Showing 165001 words to 168000 words out of 382522 words

Chapter 56 - Raina Kama 1 And 2 Hausa Novel Complete

03 Jan 2025

2987

seat yana kallonmu cikeda birgewa.
Nikam nama manta ko gaisheshi banyiba, saida yay gyaran murya sannan Na d'ago Na kallesa, murmushi namasa ina fad'in “yalla6ai barka da dare”.
Shima wani miskilin murmushi ya min yana d'agamin hannu batareda yayi magana ba.
Aiyaan yay saurin fad'a “auntynmu bafa yalla6ai sunansa ba, sunansa Uncle”.
Kamar zan harari yaron sai kuma nad'an murmusa ina kallon Galadima dake kallonmu shima. janye idona nayi daga gareshi Na cema Aryaan to naji zanke fad'a.

Har muka kai gida basu barmu mun hutaba, sai surutu suke da bani labarin abinda yafaru a gida bana nan, danaji zasu kauce hanya kuma sainai saurin waskewa.



★★*★*★★*★*★★


Sarkin mota yana ajiye su munaya ya duba gefen seat d'in data zauna, takarda ya gani ya d'auka, dan sanda zasu shige tamasa wata inkiya da hannu.
Dubawa yay yaga mita rubuta. Sallama yayma sauran 'yan uwansa sallama akan zai shiga gida.
Daga nan ba gidan ya shigaba, saiyay dabarar da yabar masarautar gaba d'aya.
Sun had'u da Saleem a inda suka shirya, saleem Ya bama sarkin mota handkerchief d'in da zasu shak'ama Muftahu.
Sarkin mota ma yaje ya bama Ameer ne, daga nan ya dawo k'ofar fada amma k'aramar k'ofa tacan baya inda keda k'arancin tsaro.
Agaban idonsa su Ameer suka sauke Muftahu a mashin yana cikin yanayin barci saboda abinda suka shak'a masa, saida ya tabbatar sunbar wajen sannan shima ya koma ciki.


Yau dai kam ni kad'ai Na kwanta a d'akina, Galadima ko lek'e bai lek'oba, yana can tare da su Aiyaan a d'akinsa.
Nima kawai saina kira Momma mukasha hirarmu, tana bani labarin yanda jikin Abie yaketa k'yau a tsakaninnan, dukda kar yanzu maganar bata fita amma yakanyi bamai tsawoba, naji dad'i sosai, na masa addau'a mai tsawo tareda fatan alkairi, daga nan muka cigaba da tattaunawa akan maganar Abbana, da zancen su innarmu dasuka k'i yarda su zauna a gidan, innarmu ta dage bazata zaunaba tunda muma anan muke, saida Momma ta saka baki da mata bayanin da zata gamsu sannan ta amince zata zauna. Nasha dariya, dan dama nasan za'ayi hakan, innarmu kawai kunya da kawaici.
Daga nan har muka dawo kan ta Muftahu, dayake tasan komai a kai, da taimakonta nima nake samun k'arfin gwuywa.
Itama tasha mamakin jin Harun a lamarin, ta dad'e tana jinjina maganar nan. ta bama Samha muka d'ora da hira, saida naga time yaja ga zazza6in fama ya rufeni, sallama mukayi nai addu'a Na kwanta.
Masu iya magana since sabo tirken wawa, saina kasa barcin, naji kawai ina kewar Galadima.

Shima kansa yanacan sai juye-juye yakeyi, yakasa barci, bayan sun gama hirarsu dasu Aryaan yay musu shirin barci da kansa suka kwanta, aiki yad'an ta6a yana Neman dabaru akan binciko Muftahu, baiwani dad'eba ya kwanta shima, amma saiya kasa barci, juye-juye yaytayi agadon, ganindai da gaske ya kasa barcinne saiya mik'e yana jan guntun tsaki, kwanciya ya gyarama su Aryaan ya lullu6esu da bargo sannan ya fito da nufin wai zai duba munaya 🤣😜.

Jin shigowarsa yasani k'ara lafewa tamkar nayi barci, ya kunna fitilar d'akin yana kallona, yaja wani dogon lokaci sannan ya kashe ya tako zuwa gadon, “nasan idonki biyu ai, dama kin tashi kinbar wani kumshe-kumshe”.
Shiru nayi nakumak'i motsawa.
Kwanciya yayi a gefena, yaja bargon shima ya lullu6a, tareda juyamin baya, yace “miya hanaki barcine?”.
“farkawa nayi”. Na fad'a batareda ba kalleshi ba.
Murmushi yayi yana fad'inn “ Hummm”.
Daga nan duk mukayi shiru nawani lokaci, kamar an matse bakina nace “yalla6ai na tambayeka please? ”.
Yace, “Uhmm”.
Juyowa nayi ina fuskantar bayansa, a nutse nace, “wai dan ALLAH ina sauran matan Abie yanzu?”.
Da sauri naga ya juyo gareni, ni harma tsoro ya kamani nai baya da sauri, nazata makeni zaiyi, amma sainaji ba hakaba, yace “Munaya mi kika sani a kaina ne?”.
“yalla6ai kamarya mina sani a kanka? daga tambaya?”.
Yace, “Humm yana matsowa gareni, zan matsa ya rik'o hannuna................✍🏼



Kuyi manage da wannan please🤦🏻‍♀








*_ALLAH ya gafartama mahaifanmu😭🙏🏻_*
*_typing📲_*


💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._*


*_♦RAINA KAMA.....!!♦_*
_(Kaga gayya)_



*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*



~Book 2~ 👉🏻1⃣4⃣


................Yanda ya rik'e hannun yasani fad'in “please yalla6ai akwai zafi fa”.
Sassauta rik'on yayi, ya sauke ajiyar zuciya, muryarshi a sanyaye yace, “Miyasa kikeson 6oyemin abinda kika Sani? shin bak'ya tausayinane? kullum cikin aiki kwakwalwa ta take, aikin Neman kud'in da zan taimaki kaina da ahalina, aiki akan mak'iyana, ya kike tunani a kaina? yanzu haka ji nake tamkar kwalwar kaina zata tarwatse saboda damuwa da abubuwan da suka sakata matuk'ar nauyi, ta6a kiji yanda zuciyata takoma bugawa a slowly”. ya kamo hannuna ya d'ora a k'irjinsa, saitin zuciyarsa. da gaskiyarsa kad'an-kad'an zuciyarsa ke aiki, ba kamar kowanne bugun zuciya dake tafiya normal ba. Sai naji tausayinsa ya kamani, cikin sanyin murya nima nace,
“yalla6ai kayi hak'uri da abinda zan fad'a maka, inhar ka kawoni gidanka ne domin muyi aiki tare a matsayin Friend bai kamata ace ka gaza yarda daniba akan sirrinka. kasan minene yake saka kwalwarka da zuciyarka wannan nauyin kuwa?”.
Kansa ya girgiza mini.
Na gyara kwanciyata ina kallon p.o.p, “Matsalarka d'ayace baka yarda da kowa ba sai kanka, mu cire Momma da papi, dansu aiyukansu sunkai amusu uzuri, Momma hankalinta akan jiyya yake, dan haka kana k'ara mata damuwa, papi kuma babbane shawara da dabarun manya kawai kake buk'ata daga garesa. Sai kuma Muftahu da Harun nakula suma kakan d'an saki jiki dasu akan wasu abubuwan, to amma fa.........”.
Saitayi shiru bata k'arasaba.
Ya matso jikinta sosai, tare da d'ora hannunsa saman cikinta, murya k'asa-k'asa yace, “Harun da Muftahu amma fa mi? Please ki k'arasa mana”.
Kad'an Na juyo nad'an kallesa, Na d'ora hannuna nima akan nasa daya d'ora akan cikina. Janye fuskata nayi Na koma kallon p.o.p d'in. “kayi hak'uri da abinda nake fad'a, badan ina zarginsu bane zan fad'a d'in, dama zancene Harun da Muftahu kuma kamar bai kamata 100% susan komaiba, dan za'a iya sayensu ko tursasasu suci dunduniyarka. domin koba komai har yanzu bakada tabbas d'in cewar babu hannun wasu a cikin masarautar nan. amma kayi hak'uri idan na shiga hurumin daba nawaba”.
Shiru yay baice komaiba tsawon lokaci, har nayi zaton nayi laifi ko yayi barci, a sanyaye nakuma fad'in “please & please kamin afuwa yalla6ai”.
“is okay”. ‘kawai ya fad'a yana kuma sakani a jikinsa, tareda d'ora ha6arsa saman kaina.
Babu Wanda yasake magana a tsakaninmu, kowa yay shiru yana k'ullawa da kwancewa, har dai barci yafara fisgata.
“Kina ganin su Aiyaan bazasuyi kuka ba idan suka farka sukaga su kad'aine?”.
Naji maganarsa cikin kunnena.
“a'a” na fad'a ina girgiza masa kai, “ko'a gida sukad'ai suke kwana dama”.
“okay”.
Saikuma muka kuma yin shiru, har barci yakuma fara d'aukata yakuma fad'in “kozaki sha Magani ne?”. ‘yay maganar yana ta6a gefen wuyana’.
Kaina Na girgiza masa batareda nace uffanba. shima bai sake cewa komaiba..

Yanda numfashina ke sauka a hankali sai ya fahimci nayi barci, shiko gaba d'aya yakasa nasa barcin, tunanin wani Abu daya ta6a faruwa a baya ya fad'o masa, dukda shi ba yayi imani da hakan baneba.
👇🏻
*_Wata ranar juma'a a India, sai suka tashi da matsananciyar damuwar motsawar ciwon Abie, a time d'in ma sun zata rai zaiyi halinsa, hankalin Galadima ya tashi har ciwonsa shima yakai ga motsawa, amma yak'i yarda doctors su dubashi, yace abarsa kawai gara ya mutu ya huta, hankalinsu momma ya tashi, amma Galadima yak'i sauraren kowa, daga k'arshema saiya sulale daga asibitin ya fice abinsa, haka yayta tafiya rik'e da k'irjinsa saboda azabar ciwon da zuciyarsa ke masa, mutane sai kallonsa sukeyi, shiko baimasan sunayiba, yayi tafiya mai nisan gaske batareda yasaniba. k'arfinsa da kuzarinsa sukai gazawar da bazai iya cigaba da tafiyanba, shine yazube a wajen ya fad'i._*
*_bai tashi farkawa ba sai awani d'aki mai kama dana bunu, ya yunk'ura zai mik'e amma saiya kasa, wani tsoho ba indiye, a cikin indiyawan ma irin masu k'yawunnan sosai, ya dafa kafad'arsa, cikin harshensu yace ma Galadima “koma ka kwanta d'an saurayi, bakada lafiyane”. Galadima yace “kayi hak'uri baba gida zanje nasamu sauk'i, zamana annan bak'aramin tashin hankali bane ga ahalina”. tsohon yay murmushinsu Na manya, yace “zakaje gida d'ana, ni da kainama zan kaika, amma lallai kai acikin al'amuranka akwai abubuwan ban mamaki da al'ajabi, gakuma tsantsar rud'ani, saidai komai yanada lokacinsa, kuma lokaci zai tabbatar maka hakan, albishir d'aya zanmaka, nanda wasu shekaru dabasu Gaza 7 ba mai taimakonka zatazo, kwarai zatazo gareka, ba lallaine ka fahimci abinda nake fad'aba ko yarda dani, Dan Na lura kaid'in musulmine, kuma bad'an wannan k'asarba, amma wannan mai taimakon naka itace zata zama fitilar haska maka hanya kakai ga cinmma burinka, domin taurarinta da naka sunada matuk'ar k'arfi, harma suna gogayya da juna, zaku zama sh........”. Saikuma yayi shiru yana murmushi, ya shafa kan Galadima yana fad'in “tarin Albarka sucigaba da baibaye rayuwarka data zuri'arka”._*
*_daga wannan maganar sai barci mai nauyi ya kwashe Galadima, koda ya farka saiya gansa a asibiti tareda su Momma, yata tambayarsu INA tsohon yake sukace su basu San wani tsohoba, wasu samarine su biyu suka kawoshi asibitin, wai sungansa yafad'i a gefen hanya, zancen tsohon yata damun Galadima a time d'in har yayta bincike kozai gansa amma ko alamun mai kamarsa bai ta6a ganiba, daga hakama saiya cire abin a ransa yacigaba da harkokinsa._*

Ajiyar zuciya ya sauke, tareda kuma rungume Munaya, a kan la66ansa ya furta “ALLAH kaine mafi sani”. daga haka yay shiru tareda lumshe idanunsa, barcine yayta fusgarsa harya samu nasarar sacesa.
Can gabannin asuba yay wani mafarkin daya sakashi farkawa a firgice, har itama Munaya ta farka tana tambayarsa lafiya?.
Kansa ya dafe, da hannu yaymin nuni na bashi ruwa.
Sauka nayi daga gadon dan zazzza6inna ya fara hucewa nima, freight na bud'e na d'akko masa ruwa, na had'o da Kofi, zama nayi kusa dashi a gefen gadon na tsiyaya ruwan a Kofi na mik'a masa. kar6a yayi ya shanye, ya mik'o min kofin, zan kar6a ya girgiza min kai tare da min nuni da in k'ara masa.
Kuma tsiyaya masa nayi, yakai rabi ya d'aga min hannu alamar ya Isa, bayan yakuma shanyewa ya mik'a min kofin yana fad'in “Thanks”.
Kar6ar kofin nayi, ba tareda na tashiba nace “Yalla6ai lafiya kuwa”..
“Mafarki”. ‘yafad'a yana komawa ya kwanta’.
Idanu kawai Na zuba masa, kusan 4minutes ya juyo da kansa ya kalleni, “kizo ki kwanta mana”.
K'aramar ajiyar zuciya kawai Na sauke Na mik'e, Na d'ora ruwan da Kofi a dirowan gefen gadon na koma inda nake na kwanta.
Ganin ya sauya hannun da yay mafarkin kuma yana addu'a sai ban sake cewa komaiba, na kwanta shiru ina sak'e-sak'e a raina mafarkin mi yayi to? da har yasakashi firgita irin haka?. banida mai bani amsa dan haka nayi shiru.
Saiya zamto da asuba na rigashi tashi, harma saida nayi alwala sannan na tadashi, da k'yar ya iya tashi yana dafe kai, binsa nayi da kallo kawai harya shige toilet.
Lokacin daya fito na fara salla, dan haka saiya fice kawai. A mamakinsa saiya iske Aiyaan da Aryaan sun tashi suna alwala, hakan ya Burgesa sosai. Sai kawai ya kama hannunsu suka tafi massalaci.
Bayan an idar da salla bai yarda sun had'u da Sarki ba, ya gudo. Sai dai abinda bai saniba shi Sarki ya gansa, dan yau ya makara salla shima.


Wajen Around 9am nagama gyaran d'aki nayi wanka, saina d'an fito falon domin duba dubawa, natarar sabbin kuyangina suma komai sun gyarashi k'al, harma da mana break fast, banyi yunk'urin bud'ewa ba ma balle tunanin son ci, dukda kuwa natashi da yunwa, to amma Momma ta gargad'eni sosai akan cin abinci wani a masarautar, dan haka na fito daga kitchen d'in kawai.
Tunkan na shigo nake jiyo maganarsu Aryaan, zaune na iske Galadima su Aiyaan na kusa dashi suna bashi labari, anmusu wanka tsaf, sunsha sabbin kaya iri d'aya.
Har yanzu Galadima bayada walwala, na zauna ina gaisheshi, batareda yabar latsa wayarba ya amsa min, su Aiyaan suka dawo kusa dani suna gaisheni, kumatunsu naja ina murmushi, “oh my guys kunsha k'yau, waya muku wanka haka?”..
Atare suka amsa min da fad'in “Uncle ne, kuma ya saka mana tirare yanda kuke mana”.
Murmushi nayi, na saci kallon Galadima da yay biris damu kamar baya d'akin, alhalin sanda na shigo na iske suna hira shidasu 'yan 2.
Sallamar da wata baiwa keta kwad'awa na amsa, sannan na mik'e na fita dannaji minene? A k'ofar falona na isketa, nace, “miya farune?”.
Duk'ewa tayi ta gaisheni, sannan ta mik'omin ledojin hannunta tana sanarmin Sarkin motane yace “na kawo wannan ranki ya dad'e”.
Kar6a nayi, na koma ciki.
Ajiye ledojin nayi a gabansa, “gashi wai inji sarkin mota”.
Idanunsa ya d'ago ya kalleni, yace, “breakfast d'inku ne”.
Tashi yay ya fita yana fad'in na shirya zaije ya dawo mu shiga cikin gida gaida mutane.
Na amsa masa da to.



___________________


Tun a daren jiya wasu bayi sukaga Muftahu, dan haka suka shiga ihu, dandanan sauran bayin dake kusa da wajan suka firfito, manyan bayin cikinsu ne suka kai maganar cikin gida, shine akasakasu d'aukar Muftahu su shiga dashi.
Lamarin yabama kowa mamaki, babu wani mummunan rauni a jikinsa, inbanda d'an jini dake gefen bakinsa, saidai sun sami kwanciyar hankali ganin yana numfashi.
Maganar dawowar Muftahu bata baje masarautar ba sai washe gari.
Bayan Galadima ya fito daga sashensa zaije fada yaji anata k'ananun magana akan dawowar Muftahu, saidai kuma miskilancinsa bai barsa ya tambayi kowaba ya nufi Fada.
Ya isa mai martaba baikai ga isowa ba, dan haka suka gaisa da 'yan majilissar Sarki dake fadar, sannan ya nemi mazauninsa dake gefen Sarki Na dama ya zauna.
Zamansa baifi da mintuna 10 ba Mai martaba ya iso, gaba d'aya suka mik'e tsaye, dogaran Sarki sunata kirari da fad'in gyara kintsi da k'yau, duksun baza riguna ba'a gani mai martaba, basu bar kowa ya gansa ba har saida ya zauna a kujerarsa.
Baya suka mammatsa mai martaba ya bayyana, atare su Galadima suka rissinar dakai alamun girmamawa, sannan kowa yafito tsakkiyar fada ya mik'a gaisuwarsa ga Sarki, yayinda fadawa ke faman amsawa, tsakanin Sarki dasu kuwa shine d'aga hannu.
Mai martaba yayi mamakin ganin Galadima yau azaman fada, bawai baya zaman bane, sai dai yakan dad'e bai zaunaba, an masa uzurine kasancewar ansan ba zaune yake dindin dinba, kuma idan yazo akwai harkokinsa Na kasuwanci da yakeyi, sai dai dolene yakan shigo yayi gaisuwa.
Bayan fada ta nutsu aka fara fadanci.
K'a idane fadar gagara badau takanyi fadancine a sati sau hud'u kawai, litinin ba'a zaman fada, domin ranace da ake tunawa da abinda ya faru ga tsohon Sarki mahaifin Galadima, talata, laraba, alhamis, asabar, sune ranakun da ake fadanci, ranar juma'a ma ba'ayi saboda muhimmancin ranar ga al'ummar musulmi. A wad'annan ranakun akanyi zamanne daga 10am zuwa 12:30pm, da an tafi sallar zuhur ba'a dawowa, idan kaga anwuce wannan time d'in a fada to tabbas akwai abinda ya farune.
A wannan zaman fadancine maganar dawowar Muftahu ta fito, sun tattauna akai harda shirin kuma d'aukar matakai Na tsaro a masarautar.

Bayan anyi sallar zuhur ne Sarki ya shige gida, sauran fadawa ma kowa ya kama gabansa, Galadima bai shiga gidaba saiya nufi sashen su Muftahu domin dubashi.
Bayan an masa iso ya shiga, ya iske mahaifiyar Muftahu da 'yan uwansa zagaye dashi, har yanzu kuma yana cikin yanayin barci.
Ya jajanta musu, Yakuma kwantarma da mamansu Muftahu hankali, kusan mintunsa talatin ya fito ya koma sashensa.


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login