Showing 207001 words to 210000 words out of 382522 words
Innaro kuwa dai saita hau tsiya dataji labarin su Munaya kowa mijinta ya d'auketa zuwa gidanta, tahau zazzaga masifa anmata ba daidaiba, babu Wanda ya kulata, dan masu zugatan suma hassada ta ishesu, basuda kuzarin taya 6era 6ari😂..
Haka tagama jarabarta takoma gida tana huci, Abba yasha dariya, danshi lamarin mahaifiyar tasu yanzu kallon rikicin tsufa kawai yake masa, inba rikicin tsufaba miye abin tada jijiyar wuya anan? Sunada damar hana yaran komawa gidajen mazajen sune?.
Shikam baba k'arami ma lokacin da take jarabar zuwa yay ya ra6a ta gefenta ya fice daga gidan.
Ai lamarin innaro sai ita🤣🤦🏻♀.
******************
A 6angaren Munubiya ma Alhmdllh, dukkan wata kulawa mama rabi'a tana tsaye akan 'yarta da jikokinta, sai zuba mata gata akeyi da k'yak'yk'yawar kulawa mai ban sha'awa.
Suruka ta gari dadi alkur'an💃🏻💃🏻😘😘.
★★★★★★★★★★★★
Mom dai da k'yar suka lalla6a Munaya itada Aunty Mimi ta amince ta shayar da yaran, suna sha tana kukan zafi kuma😹, sunsan zataji zafi tunda Na farkone, ga yaran a buk'ace suke dama, amma kukan datake yawuce Na zafi kad'ai, (basusan harda haushi Galadima bane😂🤭).
Mom data fahimci hakan saita fara lallashin da nuna mata muhimmanci hak'uri, su maza komai zasu iyayi akan y'ay'ansu, musamman ma shi da yake tsaka da d'okinsu yanzu, karma tabari irin wad'annam abubuwan su dameta, shima yafad'ane kawai amma zai sayo madaran”.
Itadai Munaya kai kawai take d'agawa amma batace uffanba, dan tagama Sanin Galadima da halinsa Na kafiyar tsiya da dagiya akan ra'ayinsa.
Bayan duk sunsha sun k'oshi Aunty Mimi tace ta kwanta ta huta kafin time d'in walimar yayi. ALLAH ya taimaketa maganin yasata barci kuwa, yaran Na gefenta suma suna nasu barcin, kowa cikinsa ya cika kenan😘.
Ajiyar zuciya Aunty Mimi ta sauke tana murmushi, tace, “Mom d'an nan naki bazai canja ba dai ashe? lamarin Sameer saishi wlhy, koda bayaso susha madarar saiya fad'a da harshe mai dad'i ba fad'aba”.
“Humm, kibari kawai, nifa harna fara murnar ya canja, Ashe yana nan yanda nasan kayana, yarinyar tanada hak'uri kuma wlhy, dan zama da mai halin Sameer saika daure, muma iyayen idan mun k'ureshi ba iya mana kawaici yakeba”.
Aunty Mimi tayi dariya, “papi ne mai tankwarashi kobai soba ai, idan yak'i bari abasu madaran dashi kawai za'a had'ashi, komin wadatar nono shayar da yara uku ba sauk'i ne dashiba, balle ita farin Shiga ma”..
Mom tace, “hakanma shine kawai mafita ai”.
***************************
*_8:15pm_*
Liyafar cin abinci tafara gudana a babban d'akin taro Na masarautar gagara badau, Munaya da y'an uku duk sunsha k'yau, hakama uban gayya Baban y'an uku Galadima, duk d'insu sunci kwalliyane cikin ainahin kayan sarauta, yaranma an nad'esu cikin k'ananun alk'yabbu. (Gado kenan🥰)
Kwai da kwarkwata Na gidan nan zaka sameshi a wajen, saidai marasa lafiya da wad'anda basa nan, mai martaba ma yana wajen, dan shine da Kansa ya shirya liyafar domin taya d'ansa murnar k'aruwa da kar6ar bak'uncin jarirai, yaran duk suna kusa dashi cikin d'an gadon da aka ajiyesu a ciki.
Kowa anan yake zuwa ya lek'asu, yamusu addu'a.
Yara sunsha addu'oi da k'yaututtuka ga iyaye da kakanni, abin zakkyau da birgewa.
Ita kanta Munaya tasha nata k'yautar.
( k'yauta da bajinta kan saka zama isashe a gidan sarauta, wannan babbar al'adace tamasu mulki a masarautun k'asar hausa, shiyyasa suke ado da ita akowanne motsinsu🤩👍🏻).
Tsakanin Munaya da Galadima babu uhum babu um-um, sai y'ar wullama juna harara (🤣nifa dariya suke ban), banga abin jin haushin junaba, duk da Na lura ita dama Munaya akwai haushi kaine ka jamin shan wahala😂, kaikuma Galadima k'asaita da jinkai ya sa kakasa fahimta balle kayi lallashi da kwantar dakai aji da y'an jariranka🤣.
To maji dai maga yanda za'a kwashe😹.
Sai 11 dai-dai taro ya tashi lafiya kowa ya kama gabansa.
Shirin kwanciya Munaya tayi, suma yaran aka musu, saiga Galadima ya shigo cikin tasa shirin kwanciyar shima, mom tace, “yauwa Sameer ya za'ayi kwanciyar kenan? A falo zaka kwanta saboda tsaro ko?”.
Murmushi Galadima yayi yana shafa kansa, yace, “kai Mom wai saboda tsaro”.
“ALLAH kuwa Sameer, lamarinne yanada ban tsoro ai, dukda nasan ga dogarainan suma suna aikinsu, gakuma mu kammu, amma dole saida namiji a kusa, da canai shima Nuren ya dawo nan Ku had'u”.
“mom kincika tsoro gaskiya, karki damu, ko ina Na sashennan akwai CCTV camera, kuma koyaya aka ta6a k'ofa ko windows akwai securitys a jiki zanji insha ALLAH”.
“To shikenan Alhmdllh, ALLAH yak'ara tsaremu da tsarewarsa”.
Galadima ya amsa da “amin” yana matsawa jikin gadon wajen yaran.
Munaya dake saurarensu a ranta tace to ALLAH ya k'yauta, a gidanka kana zama saida tsaro inaga kafita?, amma jibarsu a awajen walimarnan kaikace kowa zuciyarsa fes take babu wani k'udiri, lamarin sarauta sai ALLAH, kaita buri tamkar ALLAH yamaka alk'awarin dawwama a cikin duniyar ne, bazaka mutuba bazaka tsufa ba, ALLAH ka iya mana da iyawarka, da ace inada dama saina cirema yaranan burin sarauta a ransu, amma ya zanyi, tarigada ta zama jininsu sai dai addu'a kawai....... Saukar numfashin dataji a gefen wuyanta ya sakata saurin dawowa daga tunanin data tafi, ta waigo da sauri sai taga Galadima.
Fuska ta had'e shima yaci serious yana gyara zama.
Waige-waige ta fara saitaga babu kowa a d'akin, ashe Mom ta fita.
Baki ya ta6e ya nuna mata k'ofar bayi da d'an yatsa alamar mom tana ciki kenan.
Cikin zaro ido ta kalli yanda yazo yawani shige mata, saitaja baya, ai da kunya dai mom ta fito ta gansu a haka wlhy.
Yanda tayi d'in sai yaso bashi dariya, amma saiya had'iye, ya ciji lips nashi yana kallon yaransa, “tunanin mikikeyi ne? kinsan dai doctor tace jininki har yanzu bai gama sauka ba gaba d'aya, so ki kula, shi tunani baya kawo mafita sai matsala”. ya k'are maganar yana mik'ewa tsaye, itadai kallonsa kawai takeyi, bata ankaraba taji saukar tagwayen kisses a goshinta da kan bakinta.
Idanu ta ware waje baki bud'e, ko kallonta bai sakeyiba ya fice abinsa yana murmushi.
Mom data fito daga bayin ta girgiza kai kawai, don ganinda Galadima yamatane ya sakashi ficewa.
Kallon Munaya tayi tace, “to rufe bakin kema”.
Kunya ta kama Munaya taja bargo tarufe har fuskarta tana fad'in ka kasheni wlhy yalla6ai.
A falonsa ya iske Nuren haryayi shirin barci shima, yana zaune yana shan tea da laptop a gabansa yana aiki, Galadima ya zauna yana sauke numfashi.............✍🏻
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏼_*l
*_typing📲_*
💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._*
*_♦RAINA KAMA.....!!♦_*
_(Kaga gayya)_
*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*
~Book 2~ 👉🏻2⃣4⃣
.............Kallonsa Nuren yayi da y'ar dariya, “angon jego ai dole kake sauke numfashi, irin wannan aiki dakayi haka? Y'ay'a uku fa a lokaci d'aya, a fuska dai kamar bazaka iya komaib.....”
Nuren bai samu k'arasawa ba saboda filon kujera d'aya daki bakinsa, wanda Galadima ya jefa masa.
Dafe baki Nuren yayi yana kallonsa cikin 6ata fuska.
Galadima ya cije lips yana fad'in “cigaba mana parrot ”.
Nuren ya cire hannun yana kwafa da jinjina kai, alamar zan kamaka ne.
Galadima ya ta6e baki yana hararsa, “yaro aini yanzu na daina halin yara, sai dai kayi da wani kuma”.
Dariya Nuren ya kwashe da shi, “o manya o manya, ai yakamata ma mai martaba yay murabus yabaka kujera kawai, kainefa Wanda kafara kafa tarihi a masarautar nan, Sarki Salisu barde shi yak'in filin daga yaje ya samo sunan gagara badau, kaikuwa yak'in kashe arna kaje kasamo sarakunan gagara badau”.
Girgiza kai kawai Galadima yayi yana fad'in “kai dai d'an iskane wlhy, yakamata papi sumaka aure kodan y'ay'an mutane su samu lafiya ma”.
“ni wlhy dama zakaje kace amin auren daka taimakeni”. Nuren ya fad'a cikin ta6e baki da d'aga kafad'a.
Murmushi Galadima yayi yana gyara zama, “ALLAH ya shiryeka to, mike tafiya akan al'amura?”.
Zama Nuren ya gyara yana komawa serious, “wlhy d'an uwa abubuwannan sun cika tsauri da yawa, a duka mutanen nan uku da yarinyarnan ta fad'a da gaske fa babu SD, amma ga pictures d'in wajen mutum 30 ka nunama Mumcyn Triple's ko zata ganeshi a cikinsu. dukansu yaransu tanderu ne, Sannan nifa inaga lokaci yayi da zaka binciki Muftahu face to face, dan lamarinsa yafara birkitan tunani gaskiya”.
“kafad'i gaskiya Nuren, nima kuma ina tunanin hakan shine mafita, dan ni kaina lamarin nasa yafara kaini ga dogon nazari”.
“To ALLAH yasa muji alkairi”.
“amin dai”. Galadima yafad'a yana mik'ewa, “nifa na shige zan kwanta, ka kwana lafiya”.
“ok ALLAH ya tashemu lafiya gwauro”.
Galadima yay dariya, batareda ya juyoba yace, “duk lalacewar goma dai tafi biyar albarka tuzuru”.
Nuren ya kwashe da dariya, yana fad'in, “oho dai, muma mun kusa zama gomar”.
★★★★★★★★★★★★
Zumid'i ya hana Momma komai, ta k'agara Abie yafarka yasha kanu, hakama su Samha su dawo school suji babban labari.
Ana cikin haka saiga Sauban tamkar an jehoshi, babu kunya ya rungume Momma yana fad'in “wayyo dad'i Momma y'ay'a uku fa wlhy, kuma dai-dai da ranar haihuwar Yaa Sam, dan yau birthday d'insa wlhy, ciwon aunty gimbiya ya mantar dashi”.
Itama rungumeshi tayi cikeda farin ciki, “hakane wlhy my love, yau ina cikin farinci mai tarin yawa, tarihi ya maimaita kansa da wani sabon salo mai banmamaki”.
“Wlhy nima haka Momma, kallafa pictures d'in babies d'inmu”.
Dukda tagani itama bata katse masa hanzariba ta kar6a wayarsa tana kuma kallo, harda na Munubiya.
Momma tace, “kai yau innarsu yazataji, jikoki 5 a lokaci d'aya, baiwar ALLAH, dama mahak'urci mawadacine, tayi kukan shekaru masu yawa ga lokacin dariya kuma yayi”.
“wlhy kuwa momma, nakira Yaa Sam batajeba”.
“Ai yama manta wayoyinsa a nan, kasan sun tafi hankalinsa ba kwance ba, nima da wayar Muftahu mukayi wayar”.
“wayyo Momma dan ALLAH kicema Yaa Sam mutafi gobe, wlhy kamar nayi tsuntsuwa na ganni a 9ja nakeji”.
Dariya Momma tayi, tarasa inda zata saka kanta dan dad'i.
Motsin da Abie ya farane yasakasu maida hankali garesa, idonsa ya bud'e ahankali a kansu. ganinsu tsaye kansa sunata murmushi saiya ma Momma alama da ido wai miya faru?.
Da sauri Sauban ya rungumesa yana fad'in “Albishirinka Abie d'inmu, matar Yaa Sam y'ay'a uku ta haifa”.
Ba k'aramin shock bane ya kama Abie, ya kalli momma alamar da gaske?.
Kanta ta jinjina masa tana murmushi.
Wasu hawayen dad'ine suka gangaro a kumatunsa, fuskarsa d'auke da k'ayataccen murmushi, A hankali yaketa jero Alhmdllh. Yace, “Mafarkina na shekaru da yawa yazama gaskiya Zeenah, tabbas ubangiji shine masanin gaibu, ya ALLAH na gode maka, godiya marar yankewa balle gajiyawa”.
A hankali yake maganar Amma su Momma naji saboda sun matsar da kunuwansu.
Dad'i duk yakuma lullu6esu, Abie yakuma fad'in “Zeenah wannan yarinya ta zama alkairi ga Ahalinmu, ALLAH ya albarkaci rayuwarta da abinda ta Haifa daku ma gaba d'aya”.
Sauban da Momma suka amsa da amin.
Yace a kira masa Galadima.
A time d'in sunta neman Number Mom amma bata wuceba saboda Network, hakama ta Nuren da Muftahu, daga k'arshe dai sun hak'ura ne sai wani lokacin a sake gwadawa.
Yau dai kam har doctor's d'in Abie sun shaida yana cikin farinciki, dan jikinsa ma ya nuna haka, k'arfin muryarsa ya k'aru, hakama bugun zuciyarsa dawasu yankunan halittun jiki dake bama d'an adam garkuwa, sun tabbatar a kowanne lokaci ALLAH zai iya gwada ikonsa ga wannan bawa, bayan tsawon shekaru daya d'auka a kwance sai an juyashi.
Wannan albishir ya k'ara yalwata farin cikin wannan ahali, saima dasu Samha suka iso, duk sun rikice da ihun murna, yau d'in ta dabance a ransu.
Isowarsu ce ta tunama Galadima da ranar haihuwarsa dai-dai da haihuwar yaransa, kuma dai-dai da haihuwar su Munaya ma😳😜.
Wannan abin al'ajab da yawa yake, ita kanta munaya sai lokacin ta tuna, wayar Ayusher ta kar6a ta kira Munubiya tana mata tuni da ranar haihuwarsu. dad'i ya kama Munubiya ma, dan itama ta shafa'a, sai murna kan murna ta k'aru🤸🏻♀.
**************************
Uban gayya dai Galadima da k'yar barci 6arawo yake sace sa a kowace rana, daya rimtse ido 'y'ay'an sa kawai yake hangowa, badan kar aga rashin hak'urinsa ba shikam da dasu zai ringa kwana.
O baban zumud'i😘😘😽.
A 6angaren yalla6iya ma hakane takan kasance, da taga laraba tayi barci dash Ayusher da Samha, (dayake itace take kwana dasu) saita tashi ta dinga d'aukarsu d'ai-d'ai tana runguma da musu addu'oi, jitake kamar ta had'iye kayanta ta huta kawai, takan dad'e tana Abu d'aya kafin barci yaci k'arfinta take kwantawa.
Tosu yalla6iya anaso ana kaiwa kasuwa😂😜.
*************************
Fad'a muku yanda abubuwa suka cigaba da kasance ga y'an barka ai 6ata lokacine ma, dangin Munaya ma sun taka rawar gani, Ayusher ma dai ta dawo nan zata zauna har ayi suna, hakama madam Innaro Galadima da kansa yaje ya kwasota🤣😜, aiko baki har kunne.
Gaskiya fans sannunku da k'ok'ari, irin wannan tururwa haka, lallai kunma Galadima halacci shida yalla6iya, ALLAH ya saka muku da alkairi dai my sweetness🥰🥰🥰😘😘😘😘❤🤝🏻.
Dole Galadima ya nemi waya da sim card ya lalubo su Abie da Momma d'insa da jakadiya dabasu samu zuwaba, suna shan hira a kullum shida su Abie ta video call, ga jarirai aita jera musu sunata shan kallo abin birgewa, Abie jiyake kamar yay tsuntsuwa ya gansa a 9ja, tsakanin nan yana cike da kewar k'asarsa ta haihuwa, yana fatan yakuma takata ko sau d'ayane kafin yabar duniya.
“Insha ALLAH zaka taka da yawa Abie😭”.
Mu tafi ran suna kawai😨⛹🏻♀⛹🏻♀.
Abubuwa da yawa sun faru a kwanakin bakwai d'innan, sai dai Alhmdllh bamasu tayar da hankali bane, dan jinjirai suna cikin k'oshin lafiya da kariyar ubangiji.
Samha dai konan dacan bata matsawa, duk wani motsinta nakan yaranan, tazama bodyguard d'insu itada Ayusher da hajiya innaro, dan itamafa ta kafa ta tsare🤣.
Mama Fulani dai ta danne zuciyarta tazo har sashen Galadima taga babies, harma suka samu k'yauta mai tsoka daga gareta.
Ana gobe suna masarautar gagara badaufa tayi dank'am da jama'a, dan bikin suna na ban mamaki Sarki ya shirya, abin ba'a cewa komai. Inno ma dai wannan karon ba'a barta a baya ba, tazo masarautar su sunan tatta6a kunnenta, kuma 6angaren mama Fulani ta sauka😳😜.
Koba komai zata kafa zata tsare, takuma raka ta jira🤸🏻♀😂 mana ga Mama Fulani.
Harun da baya k'asar yayi tafiya a fannin aikinsa yau ya diro a Daren suna cikin masarautar, dama tun yana can labari yagama Isar masa Galadima ya samu y'an uku, Muftahu da kansa ya kirashi ya Sanar masa haihuwar, Yakuma tura masa hoton babies😽🤥
*****************
Wajen 8pm Galadima suka dawo daga masallaci sallar isha'i, shikad'ai ya shige falonsa, dan yana son magana da Munaya, gaba d'aya yinin yau tun safe daya Shiga bai samu komawa wajensu ba saboda hidimomi sun masa yawa.
Ayusher ya kira, dan itama Munaya batazo da waya ba, lokacin da su Sauban zasu taho kuma basusan inda ta saka layinta Na Nigeria ba, sai sukaga babu amfanin d'akko wayarma.