Showing 63001 words to 66000 words out of 382522 words
damuna,
ido Mimmee ta zuba mishi tana nazarinsa dan ita kwata-kwata bata yarda da abinda yace ba,
Papu yace " kaje hospital?
Hanash yace " eh Papu,
"me sukace yana damunka?
Papu ya kuma tambayarsa,
d'an shiru Hanash yayi kafin yace " Malaria,
" to ikon Allah kai ko ina kaga sauron daya cije ka?
Mimmee ta fad'a tana kallan kwayar idansa,
murmushi yayi kana yace " Mimmee, cikin shagwab'a,
Papu yace " shi ciwo ai daga Allah ne, ba ta inda baya shiga jikin mutum ko son?
Yayi maganar cikin tsokana,
dan shima yadai ji Hanash ne kawai,
amma bai yarda da abinda ya fad'a ba,
babu yadda Papu da Mimmee basu yi akan Hanash ya sanar da su damuwarshi ba, amma yak'i yace babu abinda yake damunsa,
Papu yace " Allah ya sauwak'e,
ya amsa da " Amin, kana suka fita,
suna fita Hanash ya koma ya kwanta,
had'i da rufe idansa.
Ranar Monday jamb ta fito,
Sanah cikin murna da d'oki suka je ita da Aarib & Khulud suka duba,
a cafe, aiko taci sosai dan ta samu 251,
tsalle ta buga ta rumgume Khulud da Aarib cikin matsananciyar murna,
motar su nayin parking a harabar gidan ta fito,
ta shiga kwalawa Halan kira,
da gudu ta shiga part d'in Halan,
ta iske ta parlor zaune ita da Ziyad,
cikin murna ta fad'a kanta, ta ma manta da tsohon cikin dake jikin Halan,
Ziyad ya daka mata tsawa had'i da cewa " ke baki da hankali ne ko baki ganin abinda ke jikinta?
Bata kula da tsawar daya daka mata ba,
sai ma kiss datayi mishi a kumatu,
cikin murna tace " Yaya naci jamb,
ta fad'a tana tsalle,
dariya Halan tayi tace " kai masha Allah gaskiya nima nayi murna,
badan kayan dake gaba na ba,
da har dani za'ayi tsallan,
Ziyad yayi dariya yace " bani abu na inyaso sai kije kiyi tsallanki,
Halan ta kalleshi had'i da zumb'uro baki tace " Allah da ana bayarwa ai bama sai ka tambaya ba,
Sanah da Khulud suka fita da gudu suka nufi part d'in Mamu,
suna zuwa Sanah ta fad'a kan Abbu,
yace " kai Sanah ke dai baki girma,
naga alamar so kike ki karya ni tunda baki ganin na tsufa yanzu,
Sanah tayi mishi kiss tace " Abbu albishirinka,
yana dariya yace " goro,
tace " fari ko ja?
Yace " fari tass,
tace " Abbu na ci jamb,
Abbu yace " wai dole ayi murna,
Mamu tace " masha Allah,
saura waec & neco,
Abbu yace " suma duka za'a cinye su,
in sha Allah,
fita sukayi suka nufi part d'in Juju,
nan ma aka sanar mata anci jamb,
murna kam ba'a magana,
a week d'in waec ta fito,
Sanah ta samu result mai kyau,
result d'inta yayi mugun kyau,
bayan two weeks BUK ta kira su first UME,
bayan week nan ma result ya fito,
ta samu taci, suka bata Admission letter na BSC COMPUTER SCIENCE.
Kullum Hanash bashi da wani aiki sai mafarkin Khulud,
da tunaninta ko idansa ya rufe ita yake gani,
koyaya ya rufe idansa ita yake ya gani,
abun duniya duk ya dame shi,
ba shi da wani burin daya ce na sake ganinta a yanzu,
ko da sau d'aya ne a rayuwarsa.
Yau itace rana ta farko da Sanah zata fara hallartar BUK,
ta gama shirinta tsaf cikin riga da siket na material red color d'inkin yayi masifar yi mata kyau,
ya amshi jikinta sosai, ta saka high hill shoe ta yafa mayafinta mai kyau kalar flowers dake jikin material d'in black,
sosai Sanah tayi shegen kyau,
duk da ba wani make up tayi ba,
ta dayyi simple make up abinta,
wanda ya bayyanar da tsantsar kyauta,
har cikin makarantar Aarib ya kaita,
sai da yayi mata fad'a sosai kana ya tafi,
sannu a hankali take tafiya harta isa department d'insu,
tambaya tayi,
aka nuna mata, inda zasuyi lectures yau,
dayake tana da time table na duka courses & time d'in su,
a hannunta tasan Computer lectures zata fara attending,
zama tayi a inda taga students na zama,
zamanta ke da wuya ta fara jiyo hirar students,
" yau fa Sir Aryan ne damu,
kasan ko ba sauk'i, d'ayan yace " wallahi ko ni gaba na ma sai fad'uwa yake yi,
tun jiya dana duba naga shine damu hankali na yake a mugun tashe,
wani daga gefe yace " kai ai Malamin nan bai da kyau,
d'ayan yace " kaga fito sak a mutum kai tsaye kace bai da mutunci,
d'ayan yace " ni fa yana mugun ban mamaki shi ko irin na sauran lectures d'in nan bayyi,
d'aya yace " me?
" San mata mana,
d'ayan yace " kai tanan wajen ai Sir Aryan yayi wallahi,
ba ruwanshi da mata, duk kyanki yanzu zai yarfa ki,
ba kamar sauran lectures d'in ba,
shegu da sunga mata sai suyi ta rawar jiki,
idan mune 'yan uwansu maza tsakanimu dasu ba mutunci,
sai su rufe ido su karta mana,
amma shi kwata-kwata mace bata isheshi kallo ba,
naga 'yan mata dayawa sunyi mugun matuwa akansa,
d'ayan yace " aiya had'u ne ga kyau ga kud'i, kaga kuwa ai dole mata su matu,
tunda ready mate ne,
d'ayan yayi dariya yace " aiko suna shan dizgi da wulak'anci a wajensa ba,
dan yanzu zai kartawa mutum rashin m,
idan ta kama ma ya yarfa maka mari ba ruwanshi,
shege ga girman kai da d'agawa da jan aji dan sai kayi mishi magana goma amma dakyar idan yaga dama zai amsa maka d'aya ,
d'ayan yace " kai ai ya iya d'aukar wanka dacin uwar sutura,
yana zagin gizna ta asalimma,
ni na rasa uban me yake yi a makarantar wallahi,
"hmmmm ga babu ruwanshi da ke wai mace ce,
shi hukunci d'aya yake yi tsakanin mace da namiji,
idan ya riga ka shiga class ko waye ubanka kuma ko uban ya tsaya maka ya d'aure maka gindi baka shiga,
d'ayan ya duba agogo yace " sauran just 5 minutes ya shiga fa,
kusan kuma baya African time,
d'an tsaki Sanah tayi a hankali kana ta mik'e tabar gurin,
saboda duk gurin wajen mutum 100,
maganar mutum d'aya suke tayi Sir Aryan,
duk inda students sukayi d'an group,
maganar shi kawai sukeyi mata da maza,
daga maganar had'uwarsa kyansa, gayu, ajinsa,
sai ta wulak'anci da dizginsa da kuma girman kansa,
da yadda mata suka mato akansa yake wulak'antasu,
shiyasa duk randa yake da lectures dasu suke kaffa-kaffa.
Can gefe ta koma ita kad'ai ta zauna,
ita kad'ai kasancewar yaune farkon zuwanta bata san kowa ba,
tana daga zaune taga wata matsiyaciyar had'add'iyar mota ta danno kai cikin makarantar,
students na ganin motar suka kai duba zuwa number motar dan su tabbatar idan shi,
saboda baya hawa motar d'aya,
duk nacinka baka isa kace ga yawan motocinsa ba,
ta number motarsa kad'ai suke gane shi ne,
saboda sunan family d'in su ne a duka number motacinsa,,
ai students na tabbatarwa shine,
suka fara gudu maza da mata ana rige-rigen shiga class.
Yana yin parking, ya zare key d'in tare da komawa ya kishink'id'a jikin kujerar, ido ya lumshe tare da fesar da numfashi mai sanyi, a hankali ya kuma bud'e idon tare da sauk'e ajiyan zuciya, yana mai shak'ar k'amshin jikinsa dana mortar, a hankali ya sa hannun damanshi ya dafe saitin k'ahon zuciyarshi dan jin gabansa yana muguwar fad'uwa da k'arfi,
bugun zuciyarsa ya k'aru sosai,
zuciyarsa ta rink'a bugawa so past,
idansa ya kuma lumshe yana k'ara d'an kishingid'a akan kujerar motar,
a hankali ya furta " innalillahi wa'inna ilaihirraji'un,
saboda yadda yake jin
duk ilahirin jikinsa ya mutu, gabansa na mugun fad'uwa zuciyarsa na bugawa da tsananin k'arfi, addu'ar yayi ta maimaitawa dan baya son ayi mishi African time shiyasa shima baya son yayiwa d'alibanshi, bere daga inda yayi parking yana iya hango yadda suke sassarfan shiga class, sharshesa ya fitar tare da d'an laso lips nashi, hadi da d'an cizawa dan kauda kasalar dake saukar mai a jiki,
a hankali ya b'alle marfin motar tare da zuro k'afarshi d'aya woje, baki ya d'an tab'e ganin yadda wasu matasa suka wuceshi da sassarfa, gudun karya rigasu shiga class, ya hanasu shiga, fitowa daga cikin motar tare da jawo laptop nashi, ya bud'eta tare da dorata kan hannunshi daya mik'ar, yana kuma d'an lallatsashi cikin k'orewa, ajiyan zuciya ya sauk'e tare da fara takawa zuwa class d'in yana mai jin dad'in iskar dake busawa sirrai da fawowi suna shawagi tsuntsaye na kai komo ga k'amshin furanni dake ratsashi.
Cikin takunsa na isassun maza masu haiba da kamala ga tarin nagarta yake tafiya cap-cap sautin takalminshi ke ratsa wurin in dalibai sun hangoshi sai suna rusunawa tare da ratse mishi.
Ganin yadda students ke gudu yasa Sanah kai idanta kan motar dataga kamar an saka MOLI'S 15,
amma data duba so sai taga kamar ba haka bane,
baki tad'an tab'e kana ta mik'e cikin takunta mai daukar hankali tabi bayanshi,
ta nufi class itama,
daga bayansa ya rink'a jin kamar takun mutum a bayansa k'at-k'at,
Fuska ya kuma had'ewa dan ya gane mace ce, daga k'asa ya kalli k'afarta data sha kunshi mai ja da bak'in lalle yayi masifar yi mata kyau,
gabansa ne yayi muguwar fad'uwa lokacin daya d'ora idansa akan k'afarta, sake had'e rai yayi , kana ya cigaba da tafiya,
yana tafiya tana binsa a baya,
har suka zo gaf da isa class d'in,
Kai ya d'an jinjina tabbatarwa da yayi class d'in sa zata shiga , hankalin shi na kan laptop d'inshi, hannunshi mai yin typing d'in ya d'an d'aga shi saman kafadarshi ta yadda zata gani, sanan ya had'e doguwar yatsarsa ta tsakiya da babbar yatsarsa ya kettasu sau d'aya ta yadda ya bada sauti, sannan ya had'e yatsunsa biyu ya kad'asu kamar mai buga fiyano ya mata nuni data tsaya inda take karta biyoshi,
batare daya juyo ya kalle ta ba bai kuma tsayaba yaci gaba da takunshi zuwa cikin class,
Itako Sanah bata gane abinda yake nufi ba,
dan haka taci gaba da binsa a baya,
Kai ya jinjina tare da yin gutun murmushi, mai dauke da alamar zaki gane kurenki,
kana ya cigaba da tafiya har suka k'arasa cikin class d'in,
Sanah tazo zata wuce mazaunin d'aliban, *"Keeh"* kamar daga sama sautin muryarsa ya ratsa shirun daya ratsa ajin,sai sautin takalminta dake amsakuwa, shirune ya sake ratsa ajin duk sunsha jinin jikin su, ita kuwa Sanah kai ta d'ago ta kalleshi ,Amman bata ga fuskarsa ba dan baya ya bata, sai gashin k'eyarsa da ta tsurawa ido ganin shi a kwance lub sai wani lauyewa a yayi ya bi k'eyan nashi yana Shek'i, tana cikin nazarin da me tayi mishi ta kuma jiyo muryarshi na ratsa ajin baki d'aya taji tajiyo muryarsa nacewa yana cewa, *"kneeling down,"*
ya fad'a still bai jiyo ya kalle ta ba,
juyawa tayi bayanta taga babu kowa sai ita kad'ai,
cikin mamaki ta kalli bayansa dan ita a iya saninta tasan ba'a saka Patick a jami'a.
Cikin mamaki ta kuma kallan bayansa,
batare daya jiyo ba taji yace *"ko bazaki kiyi bane?"*
Muryar dataji ta daki dodon kunnenta,
tasa gabanta mugun fad'uwa a razane ta kuma kallan bayansa,
babu damar taga fuskarsa saboda ya juya mata baya,
a hankali Sanah ta d'an zumb'uri baki kana tayi kneeling down d'in,
gaba d'aya students mamaki ya gama cika su,
duk da sun san halinsa, sun tabbatar zai iyin abinda ma yafi hakan,
dan sun san mari ko dizgi abu ne mai matuk'ar sauk'i a wajensa,
amma basu tab'a ganin yasa wata ko wani kneeling down ba,
sai yau kuma daganinta new comer ce,
students suka rink'a yin dogon wuya suna l'eka ta,
jin muryarsa ta fara explanations yasa duk suka shiga hankalinsu.
Sanah na nan har ya gama lecture tana ta zumb'ure-zumb'uren baki,
Cikin k'asaita ya fito zai tafi , ganin ya wuce ta gabanta amma bashi da niyyar ce mata komai,
yasa ta cewa *"Sir to ni wuni zanyi a nan ne? "*
Tsayawa yayi cak a inda yake,
kana ya juyo da fuskarsa a hankali ya zuba mata ido,
had'i da hard'e hannayensa a k'irji,
mik'ewa Sanah tayi batare daya bata umarnin tashi daga kneeling d'in ba,
kanta durk'ushe tana kakkab'e siket d'inta,
tana yin magana k'asa-k'asa, "eh wato kai zaka fece gidanku ni kuwa in zauna a nan, sai kace baiwar gidan ku ko, hegen k'eya! da nad'edd'en gashi."
dan ita a tunaninta ya tafi shiyasa ta d'anyi halin, baki ta murgud'a tare da mik'ewa tsaye,
d'ago kan da zatayi, keda wuya sexy eyes d'inta,
suka sark'e cikin na *SIR MOLI* dayake tsaye hard'e da hannuwa yana kallan ta..................
_Aunty AISHA ALIYU GARKUWA_
_kina tambayar inda nakai miki Sir Molinki to gashi nan na maido miki abinki_
~To fans masu tambayar ina nakai Sir Moli na b'oye har tsayin six years, gashi nan ya dawo~
~sai a cigaba da gashi a d'ora daga inda aka tsaya~
*_Typing📲_*
*_HASKE WRITERS ASSO...💡_*
_(Home of expert and perfect writer's)_
*_♦RAINA KAMA......!!♦_*
_{Kaga gayya}_
*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*
👉🏻1⃣9⃣
.......Kallone ya koma sama yayinda kuyangin suka shigo cikin gidanmu, na d'akima tuni sun fara rige-rigen fitowa, baba k'arami da fitowarsa kenan daga sashensa yak'araso ga kuyangin, domin tambayarsu daga ina haka?.
Baiwa d'ayace tabashi amsa da fad'in basu kad'ai bane, masuyin bayanin suna waje.
Fita yayi sukuma suka ajiye kayan gefe suka kuma fitowa domin kwaso sauran.
Muna falo a zaune inna lami ta tsaremu sai mun sha romon wani nama da aka dafa k'anana, sai yatsine fuska mukeyi saboda rashin dad'in naman. shigowar Ahmad da Aryaan da gudu yasa mama Rabi'a tambayarsu lafiya?.
Ahmad yace “mama wlhy bak'ine da akwatina da yawa suka shigo”.
Gaba d'aya muka zuba masa idanu, kafin wani yay masa tambaya a cikinmu mukajiyo sallamar baba k'arami.
Innarmu ce tamik'e domin fitowa, ganinsa da manyan mutane cikin alk'yabbu yasata fad'in “baba k'arami bak'i mukayi?”.
Cikin washe baki yace, “wlhy kuwa maman biyu ”.
Itama murmushine shinfid'e a face nata, tabasu hanya suka shigo falon, duk suka zazzauna.
Muduka muka durk'usa muka gaisasu, yayinda suka kuma gaisa dasu innarmu cikin mutunci.
Fita baba k'arami yayi yasa yaa Anas ya kunna Gen..... dayake babu nepa. Shikuma yakuma fita da hanzari domin nemawa wad'annan bak'i masu bazata kayan tarba, bayan yakira Dady da Abba ya Sanar musu.
Kaf matan gidanmu suka shigo, kowa yanason jin daga ina kuma.
Mukam d'akinmu muka koma muda su Ayusher muna hasashen bak'i daga ina haka? da gani dai kasan jinin sarautane, ko kad'an ban kawo Galadima a rainaba ma, dan narigada Na shafe labarinsa ni.
Suna cikin gaggaisawa da matan gidanmu saiga innaro tashigo, kai kace an wurgotane. baki tarik'e tana fad'in “o ni Marwanatu, manyan bak'i irin wad'annan surasa gurin sauka sai 6angaren Ai'sha? kuko bayin ALLAH daga ina haka? ”.
Su aunty Mimi basu fahimci zancen taba, dan haka duk sai sukayi d'an murmushi, matan gidanmu kuwa kowacce tayi k'asa da kai dariyar mugunta Na cinta, Innarmu dai bata tankaba, hakama mama Rabi'a, sai inna lami ce tace, “yo inna in banda abinki waka hana rana fita idan lokacin fitar tata yayi?”.
Kallonta innaro tayi zatayi magana baba k'arami yashigo da sallama, su Yaa Anas na biye dashi da kayan ciye-ciye nik'i-nik'i, bayan sun ajiye suka gaishesu cikeda girmamawa suka fita.
Zama baba k'arami yayi suka sake gaisawa, sannan yace, “kufayi hak'uri, mukam duk kun sakamu a duhu wlhy”.
K'asaitaccen murmushi aunty Mimi tayi, domin dama papi yamata bayani akan komai na 6oye musu dasukayi. ta gyara zamanta sosai “Alhaji daga masarauta muke, munkuma zo kawo kayan k'anwatane Gimbiya munaya”.
Kusan kowa dake falon saida ya waro idanu waje, domin jin furicin aunty Mimi, wasuma zuciyar tasu kad'an tarage tayo tsalle waje.
Aunty Mimi bata damu da yanayin nasuba tacigaba da fad'in “kuyi hak'uri fa, nasan nakuma sanyaku a wani duhun, mai martaba sarki Abdul'fatah da maimartaba sarki Jalaludden Abubakar, sune sukazo Neman auren yarinyar Ku Munaya wa d'ansu Galadima Muhammad Sameer Saifuddeen Abubakar, sun 6oye muku kansune saboda wani dalili, amma sun aikomu da sak'on ban hak'uri a gareku, yanzu dai mun kawo kayan lefen Munaya ne gasunan”.
Jin jina kai kawai baba k'arami ke iyayi, bakinsa yakasa rufuwa saboda d'unbin farinciki da al'ajabin dake dank'are a zuciyarsa, yanzu nan daman manyan sarakunane agabansu a wancan karon sukazo Neman auren d'iyansu, lallai sun godema ALLAH dabasu aikata wani Abu Mara k'yauba agaresu, lallai ya yarda kwarjinin mulkine yasakasu mik'a Auren d'iyarsu ga mutanen dabasu saniba.
Ai su madam innaro sai aka zauna k'asa babu nauyi, muryarta har zuga take tace “ranki ya dad'e wai gaskene saboda ALLAH?, kokuwa wasa kikeyi?”.
Murmushi aunty Mimi tayi, sannan ta kalli su Ummu hasheem da suma suketa murmushi, kallonta ta maido akan innaro, “hajiya kaka mizaisa muzo muyi muku wasa irin wannan akan magana mai muhimmanci irin ta aure, tabbas maganar nan gaskiyace, munama fata gobe idan ALLAH ya kaimu iyanzu Munaya tazama d'aya daga cikin zuri'ar masarautar gagara badau”.
Innarmu da mama Rabi'a juna suka rungume suka fashe da kuka, yayinda innaro tamik'e ta callara gud'ar data jawo hankalin tawagar jama'ar 'yan biki, sai kawai tashiga taka rawa.
Dariya sosai tamaba su aunty Mimi, shi Kansa baba k'arami dariyar yayi yana girgiza Kansa da mamakin innar tasu mai kayan arzik'i Dana tsiya.
Matan gidanmu kam ba'a magana, kowacce tayi d'if takasa koda kwakwkwaran motsi, kowaccensu jitake tamkarma tafasa ihu take a nan.
Muryar gwaggon halimatu na rawa tace “wai da gasken dai Munayar gidan sarauta zatayi aure?”.
“kwarai kuwa”. ‘innaro tafad'a tana mata wani kallo, “jikata sai gidan sarauta, masu bak'in cikin kuma sai a mace”.
Lallai maganar innaro tadaki zukatan dukkan matan gidanmu, Sanin halin innaro da baba k'arami yayi saiyace duk afita abama bak'i waje susha koda ruwane.
Jiki babu kwari sukaita Jan k'afa suna fita Su da danginsu 'yan biki da gud'ar innaro tajawosu shigowa. bak'in