Showing 21001 words to 24000 words out of 91651 words
Kuma ta koma gidan Hakeem da zama
Lokaci da Zaliha ta ji labarinsu sai da ta zubda hawaye, shiyasa ta d'auke su tamkar 'yan uwanta na jini.
Kusan kullum indan Hakeem ya zo asibiti sai Miyya tai mishi godiya, baya cewa uffan saidai yasaki mata k'ayatattace murmushi. A sati na uku aka yi discharge ɗin su kai tsaye Hakeem ya nufo gidanshi dasu Sosai hakan ya daurewa miyya kai, tana da kawaici shiyasa bata tambaye shi dalili kawo su gidanshi da ya yi ba.
Zaliha ta ware musu d'akinsu dabam.....an k'awata shi da komai na more rayuwa, sai suka tsince kansu a cikin wata sabuwar rayuwa wacce ba su ta6a mafalkinta ba.
Yau satinsu biyu a gidan tuni su Amal da Amrah sun zama 'yan gida musanmman da ya kasance Rayham second born ɗin Hakeem sa'arsu ce.
Miyya ce Kaɗai ta kasa sakin jikinta, a kullum burinta su bar gidan duk da bak'ar wahala da suke sha a hannun Dadda ta gwamaci su koma can domin nan ne asali da tunshe su.
A wani yammaci ne Miyya da Zainab su na zaune a d'aki, Rayham ta shigo ta sanarda Miyya Daddy yana kiranta. Nan take ta ji wani matsananci faɗuwar gaba, ta saka hijabinta. Lokaci da ta shigo falon faɗuwar gabata ya tsananta har wani duhu-duhu take gani.
Da fuskar Baffa Sani ta fara cin karo yana zaune yasha babbar riga brown colour, sai kuma Dadda wacce tun da tashigo ta kalleta ta watsar. Cikin sanyi murya tai sallama Hakeem tare da Zaliha suka amsa mata, ta nemi sama center carpet ta zauna murya can k'asa ta gaida Baffa da Dadda ba wanda ya amsa mata a cikinsu.
Kaitsaye Baffa Sani ya fara faɗar abin da ya kawo su.
"Aslamiyya dama mun zo ne domin mu yarda kwallon mangwaro mu huta da kuda, tun daga ranar da Usman ya bijerewa mahaifinmu ya auro uwarki muke d'and'anar bakin cikinsa, sanadin bakin cikinsa mahaifinmu ya rasa ranshi, a duk lokaci da na kyala ido na ganku ji nake kamar na kashe ku.
Kwatsam....sai ga wannan bawar Allah ya zo mana da zance aurenki dama muna neman kai dake shiyasa babu 6ata lokaci na amince yau ɗinan aka daura miki aure, Kuma ina mai tabbatar miki daga ke har shegun k'anneki banaso ko kusa da katangar gidana na ganku. Ku sa aranku wannan shine danginku dama can shegiyar yarinya nan Amratu ta sha faɗar ke ce uwarsu ke ce ubansu, yanzu kuma ga dangin kun samu.
Da sauri Miyya ta ɗago idanuwanta da babu komai a cikinsu sai tsoro, ta kafe Baffa dasu ji take kamar wani yare ne yake mata ba hausa ba........
*TOP 10 TAKUN HASKE BATCH A*💪
*ALBISHIRIN KU MUTANEN KIRKI? KUNGIYAR HASKE WRITERS ASSOCIATION*
*TAZO MUKU DA SABON TAKU, SABUWAR FITA, SABON KARUWA, SABON ILIMI, SABON NISHAƊI SABON KARATU SABON AJI.*
*INDA SUKA ZO MUKU DA K'YAYATATUN LITTATTAFAI GUDA 7, WANDA ZASU NISHADANTAR DAKU SU FADAKAR DAKU. WANDA GWARAZAN MARABUTAN KU ZASU GABATAR*
*IBTISAM:- NA AYUSHER MUH'D*
*WATA SOYAYYA:- NA OUM HANAN*
*WASU MAZAN:- NA BILLY S FARI💎*
*NIDA RAHEEMA:- NA ASMY B ALIYU👄*
*ZO GARE NI:- NA HAJJA CE👈*
*KUKAN ZUCI:- NA SLIMZY*
*AZAAD JUNAID (the young billionaire):-NA JEEDDAH ALIYU*
*TAKUN HASKE TOP 10 BATCH A BASU TSAYA NAN BA, ZASU GABATAR MUKU DA WASU SHIRYE SHIRYENSU*
KALOLIN GIRKI TARE DA:- *DEEJARH BERVER*
SHIRIN
YADDA AKE HADA MAGUNGUNAN KARIN NI'IMA DA INFECTION (NI'IMARKI A TAFIN HANNUNKI) TARE DA *MAMAN KHADIJA*
SHIRIN TSAFTA YADDA ZAKI GYARA JIKINKI DA MATSALOLIN JINI TARE DA:- *UMMI AISHA*
*ZASU KARA MUKU HASKE AKAN ABUBUWA DA SUKA SHA KANKU, MATSALAR AURATAYYA MATSALAR INFECTION, MATSALAR NI'IMA, MATSALAR FUTAR ISKAR GABA, MATSALOLI DA DAMA.*
*DUK ZAMU GABATAR DA WANNAN KARATU NE TA HANYAR WAYOYIN SADARWA, WATO WHATSAPP GROUP'S*
GARABASA MAI CIKE DA ALBARKA DA KUMA KARUWA. GABA D'AYA WANNAN AJI ZAIZO MUKU NE AKAN 500 naira only...Nair ɗari biyal kacal.
*GA MAI BUKATAR BIYAWA KANSA KO KANWA KO MATA KO YAN UWA YA KASANCEWA DA TAKUN HASKE TOP 10 BATCH A*
*SAI YA TURA KUDINSA TA*
2083371244
Zenith Bank
Aisha M.Salis
*Seka tura shedar biyan kud'inka zuwaga wannan lambar*
+447894142004
*Ko kuma tura katin waya na MTN ta wannan number👇🏼👇🏼*
07043079282
*Shaidar biya ta wannan* 07065283730
*DUK AKAN 500NAIRA ONLY MACCEN DA TA'ISA TA SAN KANTA BAZATA BAR DAMAR NAN TA WUCETA BA!*
*ƳAN NIGER🇳🇪, ZAKU IYA TURA KUƊINKU 550F TA NITA, AMANA, AL'IZZA, BENIF KO ZEINA GA WANNAN LAMBAR* +227 96 91 36 36 *SUNA* RAHINA daga Niamey.
5/12/22, 12:25 - Ummi Tandama😇: *Wannan littafi na kud'i ne yana daya daga cikin top ten takun haske don Allah kada ki karanta ba tare da kin biya naira 200 kacal ba idan kina\kana buk'ata sai ku tura kudinku ta 2083371244 Asha M.Salis Zenith Bank sai ku tura shaidar biyan kud'in zuwa ga wannan lambar +447894142004 ko katin waya na MTN ta wannan number 07043079282 shaidar biya ta 07065283730*
*AJ*
11...
"Innalillahi wa'aina illahim raji'un! Miyya ta faɗa a firgice, sai k'ara zare idanuwa take yi tare da bin su Baffa Sani da kallon tsoro.
Dadda ta rafka mata katuwar harara cikin masifa ta ce.
"Ka ji min marar kunya yarinya mugun abu muka aikata da za ki bi mu da innalillahi wa'aina illahim raji'un! To bari ki ji aure dai ne an riga an daura kuma ko kinaso ko bakyaso k'arshen zaman mu dake ya zo. Saboda haka tun wuri ki rufawa kanki asiri ki kar6i k'addararki a hannu don ni nan da kika gani ba zan jure cigaba da zama daku ina tuna bak'in cikin da sanadin auren uwarku ya haifar min"
"Daina 6ata yawun bakinki Dadda domin ko za ta mutu zaman aure nan ya zame mata dole Shi din ban da kyau d'an maciji da ya rud'e shi me zai tsinta a wurinki, sau nawa ina ba dake sadaka ana barina dake. Ina tabbatar miki ba ma buk'atarki daga ke har k'anneki ku k'addara cewa ba ku ta6a saninmu ba. Ku saka aranku bamu da wata alak'a daku.
Tun da Baffa Sani ya fara magana Miyya ta fashe da kuka wani irin k'unci da bak'in cikin take ji marar misaltuwa, bata ta6a tsanmani k'iyayyar da suke musu har ta kai mizani haka ba.
Hakeem ya yi sanyayyar ajiyar zuciya yana mamaki wannan wacce irin k'iyayya ce me yara k'anana kamar su Miyya su ka yi da suka can-canci tsana irin wannan, abin takaicin shine daga kakarsu wacce ta haifi mahaifinsu da k'anishi uwa daya uba daya shi Kaɗai ne k'anishi a duniya wai su ne ke nuna musu wannan zazzafar k'iyayya.
Shi tun da yake a duniya bai ta6a jin inda aka hukunta wani akan laifi wani ba, sai akan su Miyya saboda kawai mahaifinsu ya aure Christan ta kuma haifesu an Kuma waye gari mahaifin nasu baya duniya, shine suke fuskantar wannan tasku.
Ya sake sauke ajiyar zuciya a karo na biyu cikin sanyi murya ya ce.
"Baffa ni dama burina Miyya ta ji zance aure nan daga bakinku, to Al-hamdu-lillah! Ta Kuma ji iya wannan nake buk'ata daga gareku. Kamar yadda na faɗa muku tun ranar da naje da buk'atar neman aureta, zan rik'eta ita da k'anneta bisa amana, zan kula dasu na basu tarbiyya tamkar 'ya'ya da na haifa. Kuma in-sha-Allah zan kasance mai rik'e wannan alk'awari.
Fuska Dadda ta tanke ta dubi Hakeem ta ce.
"Da ka rik'e su amana da kada ka rik'e su ni wannan bai shafe mu ba, idan ma ka ga dama ba iya ci amanarsu ba, ka yanka su kaci wannan ba damuwar mu bace. Ni dai inaso ka k'ara jaddada musu basu ba gidana dama dole ce tasani zama da 'ya'ya kafira 'ya'ya da aka daura auren uwarsu a coci, saboda haka yanzu sun dawo mallakinka.....
Cikin matsananci kuka Miyya take kallon Dadda tana girgiza kai tana faɗin.
"Haba Dadda! Haba Dadda duk da kasancewar mu 'ya'ya kafira ki tuna cewa kafira nan ita Kaɗai ba za ta samar da 'ya'ya ba dole sai tare da namiji. Wannan namiji kuma shine d'anki jinin jikinki ashe kuwa ko duk duniya za su taru su juya mana baya ke bai kamata ki wofitar damu ba. Dadda duk musgunawa da kike mana wallahi-tallahi ban ta6a jin tsanarki a zuciyata ba. Na saka araina wata rana za ki hak'ura ki so mu ashe tunanina ne ya bani hakan.....
"Ke!
Baffa Sani ya daka mata tsawa.
"To tunaninki ya gayamiki k'arya har gaba da abada ba za mu ta6a sonku ba, na Kuma faɗa banaso ko katangar gidana ku ra6a. Dadda tashi mu tafi.
Ya k'arashe magana yana kama hannun Dadda ta mik'e da kyar saboda tana fama da ciwon k'afafuwa.
Miyya tana gani haka takara sautin kukanta, tana faɗar
"Baffa Don Allah kada ku tafi ku bar mu hannun Wanda bamu gama saninshi ba, gara zama daku koda za ku yanka naman jikinmu ku yi gunduwa-gunduwa dashi. Ku dubi girman Allah Kar ku bar mu a gidanan.
"Mtsss..... shegiyar yarinya bak'ar ja'ira can ku k'arasa mu kam Allah rabamu da jafa'i, Allah yasa k'addarar mutuwarku tana hannunshi dare yau ya fara shan farfesunki, dama duk a cikin ɗiyan Usmanu kinfi debo kamani kafirar uwarki.
Cewar Baffa Sani har yana had'awa da galla mata harara da idanuwanshi, masu kama da na mujiya.
Jin furuncinshi na k'arshe yasa Miyya ta k'ara fashewa da kuka, ta rarrafa ta kama k'afar Dadda.
"Haba Dadda wannan wace irin rayuwa ce ku ke k'ok'arin jefa mu ciki, idan aure ku keso ku yi min ku aurardani gun wanda ku ke da cikkake sani akansa. Ba wannan ba da ku kanku ku ke zarginsa da yankar kai....
Da sauri Hakeem ya mik'e ya nufi Miyya, ya durkusa a gabanta cikin sanyayya murya ya ce.
"Aslamiyya ki kalle ni da kyau ban yi kama da wanda zai iya cutar da ko dabba balle mutum d'an adam mai darajar, haɗuwata daku wani babban al'amari ne wanda haɗi ne na Allah, ki d'auki haɗuwarmu a matsayin k'addararre al'amari.
Har Miyya ta buɗe baki za tai magana ta ji saukar abu akan fuskarta, Baffa Sani ya jefa mata buddle ɗin 'yan one-one thousand.
"Ga sadakinki nan indan kin ga dama ki kyasta musu ashana ki k'ona.
Yana k'arashe magana ya ja Dadda suka fice kamar makaho da dan jagora, har Miyya ta yunk'ura ta bi su Zaliha ta baro wajen zamanta da sauri ta rik'eta. Ita kuma sai turjewa take yi, kururuwar kukanta ne yasa Amrah da Amal suka fito daga d'akinsu, hankalinsu a tashe har su na had'a baki wajen tambayar dalilin kukanta.
Zaliha ce tai k'arfin halin faɗa musu a maimakon Miyya taga tashin hankalinsu sai kawai taga bayyanar farin cikinsu a fili, duk sai taji tausayin kanta saboda ta fahimci jin dad'i da hutun da ya fara ratsa 'yan uwata, yasa idanuwansu rufewa basa hango mata babban k'alubali da yake tunk'aro rayuwarta. Sai kawai ta zare hannun Zaliha daga rik'on da tai mata, ta kwasa da gudu ta shige d'akin da ya kasance mallakinsu. Ta murza key.
Ita babban abin da ya daure mata kai bai wuce yadda Zaliha bata nuna ta ji zafin aureta da Hakeem ya yi ba. Al'amarin nasu ko shakka babu akwai lauje cikin nad'i. Idan ba wata manufa a ciki wacce sakaryar mace ce za aiwa kishiya ta nuna halin ko in kula musanmman a wannan zamani da mata suke da mugun zafin kishi.
Tun Miyya tana kuka da hawaye har hawayenta suka kafe ta dawo kukan zuci, duk knocking da magiyar da ake mata bai sa ta buɗe musu k'ofa ba.
*******************
Azaad ya fito daga bathroom daure da brown towel, hakan ya bayyanar da muscles ɗinshi haɗi da six packs ɗinshi a jere jikinshi a murd'e yake ba sai an gayamaka mai k'arfi bane kai da kanka za ka gane. Cikinshi a shafe yake kamar baya cin abinci, alhali idan ya sami tuwo abin ba kyau. Irin jikin Azaad Junaid bature yai wa lak'abi da invested triangle body shape.
Azaad yana da matsakaici tsayi yana dauke da round face fatar jikinshi chocolate colour ce tsananin hutun da ya ratsa shi, yasa fatar shi take shek'i, babban abin da yake burge mata a jikinsa la66anshi da suke pink idanuwanshi masu girman gaske, suna dauke da eyes ball brown colour, kamar dai na magge gashin kanshi bak'in wulik dashi.
A natse yake tsane raguwar ruwan wanka da ke jikinsa, tsakanin jiya da yau ya rasa gane kanshi, musanmman idan ya tuna da jiya aka daura mishi aure da yarinyar da baisan ta ba. Babban tashin hankalinshi bai wuce yadda zai rayu da wata mace ba Salimarshi ba. Duk da yana da yak'ini akan Hakeem ba zai mishi za6en tumun dare ba. Lokaci da ya zo mishi da zance yarinyar ya faɗa mishi cewar har da yara biyu take da, shiyasa nan take ya amince da aurenta domin yana gani tun da har tana da yara za ta fi ba wa yaranshi kulawar da yakeso. Shima ya yi alk'awari zamewa nata yara uba kasancewar Hakeem ya faɗa mishi mahaifinsu ya rasu.
Ya shirya cikin dark grey suit bai saka coat ɗin ba ya rik'e ta a hannu, jikinsa na fitar da k'amshi turaren avon ever truth, walking majestically ya sauko downstairs parlor yaranshi na zaune a dining room su na taking break fast food.
"Good morning Daddy!
Suka faɗa a tare cikin sakin fuska har yana had'awa da murmushi, ya amsa musu.
"Morning my beautiful babies. Daddy zai yi tafiya amma ba zai wuce two to three weeks ba, uncle Hakeem zai kawo muku new Aunt za ta dinga kulawa daku kafin na dawo, ina so ku girmama ta kada wanda ya sake ya yi mata rashin kunya.
Aneesah tai dropping fork ɗin hannunta, kana kafe Daddynta da idanuwanta, can kuma ta ta6e baki tana yatsinar fuska ta ce.
"Daddy me za mu yi da new Aunt baya ga Nanny Lacey, tana kula damu dai-dai gwargwado iyawarta in fact mommy bataso kwashe-kwashe you have to ask her first....
"Aneesah!
Ya kira sunanta a fusace saboda ya tsani ko sunan Salima a anbata mishi nan take ya ji wani irin 6acin rai.....
5/12/22, 12:25 - Ummi Tandama😇: *Wannan littafi na kud'i ne yana daya daga cikin top ten takun haske don Allah kada ki karanta ba tare da kin biya naira 200 kacal ba idan kina\kana buk'ata sai ku tura kudinku ta 2083371244 Aisha M.Salis Zenith Bank sai ku tura shaidar biyan kud'in zuwa ga wannan lambar +447894142004 ko katin waya na MTN ta wannan number 07043079282 shaidar biya ta 07065283730*
*AJ*
_{The young billionaire}_
Na
Jeeddah Aliyu
Wattpad:-jeedddahaliyu
Haske writers Association.
Top Ten takun Haske Batch:A
12...
Ya nunata da yatsa cikin kakkausar murya ya ce "Bana cike da iskaci Aneesah ki natsu ki san waye a gabanki, nan gidana ne ba na Salima ba. Ni nake da ikon nasa ayi ni kuma nake da ikon hanawa, don haka wannan ya zama kashedi na k'arshe idan ina magana ki sako min zance mommynku"
Sosai Aneesah ta tsorata da yadda Azaad yake mata magana cikin kaushin murya, a tunaninta kafin ma ya kammala magana zai wanka mata mari, saboda tsawon rayuwarta ba ta6a gani yana magana irin haka ba. Cike da tsoro ta baro wajen zamanta ta durkusa gabanshi, saboda duk iskacinta tana matuk'ar tsoron Daddynta.
"I'm sorry Daddy wallahi ban faɗi wannan magana don na 6ata ma rai ba. Nayi ne saboda sani halin mommy da nayi za ta iya dawowa ku sami matsala akan hakan. Daddy ina matuk'ar sonku kai da mommy ko Kaɗan banso abin da zai kawo sa6ani a tsakaninku, amma in-sha-Allah ba zan sake maka maganarta ba"
Ta k'arashe magana tana hawaye, mik'ar da ita tsaye ya yi tare da goge mata hawaye kuncinta yana alhini ranar da za ta sami labarin rabuwarshi da Salima.
"It's okay princess ke ɗin ce wani lokaci kin cika faɗar shirme"
"Ka yi hak'uri Daddy ba zan sake ba.
"Shikenan amma inaso ki sa aranki duk abin da nake yi Ina yi ne domin farin cikinu da inganta tarbiyyarku, inaso ku zama yara nagari abin alfaharin iyayye. Saboda haka duk wani abu marar kyau princess ki daina kin ga ke ce babba k'anneki dake suke koyi"
"in-sha-Allah Daddy na daina duk abin da ka keso shi zan yi.
Ya sauke sanyayyar ajiyar zuciya tare da sumbatar for head ɗinta, ya mik'awa Airah hannu wacce tai tsuru-tsuru da idanuwa ya ce
"zo nan Mamana naga duk kin yi wani iri"
Kamar jira take yi ta taso da sauri ta rungumeshi, ya game su duka biyu ya rungume tsawon lokaci yana jin ɗumin jikin yaranshi, yayin da k'aunarsu mai tsanani gaske ke ratsa ko wane sasshe na jikinsa. Ya buɗe baki a hankali ya ce da Airah.
"Mamana je ki kira min Nanny Lacey ta zo min da Ahlam inaso naganta kafin na tafi.
Da sauri ta nufi d'akin Nanny Lacey sai gashi sun dawo tare tana d'auke da Ahlam, sai da ta fara gaidashi kana ta mik'a mishi Ahlam ya kar6e ya mannata a k'irjinshi a hankali yake shafa gadon bayanta, ita kuma lafe ya ke6e gefe da Nanny Lacey a natse ya sanar da ita zance aure da ya yi da zuwan amaryar tashi nan da 'yan wasu kwanaki. Ya faɗa mata ne domin akwai yarda mai k'arfi a tsakaninsu. Tun farkon aurenshi da Salima take tare dasu basu ta6a samunta da cin amanarsu ba.
Sai dai ya 6oye mata zance rabuwarsu da Salima a ganinshi wannan sirri ne a tsakaninsu bai kamata kowa ya sani ba.
Sosai Nanny Lacey ta kad'u da jin zance aurenshi saboda, tafi kowa sani bak'in kishin Madam Salima, akan Azaad komai za ta iya aikatawa.
Jikinta yai matuk'ar sanyi cikin tausasa murya ta taya shi murna, ya ji dad'i sosai yadda ta nuna farin cikinta akan auren nashi. Mak'udan kud'in ya bata kamar yadda ya saba bari a duk Lokaci zai yi tafiya duk da akwai wadatatce komai na buk'ata a gidan.
6angare Jadda ya shiga yai mata sallama har ya juya zai fita ta dakatar dashi ta hanyar faɗin
"Zo ka zauna Datti zan yi magana da kai"
A natse ya dawo ya zauna daff...da ita.
"Datti indan lissafina ya tafi dai-dai yau kwana goma da daura maka aure, saidai abin da ban fahimta ba har sai zuwa yaushe amaryar taka za ta tare?"
Murmushi ya yi wanda ya tsaya iya fatar bakinsa, ya yi shiru kamar mai nazari kafin ya ce.
"Jadda