Showing 90001 words to 93000 words out of 180087 words
Chapter 31 - Daudar Gora Book 2 Hausa Novel Complete
yiwu masa ba. Dan haka ya fito abinsa yana mai satar kallon Iffah da ke kuka da mutsu-mutsun kasa zama da ƙyau. Kai tsaye Gym ɗinsa ya nufa. Jallabiyar jikinsa ya zame ya canja da sport wears ya shiga motsa jiki da zafi-zafi kamar wanda ake tunzurawa.....
★Da ƙyar Iffah ta iya kai kanta bayi da taimakon Daneen Ammarah. Ashe ɗazu ba ƙaramin taimako yake mata ba da yake ɗaukar ta a komai. Sosai hankalin Malikat Haseenat da ita kanta Daneen Ammarah ɗin ya sake tashi da yanda tafiya ma ta gagari Iffah. A bayin ma duk yanda taso ganin ta nutsu a cikin ruwan ta kasa zama. Sai faman rirriƙeta take da magiyar “Mamy dan ALLAH ki fiddani, wlhy da ciwo sosai”.
Kwantar da kanta Mamy tai akan ƙafarta tana shafa kanta cike da lallashi dan tana zaune ne a bakin kwamin. “Yi haƙuri to ba'a magana a bayi zai daina”.
“Mamy bazai daina ba ƙarawa yakeyi”.
Dauriya kawai Daneen Ammarah keyi, amma ji take kamar tai kuka. Ta fahimci dole Iffah taji ciwo ne, ciwo kuma bawai ƙarami ba. Ita kam takan rasa miyasa maza basu da tausayine sam. A shekarun Iffah bai kamata namiji yay mata irin wannan zuwan na lokaci guda ba. Duk da tasan su waye mazan ahalin nan nasu akan mace, balle kuma shi da ya kasance tsahon shekaru ma babu macen, ko da ya samesu kuma ita dai Iffah'r ce ta farko dama take hasashen ya kusanta kenan ko yaya. Tunda kaf yaran randa aka kawosu garesa washe gari ake zuwa a ɗauki gawarsu sun rasa ransu. Ɗaga Iffah tai da ga ruwan, ta ɗaure fuska sosai babu alamar wasa tattare da ita, “Ki tsaya a duba ko kinji ciwo ne a wajen, dan wannan zafin da kike ta ambata dole zai kasance akwai damuwa Ibnati. Idan kuma aka bar mace da irin matsalar nan yana lalatata koma ya taɓa mata brain. Ko kina so ki samu matsala a brain ɗin ki?”.
Da sauri Iffah ta jinjina mata kai alamar a'a tana hawaye. Daneen Ammarah ta haɗiye murmushin da ke taso mata dan ta mata hakane dan ta tsoratar da ita dama kawai. Ai ko sai gashi ta yarda ta duba cikin sauƙi amma fa ta ɓoye fuska cikin tafukan hanunnta, wani irin matsanancin kunyar Mamyn na ratsa ɓargo da jinin jikinta. Amma sai take jin inba itan ba bazata taɓa iya nunama wani ba sai ko Ummu ko su Arfa da suna raye.
Rasama abin cewa Daneen Ammarah tayi, sai kawai ta miƙe jiki a saɓule cike da tausayin Iffah. Tabbas dolene ta dinga kuka, a hakan ma sai taga dauriyarta, dan in har watace tofa sai duk masarautar nan sun fahimci halin da ake ciki. Fitowa tai ta samu Malikat Haseenat da ke zaman jiran fitowarsu. “Mammah akwai matsala fa gaskiya, dole a nema likita dan yarinyar nan taji ciwo bana wasa ba”.
Idanu Malikat Haseenat ta ɗan lumshe tare da buɗewa a lokaci guda. Dama ita ta fahimci hakan ai tun sanda tasa Iffah zama, ta kuma yi hakanne dama danta fahimta. Amma saboda ta sake tabbatarwar tasa Daneen Ammarah ɗin sake taimaka mata, turarrukan data bada a saka mata in har Iffahn taji ciwo mai yawa to bazata iya zama ba daman. “Ammarah wannan sirrine mai girma na shugaban daular ruman. Bazai yiwu ya fita ba kema kin san bama zai yarda ba. Dole ke zaki bata kulawar da ta dace”.
“Hakane Mammah, amma ni na ɗauka shekaru rabona da yin wani abu a matsayin likita. Kar'a samu kuskure”.
“Baza'a samu ba insha ALLAHU Ammarah. Na sanki akan komai shiyyasa nake alfahari da ke”.
Da ƙyar Daneen Ammarah ta iya haɗiye kukan da ke taso mata. Dan in har aka tuna mata ita ɗin ƙwararriyar likitace a baya yakan sosa mata wani ɓangare na rayuwarta data shuɗe da bata son tinawa. Dan tamkar fami akan gyanbon da tasan har gaban abada bazai taɓa ya warke ba a zuciyarta ne. Muryarta na ɗan rawa ta ce, “Zanje clinic na samo kayan aiki”. Da ga haka ta fice. Da kallo Malikat Haseenat ta bita zuciyarta itama na raunana. Tana son Ammarah, matuƙar so da duk a cikin ƴaƴanta sai dai a biyo bayanta. Sai dai tana dannewa da nuna iya tausayinta kawai gudun karta raba kan zuri'arta da kanta....
★....
Tsaf Daneen Ammarah taima Iffah da ke kuka na fitar hankali ɗinkin, wai dan ma ta mata allurar kashe raɗaɗi fa kafin ma ta taɓata. Ana kammalawa ta dinga rawar sanyi na zazzaɓi kanta kam ai kamar zai fashe da ciwo. Malikat Haseenat ta tafi domin basu waje, sai dai ta aiko da lafiyayyen farfesu na musamman da wani irin kunun madara mai zafi shima na musamman. Sai tarin wasu sirrika da Iffah zata dinga amfani da su yayin sit bath da zai taimaka mata warkewa da wuri da kuma wanda zata sha dan tasan in dai wannan yaƙinne kam Iffah yanzu ta farashi. Dan in ma fitinar ce shi kam kamar yacema kowa bai iyaba a ahalin nasa. Gashi yana ɗage-ɗagen waɗan nan shegunan ƙarafunan abu goma da goma.
Daneen Ammarah sai da ta tabbatar ta gyara toilet ɗin ɗakin tsaf duk da bawani datti tunda ba'a nan suka kwana ba. Bata canja mata rigar Tajwar Eshaan ɗin da har yau take jikinta ba duk da ta mata girma da tsaho, dan ko'a wajen gashin dama sakata tai ta nannaɗe kawai. Zaunar da ita tai kan filos masu taushi amma ta kasa zama da ƙyau sai da ta karkace. Bata hanata ba ta zuba mata madarar da ke ta turiri tare da farfesun naman tsuntsayen da ke ta tashin kamshi.
“Mamy na ƙoshi bakina ɗaci barci zanyi”.
“A'a Ibnati daure kinji, idan kika sha madaran nan kikaci wannan naman sai na ƙarasa miki ɗayan alluran ki kwanta barci har sai sanda kukaso tashi kinji. Bakiji jikinki yayi zafi ba sosai. Haba ɗiyar albarka haihuwar alkairi”.
Da wannan lallaɓawar Iffah ta fara shan madarar a hankali, Daneen Ammarah na bata farfesun da kanta cike da kulawa. A haka Tajwar Eshaan ya shigo ɗakin da sallama ya samesu. A cikin kwalliya ya ke tsaf ta alfarma ga uban ƙamshinsa da ya cika ko'ina na ɗakin, a taƙaice dai a Shahan-shan ɗin sa yake. Cikin dakewar nan tasa mai ɓoye duk wani sirrin zuciyarsa da ainahinsa yake. Idanunsa sakaye da eyeglasses. Ya wani ƙara ƙyau da cikar kamala ga wani kwarjini mai ƙara yalwata haibarsa ga mai kallo. Daka gansa kasan shi ɗinne dai ɗaya tilo Shahan-shan ɗin ƙasar ruman mai rumawa da ƙasar ruman. Sai wani shining yake da ke tabbatar da yau ɗin ranarsa ce ta musamman mai ɗunbin daraja da tarihin da bazai taɓa goguwa a garesa ba.
Tun a kallo ɗaya da Iffah tai masa lokacin da yake sallamar shigowa ƙasa-ƙasa bata sake gigin hakan ba. Daneen Ammarah ma dai da ga kallo ɗaya bata sake wani ba, dan gaba ɗaya kwarjininsa ya cika ɗakin, ga wani kunyarsa da ke ɗawainiya da ita kamar itace ta aikata tsiyar ba shi ba. Koda yake shima ɗin dai ji yake Mamyn nasa a yau ta musamman ce a garesa, dan kasancewar ta a sashen nema ya sashi jin gara ya fita zuwa fada, sai kuma ga kira ya samu da ga Malikat Haseenat bayan fitowarsa Gym an wayi gari Ammien sa babu lafiya, yana shirin fitowar nan ma Jasrah tai kiran shi itama tana kuka dan tun ɗazun take kiransa ba'a ɗaga ba.
Cike da dakewa ya sake gaida Daneen Ammarah idanunsa kan Iffah da ke kai kofin madara bakinta tana sha kaɗan-kaɗan. Miƙewa Daneen Ammarah tai cikin hikima ta ce ta cigaba da shan madarar da nama bara ta amso saƙon sauran magungunan ta data bada a siyo....
Shiru ɗakin ya ɗauka sai sassanyan ƙamshin da ya gaurayesa ke tashi. Taƙi yarda ta kallesa koda da kuskure duk da yanda take jin ɗakin yay mata tsukuku saboda kasancewar sa. Idanu ya ɗan lumshe da sake buɗewa a kanta sannan ya ɗan taka gaban gadon gab, zaune ya kai inda Daneen Ammarah ta tashi a gefen gadon kusa da ita sosai. Sai kuma ya kai hannu ya zare eyeglasses ɗin da ya sakaya launin idanunsa.
“Good morning Mrs Eshaan Qutb”.
Ya faɗa da wata irin shaƙaƙƙiyar murya mai sanyi matuƙa yana kai yatsunsa biyu kan haɓarta ya ɗago fuskarta da ƙyau. Har tsakkiyar kai muryar da yay amfani da itan ta ratsa Iffah, ga wata matsananciyar kunya da shakkarsa da ke ratsata. Idanun ta da hawaye ke cikosu ta lumshe da sauri.
“Please open your eyes my life”. Ya faɗa fuskarsa gab-gab da ita batare data san lokacin da ya matsota haka ba.........✍️
*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*
*DAUDAR GORA Billyn abdul*
*KI KULANI hafsat xoxo*
*A RUBUCE TAKE Huguma*
*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*
*IDON NERA Mamuh ghee*
_LITTAFI DAYA: 400_
_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_
_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_
_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_
_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_
_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_
_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_
_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_
ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN
MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171
SAI A TURA SHAIDAR BIYAN
09033181070
IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA
09166221261
*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*
+227 96 09 67 63
Books biyar 1250CFA
Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA
KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI.
MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)
𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (47)
........Hawayen da take riƙewa ne suka ziraro, ta girgiza masa kai alamar bazata iya ba. Komai bai sake cewa ba, sai riƙo hanunta mai riƙe da kofin madarar yay cikin nasa tare da kofin, bakinsa ya kai ya sha madarar. Ta masa matuƙar daɗi fiye da duk madarar da yake sha. Still dai hanunsa nakan nata da kofin ya sake kaiwa ya sha. Sai da ya sha kusan sau biyar sannan ya kai bakinta itama.
“Hhah”.
Ya faɗa a narke yana wani irin busa mata iskar bakinsa kan idanunta da suke mar-mar, gaba ɗaya neman daburcewa take.
“Kina so na buɗe da kaina?”.
Da sauri ta girgiza kai da buɗe bakin kaɗan ya ɗaura mata kofin. Kaɗan tasha ta janye, sake ɗaura mata yay. Babu yanda ta iya dole ta cigaba da sha. Bai barta ba har sai da ta shanye duka sannan ya ajiye kofin. Naman ya ɗauka shima ya shiga bata yana ci har suka cinye tare da shanye romon ma duka a tare.
“Sai mi kuma?”.
Ya faɗa yana riƙo hanunta a nashi. Fuska a shagwaɓe ta ce, “Barci”. Murmushi yayi tausayinta da ƙaunarta na sake mamaye shi, sannu-sannu ya kai hanunta kan lips ɗinsa, babu zato taji saukar kiss a tsakkiyar tafin hannun. Idanunta ta rumtse da ƙarfi tana matse jikinta dan har cikin ɓargo sumbar ta shigeta. A tare suka sauke ajiyar zuciya, tai ƙoƙarin zamewa zata kwanta ya riƙota jikinsa. Tsam-tsam ya rungumeta yana shinshinar wuyanta da busa mata numfashinsa da ke saka tsigar jikinta yamutsawa.
Luf tayi tana mai shaƙar daddaɗan kamshin turarensa mai saka zuciyar mai shaƙa nutsuwa, yanda yake hura mata iska a cikin kunne da murza yatsun hannunta dake cikin nashi tuni barcin da keta rinjayar idanunta ya fara tasiri kanta. Jin jikinta ya saki gaba ɗaya ya sashi ɗan sakin murmushin ta sake gyarata ta kwanta da ƙyau, cikin abinda bai wuce mintuna biyu ba numfashinta ya fara sauka a hankali alamar barcinta yay nisa. Numfashi ya ɗan furzar da gyara filos ɗin gadon ya kwantar da ita. Lumsassun idanunsa ya zuba mata batare da ya ɗago da ga ranƙwafawar da yay a kanta ba. Wasu kalamanta ne na jiya suka shiga dawo masa a rai, wani lallausan murmushi ne ya suɓuce masa ba shiri, ƙoƙarin haɗiye kayansa yay da sake matsawa da ƙyau jikinta ya sumbaci goshinta da hancinta da lips ɗin da sai da ya ɗan juya su a cikin nasa sannan ya saki. Bargo yaja ya lulluɓe ta da ƙyau ya miƙe...
Koda ya fito falon bai saurari abincin breakfast da aka shirya masa ba. Hakama Daneen Ammarah bata falon, sai amintaccensa kawai da ke dakon fitowarsa. Gaisuwar amintaccen hadimin nasa ya ke amsawa yana nufar lift.. yayinda shima yake biye da shi da hanzarinsa.
Fada ya fara nufa cikin takun nan nasa ɗaɗɗaya na izza da ƙasaita. Shigowarsa da aka sanar tun kafin ya iso ya sa duk wanda ke a wajen miƙewa kai a ƙasa har sai da ya kai zaune. Suma duk zaman sukai cike da girmamawa suka shiga miƙa gaisuwa suna satar kallonsa dan yay musu wani fayau da sake cikar kamala kamar wanda akaima wankan inji. Saɓanin ko yaushe kuma yau fuskar da ɗan sassauci duk da bawai dariya yake ba ko murmushi. Tana nan dai kadaran kadahan bata tsuke sosai ba bai kuma saketa ba. Kamar ko yaushe amintaccensa ne ya amsa da yawunsa. Da ga haka aka ɗanyi zaman fadanci masu ƙorafe-ƙorafe suka kawo yana saurarensu. Hakama masu shawara akan masarautar ko wani abu da ya faru harma da wajenta. Na masarautar dai duk sun samu rinjaye ne akan abinda ya faru tsakanin Miran Jasim da iyalansa.
Komai baice akai ba, yana dai jinsu da kunne bisa ra'ayinsu har gardama ma ta ɗan nema sarƙewa sai da Sayeed Anwarus-sadat ya tsawatar. Baice komai game da rashin ganin Miran Arshaan ba, shima kuma Miran Jasim ɗin da aka sanar masa ya matsa an sallamesa tun a daren jiya baice komai ba a kai. Zaman gaba ɗaya bai wuce na awa biyu ba lokacin sallar zuhur yayi....
Bayan an idar da salla ya samu rakkiyar manyan masarautar duba mahaifiyarsa. Duk da amota suke duk inda motocin suka gitta hadimai ƙasa kawai suke zubewa kawuna a sunkuye har suka ƙarisa ƙofar sashen. Motar da yake ciki ma har cikin barandar gaban falonta ta tsaya. Amintaccensa da yay saurin fitowa da ga gaban motar ne ya buɗe masa. Shiru babu alamar zai motsa balle ya fito har sai da minti ɗaya da sakkani ya shuɗe. A hankali ya ziro ƙafarsa dake cikin takalman masu tsananin ƙyau da ɗaukar idon mai kallo farare tas heif cover, sai da ya sake jan wasu sakkanin kafin ya zuro ɗayar, nan ma ya sake jinkirtawa sannan ya fito gaba ɗayansa. Tuni mayataccen ƙamshinsa ya mamaye sashen tunkan ma ya shiga. Hadimai kam rige-rigen shigewa suke dan mai RUMAN ne fa da kansa ba aike ba. A waje kam jami'an tsaro sun zagaye sashen tamkar ba'a cikin gida ba. Ameera Danish-Ara da ke zaune a falon tare da Ameera Haifah da wasu a cikin matan masarautar masu faɗa aji da suka shigo duba Malikat Bushirat ɗin tuni sun miƙe kawunansu a ƙasa. Takun sawayensa kam tuni ya saka kowa nutsuwa kowa na satar kallon hanyar da zai shigo da kallo. Yayinda ƙafarsa ke taka cikin falon babu wanda bai ja numfashi ba, dan a wajen ado kam kowa shaidane Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdul-majeed ɗawusu ne. Ƙamshi kam ba'a magana idan yana waje kowane turare disashewa yake duk ƙarfinsa. Ko sau ɗaya bai kalli kowa ba, takunsa yake a nutse cikin izza da ƙasaita da ka gansa kaga gwarzon gwaraza mai gwara kawunan gwarzo mai son nuna gwarzantaka. Gaisuwar da suke ta faman masa Sayeed Fayzul-haq ne dake take masa baya kawai ke amsawa. Dan sauran jama'ar da ke a tare da shi duk a farkon shigowa falon suka ja birki.
Sayeed ɗin ma a ƙofar ɗaki ya dakata bayan ya buɗe masa ƙofar ɗakin da akai musu iso Malikat Bushirat na ciki. Isar ƙamshinsa ciki kafin shi ya saka Jasrah da ke kusa da ita tana bata shayi miƙewa da sauri. Malikat Bushirat kam idanunta dake matuƙar jazur ta zubawa ƙofar zuciyarta na wani irin bugawa da sauri-sauri. Tunda ya shigo shima kaifafan idanunsa dake sakeye cikin gilashi na kanta. Nata dake cikowa da hawaye ta rintse da sauri tana kauda kanta, wani irin zafi takeji, zafi mai amsa suna zafi na gaske a ƙirjinta har tana jin turirinsa a maƙoshi. A maimakon zama a kujerar da Jasrah ta gyara masa bakin gadon ya kai zaune. Hannun Ammien tasa ya kamo a hankali cikin nasa ya sumbata. Maimakon murmushi da take sakar masa a da idan yay mata hakan yanzu hawaye ne masu zafin gaske da ta kasa riƙewa suka ziraro da gudun tsiya kan ƙyaƙyƙyawar fuskarta da duk ta dame kamar ba Malikat Bushirat ɗin nan ba ƴar gaye, hamshaƙiya ƴar ƙwalisa. Idanunsa ya rumtse a hankali hawayen na ratsa har tsakkiyar zuciyarsa. Ya jima a haka kafin ya buɗesu ya sauke a kanta. Handkherciff ɗin jikinsa ya zaro ya miƙa mata, tare da motsa lips ɗinsa a hankali ya furta, *“لاَ بَأْسَ طَهُورٌ إِنْ شَاءَ اللهُ .*
_La ba'asa tahoorun in sha'al-lah._
(Ba komai, tsarkaka ce in ALLAH ya yarda).
أَسْأَلُ اللهَ الْعَظِيمُ، رَبَّ الْعَرْشِ الْعَظِيمِ أَنْ يَشْفِيكَ *.(سبع مرات)*
_Asalul-lahal-'azeem rabbal-'arshil-'azeem an yashfeek._
(Ina rokon ALLAH mai girma, UBANGIJIN Al'arshi mai girma, ya warkar da kai)”.
_(MANZON ALLAH, tsira da aminci su