Showing 60001 words to 63000 words out of 382522 words

Chapter 21 - Raina Kama 1 And 2 Hausa Novel Complete

03 Jan 2025

2930

suma.
Habaici dai kam munshashi wa su innaro da matan gidanmu, danma ita innaro gwaggo Safiyya na hanata ne, da bamu san tijarar dazata zubarba a ranar kam.
A haka aka shiga satin biki, mu bamu wani gayyaci k'awayeba, daga Bilkisu sai su Ayusher, ashe Ayusher ta buga invitation na k'awaye suka raba itada Bilkisu bamu saniba.
Abin mamaki ranar kamu sai ganin k'awayenmu mukayi harna secondary.
munji dad'in hakan sosai kuwa.
A ranar kamun saiga wasu mata hud'u sunzo wai dangin miji nane, su mama Rabi'a sukayi musu tarba ta mutunci, ba a nuna musu komaiba kuma, dukda a yanayin shigar talauci da sukazo, saidai zund'e da gulma irinta 'yan biki. Matan gidanmu kam komai ya kaimusu dai-dai, sai dariya da yada magana a kaikaice sukeyi. Da aka kaisu su gaisa da innaro taita musu yatsine-yatsine, harda tanbayarsu waisu garinsu ba'a lefene? dabasu kawoma jikartaba?.
Basuce komaiba sai murmushi kawai da sukayi.

Washe gari kuma akayi k'unshi, mudai namu aunty Salamah ce tamana, tana tsaye akan komai namu tamkar yayarmu ciki d'aya.
A ranar kuma akaje a kaima sauran amaren jere, harda Munubiya, amma ni banda ni, tunda ba'asan ina za'aje ayiba.
Aranarma Munubiya tayi kuka, nidai ina k'ok'arin danne zuciyata, saboda nabama innarmu kwarin gwuywa karta tada hankalinta.
Aiko Alhmdllh ta dake tamkar komai baya damunta, tashige cikin abokan arzik'inta sunata harkoki. kowanne 6angare yacika da dangin matan gidanmu, abin tamkar fariya, namu 6angarenne kawai keda sauk'in jama'a, hakama gidan innaro yacika da danginta da dangin kakanmu.

Tunda aunty Salamah tagama yimana k'unshi da gyaran kai dana jiki sai muka nufo hanyar gida, saboda yaa marwan yazo neman Munubiya harsau biyu, sai kiran wayarta yake yana masifa saboda tare yake da abokansa. hakan yasa muka taho gida.
Gashi Yau zamuyi sister's and brother's day, duk da dai saima da yamma.



★★★★★


Galadima dake zaune a makeken falon Ummu hasheem, yanata bin jerin akwatinan da kallo, ga wasu daga 'yan uwansa zazzaune sunata kuma kimtsa kayan, aunty Mimi ta kalleshi, “kunga zanma mantafa, my k'ani ina kayan dana baka kayo gaba dasune?”.
Yatsine fusaka yad'anyi yana gyara zamansa, “nifa nama manta inda suke, shiyyasa nace bazan d'akkoba ai”.
Wata uwar harara ta watsa masa tace, “lallai bakada kai yaro, bar ganin matarka za'a kaimawa, suka 6ata biyana zakayi ehe”
Murmushin gefen baki yasaki yana lumshe idanu, cikeda k'asaitarsa yace, “Samha! jeki bedroom d'ina ki duba, maybe suna can“.
“bama kada tabbas kenan?” cewar mom.
Bud'e idanunsa yayi yana murmushi, “no mom insha ALLAH sunama can. ni yanzu kam kun sallameni natashi natafi? dan zansa aje a d'auko su Akash a airport ”.
Ummu Hasheem tace “kaje kawai, dama dan kaga kayanne, tunda kuma kace komai yayi ai shikenan”.
Mik'ewa yayi yana fad'in “thanks you Ummu, nabarku lafiya”.

Tunda yasamu yay escape sai ya sauke ajiyar zuciya, shi dariyama suke bashi dagasu har su papi, su Dan basu san auren shekara d'aya bane dabasu dinga wannan rawar k'afarba, sun wani zauna sun had'a uban kayan lefe, yad'an ta6e bakinsa kawai yana nufar sashensa.

Komai na gidan sarauta mai tsarine, dan haka kai lefen MUNAYA da suke shirin yima a tsare akayisa, (papi ne yace Subari sai yau ana gobe d'aurin aure sai akai, tunda gidan su munaya basusan kosu su wayeba).
An tsara iya wad'anda zasu kai lefenne.
Bayan an gama zuba akwatunan a wata farar mota mai k'yau sabuwa dal aka rufe, driver ne kawai zai shiga cikin motar.
Sai kuma motoci 6 da aka zaba wad'an da zasu kai lefen.
Motar farko dogaraine, ta biyu kuma kuyangi ne, sai guda biyu 'yan cikin gidansu Galadima ne su hud'u, ko wacce mota mutum biyu, sauran biyun kuma 'yan 6angaren masarautar su Momma, suma su hud'u, kowacce mota biyu. sai Samha datasa kuka saitaje taga matar Uncle Sam.
Aunty mimi harta korata da zare mata idanu saiga Galadima motocin na niyar tashi.
Da kansa yabud'e mata gaban motar da aka saka akwatinan yace tashiga nan, idan taje ta gaida masa matarsa.
Cikeda d'oki tace zataji Uncle Sam, bazaka bada komai akai mataba.
Kansa yad'an dafe dan yakula Samha na neman k'uresa, shikuma yafad'a mata maganarne domin yanason agaban jama'a yadinga yana tsantsar k'aunar Munaya, a bad'ini kuma suna zaman aurensu na contract, shiyyasa ko lefennan baiji tsadar kud'in saba yabud'e bakin aljihu aka zuba kaya masu azabar k'yau, gakuma kud'in da Mai martaba yabada shima, dakuma sauran k'annen mahaifinsa.
Hannu yasaka a aljihunsa yana duba kozai samu wani Abu, amma babu komai sai wata chocolates guda biyu, wadda ya d'akkota ne zaiba khaleel d'azun yama manta, mik'ama Samha yayi yace “gashi kibata”.
Da dariya samha ta kar6a tace “Uncle ta gode to”.
Kansa kawai ya jinjina mata ya shirin barin wajen.
motocin suna fita daga masarautar saiya sauke ajiyar zuciya kawai.



★★★★

Gidanmu ya cakud'e da hayaniyar da akasan gidan kowanne biki da ita, bare mu daya kasance har auren mutum 6, dukda sai gobene d'aurin aure kuwa, yara sunata wasansu da tsalle-tsalle.

A jere motocin suka shigo cikin anguwar, jama'a sai binsu da kallo sukeyi, dai-dai k'ofar gidanmu driver daya san gidan yay parking.
Babu Wanda yay mamaki a 'yan kawo lefe, domin kuwa dama labari ya karad'e masarautar cewar Galadima'yar talakawa zai aura.
Dogarawa da kuyangi suka fara fitowa, sannan suka bud'e motor da akwatina suka suka fara fitarwa. Nanfa jama'ar anguwa sukayi cirko-cirko suna kallon ikon ALLAH dan ganin akwatinan da aketa fitarwa daga mota.
Batare da neman isoba Kuyangin suka fara kwasar akwatinan suna shiga dasu gidanmu..............✍🏼




😂😂😂
Team innaro kufito mu caskale yau🙊🤸🏻‍♀
⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀



Asha weekend lafiya😅✋🏻







*_ALLAH ka gafartama mahaifanmu👏🏻😭_*
*
_*RASHIN SANI.......*_




*HAUWA A USMAN*
_JIDDARH_



```Wattpad:HauwaAUsmanjiddarh```



1⃣9⃣



Khulud ta kuma zaro idonta waje tace " kai my Sanah,
cikin dariya Sanah tace " eh mana,
" ni dai please kiyi man alk'awarin baki kuma ramawa please,
tayi maganar cikin sanyinta,
Sanah ta kuma yin dariya had'i da dafa kafad'ar Khulud tana kallanta ido cikin ido,
cikin marairaicewa Khulud tace " please tana langwab'ar da kanta gefe,
Sanah ta d'an k'ura mata ido kana ta sauke ajiyar zuciya had'i da cewa " nayi miki alk'awarin daga yau har abada duk abinda zai man ban kuma ramawa,
cikin jin dad'i Khulud ta rungume ta tana cewa " yawwa my Sanah thank you so much,
murmushi Sanah tayi kawai batare datace komai ba,
ta rok'o hannun suka nufi part d'in kakannin su.


Fitowa Hanash yayi zuwa harabar gidan,
su Wajnah na biye dashi a baya,
Papu yace " au kinga na manta Hanash zai fita batare dana aike shi bank d'in bako?


Yayi maganar yana kallan Mimmee,
tace " kaga kuma yau Friday ba,
da idan ya aje su sai ya biya bank d'in,
kafin su gama walimar shi yaje yayi abinda zayyi,
Mimmee ta fad'a idanta kan Papu,
" kuma daga yau ba bank har sai Monday,
ga time na tafiya naga yanzu wajen 4:30pm,
yayi maganar yana mikewa had'i da kallan agogon hannunsa,
da sauri ya fita daga parlor'n yabi bayan su Hanash,
Hanash na niyyar yiwa mota key,
yaga Papu ya nufo su da sauri,
a hankali Hanash ya fita ya nufi Papu,
check Papu ya mik'ewa Hanash yana cewa " idan ka aje su a gidan walimar ka biya banki ka amshi wad'annan kud'in,
sai ka saka su a account d'ina ko naka,
Hanash yayi murmushi yana kallan Papu zayyi magana drivers biyu suka shigo gidan a lokaci d'aya,
Papu yace " yauwa ga drivers nan sun dawo,
bari na saka d'aya daga cikin su ya kai su gidan walimar,
kai kuma sai ga je bank d'in,
Papu yayi maganar yana nufar wajen drivers d'in,
cikin taushi Papu ya fad'a musu,
sannan ya sanar dasu Zohal su fito su shiga motar driver shi zai kai su,
kana ya koma wajen Hanash dake tsaye inda ya barshi,
Papu ya lura da yadda yanayin Hanash ya canja sosai,
sannan walwalarsa da sakin fuskarsa ba kamar da ba,
kallan Papu Hanash yayi kana yace " Papu wannan kallan fa?


Ya fad'a yana dariya,
shima Papun dariya yayi yana dafa kad'afar Hanash yace " bakomai kawai ina kallan d'ana ne,
in kuma za'a hana ni ne to,
yayi maganar cikin barkwanci,
Hanash yayi dariya batare dayace komai ba,
Papu yace " kaje maza ka dawo zamuyi magana da kai,
Hanash yayi dariya kana yace " hala Papu ya manta yau Saturday?


Papu ya zaro ido had'i da cewa " what! haba dai?


Hanash yayi murmushi yace " Allah kuwa Papu yau Saturday,
hala ka shafa'a ne?


" Ka manta jiya mukaje sallar juma'a?


Papu yace " na manta,
kasan tsufa ya fara kamamu ,
abinka da tsoho, Hanash kuma yin dariya yace " kai Papu wanne irin tsufa kuma?


"Bayan gaka nan kamar matashin sauryi kamar mu,,
Hanash ya fad'a cikin tsokana,
dayake sun saba wasa da dariya sosai da Papu,
dan wani lokacin idan ka gansu sai ka rantse abokanai ne,
Papu yace " kayya wanne matashin sauriya,
muda samartaka ai sai dai a lahira a aljanna,
jiya ai ba yau ba ,
tunda na haifi k'aton saurayi kamarka ai na tsufa,
ko yanzu Alhamdulillah dan na mori k'uriciya ta,
kai ma sai kayi k'ok'ari ka mori taka k'uruciyar,
sanda nake kamar shekarunka na haifeka,
amma kai gaka nan har yanzu 30yrs baka da ko budurwar,
ko rowa kake man dan karna ga 'ya'yanka oho,
inaga sai na mutu sannan zakayi aure ka haihu,
Jadda dake jiyo su ta window ta,
suka jiyo muryarta tana cewa " kyale ja'iri wallahi idan na gaji sai dai ya shigo gidan ya iske matarsa a b'angarensa,
imma bak'in ciki kake man dan kar naga yaranka ehe,
daga Papu har Hanash duk suka sanya dariya,
Hanash ya shafa kansa yana kallan Jadda,
Papu dake tsaye a wajen shiya hana shi ce mata komai,
sai murmushi da yayi tayi shi kad'ai yana shafa kai,
kallansa Papu yayi yana nazarin yanayinsa ya tabbatar akwai abinda yake damunsa,
amma sai ya sabar yace " ka rik'e check d'in a hannunka,
ranar Monday sai kayi kamar yadda na saka ka,
"tom Papu ba damuwa Allah ya kai mu Monday,
Papu ya amsa da " amin yana komawa part d'in Mimmee,
iske ta yayi tana k'ok'arin shigewa bedroom d'inta,
ganinsa yasa ta jiyowa tana kallan shi,
yace " wai meke damunsa ne?


Tace " wa?


Yace " Hanash mana,
naga kwana biyu yanayinsa duk ya canja,
Mimmee tace " nima dai haka nagani kwana biyun nan,
kamar yana cikin damuwa,
Papu yace " kin tambaye shi ne?


Tace " eh,
"Ok meya ce maki?


" Wai bai jin dad'in jikin sa ne,
Papu yace " ok mu barshi zuwa nan da kwana biyu mu gani,
Mimmee tace " Allah ya kai mu,
muje ciki kayi wanka ko?


Bayanta yabi yana cewa " kamar ko kinsan zafi nake ji,
Hanash na komawa b'angarensa ya kuma zubewa kan sofa,
had'i da runtse idannuwansa,
shi har yanzu bai san so da soyayyar Khulud ke d'awainiya dashi ba,
ta hana shi sakat, ta hana shi walwala da farin ciki,
haka nan kullum yake jin damuwarsa na k'aruwa,
babban burinsa a rayuwa yanzu bai wuce na sake ganinta ko sau d'aya ne a rayuwarsa ba.


part d'in Ganez suka fara shiga suka iske Nisah zaune kusa dashi,
Sanah tace " oh! ashe dai har yanzu ana tsinkar korawayen fure?


Duk sukayi dariya kana Ganez yace " a'a aini idan bada ku zan tsinki korayan fure ba,
ai a banza, Khulud tace " kinji shi zayyi mana wayo kullum yayi ta cewa idan ba mu ba sai rijiya,
Sanah tace " kuma yana tsoran matarsa ba,
Nisah tayi dariya kana tace " oh! kuji man yara,
wato kun saka mana ido, ai irin haka ake so,
Khulud tace " mijin ya rink'a jin tsoran matarsa?


Nisah tace " eh mana,
Sanah tace " ina fa dad'i miji ya zama mijin tace,
an dai mayar mana da kakanmu tace kawai,
Nisah tace " wannan ai kan tace ne ma,
duk sukayi dariya kana suka fita suka nufi part d'in Danish,
ganin Erum tayi kwalliya yasa su yin dariya,
Khulud tace " wato ke har yanzu baki dai na kwalliyya bako?


Erum tace " ina ni ina daina kwalliya,
Sanah tace " kici zamaninki kici na wasu ko?


"Sosai ma kuwa cewar Erum,
" a'a kace yau amare nane a gidan,
cewar Danish dake fitowa daga bedroom d'insa,
Sanah tace " mune, munzo a bamu abinda akaci aka rage,,
Danish yace " ku da kuke amare ina ku ina raguwa,
ai sai dai sabuwar dahuwa,
Khulud tace " ai dama kun saba yi mana wayo,
bayan duk tsoron matan ku kukeji,
Erum tace " ai irin wannan k'arshen ake so ayi yara,
ku ma kuyi addu'ar Allah ya baku ita mu,
Sanah tace " wai ma duk ba wannan ba,
ina zaku na ganku duk kunyi kwalliya?


" Mu da muke da walima yau har a tambaye mu inda zamu dan munyi kwalliya,
Erum tayi maganar tana dariya,
Khulud tace " a she walima ce daku,
a ina kuma?


Erum tace " sosai ma, kuma a nan gidan,
Sanah tace " tab wai wacce walimar kuke nufi?


Badai tamu ba ko?


Tayi maganar a lokaci d'aya,
Erum tace " walimar ku ko tamu?


"Ai muke da walima kuwa,
tunda mune manyan k'awaye,
tayi maganar tana dariya,
Khulud tace " mu dai bamu gayyace ku ba,
kuma bamu san gayyar sod'i ehe,
duk sukayi dariya kana suka fita,
part d'in Juju sukayi,
da sallama suka shiga,
Didi ya amsa musu cikin fara'a,
kana yace " 'yan candy ne yau a gidan namu?


Sanah tace " mu ne,
Didi ya kalli Juju yace " ina kika b'oye mana su ne?


Juju tace " wacce ni?


" Ai sai dai ka tambaye Mamun su,
ni tunda sukayi candy ban sa su ido na ba,
sai yau, ko irin kayan kayan candy nan ba'a kawo mana ba,
balle muce mu shaida anyi candy,
muce Allah ya sanya alkhairi,
Khulud tace " kai Juju Allah bamu zauna bane,
mu ta yawan zuwa saloon da k'unshi,
Sanah tayi dariya kana tace " Juju ku da zaku bawa wasu ma,
kayan candy kuma ga walima nan kun shirya ku da kanku,
sai ku shaida anyi candy kuyi addu'ar Allah ya sanya alk'airi,
Didi yayi dariya yace " wai Sanah baki abin magana,
ke dai ba'a tab'a k'ure ki ta wajen magana,
Juju tayi dariya tace " ai ni nayi shiru tunda an fini baki,,,
dama hausawa sunce dokin mai baki yafi gudu,
Didi ya kuma yin murmushi kana yace " Sanah yaushe jamb d'inku zata fito?


Sanah tace " naji ance this coming Monday,
Juju tace " wacce university kika cike?


"First choice BUK second kuma ABU Zaria,
Didi yace " masha Allah Ubangiji ya taimaka, Allah ya bada sa'a,
duk suka amsa da Amin,
har Khulud dabata zana jamb d'inba,
dan cewa tayi ita ta gama karatun boko har abada,
Juju ta kalli Khulud kana ta mayar da kallan ta ga Didi tace " 'yar Abbu da Mamu ita aure take so,
Khulud ta d'ago kanta da sauri suka had'a ido Juju tayi saurin sadda kanta k'asa tace " Allah Juju ba haka bane,
tayi maganar a shagwab'e,
Juju tace " idan ba haka bane to yaya ne?


Khulud tace " Allah ni ban san cigaba da karatun ne kawai,
ni kwata-kwata ban tab'a sha'awar yin karatun boko mai zurfi ba,
Juju zata kuma yin magana,
Didi yayi saurin cewa " haka ne ai kowanne mutum yana da nashi ra'ayin,
hakan ma da kikayi dai-dai ne dabaki yaudare iyayenki kin shiga jami'ar ba,
kana kik'i yin karatun ko wata matsala ta faru,
so ni ina ganin kinyiwa kanki da Abbunki adalci,
Allah ya zab'a maku abinda yafi alkhairi a rayuwarku,
ya haskaka rayuwarku ya sanya albarka acikinta,
duk suka amsa da Amin,
fita sukayi suka nufi wajen da aka tanada dan yin walimar da tuni k'awayensu sun fara zuwa,
sosai walima ta kankama haik'an,
aka ci aka sha sosai dan sosai Abbu ya saki bakin aljihunsa dan nuna tsantsar farin cikinsa na kammala karatun yaransa lafiya,
sosai aka rarraba kyaututtuka,
kana kowa ya watse cikin farin ciki aka gama walimar lafiya.


Sannu a hankali matsanannaciyar soyayyar Khulud tayi mugun kama Hanash,
ta addabi ruhi da gangar jikinsa,
kwata-kwata ya rasa sukuni da walwalarsa,
ya rame sosai dan raban dayaci ishashshen abinci ko ya samun bacci har ya manta,
kullum yana cikin bedroom ko parlor'nsa,
dan ko fituwa sosai ya dainayi sai dai ya fito ya gaida iyayshi ya koma,
yauma kamar kullum kwance yake a d'akinsa ya tsunduma duniyar tunaninta,
idanshi rufe babu abinda yake gani sai ita tsaye a gabansa,
tana sakar mishi k'ayataccen murmushinta,
jin knocking yasa shi bud'e shu'uman idanuwansa,
k'ofar ya zubawa ido na tsayin lokaci,
batare da yayi wani yunk'uri ba,
sake knocking akayi a karo na biyu,
dakyar ya iya cewa " waye?


Muryar Papu yaji yace " mu ne,
dan sun kasa jurewa ganinsa cikin wannan mawuyacin yanayin,
da sauri ya mik'e ya bud'e musu k'ofar suka shigo,
akan sofa duk suka zauna, a hankali Mimmee ta d'ora hannunta akan kafad'arsa,
had'i da zubawa d'an nata ido,
Papu ma ya zauna kusa dashi ya zuba masa ido,
kansa ya duk'ar dan ya san kwanan zancen,
muddin akace bashi da lafiya ko yana cikin damuwa to gaba d'aya gidan babu mai yin walwala,
a hankali Papu ma ya d'ora hannunsa akansa kana ya kira sunansa,
" Hanash,
"na'am, Hanash ya amsa cikin ladabi,
" meke damunka?


Cewar Papu a tak'aice,
murmushin k'arfin hali Hanash yayi kana yace " babu abinda ke damuna Papu,
yayi maganar while kanshi k'asa,
Mimmee ta shafa kansa kana tace " Hanash please karka b'oye mana abinda yake damunka,
ka daure ka sanar damu koda babu wani abu da zamu iya yi akai,
sai mu tayaka da addu'a,
ta fad'a cikin damuwa,
murmushi Hanash ya kuma yi kana yace " ba ni da lafiya ne,
Mimmee zazzab'i da ciwon kai ke


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login