Showing 18001 words to 21000 words out of 91651 words

Chapter 7 - Azaaj Junaid Book 1 Hausa Novel Complete

23 Jan 2025

803

ta amince su rabu idan ta amince, shikenan sai ya saketa amma ba wai ya yi gaban kanshi ba. Sam bata amince wannan rabuwar ba.
Saboda haka ta ci gaba da sabgoginta a dalili ta d'auki saki a matsayi shirme yasa ko sanar da aminiyarta Hafsat ba tayi ba.
***************
Aslamiyya tare da Amrah su na duk'e a gindin famfo sai darza uban wanki suke yi, yau tun da asuban fari suka k'arya kumallo da wankin kayan Baffa Sani. Tuni Baffa ya daina kai wanki sai dai su yi masa, abin takaici gashi da gardawan 'ya'ya maza sai dai su Miyya su masa ba zai saka 'ya'yanshi ba. tsabar mugunta sai ya tara kaya da yawan gaske yake saka su wanki gashi yawanci tufafinshi duk babbar riga ne. Tun da asuba yana dawowa daga masallaci ya tisa su a gaba, duk sanyi da ake tsulawa bai dame shi ba ga ruwan tanki sun yi mugun sanyi kamar na fridge Amrah tana tsoma hannunta a ruwan taji mugun sanyi ya ratsa k'asusuwanta, ta fara you wa Baffa Allah ya isa miyya tana ji ta amma bata ce uffan ba. A haka suka ci gaba da wanke kayan sai wuraren karfe biyu suka kammala, zuwa lokaci sun gaji likisss.....
Aslamiyya ta jik'a musu indomie da Hakeem ya siya musu su na cikin ci indomie ɗin suka ji muryar Dadda tana kwada musu kira.

"Aslamiyya, Amrah uban me ku ke yi kunshe a d'aki ku fito maza ga nawa wanki na fito dashi, shegu yara marasa son aiki"

Da sauri Aslamiyya ta fito jikinta sai rawa yake yi, Allah ya saka mata tsoro tsiya a rayuwarta Amrah kan zamanta tai tak'i fitowa, daga k'arshe sai Miyya ce tai wanki. Da taga akwai raguwar kumfa ta dauko nasu kaya ta zuba a ciki tana cikin wankewa Dadda ta fito, tana kyala ido taga Miyya tufafinsu ne take wankewa, ta fara surfa mata zagi.

"Eh! Lallai Aslamiyya kin nuna min ke isasshiya ce nasaki wanki ki haɗo har naku, saboda ga sabulun banza ko?"

Jikinta ya d'auki kyarma sai kakkarwa take yi, cikin muryarta mai cike da tsoro tace

"Dadda wallahi ban saka sabulunki ba ruwan kumfa ne kawai ga ma raguwar sabulunki can na kai miki, k'ofar d'aki.....

Sai da Dadda ta sakar mata bak'ar harara kafin ta shiga zazzaga mata ruwan masifa.

"Rufemin baki shegiya yarinya tsinaniya wacce ta tsotsi nonon kafurci, shegu gur6attaci. Zo nan don uwarki arniya.

Ta k'arashe magana tare da ya fito ta da hannu, tuni Aslamiyya tafara kuka, Amrah ce ta fito daga d'akinsu tana faɗar

"Haba Dadda,! Wai me muka tare miki a duniya ne kullum sai kin k'ikk'iro da hanyar da za ki musguna mana, dad'in abin ba ki da wuka kankare zamowar mu jikokinki, saboda haka kema kina da had'i da jinin arna.

Amrah ta k'arashe magana tana murguda baki.

"Iyeee.....Amratu ni ki ke yiwa rashin kunya?"

"Ba wani rashin kunya Dadda gaskiya ce na faɗa, kema ai kin zama arniya saboda abin da kike yi wani arne ba zai yi irinshi ba.

Amrah bata gama rufe baki ba Dadda ta wawuro tsintsiya da nufi dukanta, Amrah tana ganin ta nufo wajenta ta 6alla da gudu tayi k'ofar gida, sai kawai ta dawo kan Miyya.

"Ke kuma daga yau duk abin da kika san nawa ne a gidanan karki kuskura ki ta6a shi, yadda na tsani mutuwata haka na tsaneku.

Ta k'arasa magana tare da fyadawa Miyya tsintsiyar aka, Aslamiyya ta durkusa k'asa tare da ɗora hannuwanta bisan kai, tana gunji kuka.
********************
Alhaji Yusuf Junaid tare da Alhaji Buba suka kone kurmusss.....a cikin bukkar boka, Alhaji Abdallah da Ahmadu sai ihu suke har bukkar ta cinye duka sai toka kawai da gawawakin su Alhaji da suka yi bak'i k'irin.... kamar an babbaka awakai.
Boka kuma da ya zura da gudu ya shiga jaji, wuta da keci a hannunshi sai dad'a k'aruwa take yi a maimakon hannunshi yanzu kuma duka jikinsa ke ci da wuta, tun yana iya gudu har k'arfinshi ya K'are ya faɗi. Kamar fashewar bomb haka boka ya fashe naman jikinsa ya tarwatse gunduwa-gunduwa abin zallan tashin hankali.
Alhaji Abdallah da Ahmadu basu k'ara shiga tashin hankali ba, sai da wuta ta mutu suka ga gawawakin su Alhaji kuka suke yi babu mai rarrashin wani daga k'arshe Ahmadu ya jawo motar da suka zo da ita suka tattaro gawawakin suka zuba sai k'auri ke tashi, tsawon rayuwarsu ba su ta6a ci karo da mutuwar mai tashin hankali iri wannan ba. Duk lokaci da suka tuna da musanbabin mutuwar tasu sai tashin hankalinsu ya k'ara linkawa.
Gashi kuma ba su san me za su faɗawa iyalai su ba.
Gara ma Alhaji Yusuf jininsu ne watakila abin ya zo musu da sauk'i sa6ani Alhaji Buba da yake 6are kuma fitattce d'an siyasa 'yan adawa za su iya cewa an had'a baki dasu sun kashe shi.
Kaitsaye farmhouse ɗin Alhaji Yusuf suka nufo inda suka saba yi secret meeting ɗinsu har suka iso basu sami kwakwarar dabarar da za su yi ba.
Sai kawai suka kira abokan kullin tugunsu, dukansu sun tsorata da jin afkuwar al'amari ko wane su fuskarshi ta bayyanar da firgici da yake ciki ga dai babbakakin gawawaki zube cikin mota sun rasa yadda za su yi dasu. Can Hasheem ya ja dogon fasali kana yace.

"Ku bani aron hankalanku inaso ku sani muddin sanadin mutuwarsu ya bayyana, mu ma kashinmu ya bushe, Kuma ba lallai bane iyalinsu su yarda da labari yadda suka mutu ba. Saboda haka ku bar min komai a hannuna.

"Sai ka faɗa mana dabarar taka mu ji?"

Cewar Hajiya Kubra wacce ita da Alhaji Yusuf da Alhaji Abdallah uwarsu d'aya.
A natse Hasheem ya shiga koro musu bayani plans ɗin nashi, take suka yi hamdallah tare da amincewa.




*TOP 10 TAKUN HASKE BATCH A*💪

*ALBISHIRIN KU MUTANEN KIRKI? KUNGIYAR HASKE WRITERS ASSOCIATION*

*TAZO MUKU DA SABON TAKU, SABUWAR FITA, SABON KARUWA, SABON ILIMI, SABON NISHAƊI SABON KARATU SABON AJI.*

*INDA SUKA ZO MUKU DA K'YAYATATUN LITTATTAFAI GUDA 7, WANDA ZASU NISHADANTAR DAKU SU FADAKAR DAKU. WANDA GWARAZAN MARABUTAN KU ZASU GABATAR*

*IBTISAM:- NA AYUSHER MUH'D*

*WATA SOYAYYA:- NA OUM HANAN*

*WASU MAZAN:- NA BILLY S FARI💎*

*NIDA RAHEEMA:- NA ASMY B ALIYU👄*

*ZO GARE NI:- NA HAJJA CE👈*

*KUKAN ZUCI:- NA SLIMZY*

*AZAAD JUNAID (the young billionaire):-NA JEEDDAH ALIYU*

*TAKUN HASKE TOP 10 BATCH A BASU TSAYA NAN BA, ZASU GABATAR MUKU DA WASU SHIRYE SHIRYENSU*

KALOLIN GIRKI TARE DA:- *DEEJARH BERVER*

SHIRIN
YADDA AKE HADA MAGUNGUNAN KARIN NI'IMA DA INFECTION (NI'IMARKI A TAFIN HANNUNKI) TARE DA *MAMAN KHADIJA*

SHIRIN TSAFTA YADDA ZAKI GYARA JIKINKI DA MATSALOLIN JINI TARE DA:- *UMMI AISHA*

*ZASU KARA MUKU HASKE AKAN ABUBUWA DA SUKA SHA KANKU, MATSALAR AURATAYYA MATSALAR INFECTION, MATSALAR NI'IMA, MATSALAR FUTAR ISKAR GABA, MATSALOLI DA DAMA.*

*DUK ZAMU GABATAR DA WANNAN KARATU NE TA HANYAR WAYOYIN SADARWA, WATO WHATSAPP GROUP'S*

GARABASA MAI CIKE DA ALBARKA DA KUMA KARUWA. GABA D'AYA WANNAN AJI ZAIZO MUKU NE AKAN 500 naira only...Nair ɗari biyal kacal.

*GA MAI BUKATAR BIYAWA KANSA KO KANWA KO MATA KO YAN UWA YA KASANCEWA DA TAKUN HASKE TOP 10 BATCH A*

*SAI YA TURA KUDINSA TA*

2083371244
Zenith Bank
Aisha M.Salis

*Seka tura shedar biyan kud'inka zuwaga wannan lambar*

+447894142004

*Ko kuma tura katin waya na MTN ta wannan number👇🏼👇🏼*

07043079282
*Shaidar biya ta wannan* 07065283730

*DUK AKAN 500NAIRA ONLY MACCEN DA TA'ISA TA SAN KANTA BAZATA BAR DAMAR NAN TA WUCETA BA!*

*ƳAN NIGER🇳🇪, ZAKU IYA TURA KUƊINKU 550F TA NITA, AMANA, AL'IZZA, BENIF KO ZEINA GA WANNAN LAMBAR* +227 96 91 36 36 *SUNA* RAHINA daga Niamey.
5/12/22, 12:25 - Ummi Tandama😇: *AZAAD JUNAID*
_{ The young Billionaire}_


Na
Jeeddah Aliyu

Wattpad:-jeedddahaliyu

Haske writers Association.

Top Ten Takun Haske Batch:A

Last Free page.

10...


A cikin dare mummunan labari ya riske iyalan Alhaji Yusuf Junaid tare da na Alhaji Buba sun yi mummunan accident, sun kone kurmusss.....ga baki daya iyalan sun shiga tashin hankali musanmman da suka ci karo da gawarwakinsu.
Wannan duk shirin Hasheem ne su kansu 'yan uwanshi sun yabawa basirarsa matuk'a, tun a cikin daren mummuna labarin ya riske Azaad bawa Allah duk yabi ya rikice duk k'iyayyar da 'yan uwanshi ke nuna mishi hakan bai hana shi k'aunarsu ba. In ka ganshi sai ya ba ka tausayi kuka yake yi sha6e-sha6e da hawaye.
A washe gari aka yi jana'izzarsu jama'a sun taro sosai, abinka da manyan mutane. A duk lokaci da Ahmadu da Alhaji Abdallah suka yi arba da Azaad sai gabansu ya yanke ya faɗi, wani irin mashahurin tsoronshi ya shige su, shiyasa duk inda suka ganshi zaune ba su zama a gun, gani suke kamar yana sane da abin da ya faru. Tun daga ranar da aka fara zaman makoki Azaad Junaid ya d'auki nauyi kawo abinci da za a ci haɗi da lemo har ma da ruwan sha, daga wani tsadadden restaurant ake kawowa.
Bayan an yi sadakar bakwai kowa ya kama gabanshi sai raguwar 'yan uwa na jiki.
*******************
A tsakiyar dare ciwon Amal ya tashi yau kuma da sabon safuri ya zo, don kuwa sai aman jini take, kakarin amanta ne ya tashi Miyya da Amrah a gigice Amrah ta kunna bulb haske ya gauraye d'akin kan shinfid'arsu duk ya 6aci da jini hakan ba k'aramin ɗaga musu hankali ya yi ba. Miyya sarkin kuka tuni hawaye suka wanke mata kuncinta. Yayin da numfashi Amal sai ya yi sama ya dawo kasa, Amrah ta buɗe k'ofa haɗi da fallawa da gudu ta nufi d'akin Dadda ta shiga knocking tana kuma kiran sunan Dadda.
Dadda tana cikin mutane da basuda nauyin barci duk k'ank'anta motsi akan k'unneta, tun fara buga kofar ta ji ta sarai kawai biriss...tai da ita. Duk dauriya irin na Amrah sai da ta fashe da kuka, tasake ficewa da gudu ta nufi 6angaren Baffa Sani tashiga dukan k'ofa kamar za ta karyata a bisa dole Baffa Sani ya taso ya buɗe mata, tun kafin ta sanar dashi dalilin knocking ɗinta ya d'auke ta da bahagon mari, ya kuma shiga surfa mata zagi.

"Ka ga 'yar iska yarinya bashin uwarki naci da za ki dinga gana min azaba ta hanyar duka min k'ofa a sulusili dare?"

Duk da taji zafin marinta da ya yi hakan bai san ta fasa faɗar.

"Baffa ciwon Amal ne ya tashi yau har da aman jini take yi.....

"Amal ɗin taci uwarta ba aman jini take yi ba Allah yasa ta amayar da 'yan hanjinta ba abin da ya shafe ni maza 6ace min da gani tun kafin na murd'e miki wuya.

Amrah ta fashe da matsananci kuka ta durkusa, tana rokon Baffa magiyarta ya taso da mai d'akinsa Habiba, cikin murya wanda aka katsewa barci ta ce.

"Wai meke faruwa ne Alhaji?"

"Nida 'yar banzar yarinya nan ce Amrah wai Amal ce batada lafiya shine don tagadi iskanci gaba da baya take min wannan mahaukacin knocking.

"Mtss..... lallai Alhaji Amrah ta rena ka banda reni Ina ruwanka da rashin lafiyar Amal da za ta katse mana barci.

Baffa Sani ya yi kwanfa tare da maida k'ofarshi ya rufe ruff.....dole Amrah ta tashi ta dawo d'akinsu.
Aslamiyya na d'auke da kan Amal a cinyarta har zuwa lokaci numfashinta bai dai-daita ba. Sai kawai suka saka Amal gaba su na rera kuka, sai zuwa asuba Amal ta daina gurnani da take yi kamar wacce tai barci, sai kawai Aslamiyya ta shinfid'eta ta fita waje ta dauro alwala, ita ma Amrah alwalar tayo suka yi sallah su na kammala sallah Amrah ta dubi Aslamiyya ta ce.

"Miyya bai dace mu bar Amal haka ba kamata ya yi mu kai ta asibiti, saboda tun da take ciwo nan bata ta6a aman jini ba.

"Nima nayi wannan tunani Amrah saidai zuwan namu bai da amfani saboda komai sai da kud'i, mu kuma ba mu dasu.

"Duk da haka Miyya mu gwada kaita zai fi da mu barta gida tana sha wuya .

"Shikenan je ki nemo adaidaita bari na canza mata kayan jikinta duk sun 6aci da jini.

Daga haka Amrah ta fice jefi-jefi take haɗuwa da mutane unguwa saidai ba wanda ya ce da ita kazal.....tana tsaye a bakin titi har gari ya fara haske bata samu adaidaita ba, kamar daga sama taji an anbace sunanta.

"Amrah me kike neman da sassafe nan akan titi?"

Da sauri ta waiga sai kawai taci karo da fuskar mutume nan mai shago da ta yi wa satar bread, cikin sanyi murya ta gaida shi ya amsa kana ta faɗa mishi dalilin fitowarta da taimakonshi ta sami adaidaita, ya kuma biyota zuwa gidan nasu tashiga gida suka fito da Amal lokaci da za su fito da ita Dadda tana tsaye a k'ofar d'akinta ta kalle su ta watsar.
Lokaci da suka fito da Amal kamar matatciya, sosai Bello mai shago ya tausaya musu saboda tun ranar da al'amari nan ya faru tsakaninsa da Amrah ya yi nadama. Ya kuma kudurta a ranshi duk ranar da ya haɗu da ita zai taimaka mata kuma ya rok'e ta gafara, shiyasa yana ganinta ya biyo ta.

Kaitsaye Nassarawa hospital suka wuce da ita a emergency, kasancewar dama ko acan baya anan ake kawota. Har zuwa lokaci Bello mai shago yana tare dasu, hatta da katin gani likita shi ya biya musu k'udi, bayan likita ya duba ta ya basu zungureriyar takarda, mai d'auke da list ɗin magunguna da drip haɗe da allurai da za su siyo.
Amrah ta kalle miyya a hankali ta ce.

"Bari naje Bello yana jira na a waje mu siyo magani ki kula da ita yanzu nan zan dawo"

"Amrah waye wannan mutume da mu ka zo tare dashi?"

Miyya ta aika mata da tambaya tare da tsare ta da idanuwanta. Ajiyar zuciya Amrah tayi kafin ta faɗa mata waye shi.

"Amrah bakinsan mutume nan ba bai kamata ki yi sauri yarda dashi ba.

"Nasani Miyya amma dole ce tasani yin hakan amma nai miki alk'awari kula da kaina in-sha-Allah ba zan yi abinda zai ta6a martaba ba.

"Shikenan ki je amma ki faɗa masa duk abinda ya kashe mana dangin kud'i, rance ne za mu nemo mu biya shi daga baya.
Amrah ta fito waje rik'e da prescription, da tunani ina za ta nemo kud'i saboda k'arya ta yi wa Aslamiyya na cewa za su je siyan magani ita da Bello domin tun a wajen siyen kati suka rabu dashi. Kafin ya tafi ya bata dubu biyu.
Tana fitowa daga asibiti pharmacy ta wuce aka buga lissafi kud'in magani kusan dubu ashiri da biyu da d'ari bakwai, gashi dubu biyu ce da ita duk yadda taso su kar6i dubu biyu ɗin su bata Koda drip da allurai ne in ta kawo ciko kud'in su bata raguwar magani, amma suka k'i daga k'arshe korar kare suka yi mata, kusan saida ta yawace duka pharmacy dake wajen har ta sadakat....sai ta tuna da complementry card ɗin da Hakeem ya bata da sauri ta nufi bakin titi ta tari adaidaita sai gida, a gigice ta shiga gida, ta tararda Dadda zaune a tsakar gida, ko kallo bata isheta ba. Ta shiga d'akinsu a gaugauce tafara neman card ɗin, tasha bak'ar wahala kafin ta gano inda ta ajiye.
Ajiyar zuciya ta sauke yafi a kirga da ta gano card ɗin.
Da gudu ta fito Dadda sai kwalla mata kira take, a tunanina ko Amal ta mutu ne shine dalili shigowar Amrah a rikice ta kuma sake ficewa a firgice, Amrah tana jin duk kira da take mata tai banza da ita. Wayar d'an adaidaita ta ara ta shigar da number Abdul-hakeem, lokaci da kiranta ya shigo wayar shi yana tare da Azaad Junaid su na tattaunawa aKan zance neman matar aure da yasa Hakeem ɗin ya nemo masa, tai ringing har ta tsinke Hakeem bai ɗaga ba.
Amrah ba ta hak'ura ba sai mai-maita kira take, can taji an yi picking tasa kuka cikin muryar kuka ta ce.

"Don Allah ina magana da uncle Hakeem ne?"

"Shine wacece?

"Amrah ce yarinyar da a kwanakin baya ka yi bailing ɗinta a police station"

"Subhanalillah..... Amrah lafiya me kike yi wa kuka Allah yasa ba satar ce kika k'ara yi ba?"

Cikin shasshekar kuka ta faɗa mishi dalilin kira nashi da tayi, sosai tausayinta ya lullu6e shi tsabar tausayawa ko sallama bai yi wa Azaad ba ya fita, da mugun speed ya iso Nassarawa hospital ya ma ri ga Amrah isowa yana tsaye ya hangota da sauri ya nufi wajenta. Ya kar6i prescription ɗin ya je ya siyo magunguna ɗin sannan suka dunguma zuwa emergency, sosai mamaki ya lullu6e Aslamiyya na gani Amrah tare da wani babban mutum, nan take aka wuce da Amrah d'aki na musanmman likitoci suka dukufa akanta. Cikin hukunci ubangiji numfashinta ya dawo normal.
Tun zuwan Hakeem asibiti yake kallon Aslamiyya, dai-dai da second d'aya bai d'auke ganinshi daga kanta ba. Har sai da Miyya tagano da kanta yana kallonta duk sai ta bi ta tsalgu.
Sai kawai ta shige bathroom tai zamanta a ciki, gani haka yasa fita ya siyo musu abinci sai da ya tabbatar da ya yi musu duk wani abu ya dace kafin ya wuce gida.
*****************
A washe gari ya sauya musu asibiti zuwa ta kud'i, Al'awwab spine care shine private hospital ɗin da Hakeem ya kai Amal. Asibiti ne mai tsadar gaske suna da kwararu likitoci har da turawa dama ciwon zuciya ne ke damunta an haife ta da hole a zuciya{rami} wanda tun haihuwar ta ya kamata ayi mata surgery amma rashin gata ya hana.
Tana girma ne ramin yana k'ara girma shine dalili da yasa ta fara aman jini. Ba tare da 6ata lokaci ba Hakeem ya biya milliyan goma da aka buk'ata ranar Miyya tasha kuka domin abinda suka yi shekaru suna nema sai gashi Allah ya kawo Hakeem rayuwarsu, babu haɗin iya balle na Baba yai musu. Cikin yarda ubangiji aka yiwa Amal surgery kuma ana sa ran nasara. Satin su biyu a hospital ko kare bai zo ba daga dangin mahaifinsu babu kuma wanda ya damu da sani hali da suke ciki. Kullum addu'ar Dadda Allah yasa sun shiga duniya kenan bata fatan su dawo mata gida.
Sosai Amal ta sami sauk'i ta murmure kamar ba ita ba hatta da jikinta ya fara dawowa, har zuwa lokaci Hakeem da matarsa Zaliha ke dawainiya dasu, Zainab K'anwar Hakeem ke taya Miyya kwana Amrah

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login