Showing 87001 words to 90000 words out of 382522 words

Chapter 30 - Raina Kama 1 And 2 Hausa Novel Complete

03 Jan 2025

2937

da sauri naja bargon na rufe fuskata saboda kunya.
Yayinda shikuma ya kalli mama Fulani yana wani susar gefen wuya kamar gaske, “o ranki ya dad'e kune? bar kanku da zuwa Ku shigo mana, saima Ku tayani lallashi ai”.
Matannan buyu gud'a suka callara a tare, yayinda mama Fulani ta kafama Galadima idanu, alamun tuhuma. kansa ya d'ago shima suka kalli juna ya sakar mata wani lallausan murmushi, kafin ya janye idonsa ya maida a kaina danake k'udundune cikin bargo.
d'aya cikin matan ta rissinar da kanta, cikin girmamawa tace, “Ranka ya dad'e ko zaka bamu waje mu k'imtsa ta?”.
Kallonta yayi, fuskarsa d'auke da murmushin Dana sakama suna na rainin hankali, cike da k'asaitarsa yace, “na hutasheku jakadiya, danni tun a daren jiya na gyara matata”.
Mama Fulani dake kallonsa a zuciyarta tace amma dai yaronnan d'an rainin wayone wlhy, gaba d'aya ya shirya komansa dai-dai ta yanda babu wanda koda ta k'aryata zai yarda da ita, Dan tabbas tasan duk k'arya yakeyi gameda wannan k'yallen, gashi lungu da sak'o na gidan angama nuna k'yallen, saboda ma ya raina mata wayo ba 6angarenta aka kaiba, sashen matan sarki ya aika da k'yallen, zancennan ma da akeyi ita bataga k'yallen ba har yanzun, Dan ba'a kai mataba, kowa ya d'auka daga sashenta ya fito, tunda ita ake fara kaimawa tagani sannan Matan sarki.
Had'a ido sukayi da Galadima, bakin ya ta6e mata, tareda d'age gira sannan yasaki murmushin Dake k'ular da mama Fulani aduk lokacin da yayisa.
Ta had'iye wani yawun bak'in ciki tareda kauda kanta gefe, su jakadiya kam tuni sun yi nisa wajen kar6o k'yaututtukan da kuyangin kowane sashe ke kawowa daga Matan gidan da iyaye, duk abama Munaya.
Dole mama Fulani ta k'arasa gaban gadon tasakama munaya turare da Sanya mata albarka tamkar yanda al'adar gidan ta tanadar, sannan takama hannunta ta saka mata bangles na goal masu k'yau da d'aukar idanu. Ta shafa kan munaya tana murmushin yak'e. sannan tadawo gaban Galadima shima takama hannunsa ta d'aura masa agogon Azurfa mai k'yau.
Salute nata yayi yana fad'in thanks my sweet Granny ”.
Uffan batace masaba tajuya tafice daga d'akin. yayinda su jakadiya suka take mata baya.

Suna fita ya sauke ajiyar zuciya tareda dafe kansa yana jan tsaki, nima kaina na bud'e amma nakasa tashi saboda kunyarsa data dabaibayeni.
Kusan mintuna 5 muna a haka, ni inata hawaye da jamasa ALLAH ya isa a zuciya, ga la66ana sai zugi sukemin saboda Sumbata d'inma na mugunta yamin. shikam yana dafe da kansa har yanzun yana sauraren kukan danake rairawa.
Zamansa ya gyara ya juyo yana kallona, fuskarsa a matuk'ar d'aure yace “tashi ki zauna muyi magana”.
Yanda yay maganar yasani tashi zaune batare da na musaba.
Yad'an kalleni ya janye idonsa sannan ya mik'amin Handkerchief d'insa daketa tashin k'amshi alamar na goge hawayena. Kamar bazan kar6aba dai saikuma na kar6a na goge fuskata.
Nanma shiru mukai nawasu mintuna da basufi 2 ba, nakula magana yakeson min amma yanata mulmulata a zuciya saboda jin kai, kuma d'agowa yayi ya kalleni saikuma yay gyaran murya kad'an, “em kiyi hak'uri, bamuda wata mafita sai wannan, munada wata kidahumar al'adane a masarautarnan, dolene randa katare da matarka sai kowa yasani ta hanyar ganin jini ajikin k'yallen da aka shinfid'a muku a gado. mukuma namu auren yasha banban dana saura, banida niyyar zalintarki na maidaki bazawara sannan na sakeki, inason idan mun rabu duk mijin daya aureki yasameki cikin mutuncinki, shiyyasa bazan aikata abinda suke buk'atar ba. ajiya anta surutu saboda bamu bada wannan shaidar ba, shiyyasa a Daren jiya nayi wata dabarar daban, fitowata kenan daga wanka najiyo busar algaita da gud'a alamun k'yallen yagama zaga masarautar, shiyyasa nayi azamar d'akko coffee d'in da aka had'amin zansha nanufo nan dashi, Dan Muftahu yakirani ya sanarmin zafa azo har sashena domin sanyamiki albarka da k'yaututtuka dakika samu saboda kin kawo mutuncinki, yanayin dana ganki nasan zasu gane shirina, shine dalilin yimiki wannan abun dan fidda zuciyarsu daga zargi, karki d'auka nayi mikine da niyya koki kalleni cikin mutane masu sa6a alk'awari”.
yana gama fad'a yamik'e zai yafice, nidai kaina ak'asa jinake tamkar namasa masifa amma kwarjininsa ya hanani, saida yaje bakin k'ofar zai fita sannan ya kuma furta “kiyi hak'uri, Sameer baya zalunci”. ya ida ficewarsa kawai.
Duk da na yarda da abinda ya fad'a, hakan bai hanani rushewa da sabon kuka ba, nace mugu kawai ALLAH ya isana wlhy, na shafa la66ana da da haryanzu zugi sukemin suda k'irjina wlhy, dan tsabar mugunta shine yama tsaya iya bakin amma harda wani wajen, ALLAH ya isana nidai.

🤣🤣kujifa, mutum da sadakinsa Munaya ke kiransa da mugu da jamasa ALLAH ya isa😂, yau munga auren Contract readers😝⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀.

Tunda abunnan yafaru bamu sake had'uwa da shiba a ranar da yinin washe gari , kullum dai Samha kan kawomin abinci tareda kuyangin Aunty Mimi.


★★★★


Bayan sallar isha'i damuwa da rashin jin innarmu da Munubiya ya gallabi zuciyata, jinai bazan iya daurewa ba, dan haka na yanke shawarar zuwa na rok'esa ya aramin charger kona samu nayi charge wayata, duk da ma banida isashen credit aciki. na d'au turare nad'an fesa kad'an sannan nazura dogon hijjabi nafita zuciyata na d'ar-d'ar.
Na dad'e k'ofar falon tsaye ina tunanin yanda zan shiga, daurewa nayi nai Knocking, wata murya naji ta amsa sa6anin tasa, akace “waye?”.
Saida gabana yad'an fad'i, cikin rumtse idanu nace “nice”.
Galadima dake kwance cikin kujera idonsa a lumshe yana sauraren Muftahu yabud'e idonsa da sauri.
Shikam muftahu cewa yayi “bismillah ranki ya dad'e, ki shigo”.
Na tura k'ofar ahankali na shigo da wata sabuwar sallamar, Muftahu ne kawai ya amsa cikin washe baki, (yayinda k'asan zuciyarsa ke wata iriyar murna ganin shirinsa zai tafi dai-dai kenan). Galadima kam idanu kawai ya zubamin cikeda mamakin miya kawoni?.
Gaisawa mukayi da Muftahu cikin mutunci. saiya mik'e yana fad'in “ranka ya dad'e nikam na wuce, zuwa Safiya zamu k'arasa maganar kawai”.
Kansa kawai ya d'agama Muftahu n.
Muftahu ya kalleni yace “gimbiya mu kwana lafiya”.
Na murmusa sannan na amsa da “to ALLAH ya tashemu lafiya”.

Koda Muftahu yafita sainayi tsaye nakasa magana ganin ya zubamin idanu, ganin banida niyyar magana saiya nunamin kujera alamar na zauna. shima yana tashi zaune sosai.
Ban musaba na zauna.
“miya faru?”. ‘yafad'a yana zuba Hollandia fresh milk a glass cup d'in gabansa”.
d'agowa nayi nad'an kallesa, dai-dai yasaka kofin a bakinsa zai sha, janye idanuna nayi ina kuma had'e fuska. aransa yace kai wannan yarinya akwai jan ajin tsiya.
Saida naja wasu seconds sannan nace charger zaka aramin please, nabaro tawa a gida, gashi inason waya da munubiya da innarmu.
Crossing kafarsa yayi yana cigaba da shan free milk nashi tamkar bai jini ba, harna fidda tsammanin zai tanka min, sainaji yace, “ina wayar?”. yay maganar da mik'omin hannu alamar na bashi
Mik'ewa nayi na kai masa wayar ina tunanin mizaiyi da ita?.
Koda ya kar6a saiya mik'omin cup d'in hannunsa bayan yak'ara fresh milk d'in a ciki.
Na girgiza masa kai alamar na k'oshi.
wani kallo ya watsamin daya sani kar6ar dole. nadawo mazaunina na zauna, inata rik'on cup d'in amma nakasa sha, haka kawai naji hankalina bai kwanta da fresh milk d'in ba, bawai zargin yazuba wani Abu nakeba, haka kawai dai banjin sha.
Shikuma ya basar dani yanata juya wayar kawai a hannusa, basan miyake kalloba ajikinta.
Kallona yayi yace, “kin rik'e Number su?”.
“eh” nafad'a batareda na kallesa ba.
Wayarsa ya d'auka guda d'aya ya had'omin da tawan ya mik'omin, “kije kuyi wayar kawai, da safe sai a nemo miki charger d'in”.
Na tashi naje na kar6o tareda cewa “nagode” najuya nafice da cup d'in fresh milk d'in a hannu na.
Bina yayi da kallo harna fice, ya sauke ajiyar zuciyata kafin ya cije lips nashi domin jin mararsa tad'an rik'e masa kad'an.

Koda naje d'akina saina kasa ajiye fresh milk d'in, haka kawai naji kuma sha'awar nasha, nako d'aga cup d'in na shanye tas sannan na zauna ina juya wayar tasa datamin k'yau, saina tuno wayarsa daya barmin ranar idi, na ta6e bakina kawai nafara saka number innarmu..............✍🏼



Hummm mi zai biyo baya bayan shan fresh milk kuma?. da zuwan muftahu?.🤥

Wannan amsar sai ranar Monday🤫. naso yimuku wannan weekend d'in amma munada biki gsky.😄💃🏻


*_hhhh naji k'orafinku sister's, ammafa ko pages biyu nakeyi ba isarku zaiyiba😄, wlhy bama nida time d'in yin typing 2pages a rana, saboda inada aure, akwai nauye-nauye a kaina nima, masu kuma so nagama kafin azumi suma ina basu hak'uri, bazai yuwu nagama kafin azuminba, dan azumin kad'an ya rage, kuma banason datse labarin nan kamar yanda nayi a SIYASA KO KABILANCI, zanbi a hankali na gama, wlhy nafiku son nagama nima Na huta, Dan dana fara buk zai fara cizona a zuciya nima, so kawai nake naga nagama😄, karku manta ko tarihin masarautar su Galadima sameer har yanzu bamu saniba, Dan haka zamuyi, iya inda muka tsaya saimu cigaba bayan salla idan ALLAH ya kaimu da rai da lafiya, Dan kamar yaune ai.😄👌🏻._*

Ngd sosai da soyayyar dakuke nunama buk d'innan, ina sonku nima har cikin raina, ina fata zaku fahimceni😄👌🏻.

❤❤❤❤❤❤❤
⛹🏻‍♀









*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭👏🏻_*
*_Typing📲_*



*_HASKE WRITERS ASSO...💡_*
_(Home of expert and perfect writer's)_




*_♦RAINA KAMA......!!♦_*
_{Kaga gayya}_




*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*



👉🏻2⃣5⃣



..........Bugu biyu ta d'auka, jinayi tamkar anmin bishara da aljanna dan dad'i, lokacin danaji muryar innarmu tayi sallama cikin sanyinta sai kawai na Sanya mata kuka.
Ita kuma daga can batasan wayeba, a sanyaye tace “baiwar ALLAH ko bawan ALLAH lafiya kuwa?”.
Murmushi nayi, gakuma hawaye na kwaranya, nace “innarmu nice fa”.
Cikeda d'okantuwa tace, “Munaya kece? ya kuke?”.
Murmushi nayi mai sauti, nace “innarmu ina yini? inasu Aryaan? Wlhy ina missing d'inku innarmu, ALLAH kamar na dawo gida”. na k'are maganar da sakin kuka.
Kallon juna sukayi da Abbanmu, da yake girkin tane tana d'akinsa, sukama juna murmushi, Abba yace, “haba dai munaya ta jaruma ce da kuka haka? Ina aka ta6a kai mutum gidan miji yayi sha'awar dawowa gida inbada yawoba?”.
“wayyo Abbanmu I miss u so much kaima wlhy”.
Dariya suka sanyamin shida innarmu, Abba yace, “yo ga sakaran yarinya, miyeto na kukan hakan? Yaya mijin naki da jama'ar gidan?”.
“komai lafiya lau Abba, sai kewarku, musamman ma Munubiya, ALLAH ina kewarta Abba, dan ALLAH kace ya kaini na ganta”.
Yanzu kam dai su Abba sosai sukemin dariya, saikuma suka shiga tsokanata, tun ina kukan harna ware nima ina dariya, munyi hira sosai, kafin Abba yace “saida safe hakanan, karda ki k'are masa kud'in, ki gaidashi”.
Cikeda farinciki namusu sallama, da cewa zankirama gobe.
Na yanke wayar ina murmushi, Munubiya na kira itama, cikin sa'a tashiga kuwa. tana kwance jikin yaa Marwan yana d'an rage zafisa🤫, wayar tafara ring, shine yamik'o mata, ta amsa tana kallon number, irin Special number d'in Nance, wadda zaka ganta a tsare. (🤫bara na Baku, amma banda matan aure 07000000000😝)⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀.

Saida ta kalli yaa marwan ya d'aga mata kai alamar tayi picking sannan ta d'aga.
Muryar Munaya dataji yasata mik'ewa zaune zumbur cikeda d'oki.
Kowa yay kewar d'an uwansa, dan haka ko gaisuwa bamu tsaya yiba muka shiga fad'ama juna yanda mukai missing. muka 6alle hira kamar zamu ga juna tacikin wayar..
Mun d'au tsawon lokaci munayi kafin yaa Marwan yasamu dole yin sallama, wayar ya kar6a ya jawo matarsa ya rungume, zatayi magana ya d'ora yatsansa a bakinta alamar tayi shiru tareda yanke wayar ko sallamar arzik'i bamuyiba.
Inajin sukur-sukur d'insu ta wayar, dan haka na tuntsure da dariya ina fad'in oni su yaa marwan Ashe dai ashe?....😂🤭.
Number Fauziyya na gwada itama akashe, nace lallai amarci yayi dad'i kenan?, itama Ayusher na kira number busy, 'Yar tara, nasan tanacan itada khamees ana soyewa.
Feena ma wayarta Switch up, nad'anyi tsok'i na ajiye wayar Na tashi domin yin shirin barci, dan yau ina cikin farin ciki, tunda naji muryar families d'ina.

Tun bayan fitar Munaya kam Galadima yafara jin canji a jikinsa, a hankali yakejin wani feelings na bijiro masa, kamar wasa abufa yafara tsamari, tun yana basarwa har mamaki yafara kamashi, shin wai mike faruwa ne dashi haka? bazaice baya sha'awa ba, yanayi sosai, dan wani time d'inma saiyasha tablets, ko allurar kwantar da sha'awan, amma baita6a jin irin na yauba, k'arfin sha'awarsa yasashi katange kansa daga dukkan abinda zai iya zurmasa ga halaka har yazama hanyar tsanin aikata zina. duk da jiya yad'ansha wahala saboda abinda yafaru tsakaninsa da yarinyar can duk da shi yayine badan yaji wani abuba, amma Abu yaso zamar masa Matsala a yinin gaba d'aya, sai dai tunda yaje yay allura sai nutsuwa tazo masa.
Dauriyarsa ce take Neman zuwa k'arshe, sai kawai jikinsa yafara rawa, da bin bango yashiga bedroom d'insa, drowan gefen gadomsa yabud'e yad'iba drugs kusan uku ya watsa a baki, ruwa ya d'auka frigate ya korasu suka wuce.
Humm abanza wai man kare, maimakon yaji sauk'i saima abin ya k'aru. yadawo falo saman doguwar kujera Yakuma kwanciya bayan ya kashe AC n gaba d'aya, Dan k'ara dulmiyar dashi yakeyi.

Nima d'in agareni kusan hakane, kad'an-kad'an nafara jin tsigar jikina Na tashi.
Kamar wasa ina wanka sai Abu yafara shan kaina, abinda bansan ma'anarsa ba yafara bin jinin jikina da 6argo, na lumshe idona ina hango abunda yafaru tsakani na d'azun da Galadima, duk dani wahala ma nasha, wani feelings na tashin hankali yafara bijiromin, idanuna harsun sauya kamanni, da k'yar nayi wanka nafito, ko towel d'in ban cireba na saka hijjab Na d'au wayarsa Na fita, koda nayi sallama a k'ofar falonsa banji ya amsa ba, nayi har sau uku shiru kakeji, shikam yana kwance yana jina, amma bakinsa yakasa koda motsawa barema ya amsa min, saima muryata dake sakashin jin wani zirrr, duk sanda nayi sallamar sautin muryata na motsawa da tsigar jikinsa ne, gaba d'aya gashin jikinsa ya tashi.
Jin shirun yayi yawa natura k'ofar kawai Na Shiga abuna, azatona ko barci ya d'aukesa kokuma bai jiniba.
Ganinsa kwance saman doguwar kujera yasa gabana d'an fad'i, gawani iri dana kuma ji jikina yayi, dagashi sai boxer da vest, hannunsa d'aya dafe da mararsa, d'ayan kuma dafe da kansa, kauda kaina nayi daga kallonsa saboda tsorata da ganinsa a ainahinsa, gaskiya ba k'aramin namiji bane guy d'innan, duk kunya ta isheni, ban ta6a ganin namiji ba a haka, yo samarin gidanmu basa zama haka. duk tunanina barci yakeyi, na ajiye wayar saman cikinsa a hankali, kamar yanda naga d'ayar a ajiye, caraf ya rik'e hannuna da hannunsa daya dafe kansa, tsoro yakamani lokacin daya bud'e idonsa yana kallona, jazur idon yake abin tsoro. Muryarsa a matuk'ar sanyin daban ta6a Sanin yana da shiba yace “mi zakiyi?”. idanu na nad'an waro waje cikin tsarguwa nace, “mi zanyi kuma? wayarkace fa na ajiye maka”. ajiyar zuciya yad'an sauke, ya zuba min idanu batareda yasakimin hannunba. Gaba d'aya jikina yakuma rikicemin, jima nake tamkar Na fad'a kansa saboda abinda nakeji, ganin karna aikata abinda zanzo ina nadama saina zare hannuna dad'an k'arfi, jikinshi babu kuzarin kirki, danhaka yasaki hannun kawai, nikuma na juya nafice daga d'akin da saurina.
Lips d'insa ya cije da matuk'ar k'arfi kamar zai huda, Yakuma dafe mararsa datayi tamkar zata fashe masa, kai bazai iya daurewaba, domin zai iya mutuwa wlhy, ganin yarinyarnan kuma Yakuma birkita tunaninsa. idonsa yarigada yarufe, ya manta matsayin Auren Nasu, duk da gargad'in da wani sashen zuciyarsa yake masa akan alk'awarin daya d'auka, burinsa kawai ya sauke wannan nauyin kozai samu nutsuwa, da


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login