Showing 114001 words to 117000 words out of 382522 words

Chapter 39 - Raina Kama 1 And 2 Hausa Novel Complete

03 Jan 2025

3709

10 kafin yamik'e yashiga bathroom, kusan 1hour sannan yafito maybe su yalla6ai an sauke nauyine (🚽🤭).


Yau saida na jirasa harya idar da shafa'i da wutirinsa, dan magana nakeson muyi, ganin ya idar ya zauna latsa wayane nace “dan ALLAH yalla6ai in tambayeka?”.
Batareda ya d'agoba yace “uhmm”.
Zamana na gyara cikin nutsuwa nace, “shin tunda Abie yafara jiyya anta6a masa maganin gargajiya ko amaida hankali ga addu'oi haka?”.
Yanzun kam d'ago ido yayi ya kalleni, dama tunda nafara maganar ya dakata daga latsa wayar.
“lips d'insa yad'an cije, kamar zaiyi magana saikuma yay shiru.
Nace “kayi hak'uri idan nashiga hurumin daba nawaba”.
Nanma shiru yamin, saida yaja wasu mintuna kafin ya ajiye wayar yagyara zamansa, cikin alamun bak'in ciki yace, “duk an gwada masa, saidai gaskiya bakamar yanda aka maida hankali gana asibitinba, saboda anriga da an sanar mana Allurar gubace aka masa, amma muna k'ok'arin sakashi a sallalolinmu na farilla dana nafila. Kullum addu'oinmu akansa yake”.
Ajiyar zuciya na sauke, nace “ALLAH yabashi lafiya, yakawo mana iyaka, yakuma bashi ikon cinye jarabawar nan”.
“amin yafad'a a la66ansa”.

Dagani harshi babu Wanda yasake magana har muka kwanta, saidai yauma banyi isashen barciba, inata cud'awa da kwancewa, har gabannin asubahi kafin barcin ya saceni..................✍🏼



_To Alhmddlh my sweet fans, zamu dakata anan kenan, saikuma ALLAH yakaimu bayan salla darai da lafiya, zanbar wannan a matsayin *RAINA KAMA..... PART ONE* yanda zamu tafi a tsare kawai, basai mundawo ba kuma mushiga tunanin inama aka tsaya? Ina kuma za'a tashi, a *RAINA KAMA PART TWO* zamuga yanda Munaya zata taimaki Galadima kamar yanda Momma ta buk'ata, shin zai bata had'in kaima Kuwa? domin kunji Momma dai tace bashida yarda? ya matsayin auren Zarah? Muftahu yaya zata kasance idan Galadima ya cafkoshi? shin Munaya tanada wani fikra ne game da ciwon Abie?. wannan amsoshin duk suna cikin *RAINA KAMA PART TWO* da zaizo bayan sallah insha ALLAHU my guys, one Luv😍😍😍😘😘😘🥰👌🏻_

_tabbas banida bakin godiya a gareku, saboda addu'oi da mahaifina ke samu agareku, Comments naku suna matuk'ar sakani a farinciki sosai, ngd ALLAH yabar zuminci, duk inda masoyin wannan buk yake yasaka aransa yana can k'ark'ashin zuciyar Bilyn Abdull.🥰🥰🥰🥰😍😍😍😍😘😘😘😘😘😘😘👌🏻🤝🏻._


_ga azumi zamu shiga, 'yan uwana dan ALLAH mu maida hankalinmu ga ibada, sadaka da k'autatama marasa k'arfi, marayu,, k'autata mu'amullarmu da jama'a dayin amfani da abinda malamai zasu fad'akar damu, karya zam kullum muna wahalar zuwa tafseer amma bamu d'aukar komai, da bayan salla yawuce munkuma koma kan munanan ayukanmu, karmu manta irin wannan watan saikuma mai rabon gani, sau 1 tak yake zuwa mana akowacce shekara, wani yawuce agaresa kenan har Abadan, zata iya yuwuwa nice ma😭, zata iya yuwa kece 'Yar uwa👉🏻😭, zata iya yuwa kaine d'an uwa👉🏻😭. dan ALLAH mu gyara please & please, muyi amfani da damarmu kafin ta kufce mana, (kullu nafsin za'ikatul maut, kowane rai saiya d'and'ani mutuwa, ubangiji bai turo maka date d'in da rundunar mala'iku zasuzo d'aukar rayin nakaba,😭 mutuwa bata kwankwasa k'ofa, batada wata alamar yanda zatazo ta riskeka, kana tafiya ne, ko kana barci, ko kana salla, ko zaune, ko kana hira, ko kana aikata wani sa6o, ko kana wani abin alkairi😭, ya ALLAH ka d'auki ruhinmu muna masu imani agareka da tsoranka, ALLAH ka gafarta mana, kamana maganin abinda muka Sani da wandama bamu saniba._
_ina rok'on dukkan Wanda na 6atamawa a yayin wannan rubutun ko kafin shima dan ALLAH Ya gafarceni, nidai na yafema kowa._😢👏🏻

*_duk masoyina na gaskiya Dan ALLAH inason yasakani a ddu'arsa ta cikin azuminnan koda sau d'ayane, idan munada Rabon haihuwa adunaya nida mijina ALLAH ka azurtamu da samu masu albarka cikin sauk'i da rahamar ubangijin talikai, idan ba alkairi bace agaremu ALLAH kasamana hak'uri da juriyar azuciyata😭👏🏻, ALLAH kayaye mana dukkan damuwarmu baki d'aya._*😭👏🏻
Dan ALLAH ko sau 1 yane kar'a manta dani🙏🏻😊



Amin afuwa zan rage groups saboda yawan groups d'in suna cimin data wlhy, idan nayi sub na wata d'aya ko sati bata yimin take k'arewa🙏🏻.
Ngd sosai, ALLAH yabar zuminci, ALLAH yasa munada rabon sake had'uwa a bayan salla, ALLAH ka kar6i ibadunmu baki d'aya. yabamu juriya da hak'urin ibadar dake tunkaromu nanda kwana 1👌🏻.


Happy Ramadan Advance😊🥰🥰🥰🥰😍😍😍👍🏻




Binyn Ku Ce dai👌🏻

Writer✍🏼
*Abdul-maleek bobo!!*
*Auren k'addara ko biyayya!?*
*Ban saketa ba!!*
*Ciki da gaskiya...!!*
*Karayar arzeek'i!!*
*k'anwar uwace ko kishiyar uwa!?*
*Kukan krciya...!!*
*Ni da Aminiyata!!*
*Nawaff!!*
*Rashin Sani!!*
*Raina kama.....!!*
*Sabon Al-amaree!!*
*Sanadin bikin salla!!*
*Siyasa ko k'abilanci!?*






*_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*😭👏🏻
*_Typing📲_*



*_Haske writer's asso...._*💡




*_♦RAINA KAMA......♦_*
_{Kaga gayya}_




*_Bilyn Abdull Ce_*🤙🏻

____________________________

*_Dolene page d'in farko yazama sadaukarwa agareki MAMAN JUNIOR😭, ALLAH ya gafarta miki, ya raya abinda kika bari, ALLAH ya k'addara bazakiga k'arshen wannan littafiba. (Masoyan Raina kama kusaka wannan baiwa a addu'arku, ta rasu cikin azumi, kusanma k'arshe, member ce a group d'in raina kama, ALLAY ya yafe mata🙏🏻😭._*


_INA fata kunyi salla lafiya gaba d'ayanku, ALLAH ya kar6i ibadunmu. Ya yafe mana, yasa kar6a66iyar ibada mukayi🙏🏻😭._
Sai dai banci naman salla ba sosai, gashi banida d'inkin dallah🤦🏻‍♀🤥.

______________________________


~Book 2~ 👉🏻1⃣


.............Tunda mukayi maganar nan dashi banyi k'asa a gyuwa ba wajen dagewa da addu'oi wa mahaifinsa, ina buk'atar ruwan zam-zam, dan haka yau nashirya fad'a masa ya nemomin. tunda safe ya fice, dan haka bamuga juna ba.
Yauma dai haka Na tashi banida wata isashshiyar lafiya, Na tak'ark'ara nayi gyaran d'akin har zuwa falo, sannan Na had'a ruwa mai zafi nayi wanka dashi.
Ina cikin shiri najiyo sallamar Samha a k'ofar falon, rigar dana fara sakawa Na k'arasa, sannan nace ta shigo.
“humm Aunty gimbiya kina kallon kanki a mirror kuwa?”.
Cikeda mamaki Na kalleta sannan Na kalli jikina, nace, “kamarya?”.
Zama tayi a sofa tana 'yar dariya, sannan tace, “wlhy kinyi k'iba, sati uku kacal da zuwanmu India kin koma wata madam”.
Nad'an fiddo idanu waje, sannan Na harareta, “lallai Samha nagode da zagi to”.
“tab wlhy babu wani zagi gaskiya Na fad'a, halan Uncle Sam bai ta6a fad'a mi ki ba........”
Ta k'arasa Maganarta da d'ai-d'ai saboda shigowarasa d'akin da sallama ciki-ciki.
Suna had'a idanu ya watsa mata harara, hakan ya tabbatar mana da yaji maganar tata, da sauri tamik'e ta fita, Nikuma najawo gyalena na yafa sannan Na kallesa.
Saman sofar ya zauna ya dafe kai, kallo d'aya zaka masa ka karanci damuwar dake shimfid'e bisa fuskarsa.
“yalla6ai lafiya kuwa?”. ‘nafad'a cikin tausayawa’.
Shiru bai amsaniba, banyi zuciyaba nataka a hankali zuwa gabansa, durk'usawa nayi a gaban nasa, a d'arare nasa hannu Na najanye nasa dayay tagumi dashi.
Ya d'ago idanunsa da sukai jaa yana kallona. kasa jurar kallon cikin idonsa nayi, Na janye nawa gefe, cikin dakiyar zuciya nakuma fad'in “bakada lafiya yalla6ai?”.
Yanda nayi maganar a marairaice saiyaji yakamata ya fad'amin, kodan nuna damuwar danayi akansa......
Ganin yamin shiru nikuma saina yink'ura natashi ina fad'in “kayi hak'uri idan nashiga hurumin daba nawab......”
Bankai k'arshen maganarba naji tattausan tafin hannunsa cikin nawa.
Rintse idanuna nayi, saboda wani yarrr da tsigar jikina tayi, shima agaresa saiya lumshe idanu kawai. najuyo danufin zare hannun kawai ya fisgoni na fad'a saman kujerar, rabin jikinna duk yana a jikinsa, yayinda sauran rabin nake a kan kujera.
Bansan nawani lumshe idanuba saboda daddad'an k'amshin turarensa d'aya ratsa hancina zuwa magudanar jinina. shikuma ya sauk'e 6oyayyiyar ajiyar zuciya.
Ya karkato da fuskarsa inda tawa take a gefen kafad'arsa har inajin saukar numfashinsa saman face d'ina, mayun idanun nan nasa suka kuma shiga cikin nawa, na janye da sauri, sannan nafara k'ok'arin cire kannawa daga kafad'arsa.
Hannunsa na dama da nake jiki ya sak'alo ta bayana, ya maida kai na ya kwantar a kafad'ar tasa, cikin muryarnan tasa mai kama da anmasa tilas yace, “jikin Abie ne ya motsa, Ashe tun jiya basuyi barciba gaba d'aya, da safennan Akash yakirani yake sanarmin, nakasa kallon halin da mahaifina yake ciki Munaaya! Abie na yana cikin mawuyacin hali..” ‘yak'are maganar cikin zirarowar kwallar data cika masa idanu tunda yafara maganar’.
Wani matsanancin tausayinsa ne ya ratsani, duk jarumtar Galadima kaga yana kuka ai kasan lamari ya 6aci gaskiya, nima hawayen suka fara gudun fanfalak'e a kumatuna, tashi nayi zaune sosai, cikin wata jarumtar da bansan inada itaba nasaka hannu Na kamo hannunsa cikin nawa. Sai kawai naga ya zame sosai ya kwantar da Kansa bisa cinyata, tareda hard'e hannayensa a k'irji. duk da kujerar tama tsawonsa kad'an, dan ma Love's chair ce.
Kansa nafara shafawa a hankali, hawaye na zirara daga idona har yanzun.
Shikam idanunsa a lumshe suke.
Cikin tausasa harshe da tsantsar Nuna kulawa da tausayawa nace, “Yalla6ai kayi hak'uri, Abie d'inmu yana buk'ar addu'armu ne fiye da kukanmu, sannan itace jarabawarsa, wad'anda suka aikata masa hakan summa kansune, domin ALLAH bazai barsuba. idan ka amince akwai wasu addu'oi Dana Sani, Nina kakanmu ne yabama innarmu kafin yarasu, shine ta koya mana, mizai hana ka samo mana zam-zam muma mu farayima Abie su, Ubangiji gafurun rahimunne, babu abinda ya gagaresa, kuma shine yace mu rok'esa zai amsa mana”.
Tunda nafara maganar bai bud'e idonsa ba, nikuma ban fasa shafa masa kaiba. Saida nakai k'arshen zancen sannan ya bud'e lumsassun idanunsa dasuka koma launin jaa a kaina. yamotsa baki kamar zaiyi magana saikuma yayi shiru.
Nima shirun nayi ban sake yink'urin yin magana ba, nadai cigaba da shafa kan nasa a hankali. ba akai 3minutes ba barci ya d'aukesa, sai numfashinsa danaji yakoma sauka a hankali.
Ajiyar zuciya na sauke kawai, na tsurama fuskarsa ido, yaune ranar farko dana ta6a nutsuwa namasa kallon tsaff, sosai yake kamanni da dukkan iyayensa, Abie da Momma, amma yafi tsananin kama da Momma gsky, duniyar tunani nafad'a batare dana fargaba, tausayin Galadima da families nashi yana cukurkud'ar ruhina, insha ALLAH nayi alk'awarin bada gudun mawa a duniyarsu har zuwa lokacin da aurenmu zai k'are.
kaina na jingina da jikin kujera, nima sai barcin ya kwasheni, dama bajin dad'in jikina nakeyiba.


********

Bayan anma Abie allurar datake temaka masa yin barci mai nauyi idan jikinsa yamotsa irin haka su Momma suka sami nutsuwa, dan yayi barci.
Sai alokacin hankalin Momma yadawo kan Neman Galadima, tabbas taga yafita hankali a tashe lokacin da Abie ke fidda numfashi a wahale, amma hankalinta bai koma kan Galadiman ba.
Aunty Mimi ta kalla tace, “Mimi ina d'an uwanki?”.
Itama aunty Mimi sai yanzu hankalinta yadawo ta farga babu Galadima d'in, hankalinta a tashe tace, “Momma inagafa ya fita, bara na duba”.
Bata jira cewar Momma ba tafito daga d'akin da sauri. ganin babu Galadima a wajen hankalinta yak'ara tashi, fitowa tayi harabar asibitin tana tambayar securitys d'in wajen.
d'aya ya sanar mata ya fita a rikice gaskiya, dan suma sun nemi su taimaka masa amma baima tanka musuba.
Innalillahi tashiga ambata. Bata koma wajen Momma ba tashiga mota tanufo gidan.
Ta iske Samha a falo kwance, ko sauraren sannun datake mata batayiba tace, “k ina Uncle d'inku?”.
Samha tace, “yana sama Mummy”.
Da sassarfa ta haye step's d'in, itadai Samha da mamaki taringa binta da kallo.
Ko knocking bata tsaya musuba ta turo k'ofar ta shigo.
Ajiyar zuciya ta sauke dan ganin Galadima kwance, kansa bisa cinyar Munaya, hannunta d'aya na bisa Kansa, yayinda shikuma yarik'o d'ayan hannun munaya ya had'e da nasa ya d'ora kan kirjinsa, suduka barci ya kwashesu a haka. cikin sand'a ta juya ta fita taja musu k'ofar tana share hawaye dayima ALLAH godiya d'aya bama d'an uwanta mace tagari wadda take kulawa dashi. inda dane kafin yayi aure shima sai ciwonsa yatashi saboda damuwar dazai saka Kansa akan motsawar jikin Abie, amma gashi yanzun yasamu mai kwantar masa da hankali, suma kuma nasu ya kwanta suji da Abie kawai.
Momma ta kira ta fad'amawa dan hankalinta itama ya kwanta.
Momma harda hawayen farinciki, tana godema ALLAH.
Aunty Mimi bata zaunaba suka koma asibitin itada Samha da tace zata bita, itama sai yanzu takejin jikin Abie ya motsa.


*************

A k'alla munyi barcin 47minute's, Galadima ne yafara farkawa, ya bud'e idanunsa a hankali, hannuna dake rik'e a nasa yafara kallo, kafin yad'ago ido zuwa kaina, yamin kallo kusan na 2minutes sannan yad'an motsa da nufin gyara kwanciya, saina bud'e idona, ido muka had'a, kowa yay saurin janyewa cikin basarwa, hannuna dake kansa na cire, sannan nazame Wanda yarik'e d'in, dan wata matsananciyar kunya ce kuma takamani.
Shima sai ya tashi zaune sosai, a hankali yacemin “thanks”.
Daba kusa dashi nakeba ma bazanjiba. Bance komaiba, shima bai sake cewa komaiba yamik'e tsaye. takalmansa kawai yacire ya d'auki jallabiya a wardrobe d'insa yashige bayi.
A hankali na sauke ajiyar zuciya, tareda janye idona daga k'ofar bayin, komai banceba nakuma zamewa saman kujerar na kwanta.

Ya d'auki adadin wasu mintuna masu tsawo kafin yafito sanye da jallabiya ruwan toka, da alama wanka yayi, kallona yayi batareda yayi magana ba ya nunamin agogon dake ajiye a drowan gefen gadon alamar time d'in salla yayi.
Kaina kawai na girgiza na mik'e, zuciya ta na mamakin hali irinna Galadima.
Shikam turare kawai ya d'auka ya fesa yafice salla.



★★★ ((★))(())((★)) ★★★

A gidanmu kam hankalin mamansu yaa hameed da Zarah a tashe yake, dan babu Sa'eed babu labarinsa, kira Zarah tamasa yafi 50 amma yak'i d'agawa, ta tura massages babu reply, bata aikin komai sai kuka, ga ciki.
Abbanmu kuma jin sanadin sawowar tata gida yace bazai kira Alhaji halliru ba har sai Zarah tafad'i ainahin gaskiya, danshi bai yarda ba itace ta d'auki kud'inba..
Innarmu dai dasuke zagi suna kallonta mak'iyarsu batakai komaiba itace tashiga lalla6a Abba damasa magiya.
Itama da farko buris yay da ita, saida yaga tanace sannan yace, “wai kekam Ai'sha miyasa kika damu kankine? kinbi kin damu da lamarin wad'anda basu damu dakeba, na tabbatar da Munaya ko Munubiya ke cikin wannan halin su murna zasuyi a gidannan”.
Murmushi innarmu tayi, cikin kwantar da murya tace, “Alhaji ai daga Zarah harsu munubiya duk d'ayane a wajena, domin kaine mahaifin Zarah, dukkan abinda kuma yakasance naka ina kaunarsa fiye da zatonka, a duba lamarin yarinyar kodan abinda ke gabanta, ba'a son mace mai ciki da shiga tashin hankali, muyima tufk'ar hanci tun munada sauran dama, basai Abu yayi tsamariba kuma muce zamu nemo mafita, hannunka baya ru6ewa ka yanke kayar alhaji, dan ALLAH kayi hak'uri kaji”.
Jawota yayi jikinsa ya rungume yanamai saka mata albarka da aminta da buk'atarta na kiran senator halluru da safe insha ALLAH.
Innarmu tamasa godiya itama.


**********

“Babyna wai mike faruwane haka?”.
Da gyar Munubiya ta d'ago ido daga kwancen datake a kujera ta kalli yaa Marwan dake mata tambayar.
Ta shagwa6e fuska tace, “wlhy Yaya jikinne babu dad'i, kamar jiya sai kwankwatsa kasusuwane keyi”.
Zama yay kusada ita, yad'ago kanta ya jinginata a jikinsa yana ta6a wuyanta, “please ki yarda muje asibiti adubaki mana?”.
“a'a dan ALLAH Yaya, wlhy banason zuwa, kabari muga kwana biyu idan bai dainaba saimuje d'in”.
“Amma kuma k'ya zauna da ciwo, ki daure dai, kinga ko abinci kin kasa mana fa”.
“babu damuwa Yaya, yanzu zan tashi na d'ora, dan zazza6inma ya sauka ALLAH”.
“Ana dai so aima Yaya wayo kawai”.
Murmushi tayi tana tashi daga jikinsa,, takama hannunsa ta sumbata sannan tatashi tafice daga falon.
Binta kawai yay da kallo yana murmushi, yana k'aunar matarsa kuma 'Yar uwarsa, gaba d'aya Munubiya ta canjashi, dukda bawai miskilancinsa yabariba, itace kawai yanzu baya iyama miskilancin nasa, komai a d'auren da fuskarsa take da zarar ya tunkaro gida zakiga yafara sakin murmushi,


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login