya ganta yakumayi recoding d'in maganar, wannan yasa duk abinda suka fad'ama police yaji, murmushi kawai yaytayi, yayinda su Nuren sudai hankalinsu bai wani kwantaba, dukda sunji dad'in rikicewar da mak'iyar Galadima sukayi.
Abinka ga manya, tun a labaran 12am Na daren ranar aka fara saka maganar, labari yafara shiga kunnuwan wad'anda basuyi barciba.
Ciki kuwa harda y'an masarautar gagara badau.
Hankalin mai martaba ya tashi, a Daren ya aika jakadiya data rako matarsa turakarsa kiran Galadima, danya kira wayarsa switch up.
Lokacin da jakadiya taje sark'in k'ofa ya tabbatar mata Galadima ya fita tun farkon dare.
Komawa jakadiya tayi ta sanarma mai martaba, aiko yakuma shiga tashin hankali, minene haka Sameer dayake kallo mai nutsuwa da hankali ya aikata?.
Yana cikin wannan damuwa Waziri ya kirashi, ya tabbatarmasa Sameer ya turo masa sak'o shima Harun yana hannunsa.
Zuface ta shiga jik'a mai martaba, yanzunan duk jajen da akeyi Na 6atan Harun d'an waziri dama Sameer yasani amma yay kunnen uwar shegu da kowa, hazbinallahu wa ni'imal wakil, shikam baya fata wannan mummunan labarin yaje kunnen 'Dan uwansa dake kwance cikin halin matsananciyar jiyya (kunsanfa har yanzu babu Wanda yasan samun sauk'i da Abie yakeyi, bayan ahalinsa dasu papi) a gagara badau babu Wanda yasani.

Su Galadima duk suna ganin abinda ke faruwa a TV suma, amma ko'a kwalar rigarsa, damuwa d'aya kecin ransa halinda Abban Munaya ya tsinci kansa a ciki, amma sauran matsalolin dama dukya dad'e da shirya abinsa, komi zai biyo baya dama zuciyarsa ta shirya d'auka.
Yau dai kam kusan a zaune suka kwana, abin tausayi saiga Galadima da kwannan kujera, aiko yasha wahala, Dan tashi yayi jikinsa Na matuk'ar masa ciwo, d'akin da aka saka masa kayansa yashiga, yasamu yay wanka sannan yayo alwala sukayi salla a jam'i, Dan har yaran duk kwancesu akayi, wad'anda kuma basayi suna zaune daga gefe.
Galadima yace Ameer yaje da y'ammatan su had'a musu breakfast, cikin cika umarni yatasasu gaba suka fice, saidai kuma Farhat ce kawai ta iya girkin a cikinsu, gashi tanada Asthma, bakomai take iya sakewa wajen yiba, haka dai Ameer ya saka Nerh-nerh da Rahma suka taimaka mata da Abu mai sauk'i, dayake a tsorace suke, komai aka saka su yi sukeyi, sunga zuk'ek'iyar bindiga ahannun Ameer yo🤭😂.

Koda aka kawo abincin dukda tashin k'amshi da yakeyi Galadima cayay bazai ciba, sudai su Muftahu kam ci sukayi, shikuwa yak'are dacin cake da tea, Wanda dama da kayayyakinsa yazo caf (Galadima fa da shirin zama yazo🤣 fans).

Tun'a daren jiya gidan da su Galadima suke aka zagayeshi da y'an sanda, yasan kuma da hakan Dan CCTV Na nuna masa komai, amma saiyayi tamkar baima San da zuwansuba.
Harun dai yak'i ci shima, hasalima sai yankama Galadima magana yake, wai inhar ya isa shid'in shegene ya kwanceshi mana, Ashe shid'in matsoracine ma, Dan ba'a sake d'aure kowaba bayan sunyi salla saishi Harun d'in daya nemi yin gardamar k'in nutsuwa waje d'aya.
Ko inda yake Galadima bai kallaba.

Nuren yay gyaran murya, duk suka maida attentions d'insu garesa. Yace, “inhar kun shirya bamu had'inkai kowa zai fita a gidannan lafiya babu ko kwarzane a jikinsa, Dan bamuda matsala daku, da iyayenku mukeyi, Wanda yaza6i kuma tafiya barzahu babu shiri saiya nuna jarumtarsa ko rashin kunya, wannan wawanma ya isheku izna”. Yay maganar yana nuna Harun daketa bige-bige yana kumfar baki masifa.
Duk suka amsa da zasu bada had'inkai.
Yau dai Darma kam shima yashiga hankalinsa, Dan yaga lamarin yafi k'arfinsa.
Galadima ya d'auki k'aramar wata waya dake kusa dashi yafara dannawa yana shan tea d'insa hankali kwance, yayinda k'afarsa ke hard'e d'aya kan d'aya.
Munaya ya kira, wadda itama batayi isashen barciba, gashi suna a yanayin rashin tsarki balle ta duk'ufa gayama ubangiji itama, amma dukda hakan bata fasaba, zuwa dare kuma kowa ya ankara da rashin dawowar Abba akwai matsala, dan around 7:30pm Baba k'arami ya dawo gida, babu dad'ewa kuma saiga Dady shima, dawowarsu yasaka kowa Sanin mi ake ciki, innaro ce kawai aka hana kowa ya sanar mata.
Babu Wanda yay barcin kwanciyar hankali a gidan su Munaya, saidai yaran k'anana dabasu San dawan garinba, irinsu Inna ma ai akan sallaya suka kwana suna gayama ALLAH kukansu😭.
Basuda wuta a daren jiya, shiyyasa basuga abinda yake faruwaba, rashin kwanciyar hankali ya hana a kunna musu gen..., Gasu Abdurraheem kwana sukayi kuka.🤦🏻‍♀
Cikin sanyin jiki Munaya ta d'aga kiran, muryarta ta dushe saboda kuka, ahaka ta gaisheshi.
Ya amsa a sanyaye shima yana tambayar yaranshi, tace, barci sukeyi.
Cikin lumshe ido yace, “karki damu daduk abinda zaki gani, sannan karki kirani, dan duk kiran dazakiyi nasan baizama lallai nikad'aine zan jishiba, zan dinga kiranki dakaina insha ALLAH. Please take care of yourself”. Kitt ya yanke wayar batare da yajira cewarta ba.
Kanta ta cusa cikin k'afafu ta fashe da kuka, yayinda Munubiya ma ke gefenta tana nata da shayar da Ameen daya tashi barci.

Galadima kuwa yana yanke wayar ya mik'e cikin takun izza da k'asaita ya k'arasa gaban Harun da bakinsa yakasa yin shiru.
Izzarsa da k'asaitarsa Na burge matasan samarin nan, hakan yasa duk suka bishi da idanu har y'ammatan, ga fuska a cakud'e babu alamar yasan minenema dariya.
Gaban Harun ya tsaya hannayensa duka a cikin aljihun wandonsa, babu Wanda yakula da lokacinda Galadima yaciro hannunsa d'aya a aljihu, saidai k'arar mazgar Harun dayayi abaki sukaji kawai, kafin Harun ya farfad'o Galadima yakuma k'ara masa ta d'ayan gefen.
Sannan ya d'an risuno yanama bakinsa alamar zip da yatsunsa biyu🤐, Harun yamasa shiru kenan🤣.


Kutt, gaskiyafa Harun ya mazgu babu k'arya🤭🤣.

Amma d'an bala'in naku bakinsa bai mutuba, bayan ya farfad'o daga azabar dukan saiya cigaba da magana cikin haki da huci.
Sharesa Galadima yayi yakoma ya zauna dan fuskantar abinda ke a gabansa, a fusace ya d'auki k'aramar bindigar daya fiddo yanzu yafara Harbin inda Harun yake, ta saitin k'afafunsa. Rikicewa kowa yayi, Harun yashiga mutsu-mutsu da k'afafu yanasan d'agewa Dan kar Harbin ya sameshi.

K'aramin d'an iska Ashe kanajin tsoron mutuwa🤣?.

Wannan harbi ya kid'ima police d'in dake a wajen gidan, akuma dai-dai lokacinne manyansu suna iso suma, kuma duk sunji harbin.............✍🏻


Humm babbar magana, komiye shirin Galadima Na zama kidnapper?.🤦🏻‍♀
Wane ahiri kuma su Zarah sukazo dashi gida🙆🏽?.
Sannan wane shiri Galadima yake akan ku6tar Abba? tunda yace plan B😔☹.

Ina baba mai kanwa? Wane taimako zaibamu shima😭.



Kumuje zuwa my guys karku k'osa dai, sannu-sannu bata han[8/3, 3:35 PM] +234 810 341 4063: *_Typing📲_*



*_💡HASKE WRITERS ASSO...._*


*_♦RAINA KAMA...!!♦_*
_(Kaga gayya)_


*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*


*_BOOK 3_* 👉🏻1⃣6⃣


.................Jin tsayuwar motoci ya saka Ameer lek'awa ta window, juyowa yay ya kalli Galadima, “Ranka ya dad'e y'an sandane”.
Baki Galadima ya ta6e, ya share tamkarma baijiba, yana cigaba da bud'e wasu file daya fiddo a briefcase. Saida yaja kusan 1 minute sannan ya mik'ama Nuren dake kusa dashi wasu files, ya zaro takarda kuma yay rubutun dabai Gaza layi biyarba ya mik'ama Ameer da wata k'amar waya a kwali.
Kar6a Ameer yazo yayi, batareda Galadima yayi magana ba ya nuna masa window.
Muftahu daya fahimta yace, “Ameer ka jefa musu takardan da wayan”.
Ameer ya amsa da to, yanufi window d'in, cikin dabara ya jefa kwalin da takardar.
Wani d'ansanda dayaga tahowarsu yay saurin zuwa kusada window d'in, ALLAH yabashi nasarar cafewa.
D.p.o dake tsaye tare da sauran police ana shawarar yanda za'a shiga gidan ya kaimawa.
Yay salute nasu kafin ya Isar da sak'on dukda yasan duk sunga daga ina kayan suka fito, d.p.o ya gyara tsayuwarsa yana fad'in “bud'e kwalin mu gani”.
Bud'ewa yayi, yaciro wayar yana cewa, “wayace sir”.
Cikin ta6e baki d.p.o ya jinjina kansa, yace, “takardar fa?”.
Itama bud'ewa yayi, yafara karanto abinda ke jiki, wanda Galadima ya rubuta da harshen nasara.

*_Kamar yanda suka fad'a Muhammad Sameer ba d'an ta'adda baneba, inhar zakubi yanda nace lallai yarannan zasu fita lafiya, idan kuma har kuka nuna k'arfin iko, zanta jeho muku gawarsu d'aya bayan d'aya ta saman benenan, ga wayanan, idan kuna buk'atar magana koni ina buk'ata ta wadatar, Dan kar wani yay gigin cewa zai shigo. Idan nayi ba dai-daiba a gafarceni👏🏻_*

Daga d.p.o har jama'ar dake kusa dashi duk ajiyar zuciya suka sauke, ya jinjina kai yana cije bakin mamaki, cikin sauke numfashi yace, “saimu bishi yanda yakeso mugani, idan munga zai mana wasa da hankali sai a d'auki mataki, C.. babangida a zagaye gidan”.
“Ok sir”. C babangida ya amsa yana salute nashi.
Dandanan suka warware wani blue d'in zare suka zagaye gidan dashi, mutanen anguwa dasuka fara fahimta harsun fara taruwa kallo, harma wad'anda sukaji a labaran sunfara gangarowa anguwar damin ganema idonsu.

Duk abinda ke faruwa Galadima Na zaune k'afa d'aya kan d'aya yana kallo ta CCTV, sai famar buga pen yake saman la66ansa a hankali, suma dai su Muftahu dasu Harun suna kallon komai.

Kujera aka kawoma d.p.o ya zauna, dayake da sauran safiya babu maganar neman runfa ko umbrella.
Wayar d.p.o ya kar6a da kansa, dan case ne Na manya IG da kansa yakirashi, yakuma abbatar masa shima yana nan zuwa.
Shiru d.p.o yay yana bincikar wayar da Galadima ya aiko da ita, babu komai a cikinta sai Number guda d'aya, baice komaiba yaciro wayarsa yayma IG bayanin komai.
Daga can IG yafara fad'a, wai tayaya zasu saurareshi, bayan d'an ta addane, duk Wanda zai iya kidnapping aiko d'an ta'addane, kawai su nuna masa k'arfin iko wajen ku6tar da yaran.
Shidai d.p.o ya kwantar da murya cikin sigar lallashi yace, “Nidai Sir da ace za'abi ta tawa daminbishi a hankali, maybe akwai sak'on da yakeson isarwa, karfa mu manta shima d'an manyan mutanene, shikansa akwai sarauta mai daraja a kansa, ai mai martaba bazai ta6a jin dad'iba shima, tunda ya buk'aci dama mu bashi, idan munga batai manaba saimu d'auki mataki”.
IG yace, “shikenan, Ku kirashi muji miyake buk'ata, nima a had'a dukkan maganar da zakuyi dani naji komai, dukda munama hanyar isowa yanzunan”.
Cikeda farin ciki d.p.o yace, “ok sir”.
Duk kayan aikin dasuke buk'ata suma sun tanadesu, yayinda y'an jarida suka fara isowa wajen.
Shima C.P ma saigashi ya iso, duk suka k'ame wajen salute nashi har d.p.o.
Ya amsa musu cikin jinjina kai, sannan ya buk'aci jin mi'ake ciki?.
Bayani d.p.o d'in yamasa, shima ya gamsu da shawarar abi komai a sannu d'in.

Galadima ya murmusa yana lumshe idanunsa yana sauke ajiyar zuciya. Saboda dukkan wayar da d.p.o yay da IG a kunensa ne.
Sudai su Nuren sunyi jugum-jugum Dan son ganin minene shirin Galadima waine?, da har yaza6i fiddo kansa wa duniya a matsayin mai laifi?.

Kiran da C.P yayi da kansane ya shigo wayar Galadima bud'e ido yayi yana kallon su ta CCTV, sannan yay picking call d'in, shiru yay yak'i magana, saida C.P ya fara masa sallama sannan ya amsa.
C.P yace, “Ranka ya dad'e barka da safiya”.
Baki Galadima ya ta6e, ya amsa da “Barka dai”.
Gyara zama C.P yay yana kallon saman gidan, duk su Galadima suna ganinsa, yace, “Ranka ya dad'e muna saurarenka, ka fad'i buk'atar taka, inhar batafi k'arfinmu ba za'a biya maka insha ALLAH ”.
“Humm” Galadima ya fad'a yana mik'ewa tsaye, duka hannunsa Na zube cikin aljihu, dayake yana amsa call d'in ne da abin da ke kunnen sa.
Falon ya shiga zagayewa cikin takunnan nasa na k'asaita da izza, saikace namijin tantabara yana gwada gasar tafiya a gaban matarsa😜🤣.
Suko sai binsa da kallo suke tamkar wani magiji.
A hankali yace, “Buk'atata ta farko shine iyayen yarannan su fiddo Alhaji Auwal fharuk, idan sunyi haka lallai zakuji manufata kai tsaye batare dana ja muku raiba, Dan nima ina buk'atar hutu”.

C.P ya shiga jinjina kansa kawai yana sauraren Galadima da dukkan sauran police d'in dasuma sukeda alhakin jin komai ta hanyar abinda suka saka a kunne.
Bai k'ara komaiba ya yanke wayar, Yakoma mazauninsa ya zauna yana kallon yaran dasuma dukshi suke kallo, d'an murmusawa yayi yana d'aukar ruwan daya ajiye, saida ya bud'e murfin ya mik'ama Wanda yake kusa dashi.
Shima yay murmushi yana girgiza kai da fad'in “A'a ranka ya dad'e, Na gode”.
Galadima ya mik'ama sauran suma, amma duk sai sukace A'a, murmushi yayi


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login